dariyar da Khairat take masa, lotus ya d'auka a motar ya goge bakinshi yana hararan Abbakar yana cin magani, girgiza Abbakar yayi yace "Umar Faruk kenan, kamar ba kai ba wallahi duk ka canza."
"Kaga nifa akwai maganar da nake so muyi da kai."
"Ina jinka." ya fad'a yana gyara zama.
"Dama wata tafiya ce ta taso mai mahimmanci, kuma Khairat tace mahaifinta yace dole sai dai mu tafi tare, in kuma banje ba ba zasuji dad'i ba, ni kuma harna ce mata na amince, saboda akwai wani laifi da nayi mata tace zata fad'awa Baba, saboda haka yasa nace na amince, amma ni gaskiya har yanzu bana jin zan iya tafiya tare da ita haka kawai a dinga nuna ni a gari."
Saida ya gama nazartarshi kafin yace "to ita dai rayuwar duniya da kake gani inka biya ta abinda mutane zasu fad'a to babu inda zaka je, sannan a matsayinka na mijinta kuma kace zaka, amma daga baya kace a'a hakan zai iya tab'a darajarka da mutuncinka a wajenta, iyayenta kuma tunda suka ce suna buk'atarka a wajen, tofa akwai buk'atar son ganinka ne a wajen, dan haka ni ina ganin kawai ka bita ku tafi tunda dai ba siyar da kai za tayi ba, matsala d'aya ce kawai nake tunanin za'a samu."
"Matsalar me kenan?"
"Zubeida mana, da ace kafin ta tare ne, amma a yanzu data tare kuma na lura kan yarinyar yana rawa, bai zama lallai ta amince ka tafi ba."
"Nima yaya nayi wannan tunanin tun kafin kayi, amma da yake tamin alk'awarin idan har mun kwana biyu to ba zamu wuce uku ba, a lissafina ranar talata ne tafiyar ta kama, daga gobe kuma kwanan Khairat zai qare, kaga kenan a ranar da zan koma d'akinta ne za ayi tafiyar, kenan ko an shiga kwanan Zuby to kwana d'aya ne."
"Eh to da sauk'i idan hakane, dan haka ka fara shiri kawai ni zanji dasu Baba, sai kuma ka nemi izinin matarka."
"Izini kuma? haba dai, kamar itace mijin."
"A wannan qadamin kam kusan itace, dan ka sani in bata amince ba ba zaka tafi ba, idan kuma ka tafi bada amincewarta ba, tofa ka sani ranar gobe Allah zai tsayar da kai a gabanshi."
"To naji, Sheik Abbakar."
"Sheik Umar Faruk dai, kuma kayi k'ok'ari kafin ku dawo kuzo mana da babban tsaraba."
Dariyar da yake yasa yace "wane irin k'ok'ari kuma, wace irin tsaraba?"
Cikin rad'a yace mishi "baby "
Bushewa sukayi da dariya harda tapa hannu kafin Umar Faruk yace "baka da dama wallahi, taro ne fa zai kaimu ba lune da miel (honeymoon) ba."
Da haka suka isa masallaci kamar wasu abokanai suna hirarsu cikin raha, saida aka gama hud'uba kafin akayi sallah daga nan kuma suka dawo tare suka komo gidansu Khairat dan d'aukarta kamar yanda yace.
*****************
Suna zuwa tare suka shiga da Abbakar har ciki, a lokacin masu aiki na k'awata wajen cin abinci da kalolin girke girke, Khairat da fitowarta kenan daga d'akinta ta gama sallah ta dako da gudu ta rumgume Umar Faruk, "sannu baby , har kun taso?"
Kasa aiwatar da komai yayi saboda fitowar Mamie itama daga d'aki wanda Mammie dama tana zaune a falon, abinka ga yan bariki😂 ba wanda yaji wani abu, sai Umar Faruk daya ji kunya ta rufeshi, suna shirin zubewa qasa dan kwasar gaisuwa Mamie ta qaraso da sauri ta dafa kafad'un Umar Faruk duka biyun tana fuskantarshi tace "a'a a'a, haba d'ana, ai ka wuce wannan a gidan nan, kaima fa d'an gidan nan ne."
Hannunshi ta rik'e tayi hanyar wajen cin abincin dashi tana fad'in "muje ga abinci an gama kuci."
Umar Faruk dai kanshi na qasa ya kasa kallonta sai Abbakar dake kallon falon irin tsari da dukiyar da aka zuba, da kanta taja mishi kujera ya zauna ita kuma mai aiki taja mata ta zauna, Khairat ma da Mammie duka sun zauna, Biba da Saude ne suka bud'a kwanukan suka fara zuba musu abincin, suna gamawa suka koma mafakarsu su kuma suka fara cin abincin.
Ba ruwan Khairat haka kawai take jin son Umar Faruk na gaskiyar na shirgarta, da kanta take d'ibar abincin tana saka mishi a baki saboda taga baya ci, haka yasa ya fara diba kad'an kad'an yana ci, Khairat d'in da Mammie kuma hira suke sosai irin na kaka da jika , Abbakar dai kallon ikon Allah yake yana qara ganin girman Khairat, dan inba mai hak'uri ba babu ta yanda za ace kana rayuwa cikin wannan daular kamar a masarauta, abinci ma na rana kana cin kusan kala uku zuwa hud'u amma ka yarda ka fara rayuwa a gida kamar nasu, haka ma a wajen Umar Faruk abinda yake rayawa kenan a zuciyarshi tare da sake jaddada irin taushin zuciyar Khairat, lallai baka sanin asalin mutum saika zauna dashi sannan zaka fahimceshi.
Suna kammalawa kafin su tashi Mamie ta kalli Khairat tace "ki tashi kije ki shirya kizo ku tafi."
A shagwab'e ta kalli Mamie tace "to Mamie."
Umar Faruk ne yace "a'a Mama, ku barta kawai ta zauna, naga kunyi kewarta sosai, idan na taso daga aiki zan biyo saina d'auketa."
Cike da farin ciki ta kalleshi tace "da gaske baby? gaskiya naji dad'i."
Mak'ale wuyanshi tayi tare da janyoshi kusanta ta sumbaci kumatunshi tare da fad'in "na gode baby."
Mammie dake kusan Khairat ce ta zura hannu ta kama kumatunshi tace "yaron kirki, gaskiya ka kyauta, dan dama muna so muyi shirye shiryen tafiyarmu a gabanta."
Ture hannunta Khairat tayi tana fad'in "kuma shine saikin tab'a min miji , nifa bana son haka."
"Allah sarki, yo mijinki ko mijina? kaji min yarinya kai, kawai dan na ara mikishi saiki wani zak'e dayawa."
Kallon Umar Faruk tayi ta kalli Mammie tace "zak'ewa ma nake? to ai mijin naki ne ke rawar qafa a kaina."
"Kaji wani d'aurin duniya kuma, to nidai ban gani ba, kuma nasan yafi sona."
"To ai gashi nan ki tambayeshi kiji." Khairat ta fad'a tana nunashi da hannu
"Ba buk'ata, danni zai zab'a, bana so kiji kunya a gaban mutane."
Cikin taushin murya cike da jin kunya Umar Faruk yace " gaskiya ne, za tasha a wajenki."
Mammie kam bushewa tayi da dariya had'e da yiwa Khairat gwalo, turo baki tayi tana kallon Umar Faruk, shi kam kasa kallonta yayi saboda wutar tartsatsin da yake ji a kanta, haka suka mik'e gaba d'ayansu zasu tafi, bayan sunyi sallama Mammie tace "nasan dai sai mun had'u a lokacin tafiyarmu ko?
"Insha Allah." ya fad'a kawai.
"To Allah ya nuna mana."
"Ameen." suka amsa.
A hankali Khairat ta taka musu har zuwa k'ofar d'aki sannan suka tsaya, sumbatar bakinshi tayi tare da kumatunshi kafin ta kalleshi tace "Allah ya tsare, saika zo."
Su Mamie dake hangensu yasa ya d'an shafi fuskarta kawai yayi gaba, suna fita suka d'auki hanya saida ya aje Abbakar gida ko shiga baiyi ba ya juya ma'aikata dan lokaci yayi sosai, sai dai zuciyarshi ta qara narkewa da tsananin son Khairat, haka ya koma duk baijin dad'in aikin saboda manyan kayan dake jikinshi, ga kuma motsi da k'amshin Khairat daya isheshi duk sanda ya motsa, ji yake kamar tana jikinshi ko kuma tana sumbatartashi, a haka dai ya gama aikin a daddafe har aka tashi.
Bai wuce gida ba har saida ya tsaya ya siyawa Zuby kayan data buk'ata kafin ya wuce gida, yana isa ana kiran sallah magrib hakan yasa yana shiga d'akinta ya aje mata kayan ya fito yayi alwala cikin gaggawa ya tafi masallaci, bai dawo gidan ba har saida akayi sallah isha'i saboda lokacin qurarre ne kuma suna tare da Ishaq suna hira, suna gamawa ya shigo gidan saida ya fara shiga wajen Baba suka gaisa kafin ya shiga d'akin Mama da sauran iyayen, yana fitowa ya wuce d'akin Zuby.
Ya samu tana nad'e sallayar da tayi sallah, abinda ya qona masa rai da haushi shine, d'akin dai tsaf dashi sai kamshin turaren wuta amma kayan jikinta, tun atamfar safe ce daya fita ya barta da ita ya kuma dawo ya sameta da ita, kuma yanzu ma ita dai ce, ya d'auka kafin ya dawo daga masallaci zai samu ta canza, amma ina alamu dai na ba tayi wanka ba tun na safe, zaune yayi a kukerar robar dake fuskantar gadon ya kalleta fuska ba yabo ba fallasa yace, cike da ladabi tace "sannu da zuwa."
"Yawwa, sannu? ya gida?"
"An gode Allah."
Aje sallayar tayi ta tsaya tana kallonshi, a d'an dak'ile yace "zauna mana."
Zaune tayi bakin gadon tana kallonshi shima wuyanta yake kallo dake tsattsafo da zufa , a shak'e yace "kin duba kayan?"
"Eh yah, na duba."
"To miye babu a ciki?"
Cikin sanyin murya tace "eh to, kusan abinda babu kad'an ne gaskiya."
Da d'an k'arfi yace "to yanzu kamar nawa zai isheki ki siyo abinda babun?"
Nanma a ladabce tace "eh to, ko nawa ka bayar ma zai isa."
D'aga gira yayi sama ya d'an zame daga kan kujerar yasa hannu aljihu ya fito da kud'i, jikka biyar biyar guda biyu ya bata yace "gashi, sai kiyi manage dashi dan kinsan nauyi dayawa ne a kaina."
"An gode Allah ya saka da alkairi." ta fad'a a sanyaye.
Sauran canjin ya mayar aljihu kafin ya sake gyara zama ya kalleta sosai yace "ina son yin wata muhimmiyar magana dake, ina fatan zaki bani hankalinki kuma ki fahimceni?"
"Ina ji yah Umar."
"Zubeida, akwai wani babban taro da aka shirya a Germany, taro ne na manyan mutane wanda zai had'a da iyalensu, mahaifin Khairat na d'aya daga ciki, kuma ya gayyaceni a matsayina na surukinsa, tafiyar zata iya d'aukanmu kwana biyu zuwa uku, shi yasa nake neman alfarmarki kwanan d'ayan, domin zai iya yiwuwa na shiga cikin kwananki domin kinsan tafiyar hali, kosu Mama basu sani ba domin ina so na kammala daku iyalina, ina fatan zaki min wannan alfarmar ki bani kwananki d'aya tak."
Cikin mamakin kalamansa tace "tafiya kuma, har qasar waje, amma kuma kai yaya ka amince ka tafi? ba ka tsoron ko wani abu aka shirya maka."
"Me kuma za'a shirya min? tare fa da Khairat zamu tafi."
"Darammm." taji gabanta ya fad'i, cike da kasa b'oye abinda ke ranta ta mik'e tsaye tace "uhum, yanzu naji magana, kace dai tare da karuwarka zaku tafi, wato harta bud'e maka idon da har kake tunanin fara biyarta a duk inda tayi ko? yah Umar wai yaushe ka zama haka ne? gaba d'aya ka canza kamar ba kai ba, to wallahi in dai izinina ne ake nema ban yarda ba."
Wata wawura daya ma hannunta har yayi qara cikin d'aga murya yace "Zubeida , akan miye ina magana dake har zaki mik'e tsaye kina min ihu, rainani ne ki kayi kome, me yasa zaki d'aga muryarki akan tawa? wai tambaya ma kike yaushe na canza? to a ranar da kika canza na canza nima, akan miye zan zaunar dake ina miki magana cikin nutsuwa ke kuma zaki d'aga min hankali, waye ya koyar dake wannan d'abi'ar? nace waye yace kizo nan ki dinga min abinda ranki yake so, waye." ya qarashe da d'aga murya tare da hankad'ata saman gado.
D'orawa yayi da "kina tunanin izininki nake nema? to baki fahimta daidai ba, ni alfarma na nema kimin ta kwana d'aya wanda shima qila waqala na yishi a can, da har zaki wani ce wai baki yarda ba, to karki yarda mana saime? naga idan zamanki nake a gidan."
"Ba dai alfarmar dana nema bace har tasa kika min haka, to bari ki gani yanzu zanyi maganin abin."
Wayarshi ya ciro daga aljihu ya danna kira, daga d'aya b'angaren ana d'auka cike da karsashi da kashe murya tace "hello baby."
Saida ya lumshe ido saboda yanda yaji har tsikar jikinshi ta tashi, saita nutsuwarsa yayi tare da sauke ajiyar zuciya kafin yace "hello, ya kike?"
Cikin shagwab'a da wata shegiyar kissa tace "ba dad'i, ka tafi ka barni inata jiranka, duk da ina kewar gida amma har kasa naji gidan ya gundureni saboda kayi nesa dani, a gaskiya Faruk sai yanzu nake qara tabbatarwa cewa soyayya *had'in Allah ce*, yanzu fad'a min yaushe zaka taho?"
Baisan sanda wani basaraken murmushi ya sub'uce masa ba, a hankali ya furta "zanzo, yanzu fad'a min tafiyar nan da zamuyi, kina ganin zamu iya dawowa a kwana biyu?"
"Eh baby , dan a ranar da za muje ma a ranar za'a gabatar da taron, kawai dai akwai gajiyar tafiya da kuma ganin gari da zai iya kaimu kwana ukun."
Yanda muryarta ke fita yasa yasa hannunshi yana shafar saitin zuciyarsa da yake jin bugunta yana canzawa , cikin basarwa yace "to a kwana biyu nake so mu dawo, ki shirya zanzo d'aukarki yanzu."
Cike da zumud'i da qwarin murya danta daki dodon kunnensa tace "an gama ranka shi dad'e."
Kashe wayar yayi ya maida kallonsa ga Zuby dake zaune tana sauraranshi, kallon sama da qasa ya mata yace "wai duk wanda ya samu dama ba zai tsaya wasa ba sai k'ok'arin ya dama damarsa, to in dan kwana d'aya ne ki rik'e na yafe miki bana buk'ata, zan tafi a ranar da kwanan Khairat zai zagayo, naga kuma mai hanani abinda naga dama."
Wucewa yayi ya barta a zaune yana fad'in "aikin banza kawai, yara da zaran sun ganka ba kaya a jikinka saisu nemi su rainaka."
Yana fita d'akin Khairat ya nufa ya bud'e da makullan wajensa ya shiga, kayansa ya cire ya shiga wanka, bai jima ba ya fito ya shirya cikin qananun kaya yayi wanka da turare kafin ya d'auki makullin mashin d'inshi dan dashi yake so ya d'auko gimbiyar.
_Yaufa my Khairat utu utu zata hau._😁
*****************
Duk da yaso ta fito amma saida tasa ya sake shiga ciki ya gaishe dasu Mamie kafin ta fito, cak ta tsaya saboda ganin Dream a maimakon Renge rover😂, matsowa tayi kusanshi tace "baby, ina motar take?"
Gemunshi ya tattaro ya had'e guri d'aya yana murmushi, a tunaninta so yake ya gwada soyayyar da take fad'in tana masa shi yasa ya taho da mashin d'in, ba zata bari shirinta ya watse ba dan haka ta saki murmushi ta rumgumeshi taré da sumbatar kumatunshi kafin tace,
"Karo na farko a rayuwata zan hau mashin, a gaskiya soyayya za tayi dad'i akan mashin."
Cikin dariya ya fara qoqarin hawa yana fad'in "saima kin hau zaki tabbatar."
Rik'e rigarsa tayi tace "ka taimaka min na hau kafin ka hau."
Hannun damansa ya mika mata ta rik'e sannan ta tattare rigarta kafin ta hau, yana hawa ya tayar suka d'auki hanya, tintserewa tayi da dariya ta fara masa cakulkuli tana fad'in,
"Ashe haka mashin yake? gaskiya daga yau ba zan sake hawa mota ba, nima mashin zan siya sabo."
"Ke ke, dan Allah ki bari, za kisa mu fad'i fa, ki bari mana, hhhhhhh." ya qarashe da dariya.
Saida suka hau titi kad'ai ta rabu dashi amma fa tana makale a bayanshi tayi luf kamar mai bacci, surutu kawai take zuba masa shi dai nishadi da farin ciki ma ya hanashi magana, da sauri ta nuna masa wata babban restaurant da zasu wuce ta gabanta tace ai saiya tsaya sunci abinci.
"Dan Allah me zamu tsaya muyi anan? idan yunwa kike ji muke gida sai kisa Ruk'ayya ta dafa miki duk abinda kike so." cewar Umar Faruk.
Cikin raha tace "a'a ni bana jin yunwa , kawai zamu je ne a matsayin masoya kuma muci abinci."
"Um um , nifa bana son shiga irin guraren nan." ya fad'a cikin shagwab'a.
"Ai tare zamu shiga, in dai kana sona kawai muje."
Saida ya rank'wafo bayanta ya kwantota yace "an gama ranki shi dad'e."
Tsayawa yayi kamar yanda take so suka shiga babban restaurant d'in, d'aya daga cikin ma'aikatan ne suka tarbesu da kyakyawar mu'amula har suka samar musu da wajen zama, ana aka basu takardar da zasu duba abinda suke so, Khairat ce ta zaba Umar Faruk kuma yace abinda take so shi zaici, cikin k'ank'anin lokaci aka wadata gabansu da kayan tab'awa, suna ci suna hira kamar masoyan tun a ranar farko, suna daf da gamawa ma'aikacin ya dawo ya basu bill d'insu, ganin kudin da zasu biya yasa Khairat kallon Umar Faruk, shima kallonta yayi saita bawa ma'aikacin takardar ta nuna Umar Faruk tace "kaba baby zai biya." tana fad'a ta bud'a post d'inta ta d'auko kud'i ko dubawa ba tayi ba cikin dubara ba tare da kowa ya gani ba.
Nufa wajen Umar Faruk ma'aikacin yayi amma sai Khairat ta rigashi isa ta sunkuya kamar ta mishi sumba ta kamo hannunshi ta dank'a masa kud'in kafin ta dago ta kalli ma'aikacin cikin harshen frensh tace "dan Allah ina zan samu douche?"
Kwatanta mata yayi ta nufi wajen Umar Faruk kuma ya kalli a hannunshi yaga kud'i, karb'ar takardar bill d'in yayi sai yaga kud'in da aka rubuta ko kasheshi za ayi ba zai iya biyansu ba, sai lokacin ya fahimci abinda Khairat tayi, murmushi kawai yayi yayi kamar ya fito da kud'in daga aljihunshi ya bawa ma'aikacin, godiya yayi ya wuce Umar Faruk kuma ya maida kallonshi ta inda habibiyar zata fito.
Ai kuwa sai gata dama ba abinda taje tayi kawai dan tabar wurin ne, tana zuwa ya mik'e itama post d'inta ta d'auka sannan suka wuce, suna fita waje ya kalleta yace "me yasa zaki biya? bayan nine ya dace na biya."
"Ni kuma? biyan me?"
Kallonta yayi yaga raina masa wayo kawai za tayi dan haka yace "daga yau bana so ki sake shiga aikin daba naki ba, wannan ba huruminki bane, yin hakan kamar kina nuna ba zan iya d'aukar nauyinki bane."
Saida suka hau mashin d'in tace "duk da bana da ilimin addini, amma nasan abune mai kyau mata ta taimakawa mijinta, nice nace muzo nan badan kana so ba, taya zan bari kayi asarar mak'odan kud'ad'e har haka."
Jin yayi shiru yasa ta bishi da wata kissar ta hanyar rumgumeshi ta baya tana sauke numfashi tace "kayi hak'uri to idan ranka ya b'ace, zan kiyaye anan gaba, amma ban maka alk'awari ba."
Hannu ya zura ya shafi fuskarta yace "Allah ya miki albarka."
Da sauri ta d'aga daga jikinshi cikin daga murya kamar ta manta inda suke tace "wayyo Allah, yau mijina ne yake saka min albarka, gaskiya na gode baby, dan Allah kayi min alk'awarin kullum zaka dinga saka min albarka, kaji?"
"Nayi alk'awari." ya fad'a yana rik'e hannunta dake kan cinyarshi.
A haka suka kai gida cikin nishad'i da farin ciki, saida suka shiga wanka suka fito kafin ya saka doguwar riga ya shiga yiwa iyayensu saida safe, d'akin Zuby ne ya shiga qarshe ya tarar da ita kwance tana chat a
Showing 93001 words to 96000 words out of 186119 words
"Kaga nifa akwai maganar da nake so muyi da kai."
"Ina jinka." ya fad'a yana gyara zama.
"Dama wata tafiya ce ta taso mai mahimmanci, kuma Khairat tace mahaifinta yace dole sai dai mu tafi tare, in kuma banje ba ba zasuji dad'i ba, ni kuma harna ce mata na amince, saboda akwai wani laifi da nayi mata tace zata fad'awa Baba, saboda haka yasa nace na amince, amma ni gaskiya har yanzu bana jin zan iya tafiya tare da ita haka kawai a dinga nuna ni a gari."
Saida ya gama nazartarshi kafin yace "to ita dai rayuwar duniya da kake gani inka biya ta abinda mutane zasu fad'a to babu inda zaka je, sannan a matsayinka na mijinta kuma kace zaka, amma daga baya kace a'a hakan zai iya tab'a darajarka da mutuncinka a wajenta, iyayenta kuma tunda suka ce suna buk'atarka a wajen, tofa akwai buk'atar son ganinka ne a wajen, dan haka ni ina ganin kawai ka bita ku tafi tunda dai ba siyar da kai za tayi ba, matsala d'aya ce kawai nake tunanin za'a samu."
"Matsalar me kenan?"
"Zubeida mana, da ace kafin ta tare ne, amma a yanzu data tare kuma na lura kan yarinyar yana rawa, bai zama lallai ta amince ka tafi ba."
"Nima yaya nayi wannan tunanin tun kafin kayi, amma da yake tamin alk'awarin idan har mun kwana biyu to ba zamu wuce uku ba, a lissafina ranar talata ne tafiyar ta kama, daga gobe kuma kwanan Khairat zai qare, kaga kenan a ranar da zan koma d'akinta ne za ayi tafiyar, kenan ko an shiga kwanan Zuby to kwana d'aya ne."
"Eh to da sauk'i idan hakane, dan haka ka fara shiri kawai ni zanji dasu Baba, sai kuma ka nemi izinin matarka."
"Izini kuma? haba dai, kamar itace mijin."
"A wannan qadamin kam kusan itace, dan ka sani in bata amince ba ba zaka tafi ba, idan kuma ka tafi bada amincewarta ba, tofa ka sani ranar gobe Allah zai tsayar da kai a gabanshi."
"To naji, Sheik Abbakar."
"Sheik Umar Faruk dai, kuma kayi k'ok'ari kafin ku dawo kuzo mana da babban tsaraba."
Dariyar da yake yasa yace "wane irin k'ok'ari kuma, wace irin tsaraba?"
Cikin rad'a yace mishi "baby "
Bushewa sukayi da dariya harda tapa hannu kafin Umar Faruk yace "baka da dama wallahi, taro ne fa zai kaimu ba lune da miel (honeymoon) ba."
Da haka suka isa masallaci kamar wasu abokanai suna hirarsu cikin raha, saida aka gama hud'uba kafin akayi sallah daga nan kuma suka dawo tare suka komo gidansu Khairat dan d'aukarta kamar yanda yace.
*****************
Suna zuwa tare suka shiga da Abbakar har ciki, a lokacin masu aiki na k'awata wajen cin abinci da kalolin girke girke, Khairat da fitowarta kenan daga d'akinta ta gama sallah ta dako da gudu ta rumgume Umar Faruk, "sannu baby , har kun taso?"
Kasa aiwatar da komai yayi saboda fitowar Mamie itama daga d'aki wanda Mammie dama tana zaune a falon, abinka ga yan bariki😂 ba wanda yaji wani abu, sai Umar Faruk daya ji kunya ta rufeshi, suna shirin zubewa qasa dan kwasar gaisuwa Mamie ta qaraso da sauri ta dafa kafad'un Umar Faruk duka biyun tana fuskantarshi tace "a'a a'a, haba d'ana, ai ka wuce wannan a gidan nan, kaima fa d'an gidan nan ne."
Hannunshi ta rik'e tayi hanyar wajen cin abincin dashi tana fad'in "muje ga abinci an gama kuci."
Umar Faruk dai kanshi na qasa ya kasa kallonta sai Abbakar dake kallon falon irin tsari da dukiyar da aka zuba, da kanta taja mishi kujera ya zauna ita kuma mai aiki taja mata ta zauna, Khairat ma da Mammie duka sun zauna, Biba da Saude ne suka bud'a kwanukan suka fara zuba musu abincin, suna gamawa suka koma mafakarsu su kuma suka fara cin abincin.
Ba ruwan Khairat haka kawai take jin son Umar Faruk na gaskiyar na shirgarta, da kanta take d'ibar abincin tana saka mishi a baki saboda taga baya ci, haka yasa ya fara diba kad'an kad'an yana ci, Khairat d'in da Mammie kuma hira suke sosai irin na kaka da jika , Abbakar dai kallon ikon Allah yake yana qara ganin girman Khairat, dan inba mai hak'uri ba babu ta yanda za ace kana rayuwa cikin wannan daular kamar a masarauta, abinci ma na rana kana cin kusan kala uku zuwa hud'u amma ka yarda ka fara rayuwa a gida kamar nasu, haka ma a wajen Umar Faruk abinda yake rayawa kenan a zuciyarshi tare da sake jaddada irin taushin zuciyar Khairat, lallai baka sanin asalin mutum saika zauna dashi sannan zaka fahimceshi.
Suna kammalawa kafin su tashi Mamie ta kalli Khairat tace "ki tashi kije ki shirya kizo ku tafi."
A shagwab'e ta kalli Mamie tace "to Mamie."
Umar Faruk ne yace "a'a Mama, ku barta kawai ta zauna, naga kunyi kewarta sosai, idan na taso daga aiki zan biyo saina d'auketa."
Cike da farin ciki ta kalleshi tace "da gaske baby? gaskiya naji dad'i."
Mak'ale wuyanshi tayi tare da janyoshi kusanta ta sumbaci kumatunshi tare da fad'in "na gode baby."
Mammie dake kusan Khairat ce ta zura hannu ta kama kumatunshi tace "yaron kirki, gaskiya ka kyauta, dan dama muna so muyi shirye shiryen tafiyarmu a gabanta."
Ture hannunta Khairat tayi tana fad'in "kuma shine saikin tab'a min miji , nