zan saka.
Can naji tace min lalai Aisha wuyan ki nan ya isa yanka zainab ni kike fadawa magana haka kai tsaye ?
Kamar ba zan bata amsa ba saida na dauko kayan na aje na dago ina fadin nafada maki indon wanan auren kaddaran na dan uwan kine harke kuke son takura min a rayuwa don Allah yanzu ba sai anjima ba kisa ya sakeni na koma gun iyayyena yafi min zama da wanan kaddaran.
Fadila ce ta turo kofan da sallama tana fadin madam we are ready ke muke jira ki taimaka ki fito min da takalma da jakka kayan nan.
Tace yes ma ta nufi inda nake aje su tana daukowa tsuki Aisha taja tana sauka a gadon ta nufi hanyar fita daga dakin.
Yadda ta fita yasa fadila gane akwai wani abu atsakanin mu lokacin ta kalloni bayan fitan Aisha din tana fadin meya faru kuma ?
Ba komai na bata amsa tare da rolling din dan kwali a kaina ina fadin muje ko tace ok muka fito na rufo kofa da key.
Muna saukowa duk idanuwan su a kaina don shigan da nayi ya girgizasu a wurin da alama kuma akwai maganan da sukayi akaina lokacin.
Zamu fita nace dasu don su basu gajiya da kallona ni har mamaki abin ke bani yasa ban nuna masu na tsargu da irin kallon da sukan min ba a yanzu.
Bin bayan mu Rufaida tayi da leke har lokacin dana bude mota muka shiga na fice gidan ta juyo tana fadin what ?
Wai kunsan kuwa yarinyar nan wani kafirin mota take ja haka da kanta a garin nan ya mamud ne daga inda yake zaune ya dago yana fadin ina ruwan ki ko jirgi a yanzu sai zainab taja wanan ba abin mamaki bane ai.
A mota nake ba fadila rabarin yadda mukayi da Aisha da amsan dana bata ni kuma .
Fadila tace kin min daidai wallahi don raga masu baida wani amfani ko kadan gara su san yanzu ke din ba sa,an su bace ai.
Mun isa asibitin ban wani sha wuyaba muka gane inda mami take muka shiga kamar yadda ka,idan shigan su yake a kasan.
Don sukan ba,a barsu sun shiga ba don sunyi yawa kuma ba time din duba mara lafiya bane lokacin.
Muna shiga muka samu jamal da jafar a zaune shiru a dakin mukai sallama bai dago kai ya kallemu ba yana dakilan wayan shi.
Jamal ne yayi muna sannu da zuwa muka kara gaidasu tare da yiwa mami sannu da jiki ta dan dago tana amsawa.
Abinci da muka zo dashine muka aje a gabanta nace mami ga abinci munzo maki dashi.
Godiya tayi muna sai lokacin jafar yayi magana yake fadin fadila ki taimaka mata ta tashi zuwa bandaki ta dan gyara.
No ta bari zan iya mami ta fada a karo nabiyu da tayi magana ke nan tun zuwan mu dakin da take kwance din.
Da kyat ta yun kura ta mike ta shiga bayin haka yasa dakin shiru babu mai magana a cikin mu har ta fito ta hau gadon da niyar kwantawa.
Abincin nake kokarin zubawa muryan mami ya dakatar dani tana fadin dakata zainab kada ki zuba don bazanci abincin gidan ku ba.
Wani irin kallon mamaki kowa na dakin yai mata lokaci guda sai fadilace mai karfin halin fadin mami kiyi hakkuri ki danci wani abu don Allah.
Jamal ta kalla inda yake tana fadin akwai kudin kasan nan a hannun ka ka sayo min abinda zanci a waje.
A sanyayye dan nata ya amsa mata yana fadin akwai mami amma da kici wanan din don gurin sayar da abincin yana da nisa sosai.
Jeka ka sayo min zan jiraka hakanan har ka dawo ta fada tana kawar da fuskanta daga kallon mu cikin dakewa.
Jamal na fita jafar din ya mike tare da fadin mami zan koma wurin aiki sai anjima zan dawo insha Allahu.
Ko motsi batayi ba balle yasa ran amsawa ga sallaman da yayi mata haka yasa kai ya fice daga dakin duk wanda ke wajen saida yaji wani abu a ransa lokacin.
