ya dawo dake nan kuma.
Nan ma dai kaina sada kasa don nasan abune mai wuya zamana a can tare dashi tunda ba hakan ya tsaraba a tunane na.
Kai yau nasha wahala zainab sosai wurin zuwa wanan kauyen can kauyen Narasawa ne naje don shi can yake zaune yana bada magani.
Da sauri na dago kai don jin abindata fada ina mamaki kuma a raina da irin halinta na kula yanzu a kaina tayi wanan tafiyan tun safe har dare haka ?
Kinsan nasan zaman da kikeyi a gidan nan dole hankalina ya daga dan ganin zai tafi dake can inda babu kowa da zai saka maku ido tsakani ki dashi.
Duk da dai ba tsanmani da zai iya cutar dake ba ko wani abu makamancin hakan tunda naga yana da dama sosai gaskiya saidai riga kafi ance yafi magani.
Hannu ta mika tana jawo handbag dinta data fita dashi zuwa unguwa da safe tare da dauko wani dan kwalba karami tana fadin wanan yace in baki da zaran na iso dashi zaki shanyeshi gaba dayane lokaci guda saura sai ki shafa a fuskan ki amma sai kinyi bissimillah zaki kafa baki ki shanye shi.
Miko min tayi na karba hannu na rawa tace yanzu zaki shashi dan haka kiyi bissimillah kisha yanzu don nasan halinki da rashin daukan abu da muhinmaci zainab.
Dan dariya mai kama da yake na sake a fuskana tare da kokarin bude dan kwalban data miko min ba tare da tunanen komai ba danjin bissimillah datace inyi kafin insha nasan koda na cutarwa ne Allah zai tsareni don bissimillah danayi kadin insha din.
Duk da inada yakinnin tsakani da Allah take taimaka min dinndon naga alama hakan sau tari da yawa a gurinta.
Saida na zuke dan ruwan dake cikin kwalba a gabanta kafin tace makaru ne sosai kingan shinan yana da amfani sosai a jikin mutum.
Sai wanan kuma wanka zakiyi dashi sau uku kinga yau ke nan zaki fara gobe da safe kuma kiyi sai da yamma kuma shike nan kin gama dashi.
Sai wanan gaskiya shi amfani dashi kamar zai maki wuya nake gani zainab don yace zaki shafa ne ta yadda zai iya shakan shi sosai a jikin ki.
Ni kuma naga yaushe har zai shaki wanan din idan kin shafa saidai kawai mu gwada sa,an mu akai kinga kamar yadda zaku shiga jirgin nan har in wuri daya zaku zauna dashi hakan zaiyi tasiri gareshi ko ya kika gani ?
Banda abin fada don haka na kada mata kai kawai da na amince da hakan tunda banda zabi bayan wanan tunda don ni take wanan kokarin haka.
Miko min tayi na karba ina fadin nagode anty tace babu godiya a tsakani mu zainab don nima kin mun kokari sosai shiyasa dole nataimake ki ai zainab.
Kinga aikin nan wallahi ba don ke ba da yanzu na rashi ga baki daya to sai Allah ya taimakeni ke din yarinyace mai dubaiya sosai wallahi.
Don ba karamin rufamin asiri wanan aikin yai min ba wallahi don har mutane suna ganin yanzu na samu wani babban aikine don rufin asirin da suke ganin mu a ciki ni da iyayyena a yanzu.
Saidai ina jiwa karki tafi ki manta dani zainab don kin san mu mata zumuntan mu sai idan muna tarene yafi karfi sosai haka ke faruwa tsakanin mata da yawa wani lokaci idan ana wuri daya anfi zumunta mai karfi.
Saidai saukin abin tunda muna nan tare da halimatun ki zaki dinga tunawa dani don rabuwan mu a yanzu gaskiya zan shiga wani matsala nake gani.
Duk da naji wani iri a raina saidai ya zama dole in fada mata tare da halimatu din zamu tafi yace duk da ban san yadda mami zata dauki tafiya da halimatu din ba idan taji hakan.
A sanyaye nace anty ai dazun ya shigo yana fadin tare da halimatu din zamu tafi can wai bai yarda a barta na ba .
Yanayin fuskantane ya sauya lokaci guda kafin tace min dama nayi tunanen hakan tuntuni don da wuya ku bar halimatu a nan tare damu bakinan.
