kafin dayan yace dashi ko zaka samu fita yanzu muje kadan sha wani abu ko zaka samu relief a zuciyar ka ?
No ba bazan iya shan komai a yanzu ba don gidana a cike yake yanzu da family dina shan wani abu a gareni yanzu hadarine sosai.
Zaka iya don ba bakon abu bane sha a gareka don haka ka daure kawai mu fita yanzu kadan samu relief a rayuwan kan ko tunanen ka da damuwan ka zai gushe maka na dan lokaci ka koma daidai.
Tun bai yarda da hakan ba har yakai ya yarda ya biyewa son zuciyar su sukaci karfin shi akarshe suka fita tare zuwa inda sukan hadu su hole.
Ranan don bai cikin dadin rai shi ruwan kwalba yaita dinkirawa cikin sa yana kuma jan coicane har ya fara fita cikin hayacin sa.
Da haka har ya raba dare a waje cikin mayen kuma yajawo motar shi zuwa gida don shi din dan hannu ne sosai a wanan harkan.
Ina dakina da nake kwana a kwance na kulle kofa na dinga jin kamar a dukan kofan duk da nasan kofan a bude yake don bani na saba rufe part din ba .
A cikin daurewa da fargaba da tashin hankali na fito a cikin sanda zuwa falon part din babu tantama kofan ne ake duka da karfi.
Allah ya sako min wani dauriya na nufi kofan na bude saidai abinda na gani shine yafi tashin hankalin da nake ciki.
Don ya jafar ne a cikin maye yake dukan kofan gashi rataye da corth din rigan shi a kafadan shi sai layi yakeyi.
Innalillahi wa,inna alahim raj,un na ambata tare da da duban bayan shi ko akwai wani a tare dashi ko wani a falon sam na manta da darene sosai lokacin kowa ya shige part din shi ya kwanta.
Ina can ina tunane ji kawai nayi ya fado min a jiki yana fadin take me to your room zee i want sleep now.
Gabana ne ya fadi jin shi a jikina da nayi lokaci guda ya kara fadi cikin wani murya na maye take me to your bakiji ba ne ?
Ni kan ina zan iya kama mutum kamar ya jafar mai karfi haka da jin koshi a tare dashi a cikin dabara na samu na kaishi dakin nawa ya zube da takalman shi da komai saman gadon ya kwanta rub da ciki ba bata lokaci naji ya fara sakin nasari.
Da sauri na dafe bakina tare da sakin wani irin kuka lokaci guda kamar daga sama naji yana fadin are you crying zeey ?
Dago kai nayi na dan kalli inda yake kwance har lokacin yana kwance a yadda yake din ba tare daya motsa ba yake wanan maganan tashi nayi na sawa kofan dake bude key.
Ban daki na nufa a can na raba dare ina darza kuka a cikin tashin hankali sai maimaitawa nake ya jafar dama dan giya ne ashe.
Don babu tamtama nasan yadda yan giya suke mayensu idan sun sha don muna da yan giya a kauyen mu idan sun shawo muna kanana zamu bisu muna waka sunyi marisa sun sha kwaya har sai manyan gari sun kore mu zamu bar mutum.
Ashe nima zan auri mashayi da zai rika min marisa a gida ina kallo a cikin tashin hankali da fargaba.
Yanzu ni yaya zanyi wani irin hukunci zan daukarwa kaina kan zama da mashayi a gida daya ya zama dole gareni tun ban makara ba insan inda dare yai min daga hannun ya jafar din.
Dama abinda mutane ke yawan fada min kalman inyi hakkuri da hakayan sa da zan gani nan gaba ?
Dama ashe sun san komai suka boye min shima yasan yadda yake ya aureni a hakan don kawai ya cutawa rayuwana ke nan.
Dama wai mami tasan danta haka yake kuwa har ta tsaya tana nuna min wanan kyamar don kawai ina yar talaka ni ko ina yar talakka ai talaka yasan mutuncin kansa da kuma abinda Allah ya hanemu yi.
Gudawa daga garshi ne yazauna min a zuciyana saida kuma ta ya zamu iya gudawa yanzu daga kasan nan tunda shiga jirgima sai idan mutum ya shiryawa hakan.
Ina ko yaya zanyu zanyi ne don mu gudu dani da kanwata daga hannun wanan mashayin tun baikai ga illanta min rayuwa na ba.
Haka nayi rabin kwana a cikin makewayin can na dauro alwala na fito ashe ina ban dakin anyi ta dukan kofan ina ban daki a lokacin banji ba.
Ashe taju ne ya falka yaji dukan kofan da akeyi kamar a cikin mafalki kafin ya nemi tufafi ya saka a jikin shi har mun nufi dakina kamar yadda ya bukata in kaishi dakin nawa.
Ya fito bai ganshi a waje ba ya nufi kofana yana duka don yaji kamshin turaren a falon ya dade yana dukan kofan nawa ba,a bude ba har ya hakkura ya koma daki .
Ranan ba karamin hauka yayi a dakin ba shi kadai dan ya tarwatsa kayan dakin da dama yana hauka wai mun kasance a tare da yaya a daki daya yana zaton wani abu zai wakana a tsakan nin mu ke nan idan mun kebe din mu kadai.
Har washe gari ya jafar din yana kwance bai falka ba ni kuma ina takure a wuri daya naci kuka har idanuwa na sun canza kala don kukan danasha tun dare har zuwa safe ban runtsa ba ga barcin da ban samu ba shima yana barazana a idona.
Karfe taran safe a lokacin nasan su mama sun tashi ko dan ita ta saba fitowa tun safe a gida ko nan din ma da sunyi wankan safe sukan fito falo su zauna.
Ina cikin wanan tunanen lokaci guda naji ya motsa sai kuma ya sake komawa ya lafe ido na tsura mai daga inda nake zaune din a takure.
Can kamar wanda aka tsikara ya mike zubur tare da dafe goshin shi yana murza idanun shi lokaci guda kuma ya bude su ya fara bin dakin da kallo.
Zubur naga ya sauka daga kan gadon tare da karewa kanshi kallon mamaki har lokacin bai ankara dani a inda nake a zaune ba .
Zama ya koma yayi bakin gadon tare da jan wani irin uban tsuki lokaci guda kafin kunnuwa shi ya fara jiyo mashi sautin kukana a inda nake takure.
Da sauri ya mike tsaye tare da nuna ni da yatsa yana fadin ke ke lafiya na ganki haka mske faruwane wai ?
Ya akayi nazo dakin nan wai a nan dakin na kwana kome juyawa yayi ya dan kalli gadon na dan lokaci guda tare da juyowa gareni ya sake kallona yana fadin .
Wai wani abu ya farune kike wanan kuka haka ki fada mi ina tambayan ki kin yi shiru jin da yayi banda lokacin bashi amsa yasa shi jan wani itin uban tsoki ya duka yana daukan riganshi dake saman gadon.
Kai na dago ina kallon shi tare da mamakin shi wai yana nufin baisan abinda ya aikata bane a daren jiya ko me yake nufi da wanan basarwan ?


