YAU BARKAN MU DA GIDA FATAN ALHERI GAREKU A KULLUN, , ,


Haka abubuwa a kwana nan biyun suka taru sukai muna yawa ga abin daure kai mutum na gani a filin Allah don abinda zai baka mamaki bini bini mami zata kirani wai tana ban labari yadda abin yake faruwa a can kaduna.
Yanzu ma din hakane ina zaune misalin sha biyun rana wani kiranta ya shigo min sai naji gabana ya kara faduwa don nasan wani maganan daya dangaci wancan din na uwar Rufaida da ake fama a yanzu.
Ina dauka da sallama tana fadin wai zainab kin san matan nan har akanki wai taje gidan boka ai muna asiri in tsane ki da duk wanda ke tare dani.
Sai yau dai da mukaje gidan tana ganina ta shiga tono tonon asiri tana hintar kanta tana fadin kinfi karfina iyami kin fi karfina .
Sai abin ma yaso ban dariya amma na daure a fili ina fadin wa,iyazu billahi mami me wanan matar take nufine dake ?
Mami naga dai duk yadda akeyi kin masu a rayuwa ga yarta kuma a hannun ki kina rikewa tsakanina da Allah.
Mami din tace to ai zainab baki sani ba wai ashe ko zaman Rufaida din wurina wai ashe da dalili sun shirya hakane don ita Rufaida din ta auri daya daga cikin diyan dakina.
Wai ashe kuma jafar dinki take so shine suke faman neman asiri da zasu samu kan jafar dani da kuma karya wanan asirin da yanzu ya kare take wanan fallasan haka.
Na nisa tare da fadin O ikon Allah ita kuma kalan nata rayuwan ke nan mami, ba zata iya dogara ga Allah yayi mata mafita ba na rayuwa sai ta danganta rayuwan ta da gidan boka da malamai ?
Su saba ne da hakan tun farko ni kingani na ban taba yarda da irin wanan halin bin malamai da bokaye ba a rayuwana.
Komai yazo nakan saka hannu bibiyu in rungume shi in fadawa Allah damuwa akan lamari injira sauki daga gare shi.
Allah yasa mufi karfin zuciyan mu na fada tace to amin kedai zainab aisu masu wanan irin halin zakiga kullun a cikin talauci suke.
Saboda hassada da bakin ciki suka sakawa zuciyan su da haka mukai sallama da ita wanda nasa ko zuwa dare zata kara kirana a kan zancen.
Ina kashe wayan nake fadin a fili Allah mai iko yau nice da mami haka muke hiran arziki a tsakanin mu.
Dama hakkurine da wuya duk abinda kaji ana fadin kayi hakkuri a kansa har ka iyayidin insha Allahu hakkurin ka baya zama banza.
Yau da banbi maganan magabata na da shawaran manyan dake tare dani da ban kaiga cin ma hakan ba a rayuwana.
Shine ya shigo dakin yayi tsaye tare da tsura min ido kafin yace dawa kikw magana hakane tun dazun nake jin ki.
Dan dago kai nayi tare da saurin mayar da kaina kasa don yanzu tun faruwan wanan abin a tsakanin mu bana iya hada ido dashi sosai a yanzu din.
Mami ce ta kirani take ban labarin mamab su Rufaida na bashi amsa kai tsaye kafin inji yace kai mami tasaka zancen matan a ranta sosai.
Ni na riga na barta ga Allah ga duk abinda tayi min nasan dai ban taba cuta mata ba a rayuwa tunda nake ta iya min wanan mugun sihirin haka.
Ni yaushe ne matar nan zata bar gidan nan wai ya tambaya na gane fadila yake nufi don haka nace dashi ina ga rokon ta danayine yasa ta janye tafiyan har lokacin tafiyan mu.
Kina ganin hakan bata sabawa dokan aikin su ba ya tambayeni yana kallona nace bana jin hakan don da zai saba din ba zata yarda ta tsaya ba ai.
Kafada ya daga tare da fadin ok a fili idan dai ta tashi ga wanan ki bata ya miko min key da envelope sabo na karba tare da masa godiya kamar nice akaba kyautan .
Ko ban san komai ba nasan wanan makulin motane ya bata ya juya yana fadin ida ta tashi sai ta tambayi Hadi driver zai nuna mata motar ta dauka.
