banjin za a karasa lectures din dani don irin rudanin da zuciyana ya shiga tun bayan bayanin da naji daga wanan matar.
Gidan na shigo suku suku dani gaisawa kawao nayi da fadila na wuce zuwa dakina jiki ba kwari .
Don gaba daya zuciyana da kwakwalwana sun fara kawo min wami zargi akan ya jafar din.
Sai nake tariyo wasu abubuwa can kasan zuciyana wanda nake ganin zargine kawai nakeyi alokacin ba gaskiya zuciyar nawa ke fada min.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



LITTAFIN NAN NA KUDINE KIWA ALLAH KI BIYA KAFIN KI KARANTA DON FITA HAKKIN JUNA BA TARE DA SHIGA HAKKIN JUNA BA.


Washegari na kasa tashi don zazzabin daya rufeni lokaci guda saboda tunane daya tsaya akan lalai akwau ayan tambaya akan ya Jafar da wa yan nan mazan dake zaraya a dakin shi.
Ba tare da wani shamaki ko tsoro ba wanda koni matar shi banda halin yin abinda sukeyi a gidan kai tsaye sai tare da umurnin shi.
Wanan dogon tunanen ne yasa na fashe da kuka lokaci guda ba tare dana sanda zuwan shiba a lokacin.
Har yakai zazzabi ya sauka min hakana dunkule ni daya a daki ina rawan dari gashi na kasa tashi in kashe AC dake aiki a dakin.
Washegarin ma da kyat na iya tashi nayi sallah na koma na nade saman gado har saida halimatu ta shirya zata tafi ta shigo sallamana ta sameni a hakan.
Taje ta fadawa fadila suka dawo tare dakin tare da ita da kyat na tashi nasha tea din data hado min a lokacin.
Da kyat na samu na kurba sau biyu na koma na kwanta ban dade da kwanciya ba wani irin amai yazo min lokaci guda.
Da gudu na mike zuwa bandaki saidai kafin nakai bandakin har na sake aman ko sai da kyat na karasa ciki.
Hankalin fadila ya tashi sosai don halimatu ta rigada ta wuce kada ta makara bus ya wuce yasa aka turata ta tafi ba don taso tafiyan ba a lokacin.
Fadilace ta gyara dakin har ban dakin ta saka kamshi tare da bude dakin don iska ya shigo haka yasa shi sanin cewa ina gidan ban fita ba.
Don ya fito a cikin shirin shi yana sauri har ya zauda kofan part din nawa sai kuma ya dawo baya da mamakin ganin kofan nawa a bude .
Hakan ya sanar dashi ban fita zuwa school ba ranan ke nan ya shigo cikin dakin tun daga nisa ya hangoni saman gado a kwance ina rawan dari.
Lokacin fadila ta fita zuwa dakin ta don ta dauko min magani da tazo dashi irin namu na Nigeria da muke sha a can gida.
Zainab ya fada a dan rude yaji ban tankashi ba yasa yakai hannu ya kware bargon da nake rufe dashi ya kai hannun shi a hankali kamar mai tsorona yana taba jikina daya gama gashewa lokaci guda da zafi radau.
What ya fada a razane a cikin dan rudewa tare da fadin baki da lafiya kike kwance haka zainab baki fadi an kaiki asibiti ba ?
Nan ma ba amsa sai kara lefewa da nayi don kware bargon dayayi yasa na kara jin sanyi na shigana lokaci guda.
Fadila ce ta shigo da saurin ta dakin dauke da magani cikin karamin plate sai goran ruwa da cup a hannun ta daya.
Tana ganin shi ta kadu da sauri zata juya ta bar dakin sai ya dago kai yana fadin meye wanan kika dauko ?
Paracetamol ne da maganin amai na dauko zan bata tasha don jikinta da yai zafi ko zai taimaka mata ya sauka.
No kada ki bata barta na kaita asibiti yanzu zaifi waina yaya akayine ina gida baku fada min bata da lafiya har haka ba sosai.
Sir nima yanzune Sadiya ke fada min tazo sallaman ta zata tafi ta sameta kwance haka a dakin zazzabi ya rufeta.
Mayar da kanshi inda nake yayi ya dan tsura min ido kadan kafin yace dani tashi ki shiya muje asibiti yanzu.
