guda a daidai lokaci kuma na fara jin cikina na kugin neman agaji don rabona da naci wani abu tun a gida Nigeria kafin mu taso.
Banci komai da aka aje min ba a ciki jirgin don hankalina ba a kwance yake ba lokacin fin tsorin daya mamaye min zuciyana.
Ki tashi ki watsa ruwa a jikkn ki ki canza wanan kayan mu fita mu leka hjy daga nan mu samu abinda mukaci na fada ina kallon halimatu da har lokacin take kwance.
inane ban dakin ta fada a dan kasalance don har lokacin bata gama warwalewa daga gajiyan datayi a jikinta ba da hannu na nuna mata ta mike ta shiga.
Ajiyan zuciya na sauke tare da mayar da idona ina bin dakin da komai dake cikin sa da kallo ina mamaki a raina.
Yayan mu ban iya kunna ruwan ba don ban taba ganin irin wanan kayan ba muryan halimatu a kofan ban dakin ta dan rufe jikinta da tawul di bandakin dake rataye a ciki.
Mikewa nayi ba tare da nayi magana ba na tura kofan na shiga nuna mata yadda zata kunna ta kashe nayi na fito.
Bakin gado na zauna na hada tagumi ina tunane wanan rayuwan tawa shine rana zafi innuwa kuna don rayuwa rashin incin kai nakeyi a gidan nan yanzu.
Har lokacin da halimatu ta gama shirmenta ta fito daga cikin ban dakin ina zaune ina faman tunane kokarin shafa mai takeyi na dakatar da ita da fadin baki dauro alwala bane kiyi sallolin dake kanki halan ?
Ban tsaya jin amsan taba naci gaba da fadin halimatu kin dai ga rayuwan da muka fuskanta sai kinyi da gaske wurin maida hankali ga ibada a wanan gidan yanzu.
Kina daijin idan innan mu ta bugo waya zancenta garemu shine kada muyi sakaci da ibadan mu kuma mu guji duniya da abinda ke cikin ta ga baki daya.
Kada ki yarda inji ko in gani kina sakarwa wani namiji fuska koda kuwa shi wanda yakawo nan dinne don yanzu mutum ba abin yarda bane.
Don Allah halima kada ki yarda mubawa innan mu kunya a idon duniya kina daida wayau kin kinsan komai don yanzu ido aka zuba mata damu a garin mu.
Nagane yarinyar ta fahinci abinda nake nufi take naga yanayin ta ya canza itama lokaci guda take fadin yayan mu idan nayi wani abinda bai dace ba inna tace kimin fada kadana sake.
Zanyi halima kuma ina kanyi don ban yarda da wa yan nan mutanen ba wallahi don haka ki kara kama kanki da kowa wallahi.
Yanzu kiyi sallah dai mu fita kada ace mun shige daki mun kyale hjy bamu kulata ba tun da muka shiga.
Sallah ta tayar kamar yadda na umurce ta sai bayan ta idar ta shirya muka fito daga dakin gidan tsit kamar babu kowa a cikinsa.
A hankali muke takowa babu kowa dakin su hjy kuma yana kulle don na murda naji shi a rufe na juya ke nan ina shirin fadin dakin a rufe yake naji ana fadi a bayan mu.
Da sauri na juya wanan matar ne da aka kira da julie tsaye a bayan mu tana magana cikin girmamawa a garemu taci gaba da fadin dun tafi asibiti tun sha biyun rana.
Boss yace idan mun tashi a fada muna muci abinci kafin ya dawo gida a cikin harshen turanci take min bayani yadda zan fahinta.
Da taimakon ta har muka je dining din abunci ne gurin a jere ta shiga bude muna tare da muna bayanin shi duk ciki babu abincin da muka sani dan dama dama wani shinkafa da aka dafa da ganye shi nake zaton zamu iya ci daga cikin abincin dake gaban mu din.
Halimatu jan ta raja,a ga wani katon tallatalo da aka bamkareshi sai maiko yakeyi yana daukan ido naji tana fadi a hankali wanan din naman meye yayan mu ?
Ban sani ba halimatu don haka kadama ki sa rai zakici shi don bamu san ko naman halal bane.
Tace amma aishi yaya yana sallah don haka ba zai yarda a ci mushe a gidan sa ba ko ?
