dago kai na iya kallo shi ba tunda ya zauna a wurin ina a yadda nake a kwance din har lokacin dan girgiza kai yayi kafin yace .
Wai bakiji ina magana dake bane zainab meke faru dakene kika koma haka lokaci guda ?
Jin abinda ya fada yasa na dan juyo kadan na kalleshi a cikin takaici da jin hsushi da tsanar shi lokaci guda daya sauka min a zuciyana.
Da kyat na daure cikin sanyin murya nace damuwata ba matsalan ka bane yaya abinda ya shafeni ni ya shafa.
Yanayin muryan da nai magana dashi dole yaba mutum mai saurare a lokacin tausayi a lokacin don gaba daya muryata ta dakushe dan kuka.
Yace amma ai hakkin ki yanzu a kaina yake duk wani damuwan ki ya shafeni ko don haka ki fada min damuwan ki nace ko menene ?
Ko kuma a yadda kika ganni a daren jiyane ya sakaki daukan wanan matakin a yanzu kina son ki halaka kankine ko kuma addu,a ya kamata ki min a matsayina na mijin ki a yanzu.
Addua ?
Addu,a fa kace ?
Kai bakaiwa kanka addu,a ba ka daina wanam halin sai nice zan ma addua a karba min ?
Yaja dogon numfashi bayan jin abindana fada ga mamaki daya hanashi kwakwaran motsi don dai yasan girma ya gama faduwa ke nan .
Inaga nasan sauran abinda yake aikatawa bayan wanan ashe da rashin kunyar yafi wanan da bai taba zato ba a wurina.
Numfashi ya sake ja tare da fadin to tashi muje asibiti a dubaki idan lafiya kike a yanzu ?
Barshi don ni lafiyata kalau a yanzu yaudaran ka kawai ne abinda ya dameni a zuciyana .
Ya jafar ka cuceni ka yaudareni ka yaudari iyayyena da suka aura min kai a matsayin miji yau suji mijin da suka aura min suke kiranka da surukin kirki ashe tsohon mashayin dan giyane haka basu sani ba.
Haba ya jafar ya kake son nayi da rayuwana da halinda muke ciki da mahaifiyar ka da yan uwanka zanji ko da wanan halin rayuwa naka na boye da Allah ya baiyana min a daren jiyana gani.
Lokaci daya yaya kazo kashiga rayuwana ka nuna isa da gadaranka a kaina don kawai ina karkashin mahaifiyar ka ba tare da kayi tunanen nawa rayuwan ba.
Na hakkura a hakan nake zaune tare dakai don biyayya ga iyayyena duk da mutane da dama sun san da wata manufa ka aureni don ni din ba ajin auren ka bace ai.
Amma haka na hakkure nake zaune tare dakai duk da mami har gobe ta nuna bata ra,ayin zamana dakai.
Wace matakace da kai yaya ranan da ka tsaya gabab mahalicin ka don kare kanka a wanan rayuwan ka tuna fa shi mutum ba a bakin komai yake ba ga Allah.
Yanzun nan Allah na iya ikonsa a kanka kana takama da lafiya da arziki da ilimin ka zai iya mashe ka gawa lokaci guda.
Ko kuma ya karbe lafiyan da kake takama dashi lokaci guda zai iya maisheka miskini mara moriya kana kuma a raye.
Kukane yazo min har na kasa karasa zancena na juya na fara kuka sosai a cikin tashin hankali da bacin rai ga abinda ya faru din.
Kai ya dukar a kasa don wanan maganan dana fada yafi komai nauyi a wurin shi sai yaji wani irin gumi yana feso mashi lokaci guda gashi ya rasa abinda zaice dani don yasan gaskiya na fada mai .
Don nauyi mami da yan uwanshi a iya su zancen zai tsaya idan sun san da haka nawa iyayyen kuma da wani ido zai iya kallon su idan har sunji.
Don haka sai ya zuba min ido kawai yana kallona da mamaki kamar ranan ya fara ganina a duniya.
Nima ban fasa kukan takaicin da nakeyi ba can naji yakai hannun shi saman kafadana yana fadin is OK kukan ya isa haka nasan na aika abinda Allah ya haramta ga musulmi .
Saidai ina rokon ki da ki taimakeni ki mun adduan Allah ya rabani dashi har abada a rayuwana yadda ya fada a cikin wani murya mai ban tausayi zakace bashi yake maganan ba.
