adadin da akace ayi amfani dashi ke nan na fada ba tare dana dago kaina ba.
Hjy fa ta fito yau kuwa ya sake jefo min tambaya nace yau banji motsin ta a falo ba ta fito ba tukun na dai je mun gaisa da ita dazun tana lafiya.
Yunkurawa yayi yana fadin muje dakin don da ita zamu tafi gidan mami din an jima ya fada yana tashi zaune kafin ya mike nabishi da kallo.
Kada kiji wani abu zata kai masu ziyarane ita ba abinda zai kaimu zai kaita ba ya fada yana tsaye.
Ban bishi dakin hjy dakina na wuce ina tunane kafin na kira layin inna na labarta mata abinda ke faru sama sama.
Sai ji hankalin ta ya tashi lokacin kuma nayi dana sanin sanar da inna din duk da ban fito fili na fada mata ga dalili ba amma sai ta rude .
Har na dan fara zargin iyayyena a raina ina fadi cikin zuciyana wai ko sun damu da damuwana kuwa ?
Sai nake ganin kamar dan abin duniyan da ya jafar ke basu akai akai yasa basu ganin laifin shi a kan komai .
Saida abinda ban sani a lokacin shine komai munin aure ga diya babu uwa ko uban da zasu so auren yarsu ya kare sai in hakan mukaddari a wurin Allah dama akai rabuwa a cikin auren .
Sai dai kuruciya ya hana in gane hakan a lokacin nake ganin laifin iyayyena kan son na zauna gidan jafar don abin duniya da ya rufe masu ido a lokacin.
Kafin sha biyu har na shirya shi kawai nake jiran fitowan shi don bani da kwanciyan hankali a lokacin son har na fara yanke hukuncin abinda zanyi idan na bar gidan nasa don kada rayuwana dana iyayyena ya wahala gaba.
Sai gashi ya shigo dakin nawa a cikin shirin shi yasa wasu shadda masu ruwan sky clour dinkin su ya tsaya masa iya gwiwan shi hannun rigan karami shima iya gwiwan hannu ya tsaya mashi sai kamshi ture ke tashi a jikin ranan har yar hula baka mai kyau ya saka a kanshi sai hakan ya kara fito mashi da kyawon shi fili duk da ya rame a lokacin.
A falo muka samu hjy zaune tana jiran mu yake fadin lalai hjy kina jin fita yau din nan har kin rigamu fitowa ke nan suka dan taba wasan jika da kaka kafin mu fita daga gidan.
A gida nabar sadiya don tace bazata gidan mami ba ita dataji can zamu tafi duk da fadila nasan tasan komai dake faruwa a gidan sabanin sauran yan aikin da basu san abinda ke faruwa ba sai aikin gaban su da sukeyi.
Amma ita kan nasan ta san komai dake faruwa a lokacin nuna kawai take bata sani ba nima kuma ban mata wanan maganan ba sam.
Ko lokacin da muka fito zamu fita din dagani akwai magana a bakin ta saida babu idon yin maganan ne a gareni balle ta tambayi abinda take son ji din.
Mota daya mukai amfani dashi zuwa gidan mami din shine gaba zaune da driver muna baya nida hjy.
Dan tafiya muka shigo unguwar su mami din ban dago kaina ba daga yadda nake zaune a bayan mota nayi tagumi sai faman sake saken da nakeyi a cikin raina .
Tsayawan motan yasa na dago kai ina kallon get din gidan da maigadi ya bude a lokacin a raina nace kila zuwan karshe kenan da zanyiwa gidan nan a hankali na mayar da idona na rufe har muka karasa shiga cikin gidan.
Muryan jalal yasani bude ido don jin yana fadin a, a bros kune tafe ashe gara da ban fita ashe tun dazun ya fada yana karasowa bakin motan.
Ganin hjy yasa ya koma kanta yana janta da ba,a har dai muka shiga cikin gidan yana wani ja mata hannu suna tafiya a hankali ina bayan su nima tare da yaya dake waya daga gefena.
Gaba dayan su kowa na falon zaune kasancewa ranan ba aiki duk suna gida ga baki dayan su har mami tana falon tare dasu.
Sallaman suka amsa na jalal amma sai idon su ya dawo a kaina sun kasa boye kyashin su a zukatan su a kaina.
