Amai yayi sosai a wurin na kara rudewa kamar rayuwan shi zai dauke a lokacin duk ya fita cikin yanayin sa lokaci guda har halittan shi ya dan sauyawa ganina.
Nishi yakeyi sama sama can ya samu magana yazo mai da karfi yana fadin dauko wayana ki kira a kaini asibiti don Allah kada in mutu.
Da sauri na mike na nufi wurin gadon dakin ina neman wayan nashi a karkashin filo naga wayan na dauko ina tambayan shi wani nomba zan kira.
Mai 00 karshe ya fadi yana mayar da kanshi a kasa da alama sayin yake so sosai a lokacin ya ban tausayi matuka.
Kamar jira suke a kirasa baifi minti biyu ba sai gasu dakin da gagawan su suka daukemu zuwa asibitin.
Likitoci sunyi aune aune a kan aman da yake yi din basu gane dalilin aman ba, yan magunguna suka bashi tare da karin ruwa muka dawo masaukin mu dashi.
Duk ya zabge lokaci daya yayi wani irin rama mara ma,ana a jikin shi ko don ban taba ganin wani a irin wanan halin bane oho ?
Aman bawai ya tsaya bane ga baki daya don yana yinsa lokaci lokaci idan ya taso mai da kyat mukaga safe ranan dashi don a dakin nasa na kwana.
Washegari ya dan tashi da dama amma duk jikin shi ya sake bai ko iya tafiya sai da kyat da bin bango yake iya zuwa ban daki ya kewaya.
Har na gane yana tsunguni ranan ya dawo ya kwanta ina zaune na zuba mai ido cikin tashin hankali da tsoron abinda zai biyo bayan hakan a kanshi.
Wayan shi dake gefe yayi kuka na dan kalleshi idon shi a rufe baida niyar budewa balle ya dauka.
Har kiran ya katse wani ya kara shigowa sai nakai hannu na dauka sunan mami na gani da sauri nayi recieve kada ya kare katsewa irin na dazun.
Jafar lafiya banji ka kira ba tun jiya ta fada mami bashi bane gashi kwance baida lafiya tun jiya din na bata amsa .
A rude tace meya sameshi kuma zainab injin dai ba abin bane ya fara bashi matsala har muryan ta yana sarkewa a lokacin don rudewa.
Mami daga ciwon kaine sai ya koma amai da tsugunni a yau din jiya dai aman yakeyi kawai.
Yanzu kuna ina ne wai ta tambaya, nace muna nan Dubai munzo hutu ne last week kunje asibiti ko nace jiyan munje sun bashi magani muka dawo.
Barin fadawa mamud ko zai iya tasowa yau yazo idan zai samu jirgi a lokacin naji ya dan yi magana na juyo gareshi yana fadin
Kice ta barshi zamu koma chaina ne inje asibiti can likitana ya ganni a can din ba sai yazo ba.
Na fadawa mami din abinda yace nan ta fara fada hankali tashe nayi shiru ina saurarenta tana fadin zai dauki ciwo tundaga Dubai har zuwa chaina nan babu likitocine da zasu dubashi ?
Nikan karshe wayan na kara mashi a kunnen shi yana jin fadan da mami din takeyi a wayan yace a karshe mami na riga nayi booking ko zai gani da zaran mun isa can din.
Yau zamu koma insha Allah anyi booking din jirgin tafiyan mu a yau din don likitan shi yasan matsalana.
Ba zainab din waya muyi magana ta fada ya miko min wayan tace zainab don Allah idan kun isa kinga abin bai tsaya ba ki kira mu ki fada muna halin da ake ciki .
Murya na rawa nace tau mami insha Allahu ki kula dashi sosai don Allah zainab nasan halin jafar da gardama kada ki daka ta nasa don Allah.
Ni yanzu idan mami tana min magana sai abin ya dinga ban mamaki balle yanzu da har mami din taji wai muna dubai da danta bansha zagi da sheri ba.
Wai har da danka min kula da dan nata a hannuna tana wani hadani da Allah can bayan ta gama min cin fuska a baya.
Don darajana da kima baikai na wace zata shiga cikin wanan daulan ba na danta iya abinda mami ke nufi dani ke nan ba wani abu ba.
