kayiwa mutane wayau zakaiwa Allah wayau ne ?
Ina zaka da alhakin wanan yarinyar da kake cutarwa a rayuwan ka ai gara ka saketa ka zauna kaita aikata sabon Allah ka zaifi ma sauki.
Jamal ni kake fadawa magana haka kai tsaye me kake tunanen ka taka a yanzu naji jamal din na fadin Allah .
Niko ya mamud ya sake hanyar Allah zan fada mashi gaskiya a yanzu balle kai da muke da shakuwa dakai ina zaka kai Alhakin iyayyen mu a kanka ga irin tarbiyan da suka bamu a baya.
Kudi ko ilimi ba hauka bane bazan fadawa kowa wanan abin ba zan dai tayaka addua idan kana da rabo a wurin Allah Allah yasa ka daina wanan harkan daga haka naji ya fita ya gaura kofan falon yafice daga part din.
Da sauri na koma saman gado na dafe bakina don kada sautin hawayena a fito fili sai can naji kamar ana taba kofan dakin Allah yasa ban yarda in kwanta ban sakawa kofan key ba har mai tabawan ya gaji ya daina tabawa.
Washe gari har na fito kamar mai sanda a falo na samu ya jamal a zaune yayi tagumi jin motsin fitowan yasa shi dago kai ya kalli kofan da yaji an taba din.
Mukai arba dashi a dan rikicewa nayi sai naga ya kawar da kanshi daga kallo hakan ya bani daman shigewa dakina dana bude hannuna na rawa kai tsaye na fada ciki.
Sauke numfashi nayi a hankali kamar wata barauniya da aka kama a lokacin nikan na shiga uku na fada a fili .
Ban yarda na fito ba sai wani lokaci dana kwatanci ya jafar ya bar gidan a lokacin na fito na rame sosai don damuwa da nake ciki a yan kwanaki nayi wani irin fari sosai saidan wuyan dan aje.
Yunwa ya fito dani babu kowa a falon duk da nayi mamakin rashin ganin halimatu yau da banyi ba wurin dining na nufa na hada ruwan shayi babu madara don bakina da nake jin shi babu dadi a ranan kamar na kwanta ciwo da dadewa.
Babu abinda nake tunane tun daren ranan sai kakamin ya jamal din ga dan uwan shi ina kuma tambayan kaina wani abune yaya jafar yakeyi boyayye da ba wanda yasan wanan abin.
Kisha tea din kada yai sanyi mana kin zauna kina tunane ke kadai a nan da sauri na dago idanu ina saukewa a kanshi.
A cikin daurewa nake gaidashi da ya jamal ina kwana saida ya zauna yake amsa min da lafiya zainab ya kika tashi ya bakunta kuma lafiya na fada ina dukar da kai kasa.
Zainab kisha kada tean yayi sanyi ya kara fadan hakan gareni da sauri kamar mai jiran umurnin shi na dauki cup din na fara kurba a hankali.
Mama Ramatu ne ta fito daki tana dan dariya halimatu na bayan ta tana fadin wanan yar akwaiki da wayau tsiya wallahi.
Dago kai mukayi muna kallon su har suka karasu inda muke na aje cup din hannuna a hankali tare da zamewa saman kujera ina gaida ita kamar yadda na saba a kullun.
Ta amsa min a cikin fara, a kafin tace dani lafiya kike kuwa yau naga kin rame lokaci guda haka ko wani abinne ya sameki kuma anya kuwa zainab ba shigan ciki ke gareki ba ?
Da sauri ya jamal ya dan kalleni sai kuma ya kawar da kanshi daga kallona sai naji na tsargu da wanan maganan bandai yi magana ba ina zaune na tasa kofin shayina a gaba ina dan wasa da bakin kofin a hankali.
Takon shine ya mayar da hankalinsu ga kofan part din shi yana saye a cikin kananin kaya da suka fitar mai da suran jikin shi har kurciyar shi ya kara baiyana a fili zakace ko dan shekara ashirin zuwa samane a lokacin.
Ya iso gurin tare da fadin mama an tashi lafiya cikin girmamawa a gareta ta amsa mai da fara,a tana fadin yanzu nake zance da matar ka kodai rabo ya shigane bamu sani ba gata sai faman rama takeyi haka a tsaye.
Da wani irin mamaki yace ciki a dan zabure sai kuma ya mike tsaye yana kallona a cikin mamaki yake fadin mama ciki ga zainab din ?