Gaida hjy sukeyi da yayan su sai Na,imace take ce min zainab sannu da zuwa na danyi murmushi ina amsa mata a cikin dan fara, a har take fadin ga wuri kizo ki zauna tana kokarin tashi ta ban wuri.
Da sauri nace a,a anty ki barshi in zauna a nan na nuna kasa yace No cikin dakewa ya kalli Rufaida yace ke bata wuri ta zauna.
Saida tayi wani iri kafin ta mike a cikin fushi zata bar falon mami tace keko tsiyana dake ke nan wallahi saurin fushi Rufaida.
Tace to mami sai kuma tayi shiru ta kasa karasawa don wani irin kallo daya watsa mata yasa tayi shiru.
Dole ta dawo ta zauna a gefen mami din tana wani irin shagwaba mami tace kedai zuciyar nan naki zata wahal dake wallahi .
Ni kan zaune nakai a bina duk ina kule dasu irun yadda kowan su ke satan kallona tundaga kafa zuwa samana.
Na fara gaida mami bayan na zauna ta dan juyo da dan fushin fadan da takewa Rufaida ta amsa min tare da fadin ya gidan ya dawainiya da hjy.
Nayi dan murmushi na gyara zama bayan haka ba wace muka gaisa da ita a cikkn in bayan Na,ima da tun shigowan mu tayi min magana.
Sai suka wayen ce hakan da hira da hjy na nuna ban masan suna hakan ba gareni ina dakalan wayata daya dauke masu kuma hankali ga ganin ta.
Jamal ya shigo shima da alama baisan da zuwan mu ba sai lokacin suka gaisa da dan uwan shi nice na fara gaidashi yake fadin.
Zainab kun sha Nageria fa nasan ba don ciwon yaya ba da yanzun kun koma ai jalal ya karba a bayan shi daga inda yake tsaye.
Me zaisa ta damu ta koma tunda ba karatu takeyi ba yanzu Aisha da tun shigowan mu batayi magana ba ta fada a yanzu.
Ke lokacin da aka dawo kasan nan ai kuka keyi zafi ya isheki zaki koma jalal ya fada budan bakin ta sai cewa tayi aini a lokacin na tashi cikin jin dadi na sai kawai a daukoni a kawoni nan.
Amma kuma a yanzu kinsan zainab ta fiki samun dadin da kike fadin kin samuba can don haka ai ba abin mamaki bane don tace zaman Nigeria ya ishe ta a yanzu.
Wani tabe baki tayi tana kawar da kai gareshi bata ji dadi amsan daya bata ba daga inda mami take zaune tace koma dai meye a yanzu ba zaka taba hada Aisha da zainab ba ko ku ke nan kullun cikin gwatsale yar uwan ku a gaban kowa.
Look ba nazo nan da mata na bane don a riga challangen din ta haka koma meye a yanzu zainab zamana takeyi bana son jin wani zancen bataci a gareta again.
Falon yayi shiru kafin hjy tace dasu banda abinku ai ka zama matar mai hali yafi ace ai yar me halice ke a wanan zamanin.
Kafin wani yayi wani magaba akai sallama aka shigo ya mamud ne a gaba sai wani mutum mai cikar kamala a bayan shi suka shigo.
Nan aka shiga gaidashi sai lokacin na gane shine wanda zai warwale matsalan zaman mu da yaya din da mukazowa jin abinda hukuncin ya tanadar muna yanzu.
An dan taba hira kafin su mazan su fita su barmu a falon kamad kada yaya ya fita duk sai naji na tsawala a lokacin cikin su sai dai da yake hjy na wurin ba halin wani yai min wani maganan banza.
An dan dauki lokaci kafin yaya mamud ya shigo yana fadin zainab dan zo mijin ki na magana dake a waje.
Duk suka bishi da kallo ya fita na dan daga nabi bayan shi nima nasan kallona sukeyi a lokacin ba mamakin hakan a garesu.
A can na tsinkaye su zaune saman fararen kujerun roba su hudu na isa wurin da sallama a bakina suka amsa min.
Kusan a tare suke nuna min wuri in zauna na danja kafa a hankali nakai zaune a takure nake cikin su din kafin naji mutumin ya fara jan dogon addua tare da godiya ga Allah daya hadamu a wanan wurin.