ZAINAB IDRIS MAKAWA




🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅


6️⃣1️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA


Littafin kudine yar uwa don girman Allah da darajan Annabi kada ki karanta idan baki biya ba don Allah da son da kikewa Annabi.
Ranan nayi kuka har na gaji a daki ba wanda ya sani don na kulle kaina a cikin daki ni kadai kada wani ya fahinci hakan.
Tunane kala barkatai nayi a zuciyana ina nemawa kaina mafita saidai abu dayane ya tsaya min a zuciyana shine ta yaya zamu gudu daga wanan kasan yanzu ?
Gashi ko yanayin tafiyan da mukayi ya nuna ba a kusa da kasa mu muke zaune ba a yanzun don tunawa da nisan tafiyan da mukayi kafin mu iso nan.
Wayyo ni Allah wayyo kaina na fada a fili tare da kara sake wasu sabbin hawaye masu dumi daga fuskana lokaci guda.
Ya jafar me yasa ka kasance a haka dama don shine ka yaudareni ka nace saini zaka aura don ni din na kasance ba yar kowa ba ko kuma don ni din yar kauyece daba zan fahinci halin da kake ciki ba Allah masani.
Ya Allah ka kiyashe aikin aikata sabo komai kankantan shi a rayuwan mu don kawai biyewa duniya ko wayewa mutum yana dan musulmai ya jefa kanshi ga mahalaka irin wanan .
Tir da hali irin naka ya jafar dama mai hali irin naka idan kuma kai mai shiryuwane ubangji Allah ya gagauta dawo dakai hanya madaidaiciya a rayuwan ka.
Mu kuma Allah ka tsaremu daga fadawa halaka itin wanan duniya da rahira na karasa da amin ina share hawayen dake zubo min a fuskana.