Shike nan nasan sallamata zaiyi idan zaku tafi don aikina ya kare ke nan a gidan nan dama dan kunake zaune a nan.
Tausayi maganan ta ya bani a kasan zuciyana ban san lokacin danace da ita ba koda ya kama ki bimu can din anty ba zaki iya hakan ba.
Zainab ke nan yanzu har kina tunanen zai aminta da ku tafi dani can idan ma shi ya yarda da hakan idan kin roka min iyayyena nakejiwa da hakan.
Yanzu dai tashi kije kada mu makara kiyi wanka da wanan ruwan maganin kamar yadda malam din yace ban fada maki ba yace ki dage da addu,a da sadaka.
Saidai abune mai wahala a can ki samu wanda zaki bawa sadaka kamar nan hakan yasa nayi tunane idan kina da hali saiki bar dan wani abu anan wanda za a rika bayar maki da sadaka lokaci lokaci.
Ko ba a hannuna ba zaki iyabawa innan ki tana maki wanan sadakan don yana da kyau mutum ya dinga sadaka lokaci lokaci.
Mun dauki lokaci tana dan kara min haske kan abubuwa da dama sai nake jin wani iri a raina kamar nace na fasa badon hjy kakarshi ba babu inda zanje gaskiya.
Nayi kamar yadda tace dani kan maganin yayin da tafiyan mu ya kan kama don sai shirin tafiya sukeyi gadan gadan mu namu idone kawai lokacin.
Karfe uku jirginmu zai tashi zuwa kasan ghana sai ya biya can ya cika fasija kafin mu dauki hanyan tafiya kasan da zamu din.
Ranan kan na shiga damuwa sosai kafin tafiyan mu don yadda zamu rabu da anty fadila wanda ban sani ba ko mun rabu ke nan har abada kamar yadda ta fada min dasafe.
Zama nayi na dafe habana da hannayena duka biyu har hawaye na zubo min a lokacin ban sanda hakan ba.
Kai wanan kuka naki yai min yawa wallahi kada mubi hanya dake kina min wanan kukan a dauka sato ki nayi haka.
Anty fadilace nake tunane yaya ya zamu barta a nan yanzu mu tafi gashi aikin nan dashi ta dogara kuma yanzu, , , ,
Kukane ya kubuce min daga hakan na kasa fadan abinda zan fadi a lokacin don kukan daya rinjayeni a lokacin na rabuwa da matar data nuna min kauna bayan uwata da mami ke nan.
Wani irin kallon banza ya watsa min tare da fadin kinsantane ko ta dalilin wa kika santa ke wai wace irin yarinyace da bata da tunane.
Wani irin sani kake son in mata bayan wanan danayi mata mun saba da ita a gidan nan ta dauke mu kamar yan uwanta na jini tana zama damu tsakani da Allah yanzu kuma ace za a rabamu da ita.
Baiyi magana ba illa fitan da yayi daga dakin ranshi a bace nan ya barni na ci gaba da kukana ba wanda yasan inayi har sai lokacin da tafiyan mu ya gabato mai aiki ya shigo yana fadin ance mu fito da kaysn da za a tafi dashi.
Duk da yahana mu tafiya da kaya mai yawa hakan bai hanani daukan kayan da muke so ba kuma baiyi magana kan hakan ba.
Kuka sosai mukayi lokacin rabuwan mu da anty fadila din kamar ba gobe a ranmu yana ciji mota zaune yana kallon abinda mukeyi din uffan baice damu ba don haushin da muka bashi a lokacin muma yaya ya iya damu ina batun dauko mashi wata yayi ya damu mata duka can.
A airport din mun samu mami dasu hjy a can suna jiran mu sai bayan mun fito daga mota lokacin mami ta bamu baya tana magana da wani da nake zaton dan uwansune .
Muka iso inda suke tsaye gaidasu mama Ramatu nayi har kasa kafin in juya wurin mami din in gaida ita ta amsa a cikin wani irin yanayi ba yabo ba fallasa gareni haka na mike jiki ba karfi na koma gefe daya na tsaya halimatu tana biye dani duk inda nasa kafana.
Bayan mami ta gama magana da mutumin ta juyo tana fadin ita wanan fa ina rakiya tayo maku dai ko ?
Ban bata amsa ba don yadda take magana akwai rashin mutunci a idanunta gareni ya mamud ne suka karaso shida iyalinshi yake fadin.
