domin kuwa baqin cikina ne ya kasheshi saboda ya ganni da cikin Zubeida, uwata kuma, ihihi, ai da hushina ta mutu, wallahi na rantse muku da b'acin raina ta mutu, Bala kuma, hum wai wai wai, ai nice nan nasa aka tura mishi aljanu sukak
kasheshi, wannan yarinyar kuma, matarka ba, matar Umar Faruk, ai tunda ta samu ciki muka bayar da cikin ga aljanu, kuma suka zuba mata cutar da zata kasheta, amma wannan tsinannen yaron ya taimaketa."
Wannan maganganu ne da kullum saita fad'esu, shi yasa Zuby bata zuwa inda take, su Uwani ma basa zuwa gidan, ana haka tsawon wata takwas a gidan wata rana ta fita basu sani ba, ashe kiran ubangijinta ne ta amsa, a titi mota ta kad'eta sai labari mutanen gidan suka samu, sam yayanta babu wacce tayi jimamin hakan, wannan dalilin ne yasa malam ya tarasu ya musu nasiha sosai ya fad'a musu mahimmanci uwa, duk da dai yasan alhakine ke binta, duk da sun bita da addu'a amma dai Zuby kam ita dai ta riga data tsani mahaifiyarta kawai.
Ganin ta daina walwala a gidan yasa Umar Faruk ya tilasta mata komawa islamiyya itama, daga ranar suka fara zuwa tare da Khairat da sauran yara, bayan wani lokaci kuma Umar Faruk da kanshi ya nemawa Ishaq auren Ruk'ayya danshi kunya ta hanashi fad'a, a take malam yasa musu ranar tunda sun amince da junansu dukansu, daga ranar aka fara gudanar da shirye shirye, Khairat kam kai kace itace uwar amarya saboda hidimar da take yi.
Kwanahud'u ya rage bikin Ruk'ayya, yara da Khairat dukansu sunyi roqo akan Umar Faruk ya basu hutu a makaranta amma yace sam bai amince ba, hutun rana d'aya kawai ya basu shima dan a ranar ake biki, Khairat ce ta had'a yaran ta kaisu wajen lalle da kitso duk qoqarinta saida karatun yamma ya sub'uce musu, tana sallah magrib ya shigo bedroom d'in nata, amma tana hangen fuskarshi taga ba annuri sai tak'i sallame sallar ta sake tashi tsaye, gabanta faduwa yake dan sam baya wasa indai b'angaren addini ne, a hankali ta saci kallonshi sai kawai suka had'a ido, da sauri ta liqe idonta take maganganunshi suka dawo kunnenta a lokacin da zasu fita tunda sanyin safiya.
"Alkairina, kinga na lamunce muku kuje yanzu ba tare da kunyi darasin safe ba, amma ina sake jaddada miki, wallahi kiyi iya qoqarinki kiga kun dawo kafin a shiga ajin yamma, idan ba haka ba fa rai zai b'ace, ba kuma na yaran ba kad'ai, harda naki tunda ke kike daurin musu gindi, kin yarda?"
"Na yarda baby, insha Allah ma zamu dawo akan lokaci."
"Hum, Allah yasa."
"Ameen." ta fad'a tana manna mishi sumba a kumatu, shima sumbatarta yayi dan hakan harya zama jikinsu.
A hankali ta aje ajiyar zuciya dan tasan dole sai ranta ya b'ace, zata sake satar kallonshi muryarshi ta daki kunnuwanta "idan kin gama qaryar sallah kije ki had'o min kan yaran ku sameni d'akin karatu."
"Bab...." dole tayi shiru saboda harya fice daga d'akin.
Wani zazzafan iska ta furzar cikin sanyin jiki ta sulala ta nufi b'angarensu Mama, zaune ta samu yaran suna cin abinci Islam na ganinta ta sauko daga qafafun Zuby tana cin abinci ta rarrafo, d'aukarta tayi tana fad'in "yahhh, sarauniyar Papa, ya kike, abinci ake ci?"
Nufa tayi da ita wajen Zuby ta aje mata ita akan qafafu tace "rik'eta ina zuwa, zamuje wajen Papa musha bulala ne."
Mama ce tace "wai badai bai hak'ura ba?"
Cikin sanyin jiki tace "Mama ai kinsan ba zai hak'ura ba dama."
"To kinga tafi da Islam d'in wajenshi."
Da mamaki ta kalli Mama tace "me yasa Mama?"
"Ki tafi da ita kedai."
"To Mama." ta fad'a ta d'auki Islam da rigarta ta fara b'acewa da miya bakinta ma haka.
Had'a yaran tayi suka tafi d'akin karatun, da sallama dukansu suka shiga kuma yana amsa musu, dukansu zaune sukayi akan lumtsumemen carpet d'in dake shinfid'e a wajen, wani littafi ne yake karantawa dan haka yayi banza dasu, aje Islam tayi ta rarrafa wajenshi ta rik'e qafarshi, da murmushi ya d'auketa ya aza saman cinyarshi yana mata wasa, saida ya gama sannan ya kallesu duk kowa jikinshi sai 'bari yake, a kausashe yace "meya hanaku zuwa islamiyya da maraice?"
Duka yaran mayar da kallonsu sukayi ga Khairat, itama kallonsu tayi tace "ya kuma zaku kalleni?"
Kallon Umar Faruk tayi tace "baby wallahi....."
"Waye baby?"
Yanda yayi maganar yasa ta kama jikinta, had'e yawu tayi ta sake cewa "wallahi malam nay...."