Kafin yace ina gida zaune dazun malam gashi ya nuna ya mamud ya sameni da wani zance wanda ya daure maku kai .
Sai dai Alhamdullahi don addinin islama yazo da wayen kaine ga al,umman Annabi ga baki daya Annabin rahama bai bar duniyan nan ba saida ya warware muna irin matsalolin nan idan zun taso gare mu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI FATAN ANTASHI LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA MARASA LAFIYA ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYAN ALLAH YA KARA MASU LAFIYA AMIN.
YAR UWA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA KADA MU SHIGA HAKKIN JUNAN MU.
Zowan mami da ta biyo bayan mu ta samu muna zazaune malam na bayani hakan baisa malam din yayi shiru ba a lokacin har saida ya tsaya don kan shi.
Malam ya kare bayanin shi a lokacin jikin kowa yayi sanyi a wurin don irin bayanin dayayi a lokacin kan addinin Allah.
Ya dago tare da fadin kada in katse ku da bayani haka zan so wanda suke da alhakin zaman mu wanan wuri suyi min bayanin komai a tsare yadda zan fahinci zancen.
Sai lokacin mami ta samu bakin magana tana fadin akan meye akai wanan zaman ya mamud ne ya bata amsa da fadin kan matsalan matsayin auren su da kika fara magana ranan muke son malam ya warware muna.
Sai ta dan bimu da wani irin lalattacen kallo tana kawar da kanta gefe daya ba tare datayi magana ba a lokacin.
Sai ya mamud yayi sauri fadin dama watau malam kamar yadda na fada ma dan matsalane aka samu tun farkon auren har yakai an kwashi tsawon shekarun nan, ana zaune ba wani abinda ya taba shiga tsakanin su shiyasa muke son a warware muna matsayin wanan auren a yanzu.
Saboda mahaifiyan mu ta fara furta wanan kalamin wai an dade an dauki lokaci a yanzu kan ba sauran aure a tsakanin su.
Da sauri mami ta dan dago kai ta kalli ya mamud din tana fadin au don hakan dana furta kuka kira malam a kanshi to ai gaskiya na fada dan aure ko watani masu tsawo ya diba ba saduwa a tsakani ai akwai bincike a kai.
Malam din cikin murmushi ya karkada kai ba tare dayayi magana ba sai murmushin da yakeyi a lokacin.
Ya jafar yace dakata mamud jin haka kowa yayi shiru a wurin a lokacin ina faman tunanen zancen ya mamud din da yace mami ne tazo da wanan zancen ke nan haka na nufin mami dai har yanzu tana son in bar mata danta kota halin kaka ke nan yasa take wasu tsire tsire zance a yanzu din.
Sai gashi kuma yanzun din ma ta kara maimaita hakan a gaban kowa ba tare da jin komai ba a zuciyan ta.
Wani dan iska ya furzo mai cike da sautin zafi da takaici irin yadda yake jin kanshi din a lokacin nan dai ya bude bakin shi da yai mashi nauyi a lokacin kafin ya fara fadin .
Watau malam bayanin da zan ma ba akan wanan zaman bane kawai kamar yadda dan uwana daya gaiyace ka yayi maka bayani a yanzu.
Duk kallon shi mukayi kafin yaci gaba da fadin malam ni din dai na kasance mai aikata sabo a baya, da sauri malam yace wa,iyazu billah.
Yace kwarai malam a kuma cikin irin wanan halin na auri matata zainab gata nan zaune a gaban kowa .
wanda da farko nayi wanan auren ne don in fake a gareta da sunan aure a kaina ga idon mutane don kowa ya san ina da aure kada mutane su kawo wani zargi a gareni.
Duk kallon shi sukeyi har ni din da yanzu na kara gaskanta manufarshi a kaina a baya daya aureni din sai naji wani irin bakin ciki ya kara tokare min makoshina lokaci guda kafin sauti muryan shi ya dawo dani a daidai lokacin da yaci gaba da fadin.
Watau malam bayan auren namu da ita hakan baisa na bar aikata fasadi a doron kasa ba wai don ina da mata sai na dauki abin kamar yadda na tsara zaizo min a baya yadda nake so
A gaskiya na auri zainab ne akan zan samu rufin asirina a wurinta don tana yar tallakawa zata zauna dani ko don talaucin ta dana iyayyenta alokacin a yadda nake hange.