Amma yanzu data ga dan nata yana da mugun tabo masu yawa da kyama a rayuwan shi shine take kokarin nuna min cewa tana sona a cikin ahalin ta a yanzu.
Idona na runtse wasu hawaye masu dumi suna zobo min meta fada maki daya sakaki kuka a yanzu muryan shine cikin sanyin murya yake min wanan tambayan.
Ban iya bashi amsa ba sai mikewa da nayi don barin dakin da sauri kada ki fita ki barni haka a cikin wanan halin da nake ya fada.
Ja nayi na tsaya wuri daya ban kara gusawa ba daga inda nake tsaye din yaci gaba da fadin banji ta fada maki wani abinda zai sakaki kuka haka har ki fushi ki fita ba ki barni ni kadai ina cikin wanan halin.
Don koma ta fada maki bazan yarda da hakan ba kema kin sani don haka ki dawo ki zauna har na dan kara jin karfin jikin nawa.
Zan je na fara shiri ne na bashi amsa ba tare dana juyo inda yake ba nake magana ina kokarin fita duk da ya hanani ina son kebewa inda zanyi kuka ma,ishina ba wanda zai hanani a yanzu.
Bina yayi da kallo har na bace mai da gani kafin ya sauke ajiyan zuciya yana runtse ido cikin takaici don shidai ya rasa meyasa ni kuka a cikin wanan maganan kuma ?
Ban iya zama dakin ba don halin dana barshi a ciki koda na koma na samu ya fito ban daki ya zauna a kofan don bai iya karasowa cikin dakin da kafafun shi a lokacin.
Nan kan hankalina ya tashi sosai don sai dana kamashi ya koma saman gado ya kwanta na shiga fadi a raina shike nan nine zanyi ajalin yaya ke nan ashe ?
Kofa aka buga don shigowa na mike na bude kofan wasu mutum biyu ne na sama a wurin tsaye suke tambayana shi na nuna masu ciki da hannu suka shiga.
Ashe likitane da wani abokin shi suka shigo basu fita ba saida aka daura mai ruwa da sauran magani sai gashi ya samu karfi har sallah naga yayi a tsaye bayan fitan su.
A lokacin hankalina ya fara dan kwantawa don ganin ya soma samun lafiya a jikin shi yanzu dama ni tsorona shine kada ya halaka a sanadiyar maganin da na zuba mai wani abu yazo ya same shi kuma.
Karfe takwas na dare muka bar cikin hotel din mun dan jira kafin jirgin ya tashi zuwa tara na dare muka bar kasan zuwa chaina.
Muna isa asibiti aka wuce dashi daga can duk gwaji likitan yace shi baiga courses din ciwon nasa ba sai dai idan wani abu yasha na daban da ya jawo mashi hakan.
Sai dai nan din sun kwatar dashi na kwana biyu kafin su sallamoshi ya dawo gida ya karasa jinya a gida kuma yana shan magani.
Bashi dake jinyar ba koni na rame sosai don ciwon nasa ya daga mi hankali amma yanzu da naga ya dawo normal na fara sake jikina nima.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DON SAUKE HAKKIN WANI A KANKI, , ,
Alhamdullahi zan iya cewa don jikin yaya yayi sauki sosai kuma ina bashi kulawan daya dace sosai a matsayina na sunan matar shi.
Yar uwan shi kuma mafi kusa dashi a yanzu haka yasa na zage sosai wurin kula dashi din don shima a iya yin shi gaskiya yana nasa kokarin damu tankar yan uwansa na jini.
Don haka naba kaina shawara dama kuma kinsan mace ga rauni da sanyi hali a wurin namiji nima hakan ne yaci don shi kanshi saida yayi mamakin yadda nake bashi kulan a lokacin.
Ba tare da wani jin komai ba tsakani da Allah nake masa komai yadda ya kamata don shi kanshi ya fahinci hakan.
Safiyane yau na shirya cikin wani riga ja na daure kaina da ribon mai ja shima da farin duwatsu.
Dan gyale ja na dora saman kaina sai dai bawai rufe kai din nayi ba sosai sai kamshi da jikina keyi a lokacin .