A tsawace yace "wai magabar ba zata yiwu ba sai anyi rantsuwa, alamar qarya zaki fad'a kenan."
"A'a malam, dama dan ince ne nayi iya qoqarina naga mun dawo da wuri, amma abin yaci tura, gashi ni kaina ban samu lallan qafafu ba, dole sai dai gobe na koma ayi min."
Wani kallon kin rainani ya bita dashi, wani coffre ya bud'a ya d'auko wata zungureriyar bulala ya taso yayo kansu da ita, ai da sauri kowa ya fara qoqarin gyara zama, cikin muryar kuka suka fara bashi hak'uri, aje Islam yayi akan qatuwar kujerar dake d'akin yace "kiyi kallon yanda mamanki zata sha bulala, bata jin magana."
Daga kan Fateema ya faro yace ta bashi hannunta, tuni Fateema ta b'arke da kuka tana bashi hak'uri, ganin yanda take kuka yasa Khairat cewa "malam, nice babba kuma ni na tafi dasu, dan haka amin bulalarsu na d'auka."
Tabe baki yayi yana kallonta kafin ya kalli yaran yace "to an d'auki kaifinku, amma ku sani idan kuka sake ku zan daka ba wani ba."
Cikin tsawa yace "ku b'ace min da gani."
Duk a sanyaye suka tashi suna kallon Khairat, suna fita ya dawo kanta yace "bani hannunki, kuma kiji da kyau, wallahi idan kika sosa hannunki ko kika janye hannun, to duk sun zube koda kuwa na miki bulala ta kusa data qarshe ne."
Bud'e baki tayi tana kallonshi tana tunanin yanda haka zai yiwu, zaro mata ido yayi yace "kinji dai na rantse miki ko, wallahi nace miki."
"Hannunki." ya sake fad'a.
Had'e wani irin abu tayi mai nauyin gaske daya tokare mata maqoshi, rintse ido tayi ta fara zuro hannun dama a hankali kuma tana d'an janshi da baya, tsawar daya sake mata ce yana fad'in "kefa nake jira." yasa ta zabura ta mik'o hannun.
D'aga bulalar yayi ya sauke mata ita ira a hannu, qara ta saki tare da mayar da hannun cikin hijabi, a kaurare yace mata "kinsan dai ba zaki sani kaffara akan wannan abunba ko, dan haka ki d'auka ban fara ba har yanzu."
Kallonshi tayi sai dai tsagwaron gaskiya kawai ta gani a idonshi, dan haka ta yanke shawarar tsayawa maimakon ta wahalar da kanta a banza, fito da hannayen tayi duka ta mik'a mishi amma idonta rufe, ai kuwa tsuga mata ya dinga yi kai kace qiyayyace tsakaninsu, kamar wasa saida ya mata bulala goma sha biyar ta mutum uku, dan duk d'aya yana da biyar ne, zai zuba mata ta sha shida tayi saurin bud'e idonta ta sauke akanshi, saida gabanshi ya fad'i saboda ganin yanda idonta sukayi jawur dasu, hawayene suka gangaro mata langab'e kai tayi ta marairaice cikin muryar kuka tace "baban Islam, dan Allah."
Shiru tayi daga nan, da sauri ya kawar da kanshi yayi qoqarin mayar da qwallan da yaji na barazanar taho mishi, juyawa yayi ya kalli Islam dake son saukowa daga kan kujerar, maida kallonshi yayi ga Khairat d'in data kasa janye hannayenta, dakewa yayi yace "meye?"
Lumshe ido tayi yayin da gashin idonta yayi sharkaf da hawaye, kasa rik'e kanshi yayi baisan sanda ya jefar da bulalar ba ya durqushe gabanta ya rumgumota a jikinshi, cikin kunne ya rad'a mata "ki gafarceni alkairina."
Kafin tayi magana ya d'agota ya kamo hannayen nata ya rik'e yana kallo, sunyi jawur duk shatin bulala ya fito, sumbatar hannayen yayi ya had'esu wuri d'aya yana kallon fuskarta cike da nadama, a hankali ya sake furta "kiyi hak'uri kinji baby."
Fizge hannayenta tayi ta mik'e tsaye tace " naki nayi hak'urin, kullum nayi laifi baka tab'a min uzuriba saika dakeni, kuma kafin ka dakeni saina baka hak'uri amma baka hak'ura, shine yanzu ni zaka bani danka rainani."
Fita tayi daga d'akin ta koma b'angarenta, bin bayanta yayi da Islam a hannunshi, hak'uri ya fara bata da rarrashinta amma tak'i sauraronsu, saida taga ya damu sosai kad'ai tace "na yarda zan hak'ura, amma da sharad'i?"
"Meye sharad'in to."
"Sai inka amince zaka dawo da Zubeida d'akinta."
Wani tar yayi da ido tare da jan tsaki, shiru ya mata dan haka tace "yanzu baby wannan alfarmar ce ba zaka iya yi min ba? alhalin kana fad'a min zaka iya yin komai saboda ni, kana cewa ranka fansane ga nawa ran, amma ace wannan alfarmar na gagara samunta a wajenka, bafa sab'on Allah nace kayi ba, hasali ma wata sunna ce zaka qara dabb'aqawa mai k'arfin gaske, amma shikenan tunda ba zan samu ba, kaga yanzu saina dinga rik'e kaina wajen tambayarka alfarma dan nasan ba zan samu ba."
Harta juya zata koma d'akinta ya rik'e hannunta, zaunar da ita yayi akan cinyarshi yace " indai wannan ne zaisa kiji a ranki kin wuce komai a wurina, to na amince, ki fad'i ranar da kike so ta dawo gidanta."