Kada ki fara kici wanan nama na fada fuska a daure abincin dana zuba na mika mata taja plate din zuwa gaban ta dagani har ita bamu iya cin wani abin kirki ba don dan danon abincin da mukaji daban danamu na Nageria.
Bamu kai ga tashi wurin cin abuncin ba aka turo kofan duk da muna dan nisa da wurin hakan bai hanani jin lokacin da aka shigo gidan ba.
Shine tafe tare da mama Ramatu sai jamal dake bayan su dauke da jakkar kayan hjy da suka fita dashi .
Da sauri na mike tsaye ina masu sannu da zuwa shida jamal suka amsa min gaidasu danayi mama Ramatu idon ta ta sauka kan abincin dake gaban mu din.
Yauwa jamal mama sai ku zauna kuci abinci zan dan shiga in watsa ruwa a jikina don duk a gajiye nake wanan tsohuwar taku duk ta rudani wallahi.
Ya jikin nata mama na tambaya ina kallon fuskanta jiki da sauki tana asibiti anbarta can suna dubata koda yake ku ai ba damuwa da jikin nata kukayi ba kuna nan kun saka abinci haka a gaba.
Da sauru na dago kai ina kallon mama Ramatu din don jin abinda ta fada haba mama idan basuci abinci ba zamu taru a hakane a rasa wanda zai kama wani a cikin mu.
Jamal ai gaskiya na fada kana sane dai hjy tanace sai azo da zainab kasan nan anzo din kuma har ta fara manta abinda ya kawo ta nan yanzu.
Amma mama sai nake ganin itama mutumce kamar kowa dole tana bukatan hutu tare da ita don me kuma yanzu za a kawo wanan magana koke da kika tafi ai cewa akayi ki dawo basu bukatan kowa a can.
Ni dai jikina ya mutu ina tsaye ko kwakwaran motsi ban iya ba don cin fuskan da nake fuskanta a wurin sarakuwan nawa ina tunanen na rabu da mami ashe kuma ga wata tare damu yanzu.
Juyawa nayi na fara tafiya don zuwa dakin mu naji halimatu ma ta biyoni a bbaya gado na fada ina sake kuka lokaci guda.
Yayan mu ki daina masu kuka haka shi yasa suke jin dadin maki abinda sukaga dama ko yaushe dan Allah kiyi shiru ki kyalesu yaya.
Halimatu cin abinci laifi ne kuma yanzu shike nan yanzu mu bamu da yancin yin komai a gidan nan don kawai mu din iyayyen mu suna tallakawa kome halimatu ?
Kyalesu yayan mu muma ai watarana zamuyi kudi mu rama abinda suke muna tunda suma badashi aka haifesu ba ai.
Zancen halimatu ya dan sakani dariyan yake a cikin kuka har nace kai halimatu kedai yarinya ce yaushe zamu arziki irin nasu a duniyan nan mu da gidan mu ko akuya bamu da balle shanu.
To aini ina tara kudin da nake samu tun zuwana wurin ku sunanan idan mun koma gida sai inba inna tasai abin kiwo dashi ko karamane ta sake.
Halimatu amma dai ke din nan da sheg, , , , ban karasa ba aka turo kofan dakin wanda ke rufe da sauri muka juya don ganin waye mai shigo muna indai ba mama Ramatu bace ta biyomu har daki tazo tayi muna wani cin mutuncin na fada a cikin zuciyana.
Ya jafar ne ya shigo yayi wanka ya sauya kayan jikin shi zuwa na mazan kasan maleshia mai zubi irin na indiyawa a jikin shi sai kamshi ke tashi jikin shi sosai.
Da murmushi dauke a fuskanshi ya karaso yana fadin halimatu bataci abincin ba kema baki ci ba donta tashi kada ki damu da rashin cin abincin ta damuwa ta saka a zuciyar ta ita.
Keko kinga idan kina wasa da cin abinci mama zasuce ban rike amanan dana dauko naki ba idan kin koma gida akaga kin rame sosai.
Zan dinga ci ta fada sai kuma tace saidai abincin ne baya da dadi a bakin mu naso kuma in dan dibi naman nan naci sai yayan mu ta hanani ci wai don ba a san ko naman meye ba.
Zainab kika hanata cin abincin ko me ya fada a dan hasale yana kallon fuskana a cikin mamaki yaci gaba da fadin ko kina zargin naman ne ko wani abu.