Dakin na part din shi na nufa don gaida shi da kwana akwance na hango shi ya kurawa silling din dakin ido kamar mai tunane.
Kamar yadda na saba idan ni nazo gaidashi da kwana bashi ya sameni a zaune part dina ba.
Jin motsina baisa ya motsa a yadda na riskeshi ba har nakai bakin gadon na gurfa gwiwa bibiyu ina fadin yaya ina kwana ya karfin jikin kuma ?
Zainab na dago kai na kallo shi sai kuma naga ya danyi gajeren murmushi ya kawar da kanshi daga inda yake kallo.
Haka sai yasani tsarguwa da yadda yai min din ina a yadda nake ban motsa ba nayi shiru shima hakan baiko amsa min gaisuwan da nayi masa ba na safen dana
saba zuwa part din in gaida shi don da sadiya mukan zo gaidashi din ranan kuma ni daya nazo.
Sai can nace dashi a hada ruwan wankane ka watsa yanzu na fada ina kallon shi don jin amsan da zan bashi.
Ki hada nima ina son inyi wanka yau in dan fita tunda naji sauki sosai mikewa nayi zuwa ban dakin na hada mai ruwa kamar yadda yake son yi dashi tun ranan farko daya fada min yadda zan hada mai din.
Na hado ruwan na dawo na fada mai zan bar part din tunda ba wai wani hira mai tsawone irin na mata da miji a tsakanin mu ba dama.
Muryan shi ke fadin sai ki fitar min da tufafin da zan saka idan na fito tunda yanzu naga zaki fara aikin ki na mata a gareni.
Wani irin juyowa nayi ina kallon shi a cikin mamaki a fuskana don jin abinda ya fada din gareni.
Ba matsayin mata ya saka nake maka wanan ba a matsayi kanwa a gareka da kuma Allah nake maka komai don ka cancanci hakan a gareni .
Ina fadan hakan na sa kai na fice daga dakin don jin da nayi yace fita zaiyi a lokacin da ba haka ba idan na shigo bana fita haka zan zauna a wurin shi.
Duk da ba wani magana mai tsawo ko hira a tsakanin mu saidai kowa yayi sha,anin gaban shi a dakin ko ina tunane ko taba waya wanda hakan yakan daukeni wani lokaci mai tsawo a wurin shi.
Wanda bai sani ba sai ya dauka wani hiran arzikine ko wani abin miji da mata ya tsayar damu a cikin dakin lokacin.
Alhamdullahi gaskiya don jikin nasa yayi sauki sosai saidai da alama har yanzu baya jin karfin jikin nasa ko kadan.
Karfin hali irin na mazane kawai yakeyi yana fita don kada ya zauna don da mace ce nasan har lokacin nan tana kwance tana fama da jikin ta.
Saidai wani abin dana dan kula dashi a yanzu shine irin kallon da yaya yakan min wani lokaci kallo ne mai tare da ma,ana iri daban daban.
Na kasa fahintar dalilin hakan da yake min wani lokaci idan zamu hada ido dashi zaiyi saurin kawar da idon shi gareni.
Gashi a yanzu ya dora min nauyin hada mai ruwan wankan shi duk safiya duk da komai a hade yake amma dole sai naje na hada mai zai tashi yayi.
Haka cin abincin sa dole ina wurin har ya gama zamu tashi duk da ba wani hira tsakanin mu a lokacin.
Ga mami da ke kira yanzu kamar ta bude ido ta ganta a kasan takeji don zata kira akalla sau uku a rana tana jin halin da muke ciki a nan.
Wanda wanan kiran har ya soma samin zarginta kan dan nata watay ita duk abinda yakeyi ma bata ganin laifin shi ashe ga hakan don yadda naga ta damu da halin da yake a yanzu.
Har take fadin idan azumi yazo zasu shigo su ganshi su danyi azumi tare damu suna jiran Aisha ta karasa karatun tane aiyi bukin yayye su yasa basu zo a yanzu ba.
Tabdi ba zuwan mami din ba sai irin takura min da sukeyi idan sun zo da fanin laifina ko kyashin da baya boyuwa a fuskokin su.
Shiko cewa yayi yana farin cikin da zuwan su indai zasu zo din suyi azumin a tare damu zaiji dadin hakan..
