don jin ya ambaci waini matarshi ce a yau a karo na farko zamana dashi.
Nace am not your wife dan dama dama ka kirani da sister ka zaifi sauki garemu hakan .
Cikin daga hannu kada mama ta fahinci make faruwa a tsakanin mu yace dani to to naji dama aike kanwatace tunda ke din yar mamice.
Yana fadin haka ya mike don gudun kada asirin shi ya tonu a gaban mama da halimatu dake can zaune dan nisa damu.
Nan ya wuce ya barni zaune na tasa abinci a gaba ina kallo naji mama na fadin har zaka fita ke nan yau dai ka saka zainab karyawa da wuri haka.
Bata son cin abinci bansan meyasa hakan ba ta saba zama da rashin karyawa da wuri tun a gida.
Tun daga wanan ranan ya saka min ido kan karyawa da safe na dai gane yana neman wani hanya na dan shakuwane a tsakanina dashi don haka na kara shan nin jikina dashi.
Allah da ikon sa sai ga hjy an sallamota gida taji sauki sosai kamar ba ita bace akazo kasan da ita a tallabe.
Dawowan hjy gidan ya kara muna sakewa da an,nashuwa ko yaushe muna kusa da ita tana kara jan mu a jiki tare da bamu dariya da barkwanci kamar yadda muka saba a baya da ita a gidan mami kafin mu bar gidan.
Saidai tsakanin ya jafar da ya jamal har yanzu babu jittuwa a tsakanin su suna dai gaisawa sama sama a tsakanin su.
Tun hjy bata farga da har yanzu babu shiri a tsakanin su ba har yakai yanzu ta soma fahintar suna nan a yadda suke sai ta soma zargin akwai wani abu dake faruwa mai girma a tsakansu.
Babban abinda yafi damunta shine ni kaina ta fahinci irin zaman da mukeyi dashi na wasa da hankalin mutane gashi idan ta fambayeni sai ince mata lafiya muke zaune dashi.
Don haka tasha alwashin tambayana don jin irin zaman da mukeyi a tsakanin kafin shi ta tunkareshi tasan ba zata fahinci komai a bakin shi.
Ranan ya jamal zai fita da mama data matsa ya kaita wani shago daya bata labari nima nace zan bisu zuwa shagon muyi kallo.
Saida muka shirya hjy tace na zauna gida ba zamu barta a gida ita kadai ba badan naso na zauna din don naso fitan tunda a gaban yaya mukai maganan fitan har nace nima zan bisu y yarda.
Bayan fitan sune tasa na debo fruit muna na debo a cikin bowl biyu na shigo dashi falon hjy kan tana shan nata saidai ni na saka nawa a gaba sai wasa da spoon din hannuna nakeyi ina faman tunane.
Hjy ta aje cibin dake hannun ta ta tsura min idanu na dan wani lokaci sai ta lura ban ma san tana kallona ba a lokacin.
Abu lafiya kike kuwa shiru ban dago kai ba ta kara fadin Abu nace meke damuwan ki haka kike wanan tunane haka ?
Abu fa ta fada a karo na uku tana tafa hannayen ta idon ta a kaina firgigit na dawo a cikin hankakina ina dago kai tare da duban inda hjy take zaune.
Ni take kallo a cikin mamaki baiyane karara a fuskan ta kafin tace dani me kike tunane haka yar nan kinga mu kadai ne a gidan nan yanzu.
Ki saki jiki ki fada min abinda ke damun ki a rai ki dauka ni din mai baki shawaran da zai fitar dake daga hakin damuwan da kikene .
Ko yanzu kin daina daukana a matsayin kawarki jafari ya kwace min ke kin daina yayina sai shi kadai ?
Da sauri nace a, a hjy har gobe kina nan a matsayinki na kakata a zuciyana yanayin fuskana kawai ta kalla ta fahinci akwai wani abinda ke faruwa a tsakani mu da yayan.
Duk sai nabi na tsargu da irin kallon da take min a lokacin don haka sai na dukar da kaina kasa ina ci gaba da wasa da cibin dake hannuna.
Zainabu hjy ta sake kiran suna na dago kai a hankali ina amsawa da na,am tare dan kallon ta tace .
Kinga ki fada min meye damuwan ki da mijin ki kada ki boye min komai ki daukeni tankar nice na haifi mahaifiyar ki ko mahaifin ki.
