tsaye da karfi tana fadin ni ni ni sai kuma ta gitgiza kanta tana fadin karyane iyami karyane wallahi.
Ba zaki shigo ki fini ba a gidan nan na fada maki iyami sai naga bayan ki har diyan ki wanan dan naki jafar da ake fadin yafi kowa taurari masu haske a cikin zirian nan sai na mayar maki dashi abin kyama a gun jama,a.
Wani tsaya Alhaji Adamu ya dakawa matar tashi uwar gidan shi kuma uwar yayan shi manya ke nan a gidan.
Yana fadin wai haulatu kina da hankali kuwa kikw fadin wanan maganan haka Rakiyan hayi dake mukaje dauko kwalba wai yanzu kwalba ya fashe ya tarwatse a sanadiya wata.
Zance ta fara sakewa kamar mai bada labari sai salati duk wanda ke wurin suke sakewa diya ta naja baya daya bayan daya suna kuka.
Hankalin kowa a tashe don sun gama fahintar abinda ke gudana a lokacin yayiwa iyami da jafar danta asirine yanzu asirin ya kare ya koma mata..
Dole aka sakata daki aka kulle don tonon asirin yayi yawa a lokacin suka dawo sukai zugun zugun a waje suna jinta tana ci gaba da fadin irun abinda tayi a gidan.
Kowa hankali tashe gabani asuban farko sukaji dukan kofa a zabure samarin gidan dake waje cirko cirko suke tambayan waye da daren nan haka.
Alhaji hayi yace nine Alh hayi na layin ku mijin aminiyar hajiya haulatu matar kanin mahaifin su jafar uwa kuma ga Rufaida a yanzu.
Da sauri Alh Adamu ya karaso kofan yana fadin lafiya Alh a cikin daren nan haka yace daga waje inda yake tsaye ina fa lafiya Alh wanan matar Rakiya mai dakina tun cikin dare muke fama da ita da hauka tuburan .
Sun je sun aikata sheri tare da maidakin hjy ta nan gidan yanzu kuma abu ya koma mata tana can tana faman tonawa kanta asiri gaban diya da kishiyoyin ta tun dazun.
Kai innalillahi Alh Adamu ya fada yana bude kofa kafin yace muma nan tun misalin sha biyun dare muke fama da Haulatu cikin irin wanan halin.
Wa,iyazu billahi ai zance ya baci ke nan kuma da na dauka tana a hayacin tane muji abinda ya kawo haka a bakin ya don sai sunan hjy iyami da danta take ambata cikin sambatun nata.
Abinda itama take fada ke nan shiyasa na gane cewa sunyi wani aiki akan iyamin da yanzu ya karye ya koma kan su kuma.
Yanzu dai dole mu nemi malamai su warware muna abinda ke faruwa ko kuma a kira ita hjy iyamin aji ko tana da masaniyan hakan.
Ba sai an kirata ba a yanzu don hakan kamar sirin mu ne Alh gara a fara neman malamai din don kada hakan ya kawo wani fitina kuma.
Fitina Alh Adamu ai ita da ta dauko fitan sai dai ya kare a kanta wallahi banji ban gani ban kuma aiketa aikata hakan ga wani ba balle abun ya dameni.
Wanan zancen ma yasa ka fargar dani hanya yanzu gidan su zan bugawa waya suzo su dauke ta su tafi can su karasa wanan abin kunyan badani ba wallahi.
Da sauri Alh Adamu yace kada ai haka Alh ai lafiya suka baka ita shi zaka duba ba sai yanzu da haka ya cika da ita ba zaka tura masu ita gida yanzu.
Nasani amma hakan zanyi kai in zaka tsaya gidan ka ya koma gidan kallo zuwa safe daga haka ya juya Alh na kiran shi bai tsaya sauraron shi ba ya tafi.
Sai dai abinka da babban gida sai gashi tunda asubahin nan a samu wanda ya kira mami ya fada mata duk abinda ya wakana a gidan.
Hankalin mami din ya tashi sosai haka yasa bata iya kara komawa barci ba da sasafen nan ta tayar da yaran ta take fada masu abinda ke faruwa a kaduna din.