Saidai kuma nima ba wai haka kawai wanan tunanen yazo min ba sai bayan nayi nazarinta da irin hakkurin ta naga ya kamata in taimaka mata ta wanan hanyan kaga kenan zamu taimaki juna a takaice dani da ita amma ba cikin ta sanda hakan ba saboda tana da karancin shekaru sosai a lokacin.
A lokacin mami bata gane hakan ba don tana ganin na bijirewa zabin tane don tana ganin zainab din bata cancanceni ba ga aure.
Malam ya dago kai ya dan kalleni a hankali ya mayar da kanshi kasa yaci gaba da fadin.
Sai dai kakata da take jin ina yawan fadin zainab ce ta dace da rayuwana a lokacin duk da bata san mugun halina na boye ba da nake aikatawa a lokacin.
Amma hjyn ta bani goyon baya dari bisa dari ga wanan auren da nake son yi da zainab din.
Inda a karshe da mami din taki jin magana da shawaran mahaifiyan nata muka yanke shawara da hjyn da yayana mamud gashi a zaune kan naje na nemi auren zainab din a boye tunda mahaifiyarmu ta kafe kan sai zabin ta a lokacin.
Wanda ni kuma nake hangen zabin nata a gareni kamar wani hanyar tonon asirinane a wurin jama, a wanan auren na mami, don zai iya jawo min ga duniya don nasan koni waye.
Saidai ashe wanan zaben da nake ganin nayishi ne kawai don bukatana, shine haske a garemu baki daya .
Don shigowan zainab a cikin rayuwana a sannu a hankali ta fara kawo min sauyi na canza min lissafina da nakeyi da farko a kanta.
Kasancewan zainab din yarinya mai wayau da ilimin addini yasa abubuwa suka fara cabe min a rayuwa .
A lokacin haka nake gani don yawan nasihanta a gareni da saka min ido kawai da tayi kan duk wani abinda nakeyi ba tare da takura min ba .
Sai hakan yasa na fara kunyar kaina na da jin nauyin ta har ya kai na rage wasu abubuwan da nakeyi a fili saboda kaucewa idonta din.
Tunda nasan tasani amma bata nuna min tauye mata hakkinta da nakeyi yana damunta ko abin yana bata mata rai sai har idan ta kamani da idon tane mukan kwashi fitina sosai da ita.
Nasan kuma hakan da take min yana a cikin rashi gatan da take ganin bata dashi ko kuma fin karfi iyayyene dake aiki a kanta.
Don ga nawa tunane sai nakan yawaita yiwa iyayyenta da yan uwanta alheri don na kawar da zargi ko kaskanci a idanu su.
Nasha shawaran da zuciyana akan in rabu da ita kamar yadda mahaifiyan mu keso hakan, amma sai in kasa hakan don hankalin yarinyar da nake gani kuma gashi duk da tasan dabi,u na marasa kyau baisa ta wullakantani ba.
Ban kara tabbatar da hakan ba saida na sakasu karatu ita kanwarta da suke tare idon ta ya kare budewa a can chaina din sosai amma hakan baisa zainab ta raini ba ko naji watarana ta fadawa wani ga halaiyana marasa kyau.
Mun sha fama da zainab akan rayuwan maza da maza da nakeyi wanda take iya kokarin ta a kai taga na daina wanan akidar .
Amma sai hakan ya gagareta da farko na dauka tanayine don na kasa, kasancewa da ita a matsayun muna ma,aurata .
Sai daga baya na gane abin ba haka yake ba har kasan zuciyar ta tanayine kawai don ta fitar dani cikin wanan rayuwan na fasadi danake aikatawa.
Yan kungiyan mu sun sha ban shawara in kasheta in huta idan zata kawo min matsala a rayuwana, ko su kansu suyi yunkurin hakan in hana su.
Naji mami tace ikon Allah wai a kashe mutum kamar dan kiyashi kai haba jafar wanan wani irin rayuwa ka jefa kanka a ciki hakane ?
Lokacin na dago kai na kalle shi da idona da yake tab da hawaye bakin ciki tare da tausayin kaina da nakeji akan abubuwan da yake fadi din da bakin sa.