Na kara mashi godiya ya fita daga dakin sai abin ya ban mamaki kwarai da gaske don ban taba tsamanin zaiwa fadila irin wanan kyautan ba haka.
Dakin ta na nufa kai tsaye bata cikin dakin yasa na fito na shiga surun sadiya a can na samesu zaune suna kallo nace ashe kina nan yanzun daga wurin ki nake tafe ai baki dakin.
Tace ina nan tare da mutumiyar muna kallo sakon ta dake hannu na na mika mata ta kalla a cikin maki kafin ta karba daga hannuna.
Yayan mu yace a baki idan zaki tafi naga ya dace in baki tun yanzu don ki sani ta bude baki cikin mamaki sai kuma tace wanan duk nawa ni kadai a take yanayin ta ya sauya.
Sauka tayi daga saman gadon sai kawai naga ta zube a kasa tana godiya kai haba anty bani ya kamata kiwa hakan ba ai na fada ina zama.
A sanadiyan ki ai na samu duk wanan alherin da ace banyi zaman lafiya da kuma tsakani da Allah daku ba duk wanan alherin ba zan sameshi ba ai.
Sadiyace ta katsemu da fadin yaushe zamu tafi gurin su inna anty ta jefo min tambayan nace ina gadai a cikin satin nan ne don baiyi magana akan tafiyan ba har yanzu.
Ke nan zakuyi tafiyane kuma nace eh zamu mayar da hjy daga nan mu wuce gida muyi masu sallama.
Lalai hakan na da kyau ku koma kafin ku bar kasan nan zaifi amma kuma kune zaku mayar da ita gida ke nan na dauka mamice zata kaita gida ?
Mami yanzu haka tana kaduna a can zamu samesu don gaba dayan su suna can kadunan kwana biyu ke nan da tafiyan su.
Naji hjy na fada jiya a waya wai mami tayi hakkuri ta bar zancen ga Allah sadiya ta fada ba zata iya kyale zancen ba don ko waye dole hankakin shi ya tashi .
Amma tunda Allah ya mata fada a yanzun gaskiyane ta barta da Allah zaifi laifi akai mata ke nan ko fadila ta fada ?
Eh to laifin ne nan dai na dan fada masu komai sama sama tayi saurin fadin ummhum nasan da hakan wallahi don inda ta taba zuwa a kanki wani lokaci an fada min hakan .
Sai dai abinda bai shafeka ba tunda bashi ya kaini ba a lokacin yasa ban dauki zancen da karfi ba mun dan dade muna hira kafin mu watse a dakin.
Duk kwana kin nan yaya bai kara cewa zai nemini ba nima kuma naji dadin hakan da darene mun kwanta yake fadin ya gama shirin tafiyan hjy mu shirya gobe da yamma zamu kaduna daga nan muje anchau muyi sallama dasu.
Allah ya kai mu na fada ina gyara kwanciya naji saukan hannun shi yana fadin ban son zuwa kaduna a yanzu don gaba daya garin ya fice min rai.
Dan juyowa nayi ina fadin laifin mutum daya zai shafi sauran yan garin itama din da tayi ai Allah ya fitar ma da hakkinku tun a nan duniya ta fara ganin mugun halin ta.
Kome mutun zai aikata idan ba alheri bane a rayuwan shi banzane don komai dadewa sai ya tambayi mutum ?
Abinda nake tunane ke nan a yanzu na rasa me nayiwa wanan matar har bata sona haka ?
Bakai tawa ba da farko ta dauka ta cuci mami ne don da ita take hamaiya bada kai ba.
Ajiyan zuciya ya sauke tare da dora hannun shi saman jikina naji gaba na ya fadi lokaci guda duk da tsorin shi da nake yanzu har ya san da hakan.
Shine dalilin da ya dan sarara min ya kyale ni a yanzu din amma ni kuma sai nake ganin ai rashin sabawa da zama da mace da bai iya bane yasa bai wani damu da kulani din ba.
Ko wanan ranan gaskiya nasha bakar wahala gun yaya don bai tausaya min ba haka ya koma kamar wani zaucace a gareni.
Washe gari mun isa kaduna bayan sallah magariba gidan na mami shiru da a yanzu duk sai na ganshi wani iri can kamar bashi ba.