Da farin ciki a ranta tace "kawai a sake d'aura muku aure ranar d'aurin aurensu Ruk'ayya."
"An gama alkairina."
Sumbatar kumatunshi tayi sannan ta mik'e ta shiga d'akinta, shi kuma Islam ya d'auka yana fad'in "qaramar alkairina, ina fatan zakiyi koyi da hallayen mahaifiyarki, ita rayuwata ce, ita aljannata ce, ita komai tawa ce, ita dabance a gareni, ba ayi ba kuma ba za'a tab'a yin wacce Umar Faruk zaiso ba kamar mahaifiyarki, ita alkairi ce a wajen Papanki, ina sonta ina qaunarta fiye da komai." ya qarashe da sumbatar bakin yarinyar.
**************
Lokacin da Umar Faruk yaje wa da Zuby da maganar bata amince ba yanzu ma, amma da Mama tasa baki saita amince a sake d'aura musu aure a karo na biyu, nanfa hidima ta qaru yayin da Khairat tayi farin ciki da hakan, washe gari ganin babu wani shiri da Zuby keyi yasa Khairat had'a wani sirri daga cikin sirrin da Mamie ta bata ta aika aka kai mata, da farko taji d'ar a ranta amma data tuna Khairat ba kamar ita bace mai barbad'e saita daure tasha, daga ranar har zuwa kwana ukun daya rage musu ita ta dinga musu gyara, dama kuma ita kema Ruk'ayya d'an abinda zata iya.
Gobe d'aurin aure, anyi sallah magrib gidan ya qara kaurewa da hayaniya, yayin da su Khairat suka kama aiki gadan gadan, duk wanda yasan Khairat ya ganta tana qoqarin d'ora babbar tukunya da ita kanta zata iya shiga ciki a rufeta sai yayi mamaki, tana tsakiyar mutane ta d'ora tukunya Umar Faruk ya shigo da Islam a hannunshi tana kuka, kamar daga sama taji muryarshi yace "alkairina."
Juyowa tayi tana goge zufa da zaninta, takowa tayi ta nufo wajenshi, kallonta yake harta tsaya gabanshi yace "me ki keyi hakane? yaushe kika fara aikin da har zaki fara gwagwarmaya da waccen manyan tukunyan?"
Shagwab'ewa tayi tace "baby, me yake damuna to? yanzu fa Islam watanta tara da haihuwa, kana gani yarinyar dake qoqarin tafiya ma."
"Sai akayi me?"
Shiru tayi tana kallon Islam dake kuka har yanzu tana qpqarin zuwa wajenta, hannu tasa zata karb'eta yace "dan Allah ki daina sakarwa yaran nan ita suna fita da ita waje ana magrib."
Karb'arta tayi tana fad'in "kayi hak'uri ba za'a sake ba, bansan sun fita da ita Ba."
Saida ya d'an saci kallon mutanen dake wajen sannan ya aika mata da sumba, itama mayar masa tayi ba tare da sun tab'a juna ba, juyawa yayi zai fita tace "ango ango, ango Zubeida."
Juyowa yayi yace "ango Khairat da Zubeida dai."
"Kuma baban Islam ba." cewar wata abokiyar wasanshi Chapa'atou.
Hararanta yayi yace "ke kuma wa yasa bakinki?"
Dariya Khairat tayi taja kujera ta zauna zata bawa Islam nono tana fad'in "dama baban qaramar Khairat ki kace da baice miki haka ba."
"Fad'a mata dai, ai kune ke kiranta da Islam, amma ni inkiyar da nake mata itace alkairi."
Kallon Khairat yayi yace "na manta ban fad'a miki ba, Papa yazo fa suna tare da malam."
"Da gaske, amma shine basu fad'a min ba? koda yake ma yanzu sun daina sona sunfi son Islam, amma zasu shigo hannuna, nasan ba zasu bar nan ba dole zasu nemi Islam."
"To ai shi yasa na kawo miki ita danki bata nono tasha, dan da ita zasu tafi gida ta kwana acan."
Waro ido tayi tace "wa, autar tawa zan bayar ta kwana ba kusa dani ba? a'a ma karku fara."
Duk da mutanen dake wajen bai hanashi yowa kanta ba yana fad'in "ina autar take?"
Tashi tayi daga kujerar ta nufi wajen Mama Sa'a ta zauna akan tabarmar tana dariyar mugunta, wani shegen kurmanci ne sukayi daga nan dani kaina ban fahimta ba, naga dai ya kashe mata ido tare da cije lips d'inshi, itama idon ta kanne mishi ta d'aga gira sama ta lashe baki, juyawa yayi zai fita ya nuna mata yatsa yace "zan kamaki."
Gwalo ta bishi dashi harya fita mutanen wajen suna mamakin yanda Umar Faruk ya canza sosai, a da idan ana taro irin haka idan har kayi sa'ar samun ganinshi to da qyar zai tsaya ku gaisa saboda miskilanci da rashin san magana irin nashi, amma yanzu gashi a arha, Chapa'atou dake tare da wata yar uwarsu dattijuwa ce tace "gaskiya idan nice yah Umar, wallahi babu abinda zai sani na maido da Zubeida bayan nasan komai game da ita."
Dattijuwar tace " to ai bashi bane zai maidota gaban kanshi, nida na kwana biyu gidan ai naji meya faru, Khairat ce da kanta tace ya maidota, amma fa harda wani cijewa ita ba zata koma ba, saida Maryam d'in tasa bakinta kad'ai."