Na dan gyada kai a hankali alaman gamsuwa a gareta kan abinda ta fada taci gaba da fadin tun zuwan mu ina kule da yanayin yadda kuke zaune dashi.
Nayi shiru na tsayin lokaci kaina na a duke a kasa ina dan guntun tunane anya zan iya fada mata matsalan mu kuwa ko banza fa itace ta haifi mahaifiyar shi.
Kuma ta nuna tafi son shi a cikin jikokin ta kaf idan na fada mata a wani yanayi tsohuwar zata shiga don jin jikan nata ashe mashayine na gaske.
Don haka na yanke shawaran fada mata wani abin na daban na dan dago kaina tare da fadin hjy bana cikin matsalan komai dashi
Ta dan tsura min ido na tsawon lokaci kafin tace kin tabbatar da hakan zainabu na gyada mata kai kawai sai naga tayi murmushi kadan a fuskanta kafin tace dani.
Amma ni ga dan nawa fahintar sai naga kamar har yanzu babu wani mu,amulan aure dake wakana a tsakanin ku illa kawai gaisuwa da dan kulawa a gaban mu koba haka bane zainabu ?
Da sauri na dago kai na kalleta sai kuma na dukar da idona saiga hawaye yana zubo min daga idanuwana lokaci guda.
Ai kinga irin ta zainabu ina son ki sani ni mace ce yar uwan ki kuma manya sunce kowa ya rigaka kwana yana rigaka tashi.
Hjy babu komai da dawani matsala ai zan sanar dake kawai dai ni karatu nake son inci gaba dashi yasa nake tunane na tsunci kaina da fadin haka a gareta.
Hjy ta kalleni ta girgiza kai tare da fadin to shike nan amma kada ki dawo da baya kina dakin sanin kin fada min gaskiyan da bakiyi ba.
Koda yake dai mai daki shiyasan inda ruwa ke masa yoyo ai idan kinfi bukatan ki tafi a hakan dake dashi aiga fili ga mai doki sai mu zuba ido mu gani zainabu.
Ban yarda abinda kika fada ba a yanzu domin ni nasan kin boye min ne kawai don kina daukana ta bangaren jafari nake.
Amma ni nasan da akwai abinda kike boye min a zuciyar ki namiki tambayan amsan daya ce ki bani sai baki ban ban ba kina kawo min wani zancen karatu.
Karatu kan ai dole kiyishi zainabu tunda kina auren wanda boka ya huda ko jiyan nan naji yana magana akan karatun ki har nace ya barki a nan basai kin koma gida kinyi a can ba nan kusa dashi zaifi mai saukin yawan sintirin da zaiyi idan kina can Nageria din.
Da sauri na dago kai a karo na barkatai na sauke kan hjyn don jin abinda ta fada na wai in zauna nan tare da yaya a kasan mutane inda bansan kowa ba.
Eh hakan nace kuma ya amince da hakan don haka idan zamu koma ba tare dake zamu tafi ba a nan zamu barki keda kanwarki.
Amma hjy da baki fada masa haka ba don shi kanshi yayan zaifi bukatan zamana a can gida da nan din ya dai amsa makine don baya iya mussata maki zancen ki gareshi .
Eh hakan yana da kyau tunda harkin fahinci hakan keda kanki sabanin ke da yanzu kika fara daukana a wani matsayi na daban.
Zainabu nasan ki nasan halinki don haka ban yarda da abinda kika fada ba a yanzu.
Domin ke kullun yar ba komai ne saidai duk wanda yasan ki ya dubeki a yanzu yasan da akwai matsala a tare dake zainabu.
Na dauka nice mutum ta farko da ko ban tambayeki ba zaki iya budan bkin ki ki fada min halinda kike ciki da mijin ki a gidan shi.
Tunda ninayi tsaye har wanan auren naku ya kullun a tsakanin ku saboda ni nasan halinki da nasa da kyau don ke yarinyace da bata gama mallakan hankalinta ba har yanzu.
Hawaye naji sun taru min a idanuna lokaci guda ina tausayawa kaina halin kuncin da nake ciki a wanan lokacin da abin zai fadu tabbas hjy kece ta farkon da zan fara fadawa wanan maganan a yanzu.
Amma a fili nace da sauri na mayar da hawayen nawa ban yarda sun digo a gabanta ba sainace hjy addu, a kawai zaki tayamu dashi a yanzu nan gaba idan bai daina ba zan fada maki insha Allahu.