A raina nace tunda kai da uwarka baku da matsala duk tudun laifin ka bata ganin hakan gareka sai ma so da take nuna maka zallah ai kace kana farin ciki da hakan .
Muryan shine ke fadi yana kallona yace zainab na san kema zaki fini jin dadin hakan tunda yanzu naga naku da mami din yanzo daya har tana maki sako a boye ko ?
Ban sani ba don wani aiki sai mami na sani da sauri na dago kai na kalleshi tare da fadi cikin mamaki sako kuma ?
Daga wurin mami yaushe mami tayi min sako dana zo kasan nan idan ma har mami zata aiko min wani abu ai ta hannun ka abin zai fito.
Hakane fa kuma ya fada yana murmushi yana batun mikewa tsaye na sake fadin sai dai idan ka manta baka ban sakon ba yana hannun ka ?
Banjin yana a hannu na gaskiya sai dai idan na manta nima nake ganin kamar ke ra aikowa anywhere forget it ba damuwa.
Bayan shi nabi da kallo har ya fice kafin in tabe baki ina mayar da kaina ga kujeran da nake zaune tare da lumshe idanuwa na nadan lokaci.
Tunda mami ta furta zata zo yake shirin zuwan su din duk da bai fads ba nasan abinda yasa ake wasu yan gyare gyare a gidan wanda ya dace.
Dare ne naga bai shigo ba yasa na shiga part din shi tunda nasan yana gidan bai fitan nan da yakeyi a baya yanzu ya daina tunda yayi ciwo baya yawan fita koda rana da ya dawo office yana gida sai kuma gobe idan ya fita.
Wando ne da riga tie a jikina baki rigar kuma yellow mai dan fadi wuyan shi ma da fadi sosai.
Sai dai rigan ya dan sauka ya rufe min mazauna na rabi kayan sun matukar karban jikina sosai sun dane min jiki da kyau.
A falon shi na saneshi zaune da kwalba da cup a gaban shi ya zauna ya mike kafafun shi saman karamin table din dake gabab shi .
Yayin da dukkan maballeyan riganshi suke bude mashi duk chest din shi a waje ya dafe kanshi da hannun shi daya kamar mai barci.
A hankali na tako zuwa inda yake zaune ganin kamar yana barci yasa dana kare mai kallo nake batun juyawa na bar dakin.
Ina zaki kin shigo kuma zaki fita yana sauke hannun shi data dafe goshin shi yake fadin hakan .
Kallon kwalban da cup nayi na turo baki kafin nace naga kamar yau dakin yafi karfin shigana ai don naga kamar ka gama warkewa yanzu.
Dan murmushi yayi yana gyara zama tare da fadin zoki zauna a nan mu sha tare don na yau din tare zamu sha dake ai.
Wa ni na fada har ina nuna kaina da hannuna nace Allah ya tsare ya kareni don ni na zabi na Allah da wanan na nuna da bakina inda kwalban yake.
Kanshi ya dan mayar ga makarin kujeran ya lumshe idanun shi a hankali yace yana taba wurin da yake zaune ta gefe zo zauna a nan nace maki ko ?
Kallin shi nayi kamar in tafi nake ji sai kuma wata zuciya tace min naga iya gudun shi ga hakan sai na tako na zauna kamar yadda yace min din.
Na zauna a dan takure ban sake jikina ba da zaman ya dago yana zuba abin a cikin kofi ya miko min yana fadin karba ki dan sha.
Wani kallo nayi mai ina kawar da kaina gefe daya nake fadin har abin yakai can yaya ka koya min shan wanan haramiyan abin ?
Dauki kwalban ki karanta idan na cutarwane na baki yana komawa yadda na sameshi da farko saman kujeran.
Ban karba sai mikewan da nayi na fice part din ga baki daya raina a bace ina tunanen irin halin yaya da abin haram ba komai bane a gareshi shi ?.
Har ni yakecewa yau wai nasha giya a tare dashi don kawai ya mayar dani yarinya ko me ?
Ko wawiya ya daukeni ko bakyauya har yanzu ban san komai ba kan hakan har yake kokarin juyani ga halaka.
Ranan banyi barci ba sai na daman sanin sa da nayi ga baki daya ina jin wani irin tsanar shi yana karuwa a zuciyana lokaci guda.