Itama Rufaidan yan uwanta sun kirata tun a cikin dare suka labarta mata abinda ke faruwa kuka ta rushe dashi har hankalin yan uwanta ya tashi sun dauka ko mutuwa aka aiko mata anyi.
Sunyi tambayan duniyan nan tana cewa dasu ba komai har suka gaji suka kyaleta saidai basu koma barci ba suna hira a dakin su.
Har akai sallah kowa ya watse don zuwa office da zasuyi don ranan aikine ranan sai dai kuma jin tun safe an bude get dib gida mami ta fita yasa hankalin su kuma tashi.
A falo suka hadu da Aisha data fito tana mamakin fitan mami din a wanan lokacin suka hade dssu falon nan suke fada mata zancen Rufaida din ta shiga dakin wurin ta.
Tayi tambayanta tana ce masu ba komai ita gida zata tafi ranan ganin haka yasa Aisha daga waya ta kira hjy dake hanyar gidan mu tana fada mata abinda ke faruwa da Rufaida din.
A cikin hasala hjy ke fadin kada ku barta taje ko ina munafukan banza da wofi kawai ta kashe wayan.
Mamakine ya kama Aishan jin abinda mahaifiyan nata ta fada kan rufaida din da take ji da ita kamar yar cikin ta.
Ganin irun mikan da yake faman yi yana hamma da wani irn nishi yasa naja jikina da kyat har na sauka saman gadon ni kaina ina cikin wahala don yadda ga baki daya nake jin jikina kamar ba nawa ba a lokacin.
Ga zafin wahala dake cina ga hankalina da yake tashe a lokacin don tabbasa nasan da a cikin hayacin shi yake da ba abinda zai hana shi taimaka min a lokacin.
Bandaki nayi karfin halin shiga na sakewa kaina ruwan zafi kafin na dan fara jin sa,ida a karkashina da nake jin bakon yanayi a gareni.
Da kyat na fito bandakin da bin bango har na kai kofa na bude na fita zuwa dakina Allah ya taimakeni ba kowa daya ganni a lokacin har na bincika kayana nafito na koma dakin da sauri.
Na shiga na samu ya fado saman gadon da gani akwai alaman ciwon ciki mai karfi ko wani abu dai yana damun shi sosai a lokacin.
Da kyat na iya kai gwiwana kasa na dago kansa da kyat ya dan bude idanun shi kadan ya mayar dasu ya rufe nayi dubaran bude bakin sa a hankali na fara dura mai maganin ya hade.
Yana shiga makoshin shi ina jin wani kara da yakeyi har ya sauka mai lokaci daya naga yayi wani irin zabura da karfi badan Allah ya gyara ba daya barar da kofin maganin dake hannuna a lokacin.
Idanuwan shi ya ware yana kallona nayi mai sannu tare da kara daga kofin ruwan maganin da niyar kai masa a bakishi.
Yayi saurin rike min hannu yana kallona kasha zaka samu lafiyan abindake damun ka a yanzu na fada a cikin damuwa.
A take ya bata fuska nace yi hakkuri ka hade ya bude bakin na kara dura mai ya karba yasha yana bata fuska ya hade da sauri.
Ya maida idon shi ya lumshe wanan karon kan zaune ya mike da sauri jikin shi yana wani irin karkarwa tsoro ya kara kamani lokaci guda can naji ya sake wani irin gyatsa mai karfi saidana zabura.
Bai jima a zaunen ba ya koma ya kwanta a kasa inda yake da farko din sai ga wani irin zufa yana karyowa a goshin shi lokaci daya kuma sai gaba daya jikin shi zufa ya karyo mai.
Nidai ina gefe daya ina kallon ikon Allah kafin ya bude idon again ya sauke a kaina yana nuna min AC dakin da hannu don har yanzu ya kasa bude baki yayi magana har lokacin.
Tambayan shi nayi a kara ko a rage ya gyada min kai haka yasa na mike da kyat na kara karfin AC har karshe a hankali ya fara sauke ajiyan zuciya.
Ganin da nayi kamar zaiyi barci a lokacin yasa nace dashi ko zaka daure ka koma saman gado ka dan kwanta a can .
Kamar bai jini ba sai can ya mike da karfi a lokacin ma na farga da jikin shi babu komai dan abin rufane kawai daya kwaso ya dan rufa a gaban shi.