Bayan ta dan tsura min ido tace to shike nan Allah yai maki albarka kin nuna min kedin mace ce ta gari mai rikon amnan mijinta ako wani hali ta tsunci kanta zata iya rike mai sirin sa a rayuwa.
Madalla dake zainabu insha Allahu hakkuri ki ba zai tabe a banza ba kici gaba da hakkuri da addua kuma kada ki yarda ki saka damuwa a ranki kinji.
Har muka bar wurin hjy tana min kallon tausayi don nasan tana da magana a zuciyar ta saidai ban bada daman hakan ba a lokacin.
To me zan fada mata ince ga yadda jikan ta yake ai saidai tajishi a bakin wani na sani ko in fada ta sake ribcewa ciwon dayafi wanda ta taso a yanzu.
Dakina na shiga cike da tunane na dan watsa ruwa tare da dauro alwala na fito na tayar da sallah azahar sai uku da rabi su mama suka dawo da sayyaya mai yawa tare dasu.
Ban fito ba don tunanen da nakeyi kan zancen mu da hjy ba abinda ya tsaya min a rai sai zancen karatuna da zanyi a nan .
Shike nan yanzu babu zancen komawa gida a garemu ke nan sai tsawon wani lokaci anya kuwa zan iya daurewa in zauna da wanan mashayin haka?
Idan na zauna a nan dagani sai shi ta yaya zan iya shawo kansa babu kowa nasa a kusa dashi irin ya jamal da zai saka mai ido kan abinda yakeyi tunda ni ba zaiji magana na ba.
Ya zama dole ke nan a gareni in kara jajircewa akan yadda zaman mu zai kasance a yanzu bayan tafiyan su hjy da mama.
Zan kuma kara sa mai ido inyi iya kokarina wurun rabashi da wanan halin da yardan ubangijin mu sai dai babban matsalana a yanzu shine rashin layin waya da banda shi a tare dani.
Don ina son muyi siri da malam mijin mai zube sai kuma matsalan anty fadila da nake son ya dawo da ita kusa dani don da taimakon ta zan iya samun nasaran abinda na dosa a yanzu.
A takw dabara ya fado min a rai nace da hjy ya kamata na hada wurin shawo kan shi ya yarda fadila ta dawo nan mu zauna tare da ita .
Ko abunuwa zasu zo min da sauki yadda nakeso don tafini sanin ta kan duniya ko naso yin abu bazan iya ba don hankalina baikai na hakan ba a yanzu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Ya fito daga wanka da safe ya samu wayan shi dake ajiye saman bedside din shi yana ringing yayi saurin kai hannun shi ya dauka kada ya katse.
Bakon lamba ya gani yayi kamar kada ya daga saidai ya daure ya dauka don baisan wanda ke kiranshi da wanan layin ba.
Don tsayin kwanaki biyu ke nan maishi yana yawan kiranshi a daidai wanan lokacin don haka maishi yasan shi kenan farin sani yasa ya kirashi a wanan lokaci .
Ya dauka da hello muryan taju ne akan layin ya fara magana da fadin nasan kayi fushi dani sosai yasa na kiraka na baka hakkuri don banzaci hakan zai faru ba ni kaina zafin kishine ya sakani yin hakan a lokacin.
Saida ya gama sauraren shi yake fadin ka dauka dolene nake tare dakai dama ko kuma bazan iya zama idan babu kaiba.
Taju ya saki wani dan ajiyan zuciya yace kayi hakkuri bana iya rayuwa idan bada kai ba boss kasa ka maye gurbin na da son wani bayan ni.
Hankalina a tashe yake tun ranan da haka ya faru a tsakanin mu kayi hakkuri ka rike kaunar dake tsakani da kai bana iya jure ganinka tare da wani kuna rayuwa ina kallo.
Ya jafar yayi murmushi a tausashe kafin yace taju ke nan kana sane kayi kokarin tona min asiri don kawai wani bakin kishin ka na banza can.
Taju ya katse shi yana fadin Iam sorry boss banyi haka a cikin hankalina ba a lokacin kasan irin son da nake maka a rayuwana.
Jafar din yaja wani uban tsoki tare da furta is too late now don na dade maye gurbin ka da wani so ka manta da wanan a tsakanin mu.