A hankali na girgiza mai kai ina fadi da kyat naga munyi kankanta da mu fara cin abinci hakana manya basu fara ba .
Halimatu tace kuma yayan mu kaji abinda wanan maman ta fada dazu bayan ka shige daki wai bamu saba ganin abinci haka ba munzo mun zauna munaci bamu damu da ciwon hjy ba.
Da sauri ya dago yana kallona tare da fadin wace mama kardai nace mama Ramatu ne tayi wanan maganan mara dadin ji gareku ya tsatsareni da ido yana kallona ranshi a bace.
Ganin nayi shiru na dukar da kaina kasa sai hawayen dana fara fitarwa daga idanuna yasa shi fita daga dakin da sauri ya barmu muna binshi da idanu.
Halimatu zaki ja min wani tsana a gidan nan kuma wurin mama yanzu don mami zata kira tace ga abinda nayi mata yanzu kuma shiyasa duk abinda akai min bana yarda ya sani ko yaji don gudun irin hakan.
Bansan ya sukayi ba dai can da dare shi da kanshi yazo ya kiramu har dakin wai mu fito muci abincin zance mai a koshe muke sai dai yanayin fuskanshi bai barni na fadi hakan ba.
Bayan fitan shi daga daki na kalli halimatu ina fadin tashi kije kuci bana jin cin komai a yanzu kuma na koshi dana dazun.
Haka ta fita kamar bata so jin abindana fada ba can sai gashi dakin yana fadin ki taso muci abinci na fada ko bakiji bane a cikin umurni yana tsareni da idanun shi manya masu ban tsoro.
Da sauri na aje littafin dana dauko ina karatu na nufo inda yake saida yaga fitana daga dakin kafin ya biyo bayana naji yace min dakata a nan.
Da sauri naja na tsaya ya karaso inda nake hannayen shi ya raba yasani a tsakiya yana bina da idanuwan shi.
Da sauri nayi kasa da kaina don irin kallon da yake min din ki saurareni da kyau kiji me zan fada maki kuma ki kiyayye.
A duk lokacin da muke tare dasu mama ko wani na gida dole ki nuna masu cewa ni di mijin kine kuma kina kula dani kina bani hakkina na miji ki a gaban kowa.
Da sauri na dago kai yace yes kin san dai abinda nake nufi da hakan ba sai na tsaya maki gwarigwariba kan hakan.
Don ban son wani ya zargi wani abu a tsakanin mu zamu zauna a daki daya yanzu har zuwa lokacin da zaku bar kasan nan ku koma Nigeria tare dasu.
Don zaman ku a nan zai iya takurawa rayuwana da sauran aiyukana amma for now zaki nunawa kowa cewa kina kula da hakkina nima hakan zanyi kokari in nuna masu a fili.
Understood ya fada yana kara tsareni da idanuwan shi sosai cikin warning dina ga abinda ya fada din da sauri na gyada mashi kaina don dai kawai ya jaye jikin shi a kaina lokacin.
Jikina sai wani irin rawa yake min don tsoro banji ya daga gurin ba kamar yadda nayi tsamani sai can naji ya sauke ajiyan zuciya ya ya jaye jikin shi a hankali.
Nima jin hakan yasa na bude idanuwana da suke min a rufe na sauke a bayan shi don har ya fara tafiya a lokacin cikin wani irin yanayi sai kuma naga yaja ya tsaya nima tsayawa nayi dan nisa kadan dashi.
Zoki rike hannuna a haka zamu karasa wurin su ya fada ba tare da ya juyo ya kalli inda nake ba yake magana.
A hankali na tako zuwa inda yake hannu shi daya miko mi har lokacin bai kalli inda nake ba na rike tare da dan runtse idanuwana ina jin wani zafi a raina naji ya fara takawa dani kara matso dani yayi a cikin jikin shi sosai a haka muka karasa wurin daning din.
Suna zaune su uku halimatu mama Ramatu da ya jamal duk suka dago kai suna kallon mu kafin shi ya jamal din ya sauke kanshi daga kallon mu yana murmushi a fuskanshi na gani mu tafe haka a gaban su.
Don shi ya gama fahintar komai a game da dan uwan shi din don yayi sancin sosai ya ga me yake ciki a rayuwan shi ko kokarin boye masu hakan kawai yake yi yanzu.