"Jar uba, lallai ma ta raina mutane, ita yanzu duk abinda tayi amma har za'a nemi ta dawo tayi tirjiya, wallahi Khairat ta zama yar halak, ta bamu mamaki sosai, farkon zuwanta gidan nan da nazo ganin amarya ko kallon tsiya bata min ba, amma yanzu kaga kamar ba ita ba."
Dariya tsohuwar tayi tace "aike kad'an kika gani, kwana bakwai da nayi a gidan nan naga abubuwa da dama, kinga hidimar da take, yaran nan kowa nata ne kamar yayan cikinta, uwayen kuma kamar su suka haifeta, kai gaskiya yarinyar tayi sai dai fatan Allah ya tsare."
Haka suka dinga tattaunawa akan Khairat harta wuce ta gabansu ta nufi b'angarenta tana amsa wayar Umar Faruk, sake jaddada mata yayi ta shirya Islam yama Papa alk'awarin zasu tafi da ita, cike da jin za'a rabata da yarta tace "amma me yasa babu, yarinyar nan nono take sha, ya zasuyi idan ta hanasu bacci tana buqatar mahaifiyarta?"
Murmushi tayi tace "shikenan to zanyi, ka gafarci bahamagiyar matarka da bata jin maganarka sau d'aya."
Dariya yayi da saida taji sautinta yace "aike yar aljanna ce ba kwankwanto, buri da fatana d'aya a duniya shine, Allah yasa nima na shiga aljanna danna rayu dake."
Ajiyar zuciya ta sauke cikin jin dad'in maganganun mijinta tace "idan har na bud'a idona a aljanna ban ganka ba, to na tabbata qamshi da hazon gidanne ya b'oye min mijina."
"Ko kuma matan aljanna sun rik'eni ba." yayi maganar yana qyaqyata dariya.
"Tabdjim, aiba zata sab'ub'a, Allah ko a aljanna dani kad'ai zaka kasance."
Dariya yake kamar yana gabanta kafin yace "kina kishina har haka amma kika sani dole saina raba miki kaina biyu?"
"To ai baka sani ba, zan iya kishi da mata indai ta gidan duniya ce, amma ina jin tsoron kishi da matan aljanna, saboda nasan sunfini da komai, sannan matane da suke burin mazan duniya su riskesu idan sunga basuyi dacen mata ba a duniya."
"Amma ai ban dake, Khairat ke ba kya ciki, wallahi ke yar aljanna ce, na tabbata matan aljanna ma zasu zama hadimankine kawai, amma ba matan mijinki ba."
"Zaka fasa min kai Umariri."
"Toya na iya Khairiri, ke d'ince ta musamman a wajena, idan kika cire farin cikin da nake idan ina cikin masallaci, to nafi farin ciki idan ina tare dake."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "idan na biye maka zan kwana a haka, bara na saka mata kaya su tafi, amma ka sani yaufa zan gurzaka sosai."
"A ina?" ya ya fad'a yana d'aga murya.
Kwantar da murya tayi tace "a kan gado mana, tunda yau babu Islam a b'angaren namu, dan haka yau sai kowa na gidan nan yaji ihunka."
"Na shiga tara, dan Allah ki rufa min asiri, wallahi nasan zaki iya, kar kisa mijinki ya haukace mana ko ya zama sakarai a idon Jama'a, ki taimaki wannan bawan Allah mana, kinji babyta." ya qarashe da sigar rarrashi.
"Naqi d'in, saika gane ka shigo hannun mata."
Tana fad'a ta kashe wayar ta aje ta fara sauya mata kayan jikinta, tsaf ta shiryata cikin kyakyawan shiri sai qamshi take kafin ta fito da ita.......
Koda Papa yazo suka shiga falonshi suka gaisa sosai, sun fara tab'a hira kuma Papa yace "malam akwai wani muhimmin abu daya kawoni wajenka."
Gyara zama malam yayi yace "to Alhaji ina sauraranki, Allah yasa muji alkairi."
Murmushi kawai yayi kafin ya fito da wata enveloppe daga aljihunshi ya bawa malam d'in, amsa yayi ya kalli envellope d'in da kyau sannan ya kalli Papa yace "wannan fa."
"Malam a karatun daka mana jiya ka nuna mana mahimmancin yin wasiyya, wannan ne yasa koda naje gida na rubuta kuma na kawo maka, dan kai kad'ai ne kafi cancanta daka adanata wajenka."
"Idan ka duba zaka gani a ciki, na raba dukiyata gida biyar, uku daga ciki, ayi hidimar addini da ita, biyu a kuma a rabawa magada."
Da farin ciki malam yace "a gaskiya naji dad'i sosai da faruwar hakan, ina fatan ubangiji ya saka maka da mafificin alkairinsa, Allah kuma yasa hakan ya zama sanadiyar shigarka aljanna."
"Ameen ameen malam, dama wannan ne ya kawoni, ni zan tafi."
Tare suka fito yayi daidai da fitowar Umar Faruk d'auke da Islam, Papa na ganinta ya saki murmushi tun basu qaraso ba ya tara hannu dan karb'arta, da yake yarinyar ma ta gane Papa sai kawai ta tafi wajenshi tana bud'e baki alamar dariya, amsarta Papa yayi saida ya danna mata sumba kusan guda goma duk suna kallonshi kafin ya rumgumeta yana shaqar qamshin jikinta, ya jima a haka kafin ya dago fuskarta ya kalla, d'an qaramin hijabin da aka saka mata ne yasa Papa ya
Showing 177001 words to 180000 words out of 186119 words
kasheshi, wannan yarinyar kuma, matarka ba, matar Umar Faruk, ai tunda ta samu ciki muka bayar da cikin ga aljanu, kuma suka zuba mata cutar da zata kasheta, amma wannan tsinannen yaron ya taimaketa."