Showing 282001 words to 285000 words out of 390011 words
Nishi yakeyi sama sama can ya samu magana yazo mai da karfi yana fadin dauko wayana ki kira a kaini asibiti don Allah kada in mutu.
Da sauri na mike na nufi wurin gadon dakin ina neman wayan nashi a karkashin filo naga wayan na dauko ina tambayan shi wani nomba zan kira.
Mai 00 karshe ya fadi yana mayar da kanshi a kasa da alama sayin yake so sosai a lokacin ya ban tausayi matuka.
Kamar jira suke a kirasa baifi minti biyu ba sai gasu dakin da gagawan su suka daukemu zuwa asibitin.
Likitoci sunyi aune aune a kan aman da yake yi din basu gane dalilin aman ba, yan magunguna suka bashi tare da karin ruwa muka dawo masaukin mu dashi.
Duk ya zabge lokaci daya yayi wani irin rama mara ma,ana a jikin shi ko don ban taba ganin wani a irin wanan halin bane oho ?
Aman bawai ya tsaya bane ga baki daya don yana yinsa lokaci lokaci idan ya taso mai da kyat mukaga safe ranan dashi don a dakin nasa na kwana.
Washegari ya dan tashi da dama amma duk jikin shi ya sake bai ko iya tafiya sai da kyat da bin bango yake iya zuwa ban daki ya kewaya.
Har na gane yana tsunguni ranan ya dawo ya kwanta ina zaune na zuba mai ido cikin tashin hankali da tsoron abinda zai biyo bayan hakan a kanshi.
Wayan shi dake gefe yayi kuka na dan kalleshi idon shi a rufe baida niyar budewa balle ya dauka.
Har kiran ya katse wani ya kara shigowa sai nakai hannu na dauka sunan mami na gani da sauri nayi recieve kada ya kare katsewa irin na dazun.
Jafar lafiya banji ka kira ba tun jiya ta fada mami bashi bane gashi kwance baida lafiya tun jiya din na bata amsa .
A rude tace meya sameshi kuma zainab injin dai ba abin bane ya fara bashi matsala har muryan ta yana sarkewa a lokacin don rudewa.
Mami daga ciwon kaine sai ya koma amai da tsugunni a yau din jiya dai aman yakeyi kawai.
Yanzu kuna ina ne wai ta tambaya, nace muna nan Dubai munzo hutu ne last week kunje asibiti ko nace jiyan munje sun bashi magani muka dawo.
Barin fadawa mamud ko zai iya tasowa yau yazo idan zai samu jirgi a lokacin naji ya dan yi magana na juyo gareshi yana fadin
Kice ta barshi zamu koma chaina ne inje asibiti can likitana ya ganni a can din ba sai yazo ba.
Na fadawa mami din abinda yace nan ta fara fada hankali tashe nayi shiru ina saurarenta tana fadin zai dauki ciwo tundaga Dubai har zuwa chaina nan babu likitocine da zasu dubashi ?
Nikan karshe wayan na kara mashi a kunnen shi yana jin fadan da mami din takeyi a wayan yace a karshe mami na riga nayi booking ko zai gani da zaran mun isa can din.
Yau zamu koma insha Allah anyi booking din jirgin tafiyan mu a yau din don likitan shi yasan matsalana.
Ba zainab din waya muyi magana ta fada ya miko min wayan tace zainab don Allah idan kun isa kinga abin bai tsaya ba ki kira mu ki fada muna halin da ake ciki .
Murya na rawa nace tau mami insha Allahu ki kula dashi sosai don Allah zainab nasan halin jafar da gardama kada ki daka ta nasa don Allah.
Ni yanzu idan mami tana min magana sai abin ya dinga ban mamaki balle yanzu da har mami din taji wai muna dubai da danta bansha zagi da sheri ba.
Wai har da danka min kula da dan nata a hannuna tana wani hadani da Allah can bayan ta gama min cin fuska a baya.
Don darajana da kima baikai na wace zata shiga cikin wanan daulan ba na danta iya abinda mami ke nufi dani ke nan ba wani abu ba.