Saida naga ya kwanta ya dan fara samun natsuwa na dauki sauran maganin da yake aje nashanye gaba daya maganin idan ya sauka ciki yana da zafi nikan da cikina baida komai banji irin abinda shi yaji ba.
Na sake gyatsan kamar yadda shima ya sake din daya sha ina jin wani zafi a jikina na koma saman gadon na dan kwanta sai barci.
Lokacin dana farka shidda ta gwauta na samu nakai ban daki da kyat ina sake ruwa a jikina ina gasa ko ina .
Wai sai lokacin kuka yazo min na dade a ban dakin ina kuka kafin in fito in tayar da sallah sai da na idar na tayar dashi ya zabura yana salati kafin kuma ya koma ya dafe kai da sauri na dan wani lokaci.
Sai can ya mike ya shiga ban dakin ya dan dade kafin ya fito wurin wardrobe din shi ya nufa ya dauko riga ya saka saida naga ya tayar da sallah .
Na nufi gadon da nake gyara na canza zanin gadon zuwa sabo ban tsaya har ya idar ba na fice dakin zuwa dakina.
Don a matse nake komai wuri kawai nake nema da zan kai kwance a lokacinb kaya na saka a jikina na kwanta tunanen abinda ya faru a daren jiyan ne yake dawo min a raina.
A hankali na mayar da idona na runtse a cikin takaici da bakin ciki ina nadaman kasancewa a cikin wanan halin.
Yau mace idan ka ganta tare da mijin ta ka barta kawai a inda ka ganta ba sai ka tono abinda ke boye ba.
Don matsalan gidan wani daban yake dana gidan wani sai dai abin na wata yafi na wata abin ban mamakine .
SHI ABU A CIKIN DUHU DAI SIRINE kawai a barshi a boye a yadda yake zaifi sauki.
Barci ya dauke ni har na tsawon wani lokaci a cikin barcin nake jin ana tashe ni sadiya ce tsaye a kaina take fadin ki tashi anty ina ga kamar ba lafiya a gidan nan.
Don ga mami nan tazo tun dazun a cikin kuka har ya jafar ta shiga dakin takirashi suna dakin hjy ana hayaniya tun dazun din kowa sai kuka yakeyi.
A zatona abinda ya fado min a rai shine zancena da mami daya faro a jiyan da sukaje mata dashi.
Shine har yanzu basu bar zancen ba a tsakanin su saidana danyi wanan tunanen na dago ina cewa sadiya ki zauna nan kada ki kara fita falin ga baki daya.
Ta kalleni a cikin mamaki kamar zatayi magana sai tayi shiru kafin ta kai zaune gefen gado ta kurawa kofa ido.
Mikewa nayi a hankali cikin dabara na daure ina tafiya zuwa ban daki na samu na kai da kyar nayi fitsari na dade ina gasa kaina kafin na fito a lokacin naji dan dadin tafiya a yanzu.
A daidai lokacin da nake zama take fadin wai anty mami din tana da kishiyane jin haka yasa na dago ina kallon ta nace sadiya meye damuwan ki da zancen mami ne ?
Anty ji nayi mana yanzu suna fadin wai kishiyan mami din ta haukace jiya da dare wai tayi masu asiri ya karye.
Wani irin faduwan gaba ne ya ziyarce lokaci daya dana ji hakan a take zancen malam kakan mu ya fado min a rai.
Da yake fadin akwai asiri a jikin mijin ki karyewan shi zai samu ne kawai a jiki ki duk ranan da mijin ki yakai jikin ki komai zaizo karshe da yardab Allah.
Kedai kawai kuci gaba da amfani da maganin nan da wanda tsohuwar nan ta baku a can akwai waraka a cikin sa sosai insha Allahu.
A sannan ne za ku gane waye yake bibiyan mijin ki tun yana karamin shi har zuwa yanzu din don dai akwai hannu sosai ga al,amarin shi.
Kallon sadiya din nayi kamar zan yi magana sai naga wanan maganan bata kai ta gane abinda ake nufi ba.
Na dan jima a zaune kafin na mike ina fadin barin zo sadiya ki jirani a nan na fada na fita daga dakin.
Ina kokarin shiga dakin nake jin muryan ya mamud yana fadin ko an kaisu kotu dawa zaki sharia mami ?