Majina na share da kyalen dana aje a wurin don share hancina tunda safe kafin na dago kai ince ko nayima addu,a yaya tunda kai baka da niyar bari ba fasawa zakayi ba ai.
Shikan yau mamakin zainab din yakeyi a ransa sai fadin yake ashe haka wanan yayinyar take ina kallonta shiru shiru ashe akwai aiki ja a gabana rana data gama gane koni waye ?
Saidai a fili yace waya fada maki bana addua akan hakan ko yaushe abune dai idan Allah ya jarebaka dashi yana da wuyan sha,ani.
Duk cikin maganganun da yai min a lokacin babu kalman ban hakkuri ko nadama a tare dashi don a gadarance yake fadan maganan shi kamar yadda ya saba idan yana magana.
Kinci abinci yau ya tambaya a karshe banza nayi dashi ba tare dana bashi amsan tambayan nasa ba sai ajiyan zuciya da nakeyi don kukan dana sha a ranan.
Kinga yanzun dai ki tashi kiyi wanka ki fito mu sauka kasa kici abinci don kada wani ciwo yazo ya kamaki kuma ?
Ba zan iya cin komai ba don bakina bai da dasin cin wani abu a yanzu na fada ina gyara kwanciya ta hanyar dunkulewa a wuri daya.
Yana zaune shiru banji ya motsa daga inda yake zaune ba sai can naji yayi ajiyan zuciya da karfi ya mike tsaye.
Ni a zatona ya fice daga dakin ne a lokacin ashe ban dakina ya shiga ya hada min ruwa mai zafi sai ji nayi mutum yana kokarin cicibana lokaci daya.
Don Allah yaya ka bari bana jin yin komai a yanzu zan tashi idan zuciyana ya sake min bai tsaya saurara min ba sai daukana da yayi dani yana shiga ya tsomani a cikin bahon wankan dake ban dakin .
Lokaci guda na sake wani irin ajiyan zuciya a tare dani juyawa yayi ya fita ya ban wuri a yanzu kan idona ya bushe don na nemi kuka na rasa a idona.
Haka na daure na watsa ruwa tare da alwal bayan na cire tufafin dake jikina na samu har na gama na fito a zatona yana dakin har lokacin don haka ban yarda na fito ba sai dana leka naga baya dakin.
Zani da hijjab dina na dauko a wardrobe na nufi inda nake sallah na tada sallah ina sallah naji an kwankwasa dakin an shigo.
Ashe julie ce ya umurta da takawo min abinci ganin ina sallah tana ta mamakina har tana tuntube a dakin wurin aje kayan abincin da ta shigo min dashi.
Saida na gama sallah na mika kuka ga ubangiji kafin na mike na samu wasu kaya na zura a jikina ban ko kalli abinda ta aje min a dakin ba.
Na koma bakin gado na zauna ban koma kwanciya ba sai ga mama da sallama a dakin a karon farko data shigo dakin nawa ke nan tun zuwan mu kasan.
Amsa sallaman nayi halimatu na biye da ita a baya mama ke fadin zainab ashe bakiji dadin jikin ki bane sai yanzu mikin ke fada muna.
Ni na dauka yau yana hutune ai kuna tare shiyasa ma ban yarda wanan yar taragagan tazo inda kike ba don yau banji fitan shi ba shima.
Dan dariyan yake cikin katfin hali na kakaro a fuskana ina fadin tun darene bana jin dadi mama .
Tace haka dai shima ya fada muna ai kwa fadawa mutane tunda gamu a gidan ai yanzu ina dadin hakan da kukayi ai ko sannu kawa mutum.
Tana kai aya ta dora da fadin yace kinki cin komai tun safe ga abinci nan yasa a kawo maki sai ki daure kici don Allah don yace yayi yayi kici kin kiya.
Badon naso ba don biyayya ga mama Ramatu na daure na kurba ruwan shayin bayan shi ban taba komai ba a kayan ina gamawa na koma na kwanta har lokacin suna dakin tare dani.
A bakin su nake jin wai ya fita zuwa asibiti ya duba hjy amma ba zai dade ba zai dawo a raina nace shi dai ya sani don ni na tsane shi a yanzu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA




Kwana biyu ina daki kwance a cikin damuwa bana fitowa ko falon gidan a inda muka saba dan zama dasu mama muna hira.
Asibitin ma suke zuwa su duba hjy don ni ban iya fita yanayina kamar nayi jinyar kwanaki nake jin kaina.