Munyi shiru dukkan mu mami ke fadin kada ki damu zainab badon ke nayi haka ba wanan karon donshi mara hankali da tunane na aikata hakan don haka kada ki dauki wanan don ke nayi hakan dama.
Babu komai mami Allah ya shirya tsakanin ku na fada ina mikewa tsaye da sauri suka mike suma nace su jirani a waje ina zuwa.
Suna fita fadila ta rufo kofan hakan ya bani daman karasawa bakin gadon da mami din take kwance.
Ka nakai gurfane ina fadin mami kiyi hakkuri ki gafarce ni ban auri jafar don wani manufa da kuke fadi ba.
Asalima shi jafar di ne ya turasasa iyayyena ya aureni da wani manufa da yake dashi a zuciyar shi don cinma burin shi.
Kimarki da martaban ki hade irin kaunar da kika nuna min yasa iyayyena basu tsaya dogon bincike ba suka bayar dani ga danki.
Kuka ne yazo min na dakata na dan lokaci saida nayi mai isata naci gaba da fadin Alhamdullahi mami tunda yau kin gane waye jafar da abinda yake aikatawa na fasadi a doron kasa.
Don haka nake rokon ki a matsayin ki na uwa a gare mu mami ki tursasa jafar ya sakeni in koma wurin iyayyena tunda Allah bai nufa burin shi ya cika ba a kaina.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



ALHAMDULLILAHI RABIL ALAMIN AR RAHAMANIN RAHIM, , , ,

YAR UWA WANAN NOVEL NA KUDINE DON GIRMAN ALLAH IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA DON KADA KI SHIGA HAKKIN WATA ALLAH YA BAMU CIKAWA DA IMANI AMIN, , , , , ,

Ido kawai mami ta zuba min har na gama na barke da kuka lokaci guda mai tsuma zuciya mami bata juyo ba.
Sai da ya jamal ya turo kofan ya shigo dakin da sauri ya karaso yana fadin subbahanallahi lfy haka zainab ?
Mami me ya farune take wanan kukan haka don Allah ko wani abin kuma ya jafar yai mata kafin ya fita.
Gata nan ai katambayeta kaji abinda takewa kukan don ni ban fahinci inda ta dosa ba don ni yanzu bashi ke gaba .
Zaune yakai yana fadin zainab me ya farune haka kike kuka don Allah ?
Ya jamal a taimakeni ya jafar ya sakeni in koma gidan mu don Allah na gaji da wanan auren wasan da mukeyi.
Kiyi hakkuri mami taji sauki za a kai ga wanan don kowa yasan yana cutawa rayuwan ki ai yanzu zee.
Sai dai ke din wani baiwane a cikin ahalin don zancen rabuwa da yaya yanzu bai taso a gareki ba zainab.
Kukane ya kubce min yasa nabar dakin da sauri don jin abinda jamal din ya fada game dani don ni yanzu banda wani buri dayafi naga ya sahale min wanan auren dake kaina in hutu da bakin cikin shi a zuciyana.
A mota fadilace take ta ban baki duk da bata san abinda ya faru ba amma haka tayi ta ban baki kan hakkuri.
Mun shigo gida yamma yayi a lokacin don haka kai tsaye kowa dakin sa ya nufa direct don yin sallah .
Koda na idar ban shigo ba ina part dina don yadda nake jin zuciyana a lokacin sai suka dauka hakan wani wullakancine kuma dana samu yanzu gare su.
Ban fito ba sai washegari don a ranan zamu rufe school zuwa hutun examas daya kawo jiki lokacin.
Na sauko na nufi falon suna zaune ana hira har hjy tafito a lokacin wurin ta na nufa nakai har kasa ina gaida ita da kwana take fadin.
Niko kawata wanan karon sam ban gane maki ba don bakya son shiga mutane yanzu sam ?
Zanyi magana naji muryan Nuriya na fadin kai hjy da wani abu kike ina zata shigo mutane a yanzu bayan tana ganin tafi aji da matsayi a yanzun.
Take annutin fuskan hjy ya sauya take fadin wanan wani irin magana kikeyi yar nan yarinyar nan idan ba wani abu ba me zaisa tayi hakan.
Ai munzo munga halinta a nan din ba hakan take ba ai yanzu ma din dai kila wani abin ne dai ya taso mata na uzuri.