Shima ya jamal ranan ya kasa fitan safen da yakeyi don ashe akan idon shi dan uwan nasa ya dawo a cikin mayen sa gida yaga komai yadda ya wakana a lokacin.
Don yana shirin zuwa kofan ne ya samu ya izashi cikin part din a lokacin ne yaji fitowana daga dakin ya kara labewa yana kallon yadda muka kwashe dashi har shigan mu part din nasa.
Baiyi barci ba don damuwa da tashin hankalin daya shiga a lokaci don bai dauka abin dan uwan nasa ya girmama haka ba sai yanzu da idon sa ya tabbatar masa da komai ya gani da idon sa kuma.
A, lal hakikanin gaskiya yaso auren dan uwan shi da wanan yarinyar da farko saidai a yanzu yana jin tsoron kasancewar shi da yar mutane.
Kada yazo ya jefawa mutane yarsu a cikin halaka da dana sani a karshe duk da yana shedar zainab din da hakkuri da juriya ga ladabi gami da biyayya .
Ko wani namiji zaiso ya samu mace mai irin wanan halin nata saidai shi dan uwan nasa gashi Allah ya basa irinta mai hali na kwarai da kowani namiji yake fatan ya samu din.
Wanda yasan hakan na daga cikin abinda yaja dan uwan nasa ga zaben wanan yarunyar don juriya irin na zainab din a yadda ta zauna a gaban mahaifiyar su suna gani.
Dama ace ya mamudne yayi katari da irin wanan mace mai hali irin na zainab din yasan da yanzu lafiya lau take zaune da kowa a gidan nasu.
Yaja wani dogon tsuki yana juyawa daga inda yake kwancen a fili yace mami da ace kinsan halin da dan ki ke ciki da yau kin daina tsanar yar mutane da hattaran ta don kawai wani akida naki can na daban.
Da kinyi nasaran aura mashi yar kawar ki da kike da burin yi har yanzu akan dan naki da yanzu asirin ki dana kowan mu ya gama tonuwa a kasan nan ga baki daya .
Don babu macen da zata zauna da miji mai hali irin na ya j abin kyama ga kowa a zauna lafiya haka kamar yadda yarinyar nan ta kawar da idonta a kan hakan gareshi.
Wani tunane yazo mashi zubur ya mike zaune yana tambayan kanshi wai dama zainab din tasan halin ya j dinne take zaune dashi a haka ko kuwa dai a yanzu ne ta fara gani da idon ta ?
No no no yarinyar nan bata san komai ba don batayi wayyon da zata gane hakan ba da yanzu ta nuna wani alama kan hakan ai.
Lailai ya zama dole ya tunkareta kai tsaye da wanan zancen yaji ra,ayinta kan halin dan uwan nasa kai tsaye idan da shawaran da zasuyi suyi shi a tare tun kan wani ya ankoro da wannan halin na yayan nasa su shiga bakin mutane.
Wanan dalilin ne ya hanasa fita gidan ranan ya fake ya tsare yana jiran fitan yayan nasa da fitowan ita zainab din ya samu su maganta wanan babban maganan daya taso masu din yanzu don shi yafi komai daga masa hankali saboda yaga yayan nasa yayi nisa ga harkokin nasa ko a yanzu taron shi sai an shirya masa sosai.
Sai dai gashi a gidan yau baiga fitan ko wani daga cikin su ba haka dole ya hakkura ya tafi duba tsohuwar dake asibiti don yasan zuwa yanzu tana can cikin damuwan rashin ganin shi akan lokaci da batayi ba.