Amma yanzu data ga dan nata yana da mugun tabo masu yawa da kyama a rayuwan shi shine take kokarin nuna min cewa tana sona a cikin ahalin ta a yanzu.
Idona na runtse wasu hawaye masu dumi suna zobo min meta fada maki daya sakaki kuka a yanzu muryan shine cikin sanyin murya yake min wanan tambayan.
Ban iya bashi amsa ba sai mikewa da nayi don barin dakin da sauri kada ki fita ki barni haka a cikin wanan halin da nake ya fada.
Ja nayi na tsaya wuri daya ban kara gusawa ba daga inda nake tsaye din yaci gaba da fadin banji ta fada maki wani abinda zai sakaki kuka haka har ki fushi ki fita ba ki barni ni kadai ina cikin wanan halin.
Don koma ta fada maki bazan yarda da hakan ba kema kin sani don haka ki dawo ki zauna har na dan kara jin karfin jikin nawa.
Zan je na fara shiri ne na bashi amsa ba tare dana juyo inda yake ba nake magana ina kokarin fita duk da ya hanani ina son kebewa inda zanyi kuka ma,ishina ba wanda zai hanani a yanzu.
Bina yayi da kallo har na bace mai da gani kafin ya sauke ajiyan zuciya yana runtse ido cikin takaici don shidai ya rasa meyasa ni kuka a cikin wanan maganan kuma ?
Ban iya zama dakin ba don halin dana barshi a ciki koda na koma na samu ya fito ban daki ya zauna a kofan don bai iya karasowa cikin dakin da kafafun shi a lokacin.
Nan kan hankalina ya tashi sosai don sai dana kamashi ya koma saman gado ya kwanta na shiga fadi a raina shike nan nine zanyi ajalin yaya ke nan ashe ?
Kofa aka buga don shigowa na mike na bude kofan wasu mutum biyu ne na sama a wurin tsaye suke tambayana shi na nuna masu ciki da hannu suka shiga.
Ashe likitane da wani abokin shi suka shigo basu fita ba saida aka daura mai ruwa da sauran magani sai gashi ya samu karfi har sallah naga yayi a tsaye bayan fitan su.
A lokacin hankalina ya fara dan kwantawa don ganin ya soma samun lafiya a jikin shi yanzu dama ni tsorona shine kada ya halaka a sanadiyar maganin da na zuba mai wani abu yazo ya same shi kuma.
Karfe takwas na dare muka bar cikin hotel din mun dan jira kafin jirgin ya tashi zuwa tara na dare muka bar kasan zuwa chaina.
Muna isa asibiti aka wuce dashi daga can duk gwaji likitan yace shi baiga courses din ciwon nasa ba sai dai idan wani abu yasha na daban da ya jawo mashi hakan.
Sai dai nan din sun kwatar dashi na kwana biyu kafin su sallamoshi ya dawo gida ya karasa jinya a gida kuma yana shan magani.
Bashi dake jinyar ba koni na rame sosai don ciwon nasa ya daga mi hankali amma yanzu da naga ya dawo normal na fara sake jikina nima.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DON SAUKE HAKKIN WANI A KANKI, , ,
Alhamdullahi zan iya cewa don jikin yaya yayi sauki sosai kuma ina bashi kulawan daya dace sosai a matsayina na sunan matar shi.
Yar uwan shi kuma mafi kusa dashi a yanzu haka yasa na zage sosai wurin kula dashi din don shima a iya yin shi gaskiya yana nasa kokarin damu tankar yan uwansa na jini.
Don haka naba kaina shawara dama kuma kinsan mace ga rauni da sanyi hali a wurin namiji nima hakan ne yaci don shi kanshi saida yayi mamakin yadda nake bashi kulan a lokacin.
Ba tare da wani jin komai ba tsakani da Allah nake masa komai yadda ya kamata don shi kanshi ya fahinci hakan.
Safiyane yau na shirya cikin wani riga ja na daure kaina da ribon mai ja shima da farin duwatsu.
Dan gyale ja na dora saman kaina sai dai bawai rufe kai din nayi ba sosai sai kamshi da jikina keyi a lokacin .
Dakin na part din shi na nufa don gaida shi da kwana akwance na hango shi ya kurawa silling din dakin ido kamar mai tunane.
