Ya bude ido yana kallona kamar me nazarin wani abu ya ce dama kina dashi tare dake baki bani nasha ba nake ta wanan wahalan haka naji dadin magani sosai ina shan sa kamar an zare mi ciwon naji lokaci guda.
Ban taba amfani dashi ba na fada ina juya don na matsu in bar wurin a lokacin kada ya kureni har ya gane ba gaskiya na fada mai ba.
Kwana biyu kwatsam su mami suka diro garin shi kanshi bai san da zuwan su ba ban nuna mata komai ba don tun lokacin da mukai wayan nan da ita wani abu bai kara shiga tsakanin mu ba kuma koda wayane.
Don sai naga kamar kwata kwata dai mami bata yi danine a rayuwan ta don banga laifin da za a dora min kan mutum mai shekaru kamar ya j ace wai nice zan matsa mai ya kula da kansa bayan shine ya kawo mu kasan ai.
Nan muka shiga dawai niya da su kamar ba komai a zuciyana sai dai a gaskiya na barwa kaina duk wani abu da nake shiryawa a yanzu game da kowan su gidan.
Lafiya kalau zan shiya masu abinci idan masu aiki sun gama ba zan fita ba sai na gama dasu don wanan tafiyan ba irin wancan bane da sukazo da yawan su .
Wanan daga mami sai samarinta biyu da Aisha kawai suka zo part daya aka bar masu don hakane ba wani takura a tsakanin mu yanzu.
A yadda mami take matukar son diyan ta wanda a yanzu na kara gane hakan sosai yadda duk da ya J yaji sauki a yanzu.
Amma hakan bai sa wai mami ta nuna wai ita jinyar jafar din takeyi ba a fili tana nuna tafi kowa sanin zafin dan ta da sanin abinda yake damun shi .
Wanda banyi tunanen cewa jafar din zai fada mata ba don da zai iya fadiawa wani nasan nice ta farko da zai fadawa hakan.
Kawar da ido da kai ga komai yasa mami din bata samu wani kafan yi min wani rashin mutunci ba don haka muka zauna lafiya da kowa a cikin har azumi yazo suna kasan tare damu.
Ranan a na zaune da safe samarin basa ciki suna waje sai shi da mami da Aisha ne sai ni da na shigo gaida mami din da safe zan fita zuwa school.
Baki fita ba ke nan har yanzu kina gidan nan ya fada yana zaune a kasa kusa da kafan mami din abinda ban taba ganin yayi ba tun zuwan mu kasan zama a kasa.
Karatun ai ba wai ta saka a ranta bane nake ganin mami ta fada ya dan gyara zama yana fadin ai mami zainab ta saka karatun nan a ranta sosai kuwa.
Zainab din zaka ban labarin halinta a yanzu kuma jafar don ta zama matar ka komai ko ta canza ne ban sani ba ?
Sorry ma na mance kin fini sanin halinta ai tana nan har yanzu da sanyin halin nan nata ai sai mami din taja wani tsuki tana kawar da kai.
Aisha tace ya j ai yanzu ba zaiso a fadi wani kalma a kan zee ba koda tayi laifin ma balle yana ganin batayi ba .
Aisha ke nan ki bar ganin mami da zainab suna abin su na uwa da yarta kice zaki saka baki tsakanin su har yanzu sai Allah ni zan baki labarin hakan.
Ni dai ina zaune a inda nake ban ce da kowa kala ba a cikin su naji yaci gaba da fadin a daidai lokacin dana mike tsaye yana cewa.
Har sako fa mami zata aiko dashi tun daga can ba zan san da hakan ba sai idan tunanena ya bani haka.
Sako kuma naji mami ta fada da dan mamaki ni dai fita nayi ban karasa jin zancen su ba.
Sai bayab na dawo ne na shiga gaida ita ta tsareni tana tambayana da fadin zainab jafar ya gaya min kece kika bashi magabin da yai sanadin barin shan giyar sa ko ?
Na dago kai da mamaki tace ya fada min komai don shi a nasa zaton ko nice na aiko da abinda kika bashi din har yaji sha ya fice masa a rai ina tsaye ne a lokacin sai nakai zaune.