Muna zama yake fadin amarya da angone waya fada maki ana fushi da cin abinci zainab ai kinga angon ki yaje ya rarashe ki kada ki ja mashi wani matsala kuma ana fama dana hjy.
Zata iya yin fushi jamal tunda abincin da aka dafa don ta ana mata gori a kansa gidan nan nikuma ita nace a girkawa .
Murmushi yake mama Ramatu tayi kafin tace fadin gaskiyan da nayi dazun shine fushinta a yanzu don kawai na fadi gaskiya .
Mama bazan so wanan halinba gun iyalina gaskiya ban kawo kowa a nan dan ya takurawa wani ba ina hjy da bakinta tace a barsu su huta mu tafi dazun irin hakan bai kawo girma gun babba.
Yana magana yana kokarin zuba abincin daya bude tare da turo min plate din abincin daya diba a gabana tare da dan kashe murya yana fadin ci koda kadan ne don Allah.
Ni wanan draman na mutumin nan dame yayi min kama hakane idan yana abu sai ka rantse da Allah da gaske yake abinsa bazaka dauka hakan shiri bane yake a gaban mutane.
A haka cikin kulawa ya samu har na danci abincin zaikai cibi biyar ita kuma mama Ramatu har ta kare cin abincin bata sake yin magana ba saida zata mike ne take fadin ke sai kizo mu kwana a dakina tare dake .
Tunda ita a daki mijin ta zata kwana da sauri ya dago yana kallonta don jin abinda ta fada sai kuma ya wasance da fadin hakan ma yana da kyau zaku iya kwana a taren idan yin hakan ba a takura maki ba mama ?
Ba komai ainina bukacin yin hakan kada a barta a daki ita kadai ta juya wurin da halimatu ke zaune tana fadin idan kin gama saiki sameni a dakin mu ina kinsan dakin dai.
Zan rakota ya fada batare daya dago kaiya kalli inda maman take tsaye ba sai cewa mama tayi ina jiranta don dakin yai mi girma na kwana ni kadai a cikin sa.
Kaina yana duke a kasa zaka dauka kunyar maganan mama nake ji yasa ban dago kaina ba a lokacin.
Mama juyawa don ta tafiya dakinta yayi daidai da shigowan mutum biyo a gurin banyi saurin dago kaina ba don ganin ko suwaye suka shigo lokacin.
Saida jikina ya ban ana kallona na dan dago kai a daidai lokacin da mukai arba da taju tsaye ya dan duka a bayan ya jafar din suna magana saidai idon shi a kaina yake.
Gabana na ya fadi lokaci guda a take na tuna da kalman shahada na dinga jerosu har uku lokaci guda kafin inji dan natsuwa ya sauka min lokaci guda.
Sun gama magana yana kokari barin wurin da sauri naji ya jafar din na fadin kun gaisa da madam da tazo .
Juyowa yayi ba tare daya bashi amsa ba yana fadin anzo lafiya ya hanya lafiya kawai na bashi amsa dashi ina kawar da kaina daga kallon inda yake tsaye.
Barin su wurin yayi daidai da mikwan ya jafar din yana fadin yana zuwa suka fita tare dasu lokaci guda.
Sai lokacin na sauke wani irin ajiyan zuciya dana baiyana shi a fili wanda ke nuna nayi zurin tunane a lokacin.
Ki yi hakuri zainanb kici gaba da masa addu,a da sannu komai zai daidaita a tsakanin ku nasan ki da yawan ibada a baya ko yanzu ki dage da adduan don ba wanda yai tunanen hakan ma zai iya faruwa ga wanda yasan mijin ki ko waye.
Saukin abin bai yarda kowa ya takaki yadda yaga dama ba don yana tsaye a kanki akoda yaushe.
Dago ido nayi na kalli ya jamal din dake magana yace kwarai duk abindake faruwa a tsakanin ku na sani zainab shima yasan nasan komai akai.
Ki kara daurewa muci gaba dayi masa addua wanan shine jerabawan da Allah ya sako mai a rayuwan sa shikuma .
Ba zanso inyi magana mai zurfi dake ba a yanzu nan gaba zamuyi maganan idan muka samu lokaci irin haka kedai ki kara hakkuri har zuwa lokacin da gaskiya zatayi halinta.
Idona da suka ciko da hawaye lokaci guda na daga ina fdin
Showing 192001 words to 195000 words out of 390011 words