Kawai dai ki barsu da Allah tunda har Allah ya fara tona masu asiri tun nan duniya kowa ya gama jin abinda ya faru a gari dama duniya.
Kawai ko haka aka barsu ai ya wadatar sai mu kara godewa Allah da har aka gane su a yanzu.
Na shiga dakin da sallama sai hjy dasu yayane suka iya amsanin sallama su mami kan basu iya amsa min ba a lokacin.
Na gaida hjy tare da mami na juya wurin yaya ina gaidasu ya jafar ke fadin ni abinda yake ban mamaki me nayi mata da har take kiran sunana a zancen ta na hauka.
Dama an fada muna haka zai faru ai amma sai ta wani dalilin asirin zai karye daga wata mace kuma don komai da mata ake karya asirin shi ai dama.
Sai nayi tunanen wani sabon sheri mami kuma zata dora min don ban karkare sanin maganan da sukeyi din ba a dakin na san dai kan zancen da sadiya ta fada min ne .
Yanzu dai kunji abinda daddy sulaiman ya fada ai tana fadi wai itace sanadin hana jafar haihuwa kohin aure ys mamud ya fada.
Haba innalillahi wa,inna alaihim raji,un ga magani a jikin mu muna ta faman wahala da abu a jikin mu shekara da shekaru haka.
Dolene ma mu tafi kadunan a yau din nan don ayi komai a gaban mu su san muji komai tunda shi Alh Adamun wai baya son mu ji zancen.
Dama dazun muna hanya Aisha ta kirani wai Rufaida sai rusan kuka takeyi taki kuma fada masu abinda ya same ta.
Ina fa zata fadi wanan abin kunyan garesu hjy ta fada taci gaba da fadin ni ko zamar yar nata a gidan ku ban yarda dashi ba tun farko wallahi.
Yanzu ku tashi mu koma gidan kai jafar ka shirya sai mu hadu a airport dakai idan lokaci yayi.
Kai ya kada masu yana fadin ba inda zanje mami ku tafi kawai na barta da Allah don yau ni jikina haka na tashi bana jin dadin shi hutu kawai nake son samu a yanzu.
Ka zauna din amma mu dole ne mu tafi do ba a san iya sherin da sukai ta bin mutane dashi ba haka tunda ba imani ke gareta ba.
Ta yaya mutum zai yi wanan sherin hakan tsawon wanan shekarun kuma hankalin shi kwance ya mamud ya fada.
Ka bar mace shu,uma inda ka ganta komai akace wanan matar tayi zata iya don irin yadda akasha fama da ita a baya har saida lokacin iyayye suka shiga tsakanin su hjy ta fada.
Mami ta sauke wani ajiyan zuciya tace ni ai jikina ya mutu wallahi sai nake ganin abin kamar a mafalki.
Har suka tafi basu daina maganan ba a ranan kuma suka isa kaduna duk da sun so ganin matar amma sai suka samu wai an tafi da ita wurin mai magani.
Kafin wani lokaci magana ya zagaye unguwa da gari duka kowa yana fadin albarjacin bakin shi akai.
Ya jafar din ne yayi min bayanin abunda ke faruwa a tsanake kafin hjy kuma ta kara ban labarin zaman su da abinda akace din tayiwa mami da jafar din.
Nikan abin mamaki ya bani don nasan matan sosai zamana a gidan mami takan shigo lokaci lokaci zance ita din bata damu da zuwa gidan mami din ba sai idan haka ya kama na tazo.
Sai dai idan tazo din akwai yin iko gare ta don ban da shakat sai idan ta tafi nake samun sauki.
Ranan kan yasha waya daga mutane daban daban da suka shafi yan uwan su na bangaren mahaifin su da tunda nazo gidan ba gane mami bata yadasu ba.
Da dare ma zancen daine sukayi da hjy da take fadin ai ka bar mamaki don ba mijin su daya ba take wanan kishin da uwarku.
Shi mutum mai hassada haka Allah kan yo shi da halin sa a jini kawai kyashi da hassada ke kamasu har su aikatawa dan uwan su keta.