Kafin ta kara fadan wani abu jalal ya shigo dakin yana fadin mami garin nan yana da dadin azumi sosai don basu da zafi irin namu can Nigeria gaskiya.
Jekiki huta zamuyi maganan daga baya mami ta fada don ganin jalal din ya kai zaune a lokacin .
Ya dago ya kalleni yana fadin dama magana ake irin na uwa da yarta nima dai ina ganin irin auren ya j zanyi mami in samu mata kamar zainab din ki don bana son mace irin Nuriya gaskiya.
Fita nayi daga dakin ina dan murmushi don abinda ya jalal di ya fada saidai zuciyana cike da zargin maganan mami yake alokacin
Bata kara min maganan ba nima haka banwa ko J din maganan ba saida akai azumi ashirin suka tattaro suka dawo Nigeria.
Munyi sallah lafiya wanan sallah har idi muka tafi wanda hakan bai taba faruwa damu ba tun zuwan mu a gida zamu dai zauna .
Sai dai mu kalla yadda ake bukukuwan sallah a kasashen duniya wanda mu nan cikin gida muke babu wani celebration da mukeyi.
Sai gashi a wanan shekaran tun da daren muka bar gidan mu muka kwana a wani hotel a cikin wani unguwa ashe a can ne masallacin su yake da suke sallah a garin.
Bayan an sauko ne motocin mu suna jiran mu muka dawo namu gidan wanan kan mun san ayi sallah don yadda yaya ya nuna muna har kwana biyu muna shagalin da murna da kai ziyara a gidajen yan uwa musulmai dake kusa don suna da musulmai tsararu a cikin kasan sosai ashe.
Hutun sallah ba yawa ga ma,aikata don haka sati daya mukayi ana shagalin muka koma makaranta don ci gaba da karatun mu.
Yaya kan a bangaren shi jiki yayi sauki sosai don bai wanan dafan cikin da yake yawan yi a baya yanzu.
Gashi yayi wani kyau raman da yayi don zafin ciwo a baya duk yanzu yana shigewa ba a ganin wanan sosai a jikin shi don dan cikowan da yakeyi yanzu ba wannan kaman.
Sai dai ina yawan tuna halaiyan mami na nuna kiri kiri son danta akan komai da take min don na lura nami ba ganin laifin dan nata takeyi ba asalima tana kokarin dora komai ne a kaina a ganina.
Don ko dan zaman da mukayi dasu anan duk da da farko taso nuna hakan a fili amma daga baya sai naga kuma ta canza ta daina nuna min wani abu.
Nima sai na dauka a hakan nake nuna ba komai a raina don haka kowa ya aje a ranshi da ba komai din dai.
Ganin yadda yanzu yaya ya koma wani silent bai son hayani duk da dama can din shi din ba mai hayaniya bane sosai amma dai sai na yanzu din yayi yawa sosai.
Don zai iya zama a wuri duk abunda zamuyi ba zai ko daga kai ya kalli mutum ba balle mu saka ran zaiyi magana kan kiriniyar mu har ya gaji da zaman shi ya tashi a wurin zuwa part din shi.
Gama sadiya da har rawa da marming zata dinga yi koda yana zaune don ba karamin sabawa sukayi ba dashi sosai a yanzu.
Wanda tun ina zargi a kan hakan har yakai na debe komai a raina nima mai dan girman bai damu dani ba balle ita da keda sha uku yanzu cif a duniya.
Yau ma kamar kullun ya dawo wirin aiki da yanzu mun saba dashi idan ma ya dora dan dakiku a kai mun sani zamu fara fadin yau yaya bai dawo in time ba.
Shiko da ya dawo baya zuwa part din shi kamar yadda yakeyi a baya nan wurin mu zai shigo direct mu gaisa ya dan zauna damu na lokaci kafin ya shige part din shi sai kuma bayan sallah isha,i zai fito aci abincin dare a tare tun bayan zuwan su mami wanan ya zama muna dabi,a a gidan yanzu.
Zaune nake na tasa laptop a gaba ina aiki ban san shigowan shi part din namu ba don itama sadiya ta shiga ciki dauko littafin da take assigment kan shi.
Muryan shi ne daya duka bayan kujeran dana zauna na mike kafa ina aiki a cikin system din na shagala ga karanta abinda nake sercheing a computer din.