Wannan maganganu ne da kullum saita fad'esu, shi yasa Zuby bata zuwa inda take, su Uwani ma basa zuwa gidan, ana haka tsawon wata takwas a gidan wata rana ta fita basu sani ba, ashe kiran ubangijinta ne ta amsa, a titi mota ta kad'eta sai labari mutanen gidan suka samu, sam yayanta babu wacce tayi jimamin hakan, wannan dalilin ne yasa malam ya tarasu ya musu nasiha sosai ya fad'a musu mahimmanci uwa, duk da dai yasan alhakine ke binta, duk da sun bita da addu'a amma dai Zuby kam ita dai ta riga data tsani mahaifiyarta kawai.
Ganin ta daina walwala a gidan yasa Umar Faruk ya tilasta mata komawa islamiyya itama, daga ranar suka fara zuwa tare da Khairat da sauran yara, bayan wani lokaci kuma Umar Faruk da kanshi ya nemawa Ishaq auren Ruk'ayya danshi kunya ta hanashi fad'a, a take malam yasa musu ranar tunda sun amince da junansu dukansu, daga ranar aka fara gudanar da shirye shirye, Khairat kam kai kace itace uwar amarya saboda hidimar da take yi.
Kwanahud'u ya rage bikin Ruk'ayya, yara da Khairat dukansu sunyi roqo akan Umar Faruk ya basu hutu a makaranta amma yace sam bai amince ba, hutun rana d'aya kawai ya basu shima dan a ranar ake biki, Khairat ce ta had'a yaran ta kaisu wajen lalle da kitso duk qoqarinta saida karatun yamma ya sub'uce musu, tana sallah magrib ya shigo bedroom d'in nata, amma tana hangen fuskarshi taga ba annuri sai tak'i sallame sallar ta sake tashi tsaye, gabanta faduwa yake dan sam baya wasa indai b'angaren addini ne, a hankali ta saci kallonshi sai kawai suka had'a ido, da sauri ta liqe idonta take maganganunshi suka dawo kunnenta a lokacin da zasu fita tunda sanyin safiya.
"Alkairina, kinga na lamunce muku kuje yanzu ba tare da kunyi darasin safe ba, amma ina sake jaddada miki, wallahi kiyi iya qoqarinki kiga kun dawo kafin a shiga ajin yamma, idan ba haka ba fa rai zai b'ace, ba kuma na yaran ba kad'ai, harda naki tunda ke kike daurin musu gindi, kin yarda?"
"Na yarda baby, insha Allah ma zamu dawo akan lokaci."
"Hum, Allah yasa."
"Ameen." ta fad'a tana manna mishi sumba a kumatu, shima sumbatarta yayi dan hakan harya zama jikinsu.
A hankali ta aje ajiyar zuciya dan tasan dole sai ranta ya b'ace, zata sake satar kallonshi muryarshi ta daki kunnuwanta "idan kin gama qaryar sallah kije ki had'o min kan yaran ku sameni d'akin karatu."
"Bab...." dole tayi shiru saboda harya fice daga d'akin.
Wani zazzafan iska ta furzar cikin sanyin jiki ta sulala ta nufi b'angarensu Mama, zaune ta samu yaran suna cin abinci Islam na ganinta ta sauko daga qafafun Zuby tana cin abinci ta rarrafo, d'aukarta tayi tana fad'in "yahhh, sarauniyar Papa, ya kike, abinci ake ci?"
Nufa tayi da ita wajen Zuby ta aje mata ita akan qafafu tace "rik'eta ina zuwa, zamuje wajen Papa musha bulala ne."
Mama ce tace "wai badai bai hak'ura ba?"
Cikin sanyin jiki tace "Mama ai kinsan ba zai hak'ura ba dama."
"To kinga tafi da Islam d'in wajenshi."
Da mamaki ta kalli Mama tace "me yasa Mama?"
"Ki tafi da ita kedai."
"To Mama." ta fad'a ta d'auki Islam da rigarta ta fara b'acewa da miya bakinta ma haka.
Had'a yaran tayi suka tafi d'akin karatun, da sallama dukansu suka shiga kuma yana amsa musu, dukansu zaune sukayi akan lumtsumemen carpet d'in dake shinfid'e a wajen, wani littafi ne yake karantawa dan haka yayi banza dasu, aje Islam tayi ta rarrafa wajenshi ta rik'e qafarshi, da murmushi ya d'auketa ya aza saman cinyarshi yana mata wasa, saida ya gama sannan ya kallesu duk kowa jikinshi sai 'bari yake, a kausashe yace "meya hanaku zuwa islamiyya da maraice?"
Duka yaran mayar da kallonsu sukayi ga Khairat, itama kallonsu tayi tace "ya kuma zaku kalleni?"
Kallon Umar Faruk tayi tace "baby wallahi....."
"Waye baby?"
Yanda yayi maganar yasa ta kama jikinta, had'e yawu tayi ta sake cewa "wallahi malam nay...."
A tsawace yace "wai magabar ba zata yiwu ba sai anyi rantsuwa, alamar qarya zaki fad'a kenan."
"A'a malam, dama dan ince ne nayi iya qoqarina naga mun dawo da wuri, amma abin yaci tura, gashi ni kaina ban samu lallan qafafu ba, dole sai dai gobe na koma ayi min."