Dama irin wanan kishin yafi zafi a tsakani don daya bata kaunan taga daya ta fita da komai alhalin kuma ba miji daya suke aure ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI BARKAN MU DA
Showing 381001 words to 384000 words out of 390011 words
Ba zaki shigo ki fini ba a gidan nan na fada maki iyami sai naga bayan ki har diyan ki wanan dan naki jafar da ake fadin yafi kowa taurari masu haske a cikin zirian nan sai na mayar maki dashi abin kyama a gun jama,a.
Wani tsaya Alhaji Adamu ya dakawa matar tashi uwar gidan shi kuma uwar yayan shi manya ke nan a gidan.
Yana fadin wai haulatu kina da hankali kuwa kikw fadin wanan maganan haka Rakiyan hayi dake mukaje dauko kwalba wai yanzu kwalba ya fashe ya tarwatse a sanadiya wata.
Zance ta fara sakewa kamar mai bada labari sai salati duk wanda ke wurin suke sakewa diya ta naja baya daya bayan daya suna kuka.
Hankalin kowa a tashe don sun gama fahintar abinda ke gudana a lokacin yayiwa iyami da jafar danta asirine yanzu asirin ya kare ya koma mata..
Dole aka sakata daki aka kulle don tonon asirin yayi yawa a lokacin suka dawo sukai zugun zugun a waje suna jinta tana ci gaba da fadin irun abinda tayi a gidan.
Kowa hankali tashe gabani asuban farko sukaji dukan kofa a zabure samarin gidan dake waje cirko cirko suke tambayan waye da daren nan haka.
Alhaji hayi yace nine Alh hayi na layin ku mijin aminiyar hajiya haulatu matar kanin mahaifin su jafar uwa kuma ga Rufaida a yanzu.
Da sauri Alh Adamu ya karaso kofan yana fadin lafiya Alh a cikin daren nan haka yace daga waje inda yake tsaye ina fa lafiya Alh wanan matar Rakiya mai dakina tun cikin dare muke fama da ita da hauka tuburan .
Sun je sun aikata sheri tare da maidakin hjy ta nan gidan yanzu kuma abu ya koma mata tana can tana faman tonawa kanta asiri gaban diya da kishiyoyin ta tun dazun.
Kai innalillahi Alh Adamu ya fada yana bude kofa kafin yace muma nan tun misalin sha biyun dare muke fama da Haulatu cikin irin wanan halin.
Wa,iyazu billahi ai zance ya baci ke nan kuma da na dauka tana a hayacin tane muji abinda ya kawo haka a bakin ya don sai sunan hjy iyami da danta take ambata cikin sambatun nata.
Abinda itama take fada ke nan shiyasa na gane cewa sunyi wani aiki akan iyamin da yanzu ya karye ya koma kan su kuma.
Yanzu dai dole mu nemi malamai su warware muna abinda ke faruwa ko kuma a kira ita hjy iyamin aji ko tana da masaniyan hakan.
Ba sai an kirata ba a yanzu don hakan kamar sirin mu ne Alh gara a fara neman malamai din don kada hakan ya kawo wani fitina kuma.
Fitina Alh Adamu ai ita da ta dauko fitan sai dai ya kare a kanta wallahi banji ban gani ban kuma aiketa aikata hakan ga wani ba balle abun ya dameni.
Wanan zancen ma yasa ka fargar dani hanya yanzu gidan su zan bugawa waya suzo su dauke ta su tafi can su karasa wanan abin kunyan badani ba wallahi.
Da sauri Alh Adamu yace kada ai haka Alh ai lafiya suka baka ita shi zaka duba ba sai yanzu da haka ya cika da ita ba zaka tura masu ita gida yanzu.
Nasani amma hakan zanyi kai in zaka tsaya gidan ka ya koma gidan kallo zuwa safe daga haka ya juya Alh na kiran shi bai tsaya sauraron shi ba ya tafi.
Sai dai abinka da babban gida sai gashi tunda asubahin nan a samu wanda ya kira mami ya fada mata duk abinda ya wakana a gidan.
Hankalin mami din ya tashi sosai haka yasa bata iya kara komawa barci ba da sasafen nan ta tayar da yaran ta take fada masu abinda ke faruwa a kaduna din.
Itama Rufaidan yan uwanta sun kirata tun a cikin dare suka labarta mata abinda ke faruwa kuka ta rushe dashi har hankalin yan uwanta ya tashi sun dauka ko mutuwa aka aiko mata anyi.