Kamar banji me yake fada ba don duk da halin ciwon da nake ciki hakan bai hanani jin wani irin takaicin shi tare da tsanarshi ba a kasan zuciyana.
Kara maimaita maganan shi yayi da fadin tashi ki taimaka mata ta shirya ina waje ina jiran ku.
Da karfi na dago a hasale ina fadin wallahi ba zan tafi ba na kwanmace na mutu a hakan da ka kaini asibiti.
Mene yace da mamaki yana kallon yadda nake magana da kyat a cikin karfin hali na koma na kwanta ina kaduwa saboda sanyin da nakeji a lokacin.
Ke wani irin sakarci ne wanan kije asibiti zaki tsaya kinawa mutane gardama haka ?
Ba za a tafin ba na kara fada a yadda nake kwance ina kaduwa da kyar kake jin magana na idan inayi.
Wai meke damuwantane ya juya yana tambayan fadila ta girgiza kai tare da fadin nima haka na ganta yau sir ban san meke damunta ba.
Juyawa yayi ya fita dakin fadila ta matso kaina tana fadin tashi kisha wanan din mu gani ko zai taimaka maki kafin ku tafi.
Sai lokacin nayi magana ina fadin bazan tafi ba wallahi anty na tsani yaya jafar bana son ganin shi don, , , .
Wani irin yun kurin amaine yazo min lokaci guda ya hanani karasa zancen danake son fada a lokacin.
Da kyar na mike na shiga ban daki wanan karon yellow din amai nake alaman dai fever mai karfi ya kama jikina lokaci guda ko.
Da kyar da bin bango na samu na fito daga ban dakin na koma na samu wuri na kwanta ina mayar da nunfashi da kyar tare da lumshe idona ina jin wani irin takaicin kasan zuciyana.
Ba barci ne ya daukeni ba amma haka na lafe kamar mai barci a lokacin don yadda nake jin kaina na saramin lokaci guda.
Haka dai nake kwance tana tsaye a kaina cikin damuwa sai can kamar bayan awa guda naji ya sake shigowa dakin.
Wanan karon tare da wani likita suke shida kanshi ya hau gadon ya dagoni na bude idanuna da sukai ja don bacin rai ga ciwo na sauke a kasan zuciyana.
Likitan ne ke fadin meya sameki pretty girl tare da juyawa ya tambaye shi is she your sister ?
Yace dashi yes yace yaushe na fara ciwo haka yace da dare kamar yasan hakan sai likitan ya ciro kayan aikin shi ya shiga aunani na dan lokaci guda tare da yi min tambayoyi ina bashi amsa da kyar.
Allura yai min da magani nasha sai barci na dauki lokaci mai tsawo ina barci kafin in tashi ina neman abinda zanci ga zufa yana fetso min a jikina.
Tea nasha sai naji dan karfin jikina na tashi nayi sallah azahar kasa tashi nayi sai kuka don tunanen abinda ya tsaya min a rai.
Fadila ce ta turo kofa ta samu ina kuka ni kadai a cikin dakin da sauri ta karaso inda nake tana fadin zainab lafiya wai meke faruwa ne dake haka ?
Alama ya nuna akwai wani abinda ke damun ki a zuciyar ki kike boyewa kai na dago a hankali na kalleta tare da fadin.
Ba komai anty fadila na fada ina mayar da kaina wasu hawaye masu zafi suna fito min ido kawai ta tsura min kafin ta sauke ajiyan zuciya ta juya ta fita.
Bata dade ba ta dawo dauke da abinci ba tare da tayi magana ba ta aje a gaba kafin ta samu wuri takai zaune kasa a kusa dani.
Zainab kome ke damun ki don Allah ki daure kici abinci kada wani ciwo kuma ya shige ki a yanzu don nasan tun jiya baki ci komai a cikin ki ba.
Kai na dago da niyar yin magana sai ta dakatar dani da hannu tana fadin don Allah ki daure zainab kome meye da baya mayi zancen a tsanake dake.
Jin haka yasa na kai hannu a hankali na jawo abincin na fara ci a hankali badon yai min dadi a baki ba duk da itace ta dafa don irin abincin mune na gani.
Na dan tsakura na mayar na rufe tare da daukan ruwa na kurba sai can na sauke ajiyan zuciya ina fadin na tsani yaya jafar anty fadila.
Subbahanallahi zainab meye maki haka da har zaki tsaneshi irin haka lokaci guda.