Kana mamakin hakan ne ga macen aure yanzu fa shekara da kusan rabi da aurenku meye abin wani mamakin hakan a nan Allah ya ingatar kawai musha buki wanda ka hanamuyi da aure sai muyi shi a sunan baby.
Kai mama bata dai da lafiya ne tace yanzu take fada min da dan zazzabi ta kwana jiya nace kila gajiyan tafiyane yaja mata hakan.
Amma kuna da abin dariya wallahi wai me kuke mamaki a hakanne gun matar aure har zaku tsaya wani zance ko baka shiryawa haihuwan bane a yanzu kana dabi,an ku na turawa.
Gyara zama yayi yana fadin kai haba mama har guda nawa wanan yarinyar take da zata haihu a yanzu at list dai ta kara yan shekaru nan gaba kafin ta haihu.
A naka tsarin kenan amma aishi Allah ba ai masa dabara idan ya tashi nuna ikon sa akan bawan sa ina cikin ne aimu muna maraba dashi.
Mikewa ya jamal yayi yana fadin zan fita daga can zan leka wurin hjy in dubata duk da yau nasan basa bari a shiga da safe.
Ba zaka jira yayan ka ku tafi tare ba ko akwai motan da zaka shiga ne a wajen yace zan shiga taxi daga nan ai ba nisa da gidan nan.
Barshi ya tafi mama ya jafar ya fada ba tare daya dago kai ya kalli kowa ba a wurin yaci gaba da hada tea din shi da yakeyi.
Wai ko lafiya kake da dan uwan ka kuwa mama ta tambaya tana kalon shi yakecewa lafiya mama me kika gani ?


ZAINAB IDRIS MAKAWA



🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

6️⃣0️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA


LITTAFIN KUDINE DAN DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA SHI HAKKI BAIDA KADAN MUSULMIN KWARAI KE GANE HAKA, , , ,

Kwana biyu na rasa gane mai ke tsakanin su yaya dan ko yaro yasan akwai matsala a tsakanin su don ya jamal idan ya fita baya dawowa gidan sai dare.
Daya shigo kuma ba,a sake ganin shi sai wata safiyan ko ance ya tsaya ya karya zaice yana sauri ne kada hjy taga ya dade zai karya idan ya isa asibitin.
Ashe mama Ramatu ta fahinci hakan a tsakanin sai gashi ta kasa hakkuri muna zaune muna karyawa bayan fitan ya jamal bada dadewa ba tana tambayana .
Zainab niko sai naga kamar yaran nan akwai abinda ya faru a tsakanin su kwanan don gaskiya ba haka na saba ganin su mussanman ma shi jamal da jafar akwai shakuwa na sosai a tsakanin su.
Kofin dake hannuna ina dan kurban ruwan shayi na aje tare da fadin mama nima na kula da hakan saidai ban tsamani abin yayi nisa haka sosai ba a tsakanin su.
Gaskiya suna da matsala don shi jafar baya ko zancen kanin nasa idan ya fito bai ganshi ba da safe idan da dane da mukazo baya karyawa sai ya nemi dan uwansa sun zauna tare.
Ke mijin ki bai fada maki abinda ke faruwa bane tsakanin su da sauri na girgiza kai ina fadin ba muyi wanan zancen dashi ba gaskiya.
Tsuki tayi tare da fadin ina zakuyi wanan maganan don ko yaushe fuskan shi a daure idan bashi yaga daman yin raha don kansa ba.
Zanwa jamal magana idan ban fahinci komai ba zan fadawa hjy ko zata san maike faruwa a tsakanin su haka.
Nidai ban kara tofa komai ba naci gaba da kurban tea din dake hannuna a hankali har nakai rabin kofin na aje.
Yau ma banga shi jafar din ba ko sakkon fita yayi ne don kwanakin nan naga da wuri yake fita sai dare kuma yake dawowa wani lokacin ma bamu haduwa.
Ina ganin kamar ya fita tun dazun don yace yau yana da meetinga office na shara mata karya ina Allah Allah kada kuma ya fito ta gane karya nayi mata ashe.
Sai Allah ya taimakeni ashe ya fita din don na sara a gaba gashi ranan bamu zuwa asibiti duba hjy don tana bukatan hutu don alluran da akai mata tana son dan hutu ya sa sukai muna gargadi da hakan.