Ya jafar yakan shigo ya dubani na dan lokaci saidai zai kare tsayin shi har ya bar dakin ban dago kai na kalli inda yake tsaye ba hakan kuma bai nuna fushin shi ga yadda nakeyi mai din ba.
Ranan dai dana kwatanci ya fice gidan na dan ja kafana na sauka kasa babu kowa a falon haka yasa na dan nufi wajen gidan don nasha iska kadan ko zanji jikina ya kara sakewa.
Wasu tsuntsaye dake kiyo ne a haraban wurin suka dauki hankalina har yakai na shagala ga kallon su sun dauke min hankali yadda suke ciyar da junan su abinci.
Barka da fitowa matar yaya naji an fada a bayana koda ban juya ba nasan ko muryan waye don muryan su yana da kama dana dan uwanshi hakan bai hanani gane ko waye a wurin ba yake gaidani.
Dan juyowa nayi tare da kakalo murmushin don dole ina fadin ya jamal ina wuni a cikin ladabi shima dan gyara tsayuwan shi yayi yana amsa min lokaci guda.
Tare da fadin ashe kwana biyu baki da lafiyane duk da nasan sanadin rashin lafiyan naki mijin kine ya jawo maki shi .
Da sauri na dan dago kai na sauke a kanshi don jin abinda ya fada yace yes zainab na sani shine yaja maki wanan ciwon don halaiyan shi da kika fara gani wanda da farko yake boye muna hakan ko ?
Don mu kanmu bamu san da hakan ba saboda ya boye muna koshi waye a wurin mu saidai ni tun ganin yadda auren ku ya wakana dashi na sa ido ga harkan yaya don in gano dalilin shi na bijerewa mami.
Da kuma dalilin dayasa ya zabe ki a matsayin wace yake son luluba a cikin bargon arzikin ta ya fito a mutum sak kamar kowa.
Wai zainab kinsan ke din mai arzikine arzikin da ba kowa Allah keba irin sa ba sai kebabu daga cikin bayin sa .
Shifa arziki da kike ji a wurin Allah kala kalane gun mutanene suka dauka arzikin dukiya shine arzkin da kowa zai samu yayi alfahari dashi.
Allah nama bayin sa arzikine ta hanyoyi daban daban akwai masu arzikin "ya"ya akwai arziki na hali akwai mai arziki na baiwa da arzikin hakkuri da arzikin wadatan zuciya da dai sauran su.
Kamar ke zainab kina da arziki dana fahinta wanda Allah ya baki wanda ba kowane zai iya fahintar haka ban sai mai natsuwa zai gane baiwan da Allah yai maki zainab.
Kallon da nayi masa na ban fahince ka ba yasa yace yes Allah yai maki arzikin bawai da hakkuri wanda ba ko wace mace take da irin wanan baiwan ba haka.
Ki duba duk da karacin shekarun ki zainab amma kin iya rike sirin mijin ki a zuciyar ki ba tare da kin fadawa kowa yasan halin da dan uwana ke ciki ba.
Na gani da idona ba wani ya fada min ba irin halin da ya dawo maki a ciki gidan nan last two days da suka wuce don a buge ya shigo gidan nan ya tayar dake.
Ban sani bako wanan ne karon ki na farko da kika ganshi a cikin wanan halin idan kuma har kin sani tun baya na dai yaba maki wurin kokarin boye masa siri da kikayi.
Idona ne ya kawo kwalla lokaci guda yace no bana son kiyi kuka a yanzu don kuka ba naki bane zainab a yanzu.
Saboda yakine ja a gaban ki dake tunkaran ki a yanzu don sai da taimakon ki zamu samu har mu shawo kan wanan matsalan don wanan yakin zainab ba naki bane ke kadai yanzu ya shafi kowan mu a yanzu.
Yanzu yin fushi ko kauracewa ya J baya da amfani a garemu baki daya don ni nan na nuna mashi bacin raina yan kwanaki da suka wuce kan fahintar wasu halayan shi danayi da yake boye muna.
Sai na fahinci fushi ko bashi baya baya hanashi aikata sabon daya samu kansa a ciki saidai ma ya kara kangare muna ta wanan hanyan.
Zainab a yanzu ya zama dole muja ya J a jikin mu fiye da yadda muke a yanzu dashi mu sanman ma keda kike zama matar shi.