Wani kallon kin rainani ya bita dashi, wani coffre ya bud'a ya d'auko wata zungureriyar bulala ya taso yayo kansu da ita, ai da sauri kowa ya fara qoqarin gyara zama, cikin muryar kuka suka fara bashi hak'uri, aje Islam yayi akan qatuwar kujerar dake d'akin yace "kiyi kallon yanda mamanki zata sha bulala, bata jin magana."
Daga kan Fateema ya faro yace ta bashi hannunta, tuni Fateema ta b'arke da kuka tana bashi hak'uri, ganin yanda take kuka yasa Khairat cewa "malam, nice babba kuma ni na tafi dasu, dan haka amin bulalarsu na d'auka."
Tabe baki yayi yana kallonta kafin ya kalli yaran yace "to an d'auki kaifinku, amma ku sani idan kuka sake ku zan daka ba wani ba."
Cikin tsawa yace "ku b'ace min da gani."
Duk a sanyaye suka tashi suna kallon Khairat, suna fita ya dawo kanta yace "bani hannunki, kuma kiji da kyau, wallahi idan kika sosa hannunki ko kika janye hannun, to duk sun zube koda kuwa na miki bulala ta kusa data qarshe ne."
Bud'e baki tayi tana kallonshi tana tunanin yanda haka zai yiwu, zaro mata ido yayi yace "kinji dai na rantse miki ko, wallahi nace miki."
"Hannunki." ya sake fad'a.
Had'e wani irin abu tayi mai nauyin gaske daya tokare mata maqoshi, rintse ido tayi ta fara zuro hannun dama a hankali kuma tana d'an janshi da baya, tsawar daya sake mata ce yana fad'in "kefa nake jira." yasa ta zabura ta mik'o hannun.
D'aga bulalar yayi ya sauke mata ita ira a hannu, qara ta saki tare da mayar da hannun cikin hijabi, a kaurare yace mata "kinsan dai ba zaki sani kaffara akan wannan abunba ko, dan haka ki d'auka ban fara ba har yanzu."
Kallonshi tayi sai dai tsagwaron gaskiya kawai ta gani a idonshi, dan haka ta yanke shawarar tsayawa maimakon ta wahalar da kanta a banza, fito da hannayen tayi duka ta mik'a mishi amma idonta rufe, ai kuwa tsuga mata ya dinga yi kai kace qiyayyace tsakaninsu, kamar wasa saida ya mata bulala goma sha biyar ta mutum uku, dan duk d'aya yana da biyar ne, zai zuba mata ta sha shida tayi saurin bud'e idonta ta sauke akanshi, saida gabanshi ya fad'i saboda ganin yanda idonta sukayi jawur dasu, hawayene suka gangaro mata langab'e kai tayi ta marairaice cikin muryar kuka tace "baban Islam, dan Allah."
Shiru tayi daga nan, da sauri ya kawar da kanshi yayi qoqarin mayar da qwallan da yaji na barazanar taho mishi, juyawa yayi ya kalli Islam dake son saukowa daga kan kujerar, maida kallonshi yayi ga Khairat d'in data kasa janye hannayenta, dakewa yayi yace "meye?"
Lumshe ido tayi yayin da gashin idonta yayi sharkaf da hawaye, kasa rik'e kanshi yayi baisan sanda ya jefar da bulalar ba ya durqushe gabanta ya rumgumota a jikinshi, cikin kunne ya rad'a mata "ki gafarceni alkairina."
Kafin tayi magana ya d'agota ya kamo hannayen nata ya rik'e yana kallo, sunyi jawur duk shatin bulala ya fito, sumbatar hannayen yayi ya had'esu wuri d'aya yana kallon fuskarta cike da nadama, a hankali ya sake furta "kiyi hak'uri kinji baby."
Fizge hannayenta tayi ta mik'e tsaye tace " naki nayi hak'urin, kullum nayi laifi baka tab'a min uzuriba saika dakeni, kuma kafin ka dakeni saina baka hak'uri amma baka hak'ura, shine yanzu ni zaka bani danka rainani."
Fita tayi daga d'akin ta koma b'angarenta, bin bayanta yayi da Islam a hannunshi, hak'uri ya fara bata da rarrashinta amma tak'i sauraronsu, saida taga ya damu sosai kad'ai tace "na yarda zan hak'ura, amma da sharad'i?"
"Meye sharad'in to."
"Sai inka amince zaka dawo da Zubeida d'akinta."
Wani tar yayi da ido tare da jan tsaki, shiru ya mata dan haka tace "yanzu baby wannan alfarmar ce ba zaka iya yi min ba? alhalin kana fad'a min zaka iya yin komai saboda ni, kana cewa ranka fansane ga nawa ran, amma ace wannan alfarmar na gagara samunta a wajenka, bafa sab'on Allah nace kayi ba, hasali ma wata sunna ce zaka qara dabb'aqawa mai k'arfin gaske, amma shikenan tunda ba zan samu ba, kaga yanzu saina dinga rik'e kaina wajen tambayarka alfarma dan nasan ba zan samu ba."
Harta juya zata koma d'akinta ya rik'e hannunta, zaunar da ita yayi akan cinyarshi yace " indai wannan ne zaisa kiji a ranki kin wuce komai a wurina, to na amince, ki fad'i ranar da kike so ta dawo gidanta."
Da farin ciki a ranta tace "kawai a sake d'aura muku aure ranar d'aurin aurensu Ruk'ayya."
"An gama alkairina."