Sunyi tambayan duniyan nan tana cewa dasu ba komai har suka gaji suka kyaleta saidai basu koma barci ba suna hira a dakin su.
Har akai sallah kowa ya watse don zuwa office da zasuyi don ranan aikine ranan sai dai kuma jin tun safe an bude get dib gida mami ta fita yasa hankalin su kuma tashi.
A falo suka hadu da Aisha data fito tana mamakin fitan mami din a wanan lokacin suka hade dssu falon nan suke fada mata zancen Rufaida din ta shiga dakin wurin ta.
Tayi tambayanta tana ce masu ba komai ita gida zata tafi ranan ganin haka yasa Aisha daga waya ta kira hjy dake hanyar gidan mu tana fada mata abinda ke faruwa da Rufaida din.
A cikin hasala hjy ke fadin kada ku barta taje ko ina munafukan banza da wofi kawai ta kashe wayan.
Mamakine ya kama Aishan jin abinda mahaifiyan nata ta fada kan rufaida din da take ji da ita kamar yar cikin ta.
Ganin irun mikan da yake faman yi yana hamma da wani irn nishi yasa naja jikina da kyat har na sauka saman gadon ni kaina ina cikin wahala don yadda ga baki daya nake jin jikina kamar ba nawa ba a lokacin.
Ga zafin wahala dake cina ga hankalina da yake tashe a lokacin don tabbasa nasan da a cikin hayacin shi yake da ba abinda zai hana shi taimaka min a lokacin.
Bandaki nayi karfin halin shiga na sakewa kaina ruwan zafi kafin na dan fara jin sa,ida a karkashina da nake jin bakon yanayi a gareni.
Da kyat na fito bandakin da bin bango har na kai kofa na bude na fita zuwa dakina Allah ya taimakeni ba kowa daya ganni a lokacin har na bincika kayana nafito na koma dakin da sauri.
Na shiga na samu ya fado saman gadon da gani akwai alaman ciwon ciki mai karfi ko wani abu dai yana damun shi sosai a lokacin.
Da kyat na iya kai gwiwana kasa na dago kansa da kyat ya dan bude idanun shi kadan ya mayar dasu ya rufe nayi dubaran bude bakin sa a hankali na fara dura mai maganin ya hade.
Yana shiga makoshin shi ina jin wani kara da yakeyi har ya sauka mai lokaci daya naga yayi wani irin zabura da karfi badan Allah ya gyara ba daya barar da kofin maganin dake hannuna a lokacin.
Idanuwan shi ya ware yana kallona nayi mai sannu tare da kara daga kofin ruwan maganin da niyar kai masa a bakishi.
Yayi saurin rike min hannu yana kallona kasha zaka samu lafiyan abindake damun ka a yanzu na fada a cikin damuwa.
A take ya bata fuska nace yi hakkuri ka hade ya bude bakin na kara dura mai ya karba yasha yana bata fuska ya hade da sauri.
Ya maida idon shi ya lumshe wanan karon kan zaune ya mike da sauri jikin shi yana wani irin karkarwa tsoro ya kara kamani lokaci guda can naji ya sake wani irin gyatsa mai karfi saidana zabura.
Bai jima a zaunen ba ya koma ya kwanta a kasa inda yake da farko din sai ga wani irin zufa yana karyowa a goshin shi lokaci daya kuma sai gaba daya jikin shi zufa ya karyo mai.
Nidai ina gefe daya ina kallon ikon Allah kafin ya bude idon again ya sauke a kaina yana nuna min AC dakin da hannu don har yanzu ya kasa bude baki yayi magana har lokacin.
Tambayan shi nayi a kara ko a rage ya gyada min kai haka yasa na mike da kyat na kara karfin AC har karshe a hankali ya fara sauke ajiyan zuciya.
Ganin da nayi kamar zaiyi barci a lokacin yasa nace dashi ko zaka daure ka koma saman gado ka dan kwanta a can .
Kamar bai jini ba sai can ya mike da karfi a lokacin ma na farga da jikin shi babu komai dan abin rufane kawai daya kwaso ya dan rufa a gaban shi.