Don ta hakan har Allah ya taimakemu ya bamu sa,a akan wanan halaiyan da yake aikatawa a boye don zainab gaskiya matakin da kike kokarin dauka bashi zai sa auren ki dashi ya rabu ba a yanzu.
Yin hakan kuma kamar kara turashine ga abinda yakeyi a yanzu shike nan kinga rayuwan shi ya kara shiga wani hali ta sakacin mu ashe ?
Don ke kanki ba zaki so kiga wani cikin yana irin wanan halaiyan ba kinga shike nan ko yaushe kina cikin damuwan hakan fiye da kina gidan sa ashe.
Dama alkawarin Allahne duk wanda ya kama hanyar aljanna zaita haduwa da abubuwan da zuciyar shi bata so haka kuma wanda ya hanyar wuta zaita haduwa da abubuwan da zuciya keso .
Shi yasa akace daga cikin hakkuri da akeso mutum yayi cikin rayuwan sa harda hakkurin biyyaya don Allah .
Don hana zuciya aikata sabon data ginu akanta farat daya abune mai wahalan gaske sai a hankali ana jan hankalin maishi anayi masa nasiha da addua a hankali tare da nuni ga hukuncin da ubangiji ya tanadar kan abin sai kiga maishi ya bar abin ba tare da wani tashin hankali ba.
Don haka zainab ina rokon ki a yanzu kada kice zaki bar yaya don wanan halin da idanunki ya gane maki a kanshi dama wanda baki gani din ba a yanzu bana fatan hakan a gareki.
Don ni kaina bazan so mami ko wani namu musanman ma mama Ramatu dake nan yanzu tare damu har ta fahinci wanan abinda yaya keyi ko taji hakan daga bakin ki.
Don haka zainab hakkuri zan kara baki kan hakan saifa kin jajirce gami da masa addua da saka ido kan duk wani al,amarin daya shafi rayuwan shi.
Ki nuna kedin matar sunnace a gareshi wace tasan right din ta na aure bawai ina nufin sai kin fito fili kin nuna ya baki hakkin ki na matsayin ki na mata a garshi ba.
A,a a cikin hikima da basira irin naku na mata ya kamata ki fata yakin da kika shirya a kansa yanzu ta hanyar sake jiki dashi ki daina wanan ja bayan da kikeyi a yanzu gareshi.
Mijin kine zainab idan yayi ba daidai ba ki fito fili ki fada masa abinda yayi din baida kyau ga Allah da al,adan mu a sannu in yana da rabo sai kiga ya bari.
Katse shi nayi da fadin to amma ya jamal kana ganin a matsayina na ba kowa ba a gareshi yaya zai yarda yaji nasiha ta ?
Me zai hana zainab ya bani amsa zai saurara maki don nasan shi di yana son ki kuma yana tausayin ki a zuciyar shi.
Wanda hakan nema har ya yanke shawaran ya aureki ya kawoki gidan shi ku zauna a tare ku kuma rayu a tare dashi duk ritsi duk wahala.
A karshe ina mai kara baki hakkuri ka wanan kaddaran da kika samu kanki a ciki a matsayina na dan uwan ki yayan ki bawai kanin mijin ki ba.
Hawayen da nake dannewa ne suka zubo min lokaci guda nace ya in sha Allahu zan gwada sharanka a kansa nima a matsayina na kanwarshi kuma matarshi a yanzu.
Nagode zainab da kika fahinci ne kafin wani yasan wanan abi kunyar da yaya ke kokarin sakamu a idon duniya nima zanyi iya kokarina in dinga fadakar dashi kan abinda yake aikatawa din a yanzu.
Na barki lafiya ni zan je asibiti yanzu sai dai ina son wanan damuwan da tashi hankalin ki daina yinsa daga wanan lokacin ki fito a matar auren ki sak a gidan nan ba tare da kin damu da warning din kowa akan hakan ba.
Nina barki lafiya ya fada ya juya ya tafi ya barni a wurin ina binsa da kallo zuciyana kuma da dinbin tunane kan aikin daya dangantani dashi din a yanzu.
Duk da nasan dama wanan din aikinane yin hakan inda hali kuma da jajircewa ya zama dole in shanye duk wani damuwa don in ba haka ba zuciyana tana gab data tarwatse a yanzu.
Sake tambayan kaina nayi ta yaya zan iya duk wanan abubuwan yanzu don ni mace ce mai kunya da sanin ciwon kaina.
Don haka
Showing 204001 words to 207000 words out of 390011 words