Kara maimaita gaida ita nayi da kwana ta dan amsa da sauran hasalan a tare da ita nace zan leka makaranta in dawo.
Shi mijin naki fa ta tambaya tana kallona nace ya na ciki yana shiri shima zai fito yanzu don ni ina rigashi fita kullun.
Tace owoo Allah ya taimaka yasa a amfana ga abinda ake nema bayan ni dana amsa da amin babu mutum daya daya amsa mata wanan addu,an da tayi min.
Na juya inda suke a cikin jam,i ina ina kwanan ku ya bakunta ban jira amsan su ba nace na tafi sai na dawo.
Sai Na,ima ce tace tace min a dawo lafiya zee nace amin na leka dakin su Fadila na sallame su na fice gidan .
A waje na samu su yaya suna kallon gari daga dan wurin da suke nayi masu sallama na bude motana na tafi.
Na wuce ban dade ba jalal ya shiga ciki yana fadin ashe gaskiyan masu karin magana da sukace idan baka mutu ba ba debe tsammani a gareka.
Wai yau zee din mami ce take tuka motar da Nigeria sai dan wani dan kasuwa a lagos yake tukata wai yau ga zee a cikin shi tana ja.
Zee kan ai ta barmu da mamaki Na,ima ta fada sukan sauran shiru sukayi kamar basuji me ya fada ba a lokacin.
Hjy daga gefe tace Allah ke nan dare daya Allah kanyi bature dama abin haka yake wurin ubangiji ai.
Zaka ga dan mai kudi bai dace ba sai dan tallaka yazo shi ya bada mamaki baiwane na ubangiji hakan ai.
But Nuriya ta mike daga inda take zaune tana fadin muma din ai ba fin mu dai akayi ba dadin abin idan gidan miji sun kasa dakai ai iyayyen ka nada shi ko ?
Kaiya yar nan ai samun miji ga ya mace yafi na mahaifa don abin miji naka na kaima na iyayye kuma na sauran yan uwankane yanzu.
Har ta juyo kamar ta bada amsa sai kuma ta juya taci gaba da tafiya rai bace zuwa dakin da aka sauke su a ciki.
Yanzu kan zama gida ya kamani tare dasu dole na toshe kunnuwana akan irin maganganun da ake sake min a fakaice idan an zauna.
Ga mami an sallamo ta daga asibitin taki sake jiki da kowa a gidan tana daki ko yaushe ita kadai a ciki.
Ta fito da zancen komawa Nigeria hjy ta fatatake da fada don me take hakane tazo ne dama don ta dagawa yara hankali.
Don haka ba za a koma ba sai idan lokacin da suka diba din yayi hakan yasa mami din yin fushi da kowa a gidan babu ruwanta da kowa sai wanda ya shiga su dan gaisa sama sama kowa fushin ya same shi a gidan.
Ranan da suka cika sati daya a gidan suka shirya fita zuwa zagaya gari sun so mu tafi tare amma sai yaya yace na zauna suna sin ganina dama fadila da sadiya su rakasu.
Jin hakan da Nuriya tayi tace itama ta fasa fitan idan bada ni zasu fita ba nan kan ranan yaya yai mata jan ido akan lalai sai sun fita tunda da ita aka shirya fitan dama.
Badon taso ba ta shirya ta bisu suka fita bisa jagorancin jalal don jamal yaki shigowa gidan balle su leke mai.
Jin haka yasa na koma dakina ina zaman jiran tsamanin su basu dade da fita ba yaya jamal yazo ya kwankwasa min na bude.
Gaidashi nayi bayan ya amsa yake fadin kizo mami ke magana dake yanzu na amsa da to tare da komawa ciki na sako hijjabina na fito.
Ina shiga dakin ya mamud nagani a zaune yayi shiru kamar me tunane na gaidashi ya dan juyo yana amsa min.
Na gaida mami da jiki shiya nuna min wuri in zauna ban yarda na zauna saman kujeran da ya nuna min din ba.
Na samu wuri a kasa na zauna dan shiru ne kafin ya mamud ya kawar da shirun da fafmfin zainab tambayan ki muke son yi don Allah.
Kada ki fassara wanan abin da wani manufa ko ma,ana na daban ki tuna kema kamar mune kike a wurun mami.