Malam ne ya katse shi da fadin gaskiya malam
Showing 366001 words to 369000 words out of 390011 words
Hjy fa ta fito yau kuwa ya sake jefo min tambaya nace yau banji motsin ta a falo ba ta fito ba tukun na dai je mun gaisa da ita dazun tana lafiya.
Yunkurawa yayi yana fadin muje dakin don da ita zamu tafi gidan mami din an jima ya fada yana tashi zaune kafin ya mike nabishi da kallo.
Kada kiji wani abu zata kai masu ziyarane ita ba abinda zai kaimu zai kaita ba ya fada yana tsaye.
Ban bishi dakin hjy dakina na wuce ina tunane kafin na kira layin inna na labarta mata abinda ke faru sama sama.
Sai ji hankalin ta ya tashi lokacin kuma nayi dana sanin sanar da inna din duk da ban fito fili na fada mata ga dalili ba amma sai ta rude .
Har na dan fara zargin iyayyena a raina ina fadi cikin zuciyana wai ko sun damu da damuwana kuwa ?
Sai nake ganin kamar dan abin duniyan da ya jafar ke basu akai akai yasa basu ganin laifin shi a kan komai .
Saida abinda ban sani a lokacin shine komai munin aure ga diya babu uwa ko uban da zasu so auren yarsu ya kare sai in hakan mukaddari a wurin Allah dama akai rabuwa a cikin auren .
Sai dai kuruciya ya hana in gane hakan a lokacin nake ganin laifin iyayyena kan son na zauna gidan jafar don abin duniya da ya rufe masu ido a lokacin.
Kafin sha biyu har na shirya shi kawai nake jiran fitowan shi don bani da kwanciyan hankali a lokacin son har na fara yanke hukuncin abinda zanyi idan na bar gidan nasa don kada rayuwana dana iyayyena ya wahala gaba.
Sai gashi ya shigo dakin nawa a cikin shirin shi yasa wasu shadda masu ruwan sky clour dinkin su ya tsaya masa iya gwiwan shi hannun rigan karami shima iya gwiwan hannu ya tsaya mashi sai kamshi ture ke tashi a jikin ranan har yar hula baka mai kyau ya saka a kanshi sai hakan ya kara fito mashi da kyawon shi fili duk da ya rame a lokacin.
A falo muka samu hjy zaune tana jiran mu yake fadin lalai hjy kina jin fita yau din nan har kin rigamu fitowa ke nan suka dan taba wasan jika da kaka kafin mu fita daga gidan.
A gida nabar sadiya don tace bazata gidan mami ba ita dataji can zamu tafi duk da fadila nasan tasan komai dake faruwa a gidan sabanin sauran yan aikin da basu san abinda ke faruwa ba sai aikin gaban su da sukeyi.
Amma ita kan nasan ta san komai dake faruwa a lokacin nuna kawai take bata sani ba nima kuma ban mata wanan maganan ba sam.
Ko lokacin da muka fito zamu fita din dagani akwai magana a bakin ta saida babu idon yin maganan ne a gareni balle ta tambayi abinda take son ji din.
Mota daya mukai amfani dashi zuwa gidan mami din shine gaba zaune da driver muna baya nida hjy.
Dan tafiya muka shigo unguwar su mami din ban dago kaina ba daga yadda nake zaune a bayan mota nayi tagumi sai faman sake saken da nakeyi a cikin raina .
Tsayawan motan yasa na dago kai ina kallon get din gidan da maigadi ya bude a lokacin a raina nace kila zuwan karshe kenan da zanyiwa gidan nan a hankali na mayar da idona na rufe har muka karasa shiga cikin gidan.
Muryan jalal yasani bude ido don jin yana fadin a, a bros kune tafe ashe gara da ban fita ashe tun dazun ya fada yana karasowa bakin motan.
Ganin hjy yasa ya koma kanta yana janta da ba,a har dai muka shiga cikin gidan yana wani ja mata hannu suna tafiya a hankali ina bayan su nima tare da yaya dake waya daga gefena.
Gaba dayan su kowa na falon zaune kasancewa ranan ba aiki duk suna gida ga baki dayan su har mami tana falon tare dasu.
Sallaman suka amsa na jalal amma sai idon su ya dawo a kaina sun kasa boye kyashin su a zukatan su a kaina.