Ban iya magana ba illa fadawa jikin ta danayi ina sheshekan kuka har nayi nagaji na kyale don kaina tayi shitu tana kallona kawai tare da nazarina.
Ki daure ki tashi a kasan nan kada sayin kasan ya kamaki ki koma saman gado ta fada tare da mikewa tana dauke kayan abincin dana ci.
Mikewa nayi kamar yadda ta ban shawara na koma saman gado na kwanta a haka wani barcin ya daukeni don barcine a idona saboda rashin samun barcin dare da banyi ba.
Wasa wasa kwana biyu nayi a kwance ina jinya idan ya shigo dibani bana yarda ko in kalli inda yake haka kuma yayi maganan shi ya gaji bana tankshi haka zai fita daga dakin.
Akarshe dai koya fahinci wani abune baya shigowa sai idan ya dawo daga wurin aiki zai lekoni ya yai min sannu a tsatsaye ya fice.
Har naji sauki na fara fita school kamar yadda na saba saidai duk wanda yasan ni yasan na rame sosai a lokacin.
Don nasawa raina tsanan komai na yaya a gidan ko abinci banda yadda zaiyi ne da ba zanci abincin gidan shi ba yadda nakeji tsanarshi a raina.
Ashe wanan matar yar gargajiyan kasan kwana biyu da banzo ba ta damu da rashin ganina kuma bata san wani da nake hurda dashi ba a school din balle ta tambayeshi ni.
Bayan mun fito daga lectures ne muna break ta sameni zaune ta gaidani itama ta samu wuri ta zauna tana tambayana dalilin rashin ganina kwana biyu da batatyi ba.
Nake fada mata tun ranan nan da muka rabu banda lafiya ina gida kwance yasa ban shigo ba tayi min sannu da jiki na amsa da godiya.
Muna nan wurin zaune don na fahinci itama irinane bata son hayaniya itace ta dauko hiran lectures din da akayi bana nan har ta ban handout din ta na kofa don karatu tare dayi min bayani.
Saidai taga hankallon ya dauke ga kallon wasu mutum biyu da suka wuce mu suna rugume da juna yasa ta kura min ido na dan lokaci tana nazarina.
Dafani naji tayi na waigo da sauri take fadin lalai ni bakuwace a wanan kasan wanan ai yanzu ba komai bane a nan don yanzu basa ko boyon wanan abin.
Gashi kuma babu wani addinin daya yarda da wanan dabi,an na auren jinsi suna dai yine don ko wani addini suna da tarihin mutanen farko da aka halaka kan wanan dabi,an.
Dan murmushin yake nayi tare da fadin ni abin ya daure min kaine ai tun ranan da tayi min wanan bayanin ina mamakin yadda mutum zai auri dan uwan shi namiji haka ?
Me mutum zai gane ga hakan nan dai ta shiga bani musalan abubuwa da dama wanda ban sani ba da ace tasan halin da nake ciki da ta bar duk wani bayanin da take min a lokacin don yadda zuciyana yake tafasa.
Dala dala tayi min bayanin su a gurguje tare da irun alamoninsu da yadda sukan fara approching din mutum har su ja ra,ayin shi ga abin.
Haka na koma gida bayan mun rabu a cikin wani sabon tashin hankali har yakai na kasa rike abin a zuciyana.
A weekend din na samu anty fadila da zancen a dakin su ina kuka nake mata bayani ban boye mata ba nace na fara zargin ko yaya Jafar shima wanan akidan yakeyi da yake yawan mu,amula da maza yan uwan shi a daki daya.
Kai haba zainab yaya zaki saurin zargin mijin ki da wanan dabi,an marakyau haka har ma idan kina zargin sane ai zaki iya saka ido ki fahinci wasu halaiya nasa harki gano hakan .
Amma baki yankewa kanki hukuncin da baki sheda ba irin hakan da sauri don kinga yanzu kece dakin fada mutane zasuyi saurin yarda da maganan ki.
Wanan zancen da mukayi yasa na tsiro gyaran dakin yaya da kaina a wanan lokacin duk naci karo da wani abinda ba daidai ba a dakin zan kwashe in zubar dashi .
Haka kuma giyan shi har yakai yanzu ya boye abinsa a inda ban sani ba sai ga wautana na dauka ya barsha ne a yanzu.
Sai ranan ko yaya akayi ya shigo dashi dakin ban sani ba na gasu a falo ya aje su a cikin leda washegari na shiga gyara na gansu na kwashe duk na farfasa su.
Wanan abinda nayine ya kawo muna matsala a tsakanin mu karo na farko a zamana dashi don ina zaune a daki da dare ina karatu ya shigo min dakin kamar mahaukacin zaki yana fadin.
Ke ina abinda kika daukan min a dakina suke kamar ba zan dago kainba saida ya kara tambayane.
Na dago kai na dan kalleshi nace wani abune ke nan nidai nasan abin haramun na gani a dakin na dauke na zubar.
Ke kada ki kawo min maganan banza a nan tun kan a haifeki na haddace alkurni balle ke yanzu kizo min da wani maganan banzaki can .
Indai gyaran ke nan da kike min daga yau sai yau idan bani na bukaci da ki shiga min part dina ba.
Ba tare dajin komai ba a raina don duk wani tsoron shi ko nauyi ya kawo a zuciyana nasa don haka na kalleshi ido da ido nace yafi min nono fari yaya don dama don Allah nake maka.
Idan badon Allah me zai kaini gyaran dakin da Allah kasa na fushi da mai shi don abin haramun din da ake aikatawa a ciki.
Har ya juya ya waigo da wani irin karfi tare da fadin me kike nufi da wanan zancen naki kina nufin dakin nawa haramun ne ko me ?
Ba dakin ba yaya kai kanka haramun ne don shi kake aikatawa ga shan giya ga babban abin da Allah ya haramta da kakeyi a dakin.
A cikin wani irin tafiya ya fara takowa zuwa inda nake zaune ina karatun daya sameni a dakin banji tsoron shi ba ko kadan ban kuma motsa ba daga yadda nake zaune.
Hannun shi ya mika kamar zai cafkeni ban san abinda ya tuna ba kuma ya fasa tare da dan kafeni da ido na dan wani lokaci.
Nace idan kayiwa kowa wayau yaya kana ganin zakaiwa Allah ne yau gashi har nayi wayau gane abinda kake boyewa mutane na halin ka.
Ka tuba ka koma ga Allah tum kan lokaci ya kure maka zaifi na yarda ni yarinyace ban san komai don ka yaudareni ka yaudari iyayyena.
Amma yanzu idan na zauna da kai da wanan halin naka nina jawa kaina idan wani abu ya sameni.
Don haka yaya na rokeka ka mayar damu gurin iyayyen mu don Allah tun kan masifan ka ya kai ga shafan mu.
Gara in zauna a cikin talaucin gidan mu da in zauna a cikin wanan sabon Allah tare dakai nayi ma alkawarin in dai nice babu mai jin wanan zancen a bakina har duniya ta tashi.
Na fadi hakan don kawai ya kyalemu mu koma Nigeria don yakai yanzu tsoron lamari shi nakeyi ga baki daya.
Wani irin kallo yai min ga idanun shi sun kara rinewa lokaci guda ga baki daya halittanshi ma ya sauya lokaci guda .
Naga ya juya ya fice yabar dakin da sauri wani irin kuka na fashe dashi lokaci guda ina mulmula saman gado kamar mai iska.
Tunda wanan abin ya faru tsakanin mu ban kara sashi a idanuna ba har tsawon sati biyu gashi nasawa kaina damuwa da tsoro duk nabi na lalace lokaci guda.
Ashe tafiya yayi bamu sani ba don bani kadai ce na shiga damuwan rashin ganin sa ba kowa ma a gidan ya damu da hakan.
Ranan sai gashi kwaran ya dawo ana shigo da kayan sa gidan muna zaune a falo suke mashi sannu da zuwa da kyat na iya budan bakina na gaidashi.
Ya amsa shima a dakile ya shige part din shi kai tsaye sai daga baya aka shiga mai da kayan shi part din shi.
Har kwana biyu da dawowan shi babu wani sakewa a tare dashi nima ban bi ta kansa ba do yanzu banda damuwa a gida ga anty fadila tare damu.
Can kuma school ga kawata da yanzu muka saba da ita sosai muna kula junan mu sosai da ita kamar mun dade da sabawa .
Idan ma ina da damuwa bai wuce son komawa gida Nigeria dana sawa kaina a yanzu don hankali ga baki daya ya
Showing 237001 words to 240000 words out of 390011 words