Sumbatar kumatunshi tayi sannan ta mik'e ta shiga d'akinta, shi kuma Islam ya d'auka yana fad'in "qaramar alkairina, ina fatan zakiyi koyi da hallayen mahaifiyarki, ita rayuwata ce, ita aljannata ce, ita komai tawa ce, ita dabance a gareni, ba ayi ba kuma ba za'a tab'a yin wacce Umar Faruk zaiso ba kamar mahaifiyarki, ita alkairi ce a wajen Papanki, ina sonta ina qaunarta fiye da komai." ya qarashe da sumbatar bakin yarinyar.
**************
Lokacin da Umar Faruk yaje wa da Zuby da maganar bata amince ba yanzu ma, amma da Mama tasa baki saita amince a sake d'aura musu aure a karo na biyu, nanfa hidima ta qaru yayin da Khairat tayi farin ciki da hakan, washe gari ganin babu wani shiri da Zuby keyi yasa Khairat had'a wani sirri daga cikin sirrin da Mamie ta bata ta aika aka kai mata, da farko taji d'ar a ranta amma data tuna Khairat ba kamar ita bace mai barbad'e saita daure tasha, daga ranar har zuwa kwana ukun daya rage musu ita ta dinga musu gyara, dama kuma ita kema Ruk'ayya d'an abinda zata iya.
Gobe d'aurin aure, anyi sallah magrib gidan ya qara kaurewa da hayaniya, yayin da su Khairat suka kama aiki gadan gadan, duk wanda yasan Khairat ya ganta tana qoqarin d'ora babbar tukunya da ita kanta zata iya shiga ciki a rufeta sai yayi mamaki, tana tsakiyar mutane ta d'ora tukunya Umar Faruk ya shigo da Islam a hannunshi tana kuka, kamar daga sama taji muryarshi yace "alkairina."
Juyowa tayi tana goge zufa da zaninta, takowa tayi ta nufo wajenshi, kallonta yake harta tsaya gabanshi yace "me ki keyi hakane? yaushe kika fara aikin da har zaki fara gwagwarmaya da waccen manyan tukunyan?"
Shagwab'ewa tayi tace "baby, me yake damuna to? yanzu fa Islam watanta tara da haihuwa, kana gani yarinyar dake qoqarin tafiya ma."
"Sai akayi me?"
Shiru tayi tana kallon Islam dake kuka har yanzu tana qpqarin zuwa wajenta, hannu tasa zata karb'eta yace "dan Allah ki daina sakarwa yaran nan ita suna fita da ita waje ana magrib."
Karb'arta tayi tana fad'in "kayi hak'uri ba za'a sake ba, bansan sun fita da ita Ba."
Saida ya d'an saci kallon mutanen dake wajen sannan ya aika mata da sumba, itama mayar masa tayi ba tare da sun tab'a juna ba, juyawa yayi zai fita tace "ango ango, ango Zubeida."
Juyowa yayi yace "ango Khairat da Zubeida dai."
"Kuma baban Islam ba." cewar wata abokiyar wasanshi Chapa'atou.
Hararanta yayi yace "ke kuma wa yasa bakinki?"
Dariya Khairat tayi taja kujera ta zauna zata bawa Islam nono tana fad'in "dama baban qaramar Khairat ki kace da baice miki haka ba."
"Fad'a mata dai, ai kune ke kiranta da Islam, amma ni inkiyar da nake mata itace alkairi."
Kallon Khairat yayi yace "na manta ban fad'a miki ba, Papa yazo fa suna tare da malam."
"Da gaske, amma shine basu fad'a min ba? koda yake ma yanzu sun daina sona sunfi son Islam, amma zasu shigo hannuna, nasan ba zasu bar nan ba dole zasu nemi Islam."
"To ai shi yasa na kawo miki ita danki bata nono tasha, dan da ita zasu tafi gida ta kwana acan."
Waro ido tayi tace "wa, autar tawa zan bayar ta kwana ba kusa dani ba? a'a ma karku fara."
Duk da mutanen dake wajen bai hanashi yowa kanta ba yana fad'in "ina autar take?"
Tashi tayi daga kujerar ta nufi wajen Mama Sa'a ta zauna akan tabarmar tana dariyar mugunta, wani shegen kurmanci ne sukayi daga nan dani kaina ban fahimta ba, naga dai ya kashe mata ido tare da cije lips d'inshi, itama idon ta kanne mishi ta d'aga gira sama ta lashe baki, juyawa yayi zai fita ya nuna mata yatsa yace "zan kamaki."
Gwalo ta bishi dashi harya fita mutanen wajen suna mamakin yanda Umar Faruk ya canza sosai, a da idan ana taro irin haka idan har kayi sa'ar samun ganinshi to da qyar zai tsaya ku gaisa saboda miskilanci da rashin san magana irin nashi, amma yanzu gashi a arha, Chapa'atou dake tare da wata yar uwarsu dattijuwa ce tace "gaskiya idan nice yah Umar, wallahi babu abinda zai sani na maido da Zubeida bayan nasan komai game da ita."
Dattijuwar tace " to ai bashi bane zai maidota gaban kanshi, nida na kwana biyu gidan ai naji meya faru, Khairat ce da kanta tace ya maidota, amma fa harda wani cijewa ita ba zata koma ba, saida Maryam d'in tasa bakinta kad'ai."
"Jar uba, lallai ma ta raina mutane, ita yanzu duk abinda tayi amma har za'a nemi ta dawo tayi tirjiya, wallahi Khairat ta zama yar halak, ta bamu mamaki sosai, farkon zuwanta gidan nan da nazo ganin amarya ko kallon tsiya bata min ba, amma yanzu kaga kamar ba ita ba."