Don haka bayan karyawan mu a falo muka zauna da mama ana dan hira da kallo wanda kusan hiran na mutanen kasan da muke muke zancen irin shigan su da yadda suke magana kuma a cikin sauri.
Can mama ta fara jefo min zance kan zaman mu da yaya sai na rasa amsan da zan bata lokaci guda don haka kawai na dan daure fuskana ina dariyan yake.
Amsan da ban bata ke nan din na gane nugun cikina take son tayi taji wani abu a dangane da zaman mu ko shi kanshi yaya din .
Ganin naki bata amsa yasa ta kawar da zancen da fadin ai ban tsamani hjy zata barku ku koma a tare damu ba don naji taja fada tun kafin tafiyan nan wai ya kamata ace kin biyoshi nan kema, sai ku zauna tare a nan.
Amma mama ni nafi son in zauna Nigeria don nan din babu wanda na sani babu dadin zama a kasan nan ga baki daya wallahi.
Budan bakin halimatu dake kallo kamar tana jin yaren su sai cewa tayi amma dai anty aida mu zauna nan din tunda mijin kima yana nan ai inna fa tace kada ki yarda mijin ki yayi nisa dake.
Da sauri na kalli halimatu din ita kanta tasan irin hararan da nayi mata sai ta koma ta kwanta da sauri saman kujeran da take kwance da farko daga haka bata kara jefa muna baki a zancen mu ba .
Barci ne ya dauki mama don haka hiran namu ya tsaya a nan ina zaune sai faman tunanen maganan da mama ta fada min na rashin jittuwa a tsakan yan uwa biyu da basayi a yanzu.
Tunane nake ko a sanadiyana suke wanan fitinan indai hakane kuwa zan tun kari ya jamal da yadaina damuwa da zancen mu don nima hakan yayi min daidai wallahi don ni har yanzu tsoron ya jafar din nakeyi da ganin girman shi akoda yaushe.
Da wanan tunanen har lokacin sallah yayi na tayar da mama do muje muyi sallah kads mu shagala don a rayuwana bana yarda inyi wasa da lokacin sallah ko kadan.
A gurin dana sallame sallah nayi zaune ina ci gaba da tunane a raina na yadda zan tunkari ya jamal din karshe dai na daure dole in hakan garesu a yanzu kada hakan ya kawo masu matsala.
Ban fito ba sai bayan da nayi sallah la,asar koshi na fito ne don halimatu da har lokacin banga ta shigo dakin ba tunda tayi sallah azahar ta fita.
Bata falon danake tsamani don haka kai tsaye na nufi dakin mama da sallama tun kan na tambaya na hango halimatu din kwance tana barci saye da hijjab din datayi sallah.
Wayancewa nayi da gaida mama tare da tambaya ko taci abinci kuwa tace tun dazun mukaci da mutumiyar tawa aini naji dadin zuwa da yar nan kasan tunda gata tana debe min kewa sosai wallahi.
Mama tana dai damun ki da surutun ko yaushe indai halimatu ne shiyasa suke dasawa da ya jafar idan yana gari ai.
Yarinyar tana da shiga raine mahaifiyar ku gaskiya tana ba yaro tarbiyab daya dace wallahi kunyi sa,an uwa tagari ba kadan ba.
Mama mu gode kamar yadda anty fadila tace in dinga fada idan wani ya yaba wani abu nawa daya shafeni.
Yanzu mama yau ba zamu je gun hjy ba ke nan sai ranan da suka bayar za,a ganta yayi wanan kasa gaskiya suna da doka mai tsauri wallahi.
Ai inda sukafi kasan mu ke nan wurin sanin aiki da canne kyale duk wanda zaizo zasuyi a dameta sai idan an hadu da likitan da yasan kansa zai dan tsawatawa mutune su daina shiga.
Dan wanan hiran da mukeyi da mama yasa naji har zuciyana ya dan sake don hira sosai mukayi da ita har lokaci yaja bamu sanda hakan ba.

Zaune a office din shi ya mike kafafuwan shi saman table din dake gaban shi yana rike da kanshi da hannu daya irun zaman da yayi yana nuna yayi zurfi a cikin tunane.
Don alal hakika yana cikin damuwa da maganan da sukayi da dan uwan nasa kwanakin da suka wuya har ranan ya kasa samun natsuwa a tare dashi.