Saida naga ya kwanta ya dan fara samun natsuwa na dauki sauran maganin da yake aje nashanye gaba daya maganin idan ya sauka ciki yana da zafi nikan da cikina baida komai banji irin abinda shi yaji ba.
Na sake gyatsan kamar yadda shima ya sake din daya sha ina jin wani zafi a jikina na koma saman gadon na dan kwanta sai barci.
Lokacin dana farka shidda ta gwauta na samu nakai ban daki da kyat ina sake ruwa a jikina ina gasa ko ina .
Wai sai lokacin kuka yazo min na dade a ban dakin ina kuka kafin in fito in tayar da sallah sai da na idar na tayar dashi ya zabura yana salati kafin kuma ya koma ya dafe kai da sauri na dan wani lokaci.
Sai can ya mike ya shiga ban dakin ya dan dade kafin ya fito wurin wardrobe din shi ya nufa ya dauko riga ya saka saida naga ya tayar da sallah .
Na nufi gadon da nake gyara na canza zanin gadon zuwa sabo ban tsaya har ya idar ba na fice dakin zuwa dakina.
Don a matse nake komai wuri kawai nake nema da zan kai kwance a lokacinb kaya na saka a jikina na kwanta tunanen abinda ya faru a daren jiyan ne yake dawo min a raina.
A hankali na mayar da idona na runtse a cikin takaici da bakin ciki ina nadaman kasancewa a cikin wanan halin.
Yau mace idan ka ganta tare da mijin ta ka barta kawai a inda ka ganta ba sai ka tono abinda ke boye ba.
Don matsalan gidan wani daban yake dana gidan wani sai dai abin na wata yafi na wata abin ban mamakine .
SHI ABU A CIKIN DUHU DAI SIRINE kawai a barshi a boye a yadda yake zaifi sauki.
Barci ya dauke ni har na tsawon wani lokaci a cikin barcin nake jin ana tashe ni sadiya ce tsaye a kaina take fadin ki tashi anty ina ga kamar ba lafiya a gidan nan.
Don ga mami nan tazo tun dazun a cikin kuka har ya jafar ta shiga dakin takirashi suna dakin hjy ana hayaniya tun dazun din kowa sai kuka yakeyi.
A zatona abinda ya fado min a rai shine zancena da mami daya faro a jiyan da sukaje mata dashi.
Shine har yanzu basu bar zancen ba a tsakanin su saidana danyi wanan tunanen na dago ina cewa sadiya ki zauna nan kada ki kara fita falin ga baki daya.
Ta kalleni a cikin mamaki kamar zatayi magana sai tayi shiru kafin ta kai zaune gefen gado ta kurawa kofa ido.
Mikewa nayi a hankali cikin dabara na daure ina tafiya zuwa ban daki na samu na kai da kyar nayi fitsari na dade ina gasa kaina kafin na fito a lokacin naji dan dadin tafiya a yanzu.
A daidai lokacin da nake zama take fadin wai anty mami din tana da kishiyane jin haka yasa na dago ina kallon ta nace sadiya meye damuwan ki da zancen mami ne ?
Anty ji nayi mana yanzu suna fadin wai kishiyan mami din ta haukace jiya da dare wai tayi masu asiri ya karye.
Wani irin faduwan gaba ne ya ziyarce lokaci daya dana ji hakan a take zancen malam kakan mu ya fado min a rai.
Da yake fadin akwai asiri a jikin mijin ki karyewan shi zai samu ne kawai a jiki ki duk ranan da mijin ki yakai jikin ki komai zaizo karshe da yardab Allah.
Kedai kawai kuci gaba da amfani da maganin nan da wanda tsohuwar nan ta baku a can akwai waraka a cikin sa sosai insha Allahu.
A sannan ne za ku gane waye yake bibiyan mijin ki tun yana karamin shi har zuwa yanzu din don dai akwai hannu sosai ga al,amarin shi.
Kallon sadiya din nayi kamar zan yi magana sai naga wanan maganan bata kai ta gane abinda ake nufi ba.
Na dan jima a zaune kafin na mike ina fadin barin zo sadiya ki jirani a nan na fada na fita daga dakin.
Ina kokarin shiga dakin nake jin muryan ya mamud yana fadin ko an kaisu kotu dawa zaki sharia mami ?