Kodan yanzu idona ya bude da ganin ginan zamanine oho abinci mukaci kawai yace wai mu fito mu tafi .
Nayi mamakin jin ba a gidan zamu kwana ba ashe abinda ban sani ba shine yana da wani irin keraren gida cikin kaduna ashe haka ma ya mamud shima a yanzu ya bar gidan mami din.
Gidane na gani na fada na shiga tsara nayi mamakin hakan sosai danaga gidan lafiya lau komai ba laifi gida ya hadu.
Nan ma dai din bai kyakeni ba don mun zuba soyayya a wanan gidan sai dai kawai a kawo muna abinci daga restaurant muci safe da yamma .
Ko gidan mami bamu lekawa sai dai su ya jamal dake dan leko mu a ranan mu na ukku a gidan ne da dare muna falo bayan mun gama cin abinci wayan shi yai ringing ya dauka.
Naji yana fadin ina gida mana lafiya jin hakan yasa na dan dago ina kallon shi daga inda nake kwance na dan kishin gida saman jikin shi.
Banji me akace ba yace ku shigo mana ina kokatin jaye jikina a nasa don jin abinda ya fada din amma kuma sai naji ya rikeni ya hana in tashi din .
Ga mamakina Aisha ce suka shigo tare da wani saurayi da ganin shi irin samarin nan ne yan karya diyan masu kudin garin.
Mun gaisa dasu idon saurayin yana kaina hakan yasa ya jafar din kara daure fuskan shi sosai yake fadin umm, humm .
Kince kina son ganina ne akwai magana fadi abinda zaki fadi ina sauraren ki sai ta dago ido ta kalleni kafin tace dama magana nazo muyi yaya a kan magana na da Hashim gashi nazo maka dashi ku gaisa.
Yace waye shi tace kai tsaye shine wanda nake so kuma mami bata yarda ba har yanzu ya kalli yarin yace mami din ta fada maki haka da bakin ta sai tayi shiru.
Nan ya fara yiwa guy din tambayoyi yana bashi amsa kafin yace da ita alright zanga mami din muyi magana da ita kafin in tafi.
Daga haka ya fita batun su ni kan ba wani maganan kirki ne a tsakanin mu ba tunda na fahinci wani irin daukan kai da take min tun dawowan mu din kasan na kama kaina ga al,amarin ta ga baki daya.
Sallama sukai mai suka tafi ya tashi ya rufe gidan ya dawo ya zauna yana fadin ban san meke damun yarinyar nan ba zata kwaso min wanan ta kawo mi shi har gida.
Haba dai gidan dan uwanta tazo fa ba wani wuri ba kuma da gani tana son yaro nan sosai yasa tazo wurin ka ka taimaka masu .
In ba haka ba ai ya mamud ma yana garin da gurinshi zasu tafi ba wuri ka ba amma kuma ta zabi nan din tazo.
Wayan shi ce ke ringing ya dauka saurare ya tsaya yi har na wani lokaci kafin naji yace yanzun nan suka fita nan ita dashi.
No ban samu mata fada ba don tana tare da yaro a lokacin ni dai mikewa nayi ya bini da kallo don ranan sadiya tabi ya jalal da yazo zuwa gidan mami wurin hjy saboda idan muna daki da yaya ita kadai ke zama ba abokan hira.
Ya gama wayan ya shigo daki ya samu na shiga wanka koda na fito yana tsaye a wurin window kamar mai tunane.
Zama nayi bakin mirrow ina shafa mai yazo ya tsaya a bayana yana fadin ana magana kan Aisha kin bata rai.
Ba tare dana juyo ba muna facing din juna a cikin mirrow din nace dashi shi sha,anin aure ne yaya ba ai masa haka tunda shi take so har ta kawo shi gareku ai idan ba laifin sai ku bari tayi abinta.
Wa zai bari ta auri wana guy din kece yarinya da baki san komai ba wanan da ganin shi tashin waje ne bai koyo komai ba a can sai iskanci .
Wani kallo nayi mai da sauri don jin abinda ya fada din yace yes nasan abinda zakice ai ko nayi nawa a lokacin ina kokarin danne hakan a kasata ai.