Gaida hjy sukeyi da yayan su sai Na,imace take ce min zainab sannu da zuwa na danyi murmushi ina amsa mata a cikin dan fara, a har take fadin ga wuri kizo ki zauna tana kokarin tashi ta ban wuri.
Da sauri nace a,a anty ki barshi in zauna a nan na nuna kasa yace No cikin dakewa ya kalli Rufaida yace ke bata wuri ta zauna.
Saida tayi wani iri kafin ta mike a cikin fushi zata bar falon mami tace keko tsiyana dake ke nan wallahi saurin fushi Rufaida.
Tace to mami sai kuma tayi shiru ta kasa karasawa don wani irin kallo daya watsa mata yasa tayi shiru.
Dole ta dawo ta zauna a gefen mami din tana wani irin shagwaba mami tace kedai zuciyar nan naki zata wahal dake wallahi .
Ni kan zaune nakai a bina duk ina kule dasu irun yadda kowan su ke satan kallona tundaga kafa zuwa samana.
Na fara gaida mami bayan na zauna ta dan juyo da dan fushin fadan da takewa Rufaida ta amsa min tare da fadin ya gidan ya dawainiya da hjy.
Nayi dan murmushi na gyara zama bayan haka ba wace muka gaisa da ita a cikkn in bayan Na,ima da tun shigowan mu tayi min magana.
Sai suka wayen ce hakan da hira da hjy na nuna ban masan suna hakan ba gareni ina dakalan wayata daya dauke masu kuma hankali ga ganin ta.
Jamal ya shigo shima da alama baisan da zuwan mu ba sai lokacin suka gaisa da dan uwan shi nice na fara gaidashi yake fadin.
Zainab kun sha Nageria fa nasan ba don ciwon yaya ba da yanzun kun koma ai jalal ya karba a bayan shi daga inda yake tsaye.
Me zaisa ta damu ta koma tunda ba karatu takeyi ba yanzu Aisha da tun shigowan mu batayi magana ba ta fada a yanzu.
Ke lokacin da aka dawo kasan nan ai kuka keyi zafi ya isheki zaki koma jalal ya fada budan bakin ta sai cewa tayi aini a lokacin na tashi cikin jin dadi na sai kawai a daukoni a kawoni nan.
Amma kuma a yanzu kinsan zainab ta fiki samun dadin da kike fadin kin samuba can don haka ai ba abin mamaki bane don tace zaman Nigeria ya ishe ta a yanzu.
Wani tabe baki tayi tana kawar da kai gareshi bata ji dadi amsan daya bata ba daga inda mami take zaune tace koma dai meye a yanzu ba zaka taba hada Aisha da zainab ba ko ku ke nan kullun cikin gwatsale yar uwan ku a gaban kowa.
Look ba nazo nan da mata na bane don a riga challangen din ta haka koma meye a yanzu zainab zamana takeyi bana son jin wani zancen bataci a gareta again.
Falon yayi shiru kafin hjy tace dasu banda abinku ai ka zama matar mai hali yafi ace ai yar me halice ke a wanan zamanin.
Kafin wani yayi wani magaba akai sallama aka shigo ya mamud ne a gaba sai wani mutum mai cikar kamala a bayan shi suka shigo.
Nan aka shiga gaidashi sai lokacin na gane shine wanda zai warwale matsalan zaman mu da yaya din da mukazowa jin abinda hukuncin ya tanadar muna yanzu.
An dan taba hira kafin su mazan su fita su barmu a falon kamad kada yaya ya fita duk sai naji na tsawala a lokacin cikin su sai dai da yake hjy na wurin ba halin wani yai min wani maganan banza.
An dan dauki lokaci kafin yaya mamud ya shigo yana fadin zainab dan zo mijin ki na magana dake a waje.
Duk suka bishi da kallo ya fita na dan daga nabi bayan shi nima nasan kallona sukeyi a lokacin ba mamakin hakan a garesu.
A can na tsinkaye su zaune saman fararen kujerun roba su hudu na isa wurin da sallama a bakina suka amsa min.
Kusan a tare suke nuna min wuri in zauna na danja kafa a hankali nakai zaune a takure nake cikin su din kafin naji mutumin ya fara jan dogon addua tare da godiya ga Allah daya hadamu a wanan wurin.