Duk abinda yashafi dayan mu kamar ya shafeki ke ma don bayan kina diya a wurunta ga alaka na aurataya ya kara hadaki da mami din kuma a yanzu.
Don haka yarda da amana ya kara shiga a tsakanin mu ke nan ta ko ina yanzu don haka don Allah ki bamu amsa daudai abinda kika sani a game da mijin ki kada ki boye muna komai a game da rayuwan jafar a yanzu ?
Kaina gyada a hankali ba tare dana dago kai ba na kalli kowa daga cikin su yaci gaba da fadin don Allah zainab ki fada muna iya abinda kika sani akan jafar din dan zaman da kikayi nan dashi.
Don mun fahinci akwai sautin rayuwa wanda addini mu da al,ada bai amincewa ko wani dan musulmi dashi ba ya kasance yana aikata haka a rayuwan .
Ya jamal ya amsa da fadin kinga boye muna ko rufa mai asiri kamar kinfi kowa cutawa ne a hakan don asan ta inda za a fara taro wanan matsalan a tsanake.
Wani kuka ne yazo min ina kokarin dannewa saidai hakan bai yuyu ba gareni don saida hawayen ya zobo daga cikin idanuwana zuwa saman fuskana.
Kada kiyi kuka don Allah zainab don a wurin kine kawai zamu samu abinda muke son ji a yanzu kafin shi mu tunkare shi muji dalilin yin hakan garesh.
Nan ma dai shiru nayi masu don ban san mezan fara dashi ba a lokacin to tunda bata magana ai sai ku tambayeta muji don wanan ba abinda za a tsaya wani boye boye bane don mu fita daga zargin da zukatan mu ke ciki mami ta fada.
Hakane mami don na kula nima ba zata iya fadan komai yadda muke so ba a wirin ta ya gyara zama da kyau tare da fadin.
Zainab shin tunda kika auri jafar har zuwan ku nan akwai wani mu,a mulan aure dake shiga tsakani ku kamar yadda addini ya tanadar muna ?
Ma,ana yana kwanciyan aure dake yadda musulunci yace mata da miji suyi a tsakani ko kuma a, a wani hanya yake bi ya biya bukatanshi a gareki idan bukatan hakan ya taso a gare ku.
Kai na kara sadawa kasa don tambayan yai min nauyi da amsa hakan koda kuwa yaya jamal da yake kanin sane a wurin shi kadai.
Zainab ki fada mana mafita akeson a nema maku ga baki dayan ku do koba jafar kike aure ba yau hakan ke faruwa dole mu dage mu nema maki hakkin ki ga ko waye .
Don hakan yin shirun ki kamar kara dulmiyashi kike son yi ga aikata haramun a yanzu don baida kamarmu a fadin duniyan nan kaf da zasu tsaya akansa a yanzu.
Ki daure mun san wanan tambayan yana da nauyi ki fada muna kai tsaye amma kuma ya zama dole a gareki damu mu san gaskiya.
Kaina girgiza har lokacin kuka nakeyi da sauti a hankali mami tace kiyi magana mana kin tsaya kina girgiza kai kawai.
Mami kinsan sai anbi a hankali ba zata iya fadi kai tsaye yadda akeso ji ba sai dai a cikin fahinta za a gane komai jamal ya fada.
Kuna kwanciyan aure dai dashi ya mamud ya fada na sake girgiza kaina kamar yadda nayi da farko.
Wai kina nufin wani abu na aure bai taba shiga tsakanin ku ba tunda ya aure ki tun a can gida har zuwa nan ke nan ?
Na gyada kai innalillahi suka dauka dukan su mami kan kuka tasa saida suka bata baki suna fadin idan tayi haka ai ba za a gane komai ba karshe ma ya karta mu.
Ya juyo gareni ya sake fadin zainab ta yaya kuka zauna haka ba tare da wani ya san da wanan zancen ba kinsan kuwa kina cutuwa ?
Na girgiza kai yace wa iyazu billahi kuma ke baki taba masa maganan meya kawo haka ba don yanzu dai babu kurciya a tare dake ai ?
Sai lokacin na bude baki cikin muryan kuka ina fadin ban masa magana ba kan hakan saida nayi masa magana kan irin rayuwan da ya keyi a nan wanda bai dace ba.
Sai yace maki me
Showing 252001 words to 255000 words out of 390011 words