Barci mai dadi ya kara daukan shi bayan ya samu ya watsa ruwa a jikin shi tare da kokarin yin sallah da ya kubce masa don yanzu wurin tara da wani abu na safe ya koma gado ya sake kwanciya don nauyin da idon sa yake dashi har wanan lokacin na barci.
Abokin shi philis ne ya kirashi a waya yasa ya daure ya mika hannu a hankali ya dauki wayan nasa dake daga gefen shi a yashe saman gado wanda ya zama masifa yanzu ga mutane.
Don mutum yana tashi barci shedan zai zugashi yakai hannu a waya kafin yai yunkurin yin komai a rayuwannshi.
Yoou bros philis ya fada dayaji ya dauki wayan nasa a lokacin don jin muryan shi da yayi lokacin a cikin magagin barci.
Wai har yanzu baka gma barcin bane karfe sha biyu da wani abu yanzu fa na rana ko yau a kwance kake nufin zaka wuni don dan abinda ka taba a daren jiya din ya kare a cikin dariya.
Jafar din ya mitsike idanu dakyau yana kallon agogon dakin nasu can ya tuna da waya a hannu shi yace jiya nasha wanan abin over kan kun zugani da yawa.
Uhumm philis dinyace ta bangaren shi yana dariya tare da fadin kada ka zamo raggon maza fa don ban sanka da wasa ba mutumina ?
Zan sauka kasa yanzu inga mai gidana ke ciki idan na watsa ruwa zan fito zuwa karfe biyu nan idan na samu time ya bashi amsa da hakan tare da kashe wayan shi.
Mikewa ya daure yayi daga kan gadon a hankali sai lokacin idon shi ya sauka ga ta,asan da taju yayi mashi a dakin a daren jiya.
Dakin yabi da kallo ko ina tare da jan tsuki mai karfi yana fadin zanyi maganin wanan gay din dan iska duk akan me yayi min wanan barnan haka a daki.
Daidai zai mikene ya tuna da zancen kwanan da yayi a dakina ya kara jan tsuki don fahintar dalilin taju nayi masa wanan aika aikan haka a daki.
Daurewa yayi ya shiga wanka tare da kara tsarkake jikin sa ya fito kara bin dakin yayi da kallo yana mamakin taju din a ransa.
Tsuki ya kara yi ya nufi wurin tufafin shi yana dauka tare da magana kamar wanda ya tabu yana fadin duk ba komai ke jefani a tashin hankalin nan ba sai sakaci da addini na da nakeyi kan wanan shegun abin kyamar dana jefa kaina a ciki saboda abokai da ba addinin mu daya ba giya da wanan harkan da mukeyi.
In banda sherin wa yan nan ai da yanzu yana zaune lafiya a cikin salamansa kamar kowa amma komai a yanzu zaiyi sai a boye jamar wani mara gaskiya a cikin yan uwan shi.
Gashi saboda shan da yayi daren jiya ya jawo mai har yar mutane ta kamashi a haka saboda fita hayacin shi dayayi kan giyar da cocaine din.
Ahaka har ya shirya ya fito sai sai gidan tsit yake kamar babu kowa a cikin sa a lokacin don su mama basu dade da shiga dakin su ba lokacin.
Abinci ya fara nema don jin cikin sa da yakeyi kamar ya yi kwanaki baici abinci ba a cikin sa yake jin yanayin kansa a lokacin.

Ina kwance a dakina duk da hasken ranan daya gauraye daki a lokacin ni duhu nake gani a dakin ko ina saboda daci da radadin da nake ji a zuciyana.
Ga tunane ya tsaya wuri daya cak don ban san abin yi ba a yanzu don banda wani mafita da zai fisheni ga kangin shi a kasan mutane.
Ina daga kwance kaina na kallon sama saboda nayi kukan har na gaji nabawa kaina lafiya don idona daya fara yi min dishi dishi a lokacin.
Jin an budo kofana baisa na dago kai naga mai shigowa dakin ba a lokacin illa ina kwance a yadda maishi ya sameni.
Tun daga kofa ya hangoni yadda nake kwance din nayi motsu mutsu dani alaman nasha kuka har nagaji tun daren jiyan.
Jikinshi yaji yai mai sanyi a lokaci guda shi kanshi yasa bai kyauta min ba yana tsaye ya rasa abinda zaice min sai faman kallon .
Kallona ya tsaya yakeyi ya rasa kalman da zai fara min magana dashi wanan ne rana na farko daya taba jin kunyar wata ya mace a rayuwan shi bayan mahaifiyar shi.
A da kan bai dauki abinda yakeyi a matsayin wani abu ba face holewarshi da lokaci kawai sai gashi yau yarinyar daya raina ma wayau a da ya fara jin kunyarta a duniya.
Da kyar ya iya kaiwa zaune a bakin gadon a kusa dani yayi gyaran mutya yana fadin lafiya kike zainab na ganki haka ?
Ban
Showing 201001 words to 204000 words out of 390011 words