Yana fadin haka ya kashe wayan shi taju ya kalli wayan yaga ya kashe abinsa idon shi ya runtse yana jin wani zafin son jafar din na ratsa zuciyar shi lokaci guda.
Don tunda ya samu jafar ya bar sauran abokan harkan shi don jafar mutum ne har mutum yana da tabbacin idan jafar ya barshi rayuwan shi yana cikin gararari ke nan.
Shiko jafar din wayar ya jefar saman gado ya koma gefe ya zauna ya tallafi kanahi da hannayen sa biyu zuciyar sa tana masa azalzala.
Don shi yanzu zuciyar shi ta kasu biyu don yasan kirsis yake da asirin shi ya tonu muddin wanan yarinyar mai wayau na gidan nan.
Bai mu maganan zancen karatun mu ba ko zancen tafiya ai bada mu za a tafi ba asalima dai dan kwana biyun nan na kula da yana yawan daure fuskan shi ga kowa a gidan.
Ni hakan bai dameni ba tunda dama ba wani shakuwa bane tsakanin mu saidai abinda na zata ko hjy ta zauna dashine shima kamar yadda ta zauna dani tana bincikena kila shima sunyi hakan dashi.
Ranan dai da safe muna zaune a dakin hjy yake cewa mu shirya zamu fita karfe hudu na dauka badani yake magana ba saida ya kalloni yana fadin bakiji bane na dago kai ina fadin naji a sanyayye.
Daga inda hjy take zaune naji tace umhumm kawai tana dan kawar da kanta gefe daya daga barin kallon kowa a dakin.
Mama Ramatune tayi karfin halin da matarka zaka fita ko damu duk don kayi magana ta baibai bamu fahince ka ba gaskiya a nan ?
Da ita nake mama akwai inda zamu tafi tare yau ya bata amsa daga haka ya fice ya bar dakin hjy ta bishi da kallo tare da fadin miskilin banza kawai ya kama daure fuska kamar bai taba dariya ba.
Fushi yake don nayi masa nasiha yake faman daure fuska haka don yasan yayi laifi yana gudun naci gaba da fada.
Jin hakan yasa na dago kai da sauri ina kallon hjy don bansan me tayi mai fada a kai ba itama din ni take kallo kafin ta kawar da kai tana fadin .
Ni dai na fada mai gaskiya don kada yaga kamar amana wasane duk wanda yai sakaci da rikon amana zai fada ranan lahira.
Karfe hudu shaf na shirya don gudun kada inyi laifi a gareshi saida na dan zauna zaman jiran shi kafin ya fito daga part din shi.
Ina dakina kwance ina jiran fitowan shi ya shigo dakin tun daga nisa yake karewa kyakyawan surana kallo.
Kyakyawan suran kafafuwana da ya dan fito har zuwa sharaban kafana suna waje don yadda na kwanta din a lokacin.
Ya tsaya ya shagalta da kallon su saboda yadda ya hangosu sunyi bul bul dasu tankar bana taka kasa dasu a yanzu.
A hankali ya tako zuwa inda nake kwancen na shagalta da karatun wani littafi dana tsunta a gidan na labarai.
Banji shigowan shi ba dakin haka ma takon shi zuwa bakin gadon duk ban ji shi ba a lokacin.
Sai ji nayi girshi a na ja min rigar jikina daya tattare har zuwa sharabana dake waje tunda ni kadaine a dakin sai ban damu da hakan ba.
Wani irin zabura nayi lokaci guda ina kokarin sake ihu don nasan halimatu dai ba zatayi min wanan haukan haka ba.
Na juyo da wani irin sauri ya jafar na gani tsaye a kaina ya mayar da hannayen shi ya rungume saman kirjin shi.
Da sauri na yunkura na tashi zaune ina kokarin gyara rigan nawa ya sauka da kyau kafin in dago kai in jefeshi da wani irin fitinannen kallo.
Yace cikin daure fuska ki tashi mu tafi kina nan kwance lokaci yana kurewa gaki nan kwance ?
Yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin kai tsaye nima tashi nayi saida na gyara fuskana irin dabi,an mata kafin in fita na sameshi cikin mota zaune yana jiran fitowana.
Nayi mamakin ganin shi a gaba wurin mazaunin driver ke nan mu kadai zamu fita yau ba tare da kowa ba na tambayi kaina .