Kafin yace ina gida zaune dazun malam gashi ya nuna ya mamud ya sameni da wani zance wanda ya daure maku kai .
Sai dai Alhamdullahi don addinin islama yazo da wayen kaine ga al,umman Annabi ga baki daya Annabin rahama bai bar duniyan nan ba saida ya warware muna irin matsalolin nan idan zun taso gare mu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI FATAN ANTASHI LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA MARASA LAFIYA ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYAN ALLAH YA KARA MASU LAFIYA AMIN.
YAR UWA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA KADA MU SHIGA HAKKIN JUNAN MU.
Zowan mami da ta biyo bayan mu ta samu muna zazaune malam na bayani hakan baisa malam din yayi shiru ba a lokacin har saida ya tsaya don kan shi.
Malam ya kare bayanin shi a lokacin jikin kowa yayi sanyi a wurin don irin bayanin dayayi a lokacin kan addinin Allah.
Ya dago tare da fadin kada in katse ku da bayani haka zan so wanda suke da alhakin zaman mu wanan wuri suyi min bayanin komai a tsare yadda zan fahinci zancen.
Sai lokacin mami ta samu bakin magana tana fadin akan meye akai wanan zaman ya mamud ne ya bata amsa da fadin kan matsalan matsayin auren su da kika fara magana ranan muke son malam ya warware muna.
Sai ta dan bimu da wani irin lalattacen kallo tana kawar da kanta gefe daya ba tare datayi magana ba a lokacin.
Sai ya mamud yayi sauri fadin dama watau malam kamar yadda na fada ma dan matsalane aka samu tun farkon auren har yakai an kwashi tsawon shekarun nan, ana zaune ba wani abinda ya taba shiga tsakanin su shiyasa muke son a warware muna matsayin wanan auren a yanzu.
Saboda mahaifiyan mu ta fara furta wanan kalamin wai an dade an dauki lokaci a yanzu kan ba sauran aure a tsakanin su.
Da sauri mami ta dan dago kai ta kalli ya mamud din tana fadin au don hakan dana furta kuka kira malam a kanshi to ai gaskiya na fada dan aure ko watani masu tsawo ya diba ba saduwa a tsakani ai akwai bincike a kai.
Malam din cikin murmushi ya karkada kai ba tare dayayi magana ba sai murmushin da yakeyi a lokacin.
Ya jafar yace dakata mamud jin haka kowa yayi shiru a wurin a lokacin ina faman tunanen zancen ya mamud din da yace mami ne tazo da wanan zancen ke nan haka na nufin mami dai har yanzu tana son in bar mata danta kota halin kaka ke nan yasa take wasu tsire tsire zance a yanzu din.
Sai gashi kuma yanzun din ma ta kara maimaita hakan a gaban kowa ba tare da jin komai ba a zuciyan ta.
Wani dan iska ya furzo mai cike da sautin zafi da takaici irin yadda yake jin kanshi din a lokacin nan dai ya bude bakin shi da yai mashi nauyi a lokacin kafin ya fara fadin .
Watau malam bayanin da zan ma ba akan wanan zaman bane kawai kamar yadda dan uwana daya gaiyace ka yayi maka bayani a yanzu.
Duk kallon shi mukayi kafin yaci gaba da fadin malam ni din dai na kasance mai aikata sabo a baya, da sauri malam yace wa,iyazu billah.
Yace kwarai malam a kuma cikin irin wanan halin na auri matata zainab gata nan zaune a gaban kowa .
wanda da farko nayi wanan auren ne don in fake a gareta da sunan aure a kaina ga idon mutane don kowa ya san ina da aure kada mutane su kawo wani zargi a gareni.
Duk kallon shi sukeyi har ni din da yanzu na kara gaskanta manufarshi a kaina a baya daya aureni din sai naji wani irin bakin ciki ya kara tokare min makoshina lokaci guda kafin sauti muryan shi ya dawo dani a daidai lokacin da yaci gaba da fadin.
Watau malam bayan auren namu da ita hakan baisa na bar aikata fasadi a doron kasa ba wai don ina da mata sai na dauki abin kamar yadda na tsara zaizo min a baya yadda nake so
A gaskiya na auri zainab ne akan zan samu rufin asirina a wurinta don tana yar tallakawa zata zauna dani ko don talaucin ta dana iyayyenta alokacin a yadda nake hange.