Dariya tsohuwar tayi tace "aike kad'an kika gani, kwana bakwai da nayi a gidan nan naga abubuwa da dama, kinga hidimar da take, yaran nan kowa nata ne kamar yayan cikinta, uwayen kuma kamar su suka haifeta, kai gaskiya yarinyar tayi sai dai fatan Allah ya tsare."
Haka suka dinga tattaunawa akan Khairat harta wuce ta gabansu ta nufi b'angarenta tana amsa wayar Umar Faruk, sake jaddada mata yayi ta shirya Islam yama Papa alk'awarin zasu tafi da ita, cike da jin za'a rabata da yarta tace "amma me yasa babu, yarinyar nan nono take sha, ya zasuyi idan ta hanasu bacci tana buqatar mahaifiyarta?"
"Ba zatayi ba, ni na fad'a miki haka."
"To amma baby..."
"Amma me kuma yar aljanna, kiyi abinda hamagon mijinki yace miki mana."
Murmushi tayi tace "shikenan to zanyi, ka gafarci bahamagiyar matarka da bata jin maganarka sau d'aya."
Dariya yayi da saida taji sautinta yace "aike yar aljanna ce ba kwankwanto, buri da fatana d'aya a duniya shine, Allah yasa nima na shiga aljanna danna rayu dake."
Ajiyar zuciya ta sauke cikin jin dad'in maganganun mijinta tace "idan har na bud'a idona a aljanna ban ganka ba, to na tabbata qamshi da hazon gidanne ya b'oye min mijina."
"Ko kuma matan aljanna sun rik'eni ba." yayi maganar yana qyaqyata dariya.
"Tabdjim, aiba zata sab'ub'a, Allah ko a aljanna dani kad'ai zaka kasance."
Dariya yake kamar yana gabanta kafin yace "kina kishina har haka amma kika sani dole saina raba miki kaina biyu?"
"To ai baka sani ba, zan iya kishi da mata indai ta gidan duniya ce, amma ina jin tsoron kishi da matan aljanna, saboda nasan sunfini da komai, sannan matane da suke burin mazan duniya su riskesu idan sunga basuyi dacen mata ba a duniya."
"Amma ai ban dake, Khairat ke ba kya ciki, wallahi ke yar aljanna ce, na tabbata matan aljanna ma zasu zama hadimankine kawai, amma ba matan mijinki ba."
"Zaka fasa min kai Umariri."
"Toya na iya Khairiri, ke d'ince ta musamman a wajena, idan kika cire farin cikin da nake idan ina cikin masallaci, to nafi farin ciki idan ina tare dake."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "idan na biye maka zan kwana a haka, bara na saka mata kaya su tafi, amma ka sani yaufa zan gurzaka sosai."
"A ina?" ya ya fad'a yana d'aga murya.
Kwantar da murya tayi tace "a kan gado mana, tunda yau babu Islam a b'angaren namu, dan haka yau sai kowa na gidan nan yaji ihunka."
"Na shiga tara, dan Allah ki rufa min asiri, wallahi nasan zaki iya, kar kisa mijinki ya haukace mana ko ya zama sakarai a idon Jama'a, ki taimaki wannan bawan Allah mana, kinji babyta." ya qarashe da sigar rarrashi.
"Naqi d'in, saika gane ka shigo hannun mata."
Tana fad'a ta kashe wayar ta aje ta fara sauya mata kayan jikinta, tsaf ta shiryata cikin kyakyawan shiri sai qamshi take kafin ta fito da ita.......
Koda Papa yazo suka shiga falonshi suka gaisa sosai, sun fara tab'a hira kuma Papa yace "malam akwai wani muhimmin abu daya kawoni wajenka."
Gyara zama malam yayi yace "to Alhaji ina sauraranki, Allah yasa muji alkairi."
Murmushi kawai yayi kafin ya fito da wata enveloppe daga aljihunshi ya bawa malam d'in, amsa yayi ya kalli envellope d'in da kyau sannan ya kalli Papa yace "wannan fa."
"Malam a karatun daka mana jiya ka nuna mana mahimmancin yin wasiyya, wannan ne yasa koda naje gida na rubuta kuma na kawo maka, dan kai kad'ai ne kafi cancanta daka adanata wajenka."
"Idan ka duba zaka gani a ciki, na raba dukiyata gida biyar, uku daga ciki, ayi hidimar addini da ita, biyu a kuma a rabawa magada."
Da farin ciki malam yace "a gaskiya naji dad'i sosai da faruwar hakan, ina fatan ubangiji ya saka maka da mafificin alkairinsa, Allah kuma yasa hakan ya zama sanadiyar shigarka aljanna."
"Ameen ameen malam, dama wannan ne ya kawoni, ni zan tafi."
Tare suka fito yayi daidai da fitowar Umar Faruk d'auke da Islam, Papa na ganinta ya saki murmushi tun basu qaraso ba ya tara hannu dan karb'arta, da yake yarinyar ma ta gane Papa sai kawai ta tafi wajenshi tana bud'e baki alamar dariya, amsarta Papa yayi saida ya danna mata sumba kusan guda goma duk suna kallonshi kafin ya rumgumeta yana shaqar qamshin jikinta, ya jima a haka kafin ya dago fuskarta ya kalla, d'an qaramin hijabin da aka saka mata ne yasa Papa ya
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60 Chapter 61Chapter 62Chapter 63