A karo na barkata yana kiran layin kanin nasa yaki ya daga a karshe ma sai computer ke fada mai wai layin na busy ko yaushe idan ya kira.
Yanzun ma daya kira computer din daine ke fada mai yadda ya saba fada mai layin na busy haka yasa yagane dan uwan ya sashi a black list din wayan shi.
Kararawan office din nasa ne yayi kara hakan na nufin akwai mai son shigowa office din a lokacin.
Da kamar ya kyale maishi ya koma ya dai daure ya ya danna alaman ba mai so shigowa daman ya shigo.
Yana budewa suka baiyana mai su uku aboka shi ne tun na kurciya da suke shashancin su a tare wanda kusan ta sanadiyar sune ma ya samu aiki a kasan nasu a yanzu saboda hazakan shi da kuma basu son rabuwa dashi don zaman shi star a cikin su.
Ko wanin su yana cikin shiga ta alfarma kamar yadda suka saba shiga saidai na kananan kayane irin suit.
Ya matsa kadan daga kofan ya basu wuri don su shigo daga ciki basu shiga ba illa kokarin hugging dinsa da sukayi daya bayan daya.
Kafin su wuce suka karasa cikin office din kujerun dake officen din zube gefe daya suka zube a sama.
A sabule ya biyo bayan su zuwa ciki shima ya samu daya daga cikkn kujerun ya zauna a kai dayan mai suna philis yake fadin ya labarine na ganka a haka kuma.
Sai dayan ya karbe da fadin kwana biyu bamuga ka leko club ba yasa yau na gaiyaci friends muzo mu duba ka ko lafiya.
Jafar din bai amsa kowan su ba illa mikewan da yayi zuwa wurin firdge din dake office din ya bude tare da fito da kananan kwalabe ya dire a gaban su ya juya ya dauko kofuna hudu ya dawo inda yake zaune da farko ya zauna.
Ido ya zuba masu mai nuna alamun shi a gajiye yake ba zai iya zuba masu abinda ke cikin kwalban ba a lokacin.
Kallon shi dayan da baiyi magana ba tun shigowan su yayi yana fadin cikin kulawa wai ya nagan ka hakane gaba daya ka birkicewa sanin ka damu.
Jafar din ne ya dago idanunsa da suka kade sukai jawur alaman yana cikin tashin hankali dai sosai.
Mikewa yayi ya nufi wurin window din office din nasa ya zuge wani haske ya baiyana a office din lokaci guda ya gyara tsayuwan shi yana kallon motocin dake wucewa kasan office din nasu.
Binshi sukayi da kallo tare da mikewa suka nufi inda yake din tsaye don da alama jafar din baison damuwa cikin halin da yake ciki din a lokacin.
Ji yayi daga bayan shi a dafashi hakan yasa shi juyowa ga wanda ya dafa shi din cikin su gaba dayan sune a tsaye a bayan shi suma fuskansu ya nuna sun shiga damuwa kan damuwan shi.
Whatff bro wai meke faruwane dakai haka ka fada min damuwan ka mana ko zamu samu mafita akan matsalan dake damun ka ?
Dan dariyan yake yayi yana kallon su kafin ya girgiza kanshi yana fadin banyi tsamanin zaku iya min amfani ba a yanzu don wanan family issue ne ba maganan ku bane ko na wani.
Da matsalane dakai da family din kku ke nan a yanzu ko hakan yana da nasaba da zuwan yan uwanka da tj yace sunyi a gidan ka akan sanadiyar kakanka da bata da lafiya wai ?
Da manaki ya juyo yana kallon su watau taju har ya kasa hakkuri yakai karanshi ke nan a wurin su yanzu wanda shine dalilin zuwan su ashe ?
A dan zafafe ya buda baki da kyat don ranshi ya gama baci dasu yana fadin oh ashe kunzo ne yanzu kuyi min fada ke nan ?
No no no ka fahince mu jackson munzo nan ne yanzu a matsayin abikan ka bawai munzo muyi wani maganan daya shafi tj din bane.
Nima ai a yanzu nafi ma sha,awan ka samu sabon dan hannu dan shi tj din kakai shekuru dashi kuna harkan nan.
Hannu ya daga mai tare da wani irin tsawa yana fadin stop that nose's jooo, wuu bana cikin mude din wanan zancen a yanzu don zuciyana a jagule yake da komai.
Kallon juna sukayi
Showing 198001 words to 201000 words out of 390011 words