Amma baka zaton auren shi din a dalilin ta zai iya gyaruwa ya bar wanan a kidar ya dawo dai dai ba dai wanan din ba na fada maki ke yarinyce ya wuce ya shige ban daki ya barni zaune ina tunane.
Ban san yadda sukayi da mahaifiyar su ba ni dai ranan sai ga Aisha din da gani tasha kuka tun a gida don idonta da yayi ja ga duk wanda ya ganta.
Sun dade da dan uwan nata a dakin shi suna magana don ta shigo ni fita nayi muna waya da Nafisa da tace zasu shigo dasu umma.
Ta fito ko sallama ban samu ba ta fita tana sharan hawaye su umma suka zo gidan sai hankalina ya dauku garesu na manta da zancen nasu.
Ranan a gidan su umma suka wuni tare dani da zasu tafine yayi masu alheri mukai sallama suka tafi.
Mun je gida mun samu Asabe na cikin wani hali na rashin lafiya kai tsaye yace a kawota asibiti kaduna wanan kuma ya kara dauke hankalin mu sai dai Asabe din duk da gatan data samu lokaci yayi ba magani a wanan jinyar ta rasu tana saka muna albarka ni dashi har innan mu.
Mun kuma koma can gida muka kwana daya na dawo kaduna daga nan muka dawo Abuja .
Sai muka fara shirin tafiya sai kuma ga zazzabi har saida na kwanta asibiti don jirgitan danayi ga zazzabin.
Hankalin jafar din ya tashi sosai da ciwon nawa sai da mami take ce masa kowa fa haka yakeyi idan an samu juna biyu duk da hakan bai gane me mami din take nufi ba.
A karshe dai tana murmushi take fadin nifa naga kamar matar ka na da cikine amma a bari saka makon ya fito a gani.
Ciki mami ciki ke ga zainab din sai kuma ya shafo kanshi zuwa fuska yana dan murmushi ya rungumi mami din lokaci guda.
Itama mami din dadi taji a lokacin tana dan bubuga bayan shi tare da fadin Alhamdullahi jafar tunda baka halaka ba ga baki daya gashi yanzu har zaka iya haihuwa ashe.
Koda na falka suna zaune su uku sun tasani gaba suna kallona dan binsu da kallo nayi na dan lokaci kafin in dan motsa baki ina gaidasun
Suka amsa tare da yi min ya jikin nace da sauki ina yun kurin tashi don aman daya tayar dani daga barci a lokacin.
Shine yake tambayan ina zan tafi da yaga ina sauka daga gadon da sauri na kaaa magana sai dana ns bude baki wani amai yazo min da sauri na nufi wirin da nake zaton ban dakine a wurin daga gefen dakin.
Tin ina amai a duke har na koma yi tsugunne haka yssa shi shiga bayin yana min sannu na fito a galabaice bayan na kurkure bakina da ruwan daya ban.
Wasa wasa wanan ciwon saida yasa muka kara kwanaki a kasan don jikina yaki dadi sam ga mutane sai faman zolayata sukeyi da sunan mai ciki da har lokacin ban yarda da hakan bani.
A haka muka tatara muka koma Chaina sai dai saboda yanayin jikin nawa yasa yace in nemo wace zamu zauna ko a gidane mu tafi tare.
Akwai wata babban yar malam dake gida auren ta ya kare kuma bata taba haihuwa ba gorin kishiya ya fitar da ita gidan miji tana gida zaune da itace zamuyi tafiyan don kanwa take ga innan mu ke nan don haka muke kiranta da mama Ladi.
Duk da mami bata so hakan ba a cikin ranta ba wai bata son zuwa da ita din bane don tana bangarena a,a.
Saidai a ganin ta matar ba zata iya bani kulawan da ya dace ta bani ba don tana yar kauye har ta kula mata da abinda ke cikin cikina a yanzu.
Ba wata dole din da ita muka tafi hakana don na nuna ita nake son muje don yadda nayi zama da mahaifiyar mama ladi din maizube.
Ban samu wani wahala ba ga tafiyan don mun isa lafiya sai dai barcin da nayi tayi bayan saukan mu din.
Zaman mu da mama ladi ba wani matsala a cikin shi don ina jin dadin zama da ita sosai kuma ina bata
Showing 384001 words to 387000 words out of 390011 words