A,a mai masaukin hjy ashe har kun karaso kuma hjy dai tace sai da kece zata yarda ta je a dubata don bata zuwa gidan gwauro ta zauna ba mata a gidan.
Dariya akasa mata tana fadi da kyar kunga laifinane kan hakan muryan mami ke fadin wai wanan da kuka zo da ita fa tana kallon halimatu din.
Kila da ita zasu tafi mana mami Nuriya matar ya mamud ta fada tana wani yamutse fuskanta ita kamar me kyamar mu.
Dama abinda nakewa gudu ke nan gashi ko ya fara faruwa a mayar da gida kanar kasuwa kowa yazo cin banza ya tafi.
Haba haba mami hakan baida kyau wallahi kema ai gidan ki a cike yake da yan uwa dan ta dau, , ,
Ya jamal bai karasa maganan shi ba mami ta katseshi da fadin jamal ni kake kokarin yiwa wa,azi akan abindana sani kome ?
Ba wa,azi bane mami ya fada yana juyawa don barin wurin ranshi a bace don dashi zamuyi tafiyan ashe .
Wai me ke faruwane kuma ya jafar ne daya iso wurin yake tambaya shiru kowa yayi har mami din dai nuriya ce take fadin mami ke magana kan wanan yarinyar tana nuna halimatu din wai da ita zaku tafine ?
Eh tare zamu a ina zamu barta tunda tare da yar uwanta take zaune dama ni nace a bamu ita don kada zainab din ta zauna ita kadai dama.
Amma ai baka fada min da ita zaku tafiba ko ta fada a dan hasale shima cewa yayi but mami wanan ai issue din family dinane OK.
Zatayi magana hjy tace kai iyami ki bar wanan zancen tunda kinji abinda ya fada daga nan aka fara kiran masu tafiya har aka kawo kanmu.
Duk da na taba shiga jirgi daga kaduna zuwa abuja sai naga wanan din kamar daban ne shi saboda checking din da yai yawa sosai.
Kujeran mu daya dashi su hjy da mama Ramatu suna bayan mu sai na jamal da halimatu a can baya.
Tunda muka zauna tunane ne a gabana shiko system din shi ya bude yana wani aiki a ciki har jirgin ya daga damu na runtse idanuwana a hankali ina tunanen iyayyena da a waya kawai nayi sallama dasu.
Ba wani dadewa ake sanarwa mun iso kasan ghana za a dauki sauran fasinja anan muci gaba da tafiya tun wanan lokacin naga ya lumshe idanuwan shi a hankali.
Jirgin bai dade a nan ba ya daga bayab fasijan sun shiga mukaci gaba da tafiya har lokacin yana a cikin wani irin yanayi da ban kawo komai a raina ba a lokacun kan hakan da yayi din.
Barci ne ya daukeni har ban sani ba na dan kwanto saman jikin shi bai tayar dani ba ya barni a hakan yadda nake don na samu barci sosai a lokacin.
Bumu isa ba sai washegari mun dai dan fita a wani kasa sai lokacin na yaba da karfin halinshi dana gani na zyaa Nugeria a hakan din nabina gaji ga hjy da ake bata taimako don kada ta galabata don jikin da take ji.
Mun isa lafiya kuma mun samu taro a wurin su don har mota uku suka zo taron mu wanan baiban mamaki ba ga dan sanin da nayi koshi waye din .
Kallo kan bani kadai ba harsu hjy da mama Ramatu da jalal da suka saba shiga kasashen duniya saida suka kalli abubuwan mamakin da muke gani a kasan kamar ba duniyan mu daya dasu ba.
Bayan tafiya mai nisa daga airport din muka shiga wani unguwa mai yawan gine ginen zamani sosai na kasan wani katafaren gida aka shiga damu.
Tun abin yana babu mamaki har muka gaji da kallo muka zubawa sarautan Allah ido zuwa lokacin hjy ta gama gajiya sosai don tafiya mai nisa da mukayi.
A cikjn gidan ma munsha kallo don kamar gaba daya yan aikin gidan mazane duk suna saye da uniform a jikin su iri daya.
Wani katafaren falo aka shiga damu sai nake ganin abin kamar a mafalki wallahi ba ido bude nake ba.
A falon ne naga wasu mata biyu yan kasan sun fito suna muna sannu da zuwa tare da kawo muna ruwa da drink's suka aje a gaban mu.