Kafin in iso ya
Showing 216001 words to 219000 words out of 390011 words
Nace am not your wife dan dama dama ka kirani da sister ka zaifi sauki garemu hakan .
Cikin daga hannu kada mama ta fahinci make faruwa a tsakanin mu yace dani to to naji dama aike kanwatace tunda ke din yar mamice.
Yana fadin haka ya mike don gudun kada asirin shi ya tonu a gaban mama da halimatu dake can zaune dan nisa damu.
Nan ya wuce ya barni zaune na tasa abinci a gaba ina kallo naji mama na fadin har zaka fita ke nan yau dai ka saka zainab karyawa da wuri haka.
Bata son cin abinci bansan meyasa hakan ba ta saba zama da rashin karyawa da wuri tun a gida.
Tun daga wanan ranan ya saka min ido kan karyawa da safe na dai gane yana neman wani hanya na dan shakuwane a tsakanina dashi don haka na kara shan nin jikina dashi.
Allah da ikon sa sai ga hjy an sallamota gida taji sauki sosai kamar ba ita bace akazo kasan da ita a tallabe.
Dawowan hjy gidan ya kara muna sakewa da an,nashuwa ko yaushe muna kusa da ita tana kara jan mu a jiki tare da bamu dariya da barkwanci kamar yadda muka saba a baya da ita a gidan mami kafin mu bar gidan.
Saidai tsakanin ya jafar da ya jamal har yanzu babu jittuwa a tsakanin su suna dai gaisawa sama sama a tsakanin su.
Tun hjy bata farga da har yanzu babu shiri a tsakanin su ba har yakai yanzu ta soma fahintar suna nan a yadda suke sai ta soma zargin akwai wani abu dake faruwa mai girma a tsakansu.
Babban abinda yafi damunta shine ni kaina ta fahinci irin zaman da mukeyi dashi na wasa da hankalin mutane gashi idan ta fambayeni sai ince mata lafiya muke zaune dashi.
Don haka tasha alwashin tambayana don jin irin zaman da mukeyi a tsakanin kafin shi ta tunkareshi tasan ba zata fahinci komai a bakin shi.
Ranan ya jamal zai fita da mama data matsa ya kaita wani shago daya bata labari nima nace zan bisu zuwa shagon muyi kallo.
Saida muka shirya hjy tace na zauna gida ba zamu barta a gida ita kadai ba badan naso na zauna din don naso fitan tunda a gaban yaya mukai maganan fitan har nace nima zan bisu y yarda.
Bayan fitan sune tasa na debo fruit muna na debo a cikin bowl biyu na shigo dashi falon hjy kan tana shan nata saidai ni na saka nawa a gaba sai wasa da spoon din hannuna nakeyi ina faman tunane.
Hjy ta aje cibin dake hannun ta ta tsura min idanu na dan wani lokaci sai ta lura ban ma san tana kallona ba a lokacin.
Abu lafiya kike kuwa shiru ban dago kai ba ta kara fadin Abu nace meke damuwan ki haka kike wanan tunane haka ?
Abu fa ta fada a karo na uku tana tafa hannayen ta idon ta a kaina firgigit na dawo a cikin hankakina ina dago kai tare da duban inda hjy take zaune.
Ni take kallo a cikin mamaki baiyane karara a fuskan ta kafin tace dani me kike tunane haka yar nan kinga mu kadai ne a gidan nan yanzu.
Ki saki jiki ki fada min abinda ke damun ki a rai ki dauka ni din mai baki shawaran da zai fitar dake daga hakin damuwan da kikene .
Ko yanzu kin daina daukana a matsayin kawarki jafari ya kwace min ke kin daina yayina sai shi kadai ?
Da sauri nace a, a hjy har gobe kina nan a matsayinki na kakata a zuciyana yanayin fuskana kawai ta kalla ta fahinci akwai wani abinda ke faruwa a tsakani mu da yayan.
Duk sai nabi na tsargu da irin kallon da take min a lokacin don haka sai na dukar da kaina kasa ina ci gaba da wasa da cibin dake hannuna.
Zainabu hjy ta sake kiran suna na dago kai a hankali ina amsawa da na,am tare dan kallon ta tace .
Kinga ki fada min meye damuwan ki da mijin ki kada ki boye min komai ki daukeni tankar nice na haifi mahaifiyar ki ko mahaifin ki.
Na dan gyada kai a hankali alaman gamsuwa a gareta kan abinda ta fada taci gaba da fadin tun zuwan mu ina kule da yanayin yadda kuke zaune dashi.
Nayi shiru na tsayin lokaci kaina na a duke a kasa ina dan guntun tunane anya zan iya fada mata matsalan mu kuwa ko banza fa itace ta haifi mahaifiyar shi.
Kuma ta nuna tafi son shi a cikin jikokin ta kaf idan na fada mata a wani yanayi tsohuwar zata shiga don jin jikan nata ashe mashayine na gaske.
Don haka na yanke shawaran fada mata wani abin na daban na dan dago kaina tare da fadin hjy bana cikin matsalan komai dashi
Ta dan tsura min ido na tsawon lokaci kafin tace kin tabbatar da hakan zainabu na gyada mata kai kawai sai naga tayi murmushi kadan a fuskanta kafin tace dani.
Amma ni ga dan nawa fahintar sai naga kamar har yanzu babu wani mu,amulan aure dake wakana a tsakanin ku illa kawai gaisuwa da dan kulawa a gaban mu koba haka bane zainabu ?
Da sauri na dago kai na kalleta sai kuma na dukar da idona saiga hawaye yana zubo min daga idanuwana lokaci guda.
Ai kinga irin ta zainabu ina son ki sani ni mace ce yar uwan ki kuma manya sunce kowa ya rigaka kwana yana rigaka tashi.
Hjy babu komai da dawani matsala ai zan sanar dake kawai dai ni karatu nake son inci gaba dashi yasa nake tunane na tsunci kaina da fadin haka a gareta.
Hjy ta kalleni ta girgiza kai tare da fadin to shike nan amma kada ki dawo da baya kina dakin sanin kin fada min gaskiyan da bakiyi ba.
Koda yake dai mai daki shiyasan inda ruwa ke masa yoyo ai idan kinfi bukatan ki tafi a hakan dake dashi aiga fili ga mai doki sai mu zuba ido mu gani zainabu.
Ban yarda abinda kika fada ba a yanzu domin ni nasan kin boye min ne kawai don kina daukana ta bangaren jafari nake.
Amma ni nasan da akwai abinda kike boye min a zuciyar ki namiki tambayan amsan daya ce ki bani sai baki ban ban ba kina kawo min wani zancen karatu.
Karatu kan ai dole kiyishi zainabu tunda kina auren wanda boka ya huda ko jiyan nan naji yana magana akan karatun ki har nace ya barki a nan basai kin koma gida kinyi a can ba nan kusa dashi zaifi mai saukin yawan sintirin da zaiyi idan kina can Nageria din.
Da sauri na dago kai a karo na barkatai na sauke kan hjyn don jin abinda ta fada na wai in zauna nan tare da yaya a kasan mutane inda bansan kowa ba.
Eh hakan nace kuma ya amince da hakan don haka idan zamu koma ba tare dake zamu tafi ba a nan zamu barki keda kanwarki.
Amma hjy da baki fada masa haka ba don shi kanshi yayan zaifi bukatan zamana a can gida da nan din ya dai amsa makine don baya iya mussata maki zancen ki gareshi .
Eh hakan yana da kyau tunda harkin fahinci hakan keda kanki sabanin ke da yanzu kika fara daukana a wani matsayi na daban.
Zainabu nasan ki nasan halinki don haka ban yarda da abinda kika fada ba a yanzu.
Domin ke kullun yar ba komai ne saidai duk wanda yasan ki ya dubeki a yanzu yasan da akwai matsala a tare dake zainabu.
Na dauka nice mutum ta farko da ko ban tambayeki ba zaki iya budan bkin ki ki fada min halinda kike ciki da mijin ki a gidan shi.
Tunda ninayi tsaye har wanan auren naku ya kullun a tsakanin ku saboda ni nasan halinki da nasa da kyau don ke yarinyace da bata gama mallakan hankalinta ba har yanzu.
Hawaye naji sun taru min a idanuna lokaci guda ina tausayawa kaina halin kuncin da nake ciki a wanan lokacin da abin zai fadu tabbas hjy kece ta farkon da zan fara fadawa wanan maganan a yanzu.
Amma a fili nace da sauri na mayar da hawayen nawa ban yarda sun digo a gabanta ba sainace hjy addu, a kawai zaki tayamu dashi a yanzu nan gaba idan bai daina ba zan fada maki insha Allahu.
Bayan ta dan tsura min ido tace to shike nan Allah yai maki albarka kin nuna min kedin mace ce ta gari mai rikon amnan mijinta ako wani hali ta tsunci kanta zata iya rike mai sirin sa a rayuwa.
Madalla dake zainabu insha Allahu hakkuri ki ba zai tabe a banza ba kici gaba da hakkuri da addua kuma kada ki yarda ki saka damuwa a ranki kinji.
Har muka bar wurin hjy tana min kallon tausayi don nasan tana da magana a zuciyar ta saidai ban bada daman hakan ba a lokacin.
To me zan fada mata ince ga yadda jikan ta yake ai saidai tajishi a bakin wani na sani ko in fada ta sake ribcewa ciwon dayafi wanda ta taso a yanzu.
Dakina na shiga cike da tunane na dan watsa ruwa tare da dauro alwala na fito na tayar da sallah azahar sai uku da rabi su mama suka dawo da sayyaya mai yawa tare dasu.
Ban fito ba don tunanen da nakeyi kan zancen mu da hjy ba abinda ya tsaya min a rai sai zancen karatuna da zanyi a nan .
Shike nan yanzu babu zancen komawa gida a garemu ke nan sai tsawon wani lokaci anya kuwa zan iya daurewa in zauna da wanan mashayin haka?
Idan na zauna a nan dagani sai shi ta yaya zan iya shawo kansa babu kowa nasa a kusa dashi irin ya jamal da zai saka mai ido kan abinda yakeyi tunda ni ba zaiji magana na ba.
Ya zama dole ke nan a gareni in kara jajircewa akan yadda zaman mu zai kasance a yanzu bayan tafiyan su hjy da mama.
Zan kuma kara sa mai ido inyi iya kokarina wurun rabashi da wanan halin da yardan ubangijin mu sai dai babban matsalana a yanzu shine rashin layin waya da banda shi a tare dani.
Don ina son muyi siri da malam mijin mai zube sai kuma matsalan anty fadila da nake son ya dawo da ita kusa dani don da taimakon ta zan iya samun nasaran abinda na dosa a yanzu.
A takw dabara ya fado min a rai nace da hjy ya kamata na hada wurin shawo kan shi ya yarda fadila ta dawo nan mu zauna tare da ita .
Ko abunuwa zasu zo min da sauki yadda nakeso don tafini sanin ta kan duniya ko naso yin abu bazan iya ba don hankalina baikai na hakan ba a yanzu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Ya fito daga wanka da safe ya samu wayan shi dake ajiye saman bedside din shi yana ringing yayi saurin kai hannun shi ya dauka kada ya katse.
Bakon lamba ya gani yayi kamar kada ya daga saidai ya daure ya dauka don baisan wanda ke kiranshi da wanan layin ba.
Don tsayin kwanaki biyu ke nan maishi yana yawan kiranshi a daidai wanan lokacin don haka maishi yasan shi kenan farin sani yasa ya kirashi a wanan lokaci .
Ya dauka da hello muryan taju ne akan layin ya fara magana da fadin nasan kayi fushi dani sosai yasa na kiraka na baka hakkuri don banzaci hakan zai faru ba ni kaina zafin kishine ya sakani yin hakan a lokacin.
Saida ya gama sauraren shi yake fadin ka dauka dolene nake tare dakai dama ko kuma bazan iya zama idan babu kaiba.
Taju ya saki wani dan ajiyan zuciya yace kayi hakkuri bana iya rayuwa idan bada kai ba boss kasa ka maye gurbin na da son wani bayan ni.
Hankalina a tashe yake tun ranan da haka ya faru a tsakanin mu kayi hakkuri ka rike kaunar dake tsakani da kai bana iya jure ganinka tare da wani kuna rayuwa ina kallo.
Ya jafar yayi murmushi a tausashe kafin yace taju ke nan kana sane kayi kokarin tona min asiri don kawai wani bakin kishin ka na banza can.
Taju ya katse shi yana fadin Iam sorry boss banyi haka a cikin hankalina ba a lokacin kasan irin son da nake maka a rayuwana.
Jafar din yaja wani uban tsoki tare da furta is too late now don na dade maye gurbin ka da wani so ka manta da wanan a tsakanin mu.
Yana fadin haka ya kashe wayan shi taju ya kalli wayan yaga ya kashe abinsa idon shi ya runtse yana jin wani zafin son jafar din na ratsa zuciyar shi lokaci guda.
Don tunda ya samu jafar ya bar sauran abokan harkan shi don jafar mutum ne har mutum yana da tabbacin idan jafar ya barshi rayuwan shi yana cikin gararari ke nan.
Shiko jafar din wayar ya jefar saman gado ya koma gefe ya zauna ya tallafi kanahi da hannayen sa biyu zuciyar sa tana masa azalzala.
Don shi yanzu zuciyar shi ta kasu biyu don yasan kirsis yake da asirin shi ya tonu muddin wanan yarinyar mai wayau na gidan nan.
Bai mu maganan zancen karatun mu ba ko zancen tafiya ai bada mu za a tafi ba asalima dai dan kwana biyun nan na kula da yana yawan daure fuskan shi ga kowa a gidan.
Ni hakan bai dameni ba tunda dama ba wani shakuwa bane tsakanin mu saidai abinda na zata ko hjy ta zauna dashine shima kamar yadda ta zauna dani tana bincikena kila shima sunyi hakan dashi.
Ranan dai da safe muna zaune a dakin hjy yake cewa mu shirya zamu fita karfe hudu na dauka badani yake magana ba saida ya kalloni yana fadin bakiji bane na dago kai ina fadin naji a sanyayye.
Daga inda hjy take zaune naji tace umhumm kawai tana dan kawar da kanta gefe daya daga barin kallon kowa a dakin.
Mama Ramatune tayi karfin halin da matarka zaka fita ko damu duk don kayi magana ta baibai bamu fahince ka ba gaskiya a nan ?
Da ita nake mama akwai inda zamu tafi tare yau ya bata amsa daga haka ya fice ya bar dakin hjy ta bishi da kallo tare da fadin miskilin banza kawai ya kama daure fuska kamar bai taba dariya ba.
Fushi yake don nayi masa nasiha yake faman daure fuska haka don yasan yayi laifi yana gudun naci gaba da fada.
Jin hakan yasa na dago kai da sauri ina kallon hjy don bansan me tayi mai fada a kai ba itama din ni take kallo kafin ta kawar da kai tana fadin .
Ni dai na fada mai gaskiya don kada yaga kamar amana wasane duk wanda yai sakaci da rikon amana zai fada ranan lahira.
Karfe hudu shaf na shirya don gudun kada inyi laifi a gareshi saida na dan zauna zaman jiran shi kafin ya fito daga part din shi.
Ina dakina kwance ina jiran fitowan shi ya shigo dakin tun daga nisa yake karewa kyakyawan surana kallo.
Kyakyawan suran kafafuwana da ya dan fito har zuwa sharaban kafana suna waje don yadda na kwanta din a lokacin.
Ya tsaya ya shagalta da kallon su saboda yadda ya hangosu sunyi bul bul dasu tankar bana taka kasa dasu a yanzu.
A hankali ya tako zuwa inda nake kwancen na shagalta da karatun wani littafi dana tsunta a gidan na labarai.
Banji shigowan shi ba dakin haka ma takon shi zuwa bakin gadon duk ban ji shi ba a lokacin.
Sai ji nayi girshi a na ja min rigar jikina daya tattare har zuwa sharabana dake waje tunda ni kadaine a dakin sai ban damu da hakan ba.
Wani irin zabura nayi lokaci guda ina kokarin sake ihu don nasan halimatu dai ba zatayi min wanan haukan haka ba.
Na juyo da wani irin sauri ya jafar na gani tsaye a kaina ya mayar da hannayen shi ya rungume saman kirjin shi.
Da sauri na yunkura na tashi zaune ina kokarin gyara rigan nawa ya sauka da kyau kafin in dago kai in jefeshi da wani irin fitinannen kallo.
Yace cikin daure fuska ki tashi mu tafi kina nan kwance lokaci yana kurewa gaki nan kwance ?
Yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin kai tsaye nima tashi nayi saida na gyara fuskana irin dabi,an mata kafin in fita na sameshi cikin mota zaune yana jiran fitowana.
Nayi mamakin ganin shi a gaba wurin mazaunin driver ke nan mu kadai zamu fita yau ba tare da kowa ba na tambayi kaina .
Kafin in iso ya
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73 Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131