Saidai kuma nima ba wai haka kawai wanan tunanen yazo min ba sai bayan nayi nazarinta da irin hakkurin ta naga ya kamata in taimaka mata ta wanan hanyan kaga kenan zamu taimaki juna a takaice dani da ita amma ba cikin ta sanda hakan ba saboda tana da karancin shekaru sosai a lokacin.
A lokacin mami bata gane hakan ba don tana ganin na bijirewa zabin tane don tana ganin zainab din bata cancanceni ba ga aure.
Malam ya dago kai ya dan kalleni a hankali ya mayar da kanshi kasa yaci gaba da fadin.
Sai dai kakata da take jin ina yawan fadin zainab ce ta dace da rayuwana a lokacin duk da bata san mugun halina na boye ba da nake aikatawa a lokacin.
Amma hjyn ta bani goyon baya dari bisa dari ga wanan auren da nake son yi da zainab din.
Inda a karshe da mami din taki jin magana da shawaran mahaifiyan nata muka yanke shawara da hjyn da yayana mamud gashi a zaune kan naje na nemi auren zainab din a boye tunda mahaifiyarmu ta kafe kan sai zabin ta a lokacin.
Wanda ni kuma nake hangen zabin nata a gareni kamar wani hanyar tonon asirinane a wurin jama, a wanan auren na mami, don zai iya jawo min ga duniya don nasan koni waye.
Saidai ashe wanan zaben da nake ganin nayishi ne kawai don bukatana, shine haske a garemu baki daya .
Don shigowan zainab a cikin rayuwana a sannu a hankali ta fara kawo min sauyi na canza min lissafina da nakeyi da farko a kanta.
Kasancewan zainab din yarinya mai wayau da ilimin addini yasa abubuwa suka fara cabe min a rayuwa .
A lokacin haka nake gani don yawan nasihanta a gareni da saka min ido kawai da tayi kan duk wani abinda nakeyi ba tare da takura min ba .
Sai hakan yasa na fara kunyar kaina na da jin nauyin ta har ya kai na rage wasu abubuwan da nakeyi a fili saboda kaucewa idonta din.
Tunda nasan tasani amma bata nuna min tauye mata hakkinta da nakeyi yana damunta ko abin yana bata mata rai sai har idan ta kamani da idon tane mukan kwashi fitina sosai da ita.
Nasan kuma hakan da take min yana a cikin rashi gatan da take ganin bata dashi ko kuma fin karfi iyayyene dake aiki a kanta.
Don ga nawa tunane sai nakan yawaita yiwa iyayyenta da yan uwanta alheri don na kawar da zargi ko kaskanci a idanu su.
Nasha shawaran da zuciyana akan in rabu da ita kamar yadda mahaifiyan mu keso hakan, amma sai in kasa hakan don hankalin yarinyar da nake gani kuma gashi duk da tasan dabi,u na marasa kyau baisa ta wullakantani ba.
Ban kara tabbatar da hakan ba saida na sakasu karatu ita kanwarta da suke tare idon ta ya kare budewa a can chaina din sosai amma hakan baisa zainab ta raini ba ko naji watarana ta fadawa wani ga halaiyana marasa kyau.
Mun sha fama da zainab akan rayuwan maza da maza da nakeyi wanda take iya kokarin ta a kai taga na daina wanan akidar .
Amma sai hakan ya gagareta da farko na dauka tanayine don na kasa, kasancewa da ita a matsayun muna ma,aurata .
Sai daga baya na gane abin ba haka yake ba har kasan zuciyar ta tanayine kawai don ta fitar dani cikin wanan rayuwan na fasadi danake aikatawa.
Yan kungiyan mu sun sha ban shawara in kasheta in huta idan zata kawo min matsala a rayuwana, ko su kansu suyi yunkurin hakan in hana su.
Naji mami tace ikon Allah wai a kashe mutum kamar dan kiyashi kai haba jafar wanan wani irin rayuwa ka jefa kanka a ciki hakane ?
Lokacin na dago kai na kalle shi da idona da yake tab da hawaye bakin ciki tare da tausayin kaina da nakeji akan abubuwan da yake fadi din da bakin sa.
Malam ne ya katse shi da fadin gaskiya malam
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123 Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131