Ban yarda nayi nisa da halimatu ba duk da wuri daya muke zaune dasu mama Ramatu har hjy dake kukan kafanta yana damunta sosai shi kuma bai shigo ba har lokacin.
Muna kanta muna faman mata sannu da jiki sai gashi sun shigo tare da ya jamal da sauri sukayo kanta tare da tambayan meke faruwa da ita.


ZAINAB IDRIS MAKAWA




🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅


5️⃣8️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA


YAR UWA FATAN ALHERI A KULLUM UBANGIJI ALLAH YAJI KAN MAGABATAN MU YASA IN TAMU TAZO MU CIKA DA KALLAMAN SHAHADA AMIN, , , ,


A rude yake magana cikin waya a dan kallaman da nake dan tsunta daga abinda yake fadi shine naji cewa ai sauri ai bucking din asibitin da kuma abubuwan da za,a nema ya sani.
Su kawai na danji daga cikin wayan da yakeyi din a harshen turancin su na can mai kama da yaren kasan.
Yana gama waya yake fadin a kira masa julie sai wanan mutumin da suka ahigo tare da sauri ya nufi cikin gidan yana kiran mai suna julie din .
Kamar yare yayi mata don sai naga tana kada kai kafin ta juyo guri mu da fara,a a fuskanta tana muna magana ido kawai muka zuba mata don bamu fahinci mai take nufi da hakan ba.
Saida ya jamal yake fada muna tace mu biyota zuwa ciki za,a shigo muna da kayan mu dakin na daban aka ban za a bawa halimatu nata nayi saurin dakatar da hakan tare da fadin zamu sharing din daki daya da ita she is my sister.
Wani kallo tayi mi sai kuma ta dan dukar da kai cikin girmamawa tana fadin shike nan ta juya ta tafi muka bude dakin muka shiga.
Bamu dade da shiga ba sai ga kayan mu ta shigo muna dashi dakin lokacin ina tsaye ina bin dakin da kallo ikon Allah wai yau mune a cikin wanan irin daulan da muke gani a film din turawa.
Kofan ban daki na nema na shiga nan ma saida na tsaya naba ido abincin sa wurin kallo da dabara har na gane , inda zan danna ruwa ya zubo.
Wanka nayi sosai ga sabulan wanka nan sai wanda ka zaba kayi dashi kafin in fito har halimatu tayi barci don haka ban tayar da ita ba.
Jakkana na bude na fitar da zani sallah da hijjab sai dai ban san inda gabas yake ba a gidan don haka dabara yazo min a karon farko nayi amfani da app din wayana na gane gabas din galrin.
Sallolin dake kaina na fara ramawa a gurguje don kada lokaci ya kara wuceni na dade a zaune ina neman kariyan Allah daga duk wani sheri da tsari dazamu tunkara a wanan garin dama mutanen da zamu zauna dasu din ga baki daya.
Barcin na fara ji don haka na mike na samu gefen gado na kwanta nima a gefen halima ina kallon yadda take barcin ta hankali kwamce.
Sai tunane nake barkatai akan yadda rayuwan mu zai kasance a wanan tafiyan namu da bamu san kowa ba babu alaman kuma yan jinsin mu na hausawa a wana gidan ko akwaisu ma banga alama ba dai .
Barci sosai mukayi har suka fice kai hjy asibiti ban sani ba don ita ta hana a tayar damu don cin abinci tace muna tare da gajiya kasan yaran basu saba irin wanan dogon tafiyan ba haka.
Sai bayan karfe uku da rabi kamar an tayar dani na falka don wanan irin mafalkin danakeyi a baya shine yau ma na sakeyin shi don tun bayan da malam mijin maizube kakan mu ya ban addu,oi ban sakeyin wanan addu,an ba sai wanan ranan kuma.
Gabana ke faduwa sosai ga wani irin zufa dake fita min a duk kafofin jikina lokaci guda muryan halimatu naji a bayana tana fadin .
Yayan mu halan mafalki kikayi hakane ina ta kiran sunan ki sai faman wani irin magana kikeyi kamar kina shan wahala a cikin mafalkin naki.
Addu,an da nake karantawa ne ya hana in juyo in fuskance ta don a lokacin duk a rikice nake sosai don wanan mafalkin yafi sauran da nakeyi rikitani sosai.
Abinka da yarinta ina wanan addu,an sai na nemi damuwan nawa na rasa shi lokaci
Showing 189001 words to 192000 words out of 390011 words