Kawai dai ki barsu da Allah tunda har Allah ya fara tona masu asiri tun nan duniya kowa ya gama jin abinda ya faru a gari dama duniya.
Kawai ko haka aka barsu ai ya wadatar sai mu kara godewa Allah da har aka gane su a yanzu.
Na shiga dakin da sallama sai hjy dasu yayane suka iya amsanin sallama su mami kan basu iya amsa min ba a lokacin.
Na gaida hjy tare da mami na juya wurin yaya ina gaidasu ya jafar ke fadin ni abinda yake ban mamaki me nayi mata da har take kiran sunana a zancen ta na hauka.
Dama an fada muna haka zai faru ai amma sai ta wani dalilin asirin zai karye daga wata mace kuma don komai da mata ake karya asirin shi ai dama.
Sai nayi tunanen wani sabon sheri mami kuma zata dora min don ban karkare sanin maganan da sukeyi din ba a dakin na san dai kan zancen da sadiya ta fada min ne .
Yanzu dai kunji abinda daddy sulaiman ya fada ai tana fadi wai itace sanadin hana jafar haihuwa kohin aure ys mamud ya fada.
Haba innalillahi wa,inna alaihim raji,un ga magani a jikin mu muna ta faman wahala da abu a jikin mu shekara da shekaru haka.
Dolene ma mu tafi kadunan a yau din nan don ayi komai a gaban mu su san muji komai tunda shi Alh Adamun wai baya son mu ji zancen.
Dama dazun muna hanya Aisha ta kirani wai Rufaida sai rusan kuka takeyi taki kuma fada masu abinda ya same ta.
Ina fa zata fadi wanan abin kunyan garesu hjy ta fada taci gaba da fadin ni ko zamar yar nata a gidan ku ban yarda dashi ba tun farko wallahi.
Yanzu ku tashi mu koma gidan kai jafar ka shirya sai mu hadu a airport dakai idan lokaci yayi.
Kai ya kada masu yana fadin ba inda zanje mami ku tafi kawai na barta da Allah don yau ni jikina haka na tashi bana jin dadin shi hutu kawai nake son samu a yanzu.
Ka zauna din amma mu dole ne mu tafi do ba a san iya sherin da sukai ta bin mutane dashi ba haka tunda ba imani ke gareta ba.
Ta yaya mutum zai yi wanan sherin hakan tsawon wanan shekarun kuma hankalin shi kwance ya mamud ya fada.
Ka bar mace shu,uma inda ka ganta komai akace wanan matar tayi zata iya don irin yadda akasha fama da ita a baya har saida lokacin iyayye suka shiga tsakanin su hjy ta fada.
Mami ta sauke wani ajiyan zuciya tace ni ai jikina ya mutu wallahi sai nake ganin abin kamar a mafalki.
Har suka tafi basu daina maganan ba a ranan kuma suka isa kaduna duk da sun so ganin matar amma sai suka samu wai an tafi da ita wurin mai magani.
Kafin wani lokaci magana ya zagaye unguwa da gari duka kowa yana fadin albarjacin bakin shi akai.
Ya jafar din ne yayi min bayanin abunda ke faruwa a tsanake kafin hjy kuma ta kara ban labarin zaman su da abinda akace din tayiwa mami da jafar din.
Nikan abin mamaki ya bani don nasan matan sosai zamana a gidan mami takan shigo lokaci lokaci zance ita din bata damu da zuwa gidan mami din ba sai idan haka ya kama na tazo.
Sai dai idan tazo din akwai yin iko gare ta don ban da shakat sai idan ta tafi nake samun sauki.
Ranan kan yasha waya daga mutane daban daban da suka shafi yan uwan su na bangaren mahaifin su da tunda nazo gidan ba gane mami bata yadasu ba.
Da dare ma zancen daine sukayi da hjy da take fadin ai ka bar mamaki don ba mijin su daya ba take wanan kishin da uwarku.
Shi mutum mai hassada haka Allah kan yo shi da halin sa a jini kawai kyashi da hassada ke kamasu har su aikatawa dan uwan su keta.
Dama irin wanan kishin yafi zafi a tsakani don daya bata kaunan taga daya ta fita da komai alhalin kuma ba miji daya suke aure ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI BARKAN MU DA
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128 Chapter 129Chapter 130Chapter 131