Naji muryan kamar daga sama yana fadin wanan ai da wuyan fanhinta da kin bi ta cikin Google direct zaifi ki fahinta ai.
Ganin yadda na dan kadu ne yasa ya dan shafo kaina yana fadin kin cika tsoro da yawa duk security din dake gidan nan amma kike tsoro haka zainab ?
Ban ji fitowan ka bane yaya sai muryan ka danaji a kaina yasa na tsorata da hakan.
Zagayowa yayi ta gabana ya zauna yana fadin when last kukayi waya da mami tun bayan komawan su gidane wai ?
Da sallah ma ai munyi waya sau biyu dasu na bashi amsa ina dagowa daga duken da nake ina kallon shi don jin dalili tambayan nasa.
But tace dani mana yanzu kin daina kiran ta duk da na fada mata kin fara exam a yanzu baki da lokacin komai saidai tayi fada cewa exam ai ba zai hana ki kirasu ba .
Zan kira na bashi amsa ina tagumi don nasan wani abin ke shirin tasowa kuma a kan wanan maganan da mami din tayi yanzu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



BARKAN MU DA SHIGA WANAN WATAN MAI ALBARKA YAN UWA UBANGIJI ALLAH YA SADA MU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN WATAN ALLAHUMA AMIN, , , ,

LITTAFIN KUDINE YAR UWA KADA KI MANTA DA HAKKAN DON KAUCEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , ,


Akwana a tashi ba wuya a wurin Allah yau gashi har na kamala karatuna a ta fannin fasahar kimiya a kasan chaina inda na fito da sakamoko mai kyau wanda yaya jafar ya nuna jin dadin hakan a fili har ya kasa boye farin cikin shi ga hakan.
Yayin da sadiya take matakin yar gaba da primary a shekara na biyu zata shiga na uku a yanzu daidai lokacin dani na kare nawa karatun .
Har lokacin muna matsayin kannesa ne ga ya J da muke zaune a gidan shi wanda kuma ta dalilin shi muka samu wanan matakin na ci gaba da muka samu a rayuwan mu.
Eh ba zance ya j ya daina duk wasu mugayen halaiyan sa dana san su a baya yana yi ba don a yanzu in ma har yana yine saidai in a boye yake wanan rayuwan do banga hakan a gare shi ba gaskiya.
Asalima a yanzu ga baki daya ya koma kamar ba ya J din da muka sani a baya bane don ga baki daya ya canza gaba daya .
Ya koma wani irin mutum mai taushi da tausayi ga ibada da kula a tare dashi ga natsuwa da kamala da kullun yake kara sauka masa.
Banga wani shirin da yaya yakeyi don zuwan mu gida ba asalima ni yanzu da zaman gida kawai nakeyi yasa wanan damuwan yake damuna a raina har karshe na kasa boye hakan a zuciyana.
Yau tun safe na tashi da wanan damuwan a raina gashi ni kadai ne a gida haka zan wuni daga kallo sai in shiga interneat ina searching shine kawai aikina.
Ina zaune a babban falon mu tv na aiki saidai ba kallon nakeyi ba hankalina yana gun computer na dake gabana ina hada wani kimiyan da nake tunanen hadawa danaga ana tallan shi ko ina a kasan.
Pretty me kikeyi haka ya fada a bayana na dan dago kai na kalleshi tare da dan sake murmushi a fuskana ina fadin yau ka dawo da wuri haka yaya ?
Na dawo ne don nasan ke kadai ce zaune a gida yanzu yasa naga ya dace ba dawo ba dubaki ashe ma na manta kina da abokin hira gashi a gaban ki.
Wanan bai rage min komai yaya sai kewan gida da yanzu yake damuna sosai ina son zuwa gida na ga Inna ta da yan uwana yaya .
Wani kallo yayi min daga inda ya zagayo ya zauna a gefena gida a yanzu baki ganin yin hakan zai taba karatun sadiya ?
Ai ba don karatun ta muke nan ba na fada a dan hasale OK tunda ke kin karasa naki zaki fadi haka ko ?
Ba hakana bane yaya gani nayi kayi alkwarin hakan a baya don Allah yaya ka kaimu gida mu duba su yanzu kusan shekara biyar ke nan muke nema rabin mu da gida fa.