Kamar yadda na saba idan ni nazo gaidashi da kwana bashi ya sameni a zaune part dina ba.
Jin motsina baisa ya motsa a yadda na riskeshi ba har nakai bakin gadon na gurfa gwiwa bibiyu ina fadin yaya ina kwana ya karfin jikin kuma ?
Zainab na dago kai na kallo shi sai kuma naga ya danyi gajeren murmushi ya kawar da kanshi daga inda yake kallo.
Haka sai yasani tsarguwa da yadda yai min din ina a yadda nake ban motsa ba nayi shiru shima hakan baiko amsa min gaisuwan da nayi masa ba na safen dana
saba zuwa part din in gaida shi don da sadiya mukan zo gaidashi din ranan kuma ni daya nazo.
Sai can nace dashi a hada ruwan wankane ka watsa yanzu na fada ina kallon shi don jin amsan da zan bashi.
Ki hada nima ina son inyi wanka yau in dan fita tunda naji sauki sosai mikewa nayi zuwa ban dakin na hada mai ruwa kamar yadda yake son yi dashi tun ranan farko daya fada min yadda zan hada mai din.
Na hado ruwan na dawo na fada mai zan bar part din tunda ba wai wani hira mai tsawone irin na mata da miji a tsakanin mu ba dama.
Muryan shi ke fadin sai ki fitar min da tufafin da zan saka idan na fito tunda yanzu naga zaki fara aikin ki na mata a gareni.
Wani irin juyowa nayi ina kallon shi a cikin mamaki a fuskana don jin abinda ya fada din gareni.
Ba matsayin mata ya saka nake maka wanan ba a matsayi kanwa a gareka da kuma Allah nake maka komai don ka cancanci hakan a gareni .
Ina fadan hakan na sa kai na fice daga dakin don jin da nayi yace fita zaiyi a lokacin da ba haka ba idan na shigo bana fita haka zan zauna a wurin shi.
Duk da ba wani magana mai tsawo ko hira a tsakanin mu saidai kowa yayi sha,anin gaban shi a dakin ko ina tunane ko taba waya wanda hakan yakan daukeni wani lokaci mai tsawo a wurin shi.
Wanda bai sani ba sai ya dauka wani hiran arzikine ko wani abin miji da mata ya tsayar damu a cikin dakin lokacin.
Alhamdullahi gaskiya don jikin nasa yayi sauki sosai saidai da alama har yanzu baya jin karfin jikin nasa ko kadan.
Karfin hali irin na mazane kawai yakeyi yana fita don kada ya zauna don da mace ce nasan har lokacin nan tana kwance tana fama da jikin ta.
Saidai wani abin dana dan kula dashi a yanzu shine irin kallon da yaya yakan min wani lokaci kallo ne mai tare da ma,ana iri daban daban.
Na kasa fahintar dalilin hakan da yake min wani lokaci idan zamu hada ido dashi zaiyi saurin kawar da idon shi gareni.
Gashi a yanzu ya dora min nauyin hada mai ruwan wankan shi duk safiya duk da komai a hade yake amma dole sai naje na hada mai zai tashi yayi.
Haka cin abincin sa dole ina wurin har ya gama zamu tashi duk da ba wani hira tsakanin mu a lokacin.
Ga mami da ke kira yanzu kamar ta bude ido ta ganta a kasan takeji don zata kira akalla sau uku a rana tana jin halin da muke ciki a nan.
Wanda wanan kiran har ya soma samin zarginta kan dan nata watay ita duk abinda yakeyi ma bata ganin laifin shi ashe ga hakan don yadda naga ta damu da halin da yake a yanzu.
Har take fadin idan azumi yazo zasu shigo su ganshi su danyi azumi tare damu suna jiran Aisha ta karasa karatun tane aiyi bukin yayye su yasa basu zo a yanzu ba.
Tabdi ba zuwan mami din ba sai irin takura min da sukeyi idan sun zo da fanin laifina ko kyashin da baya boyuwa a fuskokin su.
Shiko cewa yayi yana farin cikin da zuwan su indai zasu zo din suyi azumin a tare damu zaiji dadin hakan..
A raina nace tunda kai da uwarka baku da matsala duk tudun laifin ka bata ganin hakan gareka sai ma so da take nuna maka zallah ai kace kana farin ciki da hakan .
Muryan shine ke fadi yana kallona yace zainab na san kema zaki fini jin dadin hakan tunda yanzu naga naku da mami din yanzo daya har tana maki sako a boye ko ?
Ban sani ba don wani aiki sai mami na sani da sauri na dago kai na kalleshi tare da fadi cikin mamaki sako kuma ?
Daga wurin mami yaushe mami tayi min sako dana zo kasan nan idan ma har mami zata aiko min wani abu ai ta hannun ka abin zai fito.
Hakane fa kuma ya fada yana murmushi yana batun mikewa tsaye na sake fadin sai dai idan ka manta baka ban sakon ba yana hannun ka ?
Banjin yana a hannu na gaskiya sai dai idan na manta nima nake ganin kamar ke ra aikowa anywhere forget it ba damuwa.
Bayan shi nabi da kallo har ya fice kafin in tabe baki ina mayar da kaina ga kujeran da nake zaune tare da lumshe idanuwa na nadan lokaci.
Tunda mami ta furta zata zo yake shirin zuwan su din duk da bai fads ba nasan abinda yasa ake wasu yan gyare gyare a gidan wanda ya dace.
Dare ne naga bai shigo ba yasa na shiga part din shi tunda nasan yana gidan bai fitan nan da yakeyi a baya yanzu ya daina tunda yayi ciwo baya yawan fita koda rana da ya dawo office yana gida sai kuma gobe idan ya fita.
Wando ne da riga tie a jikina baki rigar kuma yellow mai dan fadi wuyan shi ma da fadi sosai.
Sai dai rigan ya dan sauka ya rufe min mazauna na rabi kayan sun matukar karban jikina sosai sun dane min jiki da kyau.
A falon shi na saneshi zaune da kwalba da cup a gaban shi ya zauna ya mike kafafun shi saman karamin table din dake gabab shi .
Yayin da dukkan maballeyan riganshi suke bude mashi duk chest din shi a waje ya dafe kanshi da hannun shi daya kamar mai barci.
A hankali na tako zuwa inda yake zaune ganin kamar yana barci yasa dana kare mai kallo nake batun juyawa na bar dakin.
Ina zaki kin shigo kuma zaki fita yana sauke hannun shi data dafe goshin shi yake fadin hakan .
Kallon kwalban da cup nayi na turo baki kafin nace naga kamar yau dakin yafi karfin shigana ai don naga kamar ka gama warkewa yanzu.
Dan murmushi yayi yana gyara zama tare da fadin zoki zauna a nan mu sha tare don na yau din tare zamu sha dake ai.
Wa ni na fada har ina nuna kaina da hannuna nace Allah ya tsare ya kareni don ni na zabi na Allah da wanan na nuna da bakina inda kwalban yake.
Kanshi ya dan mayar ga makarin kujeran ya lumshe idanun shi a hankali yace yana taba wurin da yake zaune ta gefe zo zauna a nan nace maki ko ?
Kallin shi nayi kamar in tafi nake ji sai kuma wata zuciya tace min naga iya gudun shi ga hakan sai na tako na zauna kamar yadda yace min din.
Na zauna a dan takure ban sake jikina ba da zaman ya dago yana zuba abin a cikin kofi ya miko min yana fadin karba ki dan sha.
Wani kallo nayi mai ina kawar da kaina gefe daya nake fadin har abin yakai can yaya ka koya min shan wanan haramiyan abin ?
Dauki kwalban ki karanta idan na cutarwane na baki yana komawa yadda na sameshi da farko saman kujeran.
Ban karba sai mikewan da nayi na fice part din ga baki daya raina a bace ina tunanen irin halin yaya da abin haram ba komai bane a gareshi shi ?.
Har ni yakecewa yau wai nasha giya a tare dashi don kawai ya mayar dani yarinya ko me ?
Ko wawiya ya daukeni ko bakyauya har yanzu ban san komai ba kan hakan har yake kokarin juyani ga halaka.
Ranan banyi barci ba sai na daman sanin sa da nayi ga baki daya ina jin wani irin tsanar shi yana karuwa a zuciyana lokaci guda.
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95 Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131