Ba yanzu ba zainab gaskiya don so nake kici gaba da karatun ki a cikin shekaran nan in Allah ya yarda.
Ba zan tsaya karatu ba a nan gida zan koma karatun ya isheni haka yaya nima fa haifana akayi zanso na samu ladan da ko wani da ke samu ga hakan.
Bai min magana ba sai mikewan da yayi lokaci guda ba tare da yai min magana ba ya fice a falon na bi shi da kallon mamaki.
Wanan dan maganan ya jawo muna dan tashin hankali a tsakanin mu har yakai munyi dan kwanaki baya kula wani harkana a gidan yana shan kamshi dani.
Ban shiga harkan shi ba duk da hakan yana damuna sosai don sai yanzu na san ashe ba karamin sabone tsakanin mu a yanzu.
Tun ina daurewa har ya kai na kasa hakan ina shawara kan na same shi na bashi hakkuri sai dai nakan tambayi kaina idan naje ince masa me ?
Ban san ya ake abi sallon ba miji hakkuri ba indan irin haka ya faru a tsakanin su balle mu dake zama irun na wacin gadi da juna kinga hakan ashe zai min wuyan fahinta don nawa kaddaran auren yana daban dana sauran mata gaskiya.
Don haka ban kara gigin wanan shawaran a raina ba don haka na kawo ido na zuba mai kawai na bisa a hakan kowa yana harkan gaban shi a tsakanin mu.
Ina kallo sai dai ya dan shigo yai magana da sadiya ba zai dade ba ko ya zauna zai fita sai kuma gobe.
Saidai hakan ni bai hana in ya shigo da safe na gaidashi ba ya amsa min a dakile gashi ba inda zan kaishi kara inji sanyi .
Wurin mamine nasan ko nakai goya masa baya zata yi kan hakan karshe ma ta kara min wani zafin da yafi wanda nake ciki a yanzu din.
Don kanshi ko me ya gani ranan muna zaune falo da dare da sadiyan ba wani hira mukeyi ba sai rage dare a tsakanin mu ya shigo.
Ga hasken kwan falon na wuta ya haska mu tar ina zauna a cikin wani riga mai shara shara a jikina rigan baida hannu sune irin kayan dana sakawa a kasan don yana sauka min har kasa .
Gasu su ba jallabiya bane ba kuma abaya ba haka suke kamar kayan yan brazil da sukafi amfani dashi wurin wani bukukuwan su na shahara.
Sai dai ni da ba bukin nake zuwa ba a gida nakan saka abina ko shi ba don kwaliya ba don dai kawai ina dasune da yawa nake amfani haka dasu.
Kayan suna min kyau sosai a jikina idan na saka saidai ba wanan a raina nidai zan saka kawai don ba wanda zan burge ga hakan idan ma nayi ne don shi din ba wai burgeshi zanyi ko jan ra,ayin shi ba a kaina.
Sadiya yau kuna wani show ne a nan banda labari ya meka gani ta fada tana dagowa daga kwancen da take tayi rub da ciki saman kujera.
Gani nayi dai yau kunyi wani kyau daku ko zamu fitane ku ga gari ko kada wanan kwalliyan haka ya tafi a banza.
Ba a banza bane yaya tunda ka gani har ka yaba ai idan mace tayi kwalliya a mijin ta tayi akace .
Daga inda nake zaunw na watsa wa sadiyan wani kallo mai harara don abinda ta fada din nake fadin.
Miji sadiya yaushe nayi auren har zan wa mijin kwaliya ya gani dani da wance bata da aure babu bambanci a tsakanin mu a gun wasu daine nake matar aure kamar su inna da sauran yan garin mu.
Maimakon yai fushi da abinda na fada sai gashi ya wasance yana fadin sadiya kin yarda dav zancen nan nata wai ?
Gaskiyane yaya duba ga har yanzu bata haihu ba tana da wanan hujjan don burin su inna a kullun tayi waya damu zanji tana tambaya wai har yanzu shiru babu labarin haihuwa gareta ?
Killa shiyasa ta fadi hakan yanzu duba ga sauran yan kauyen mu sa,annin auren ta ai duk
Showing 288001 words to 291000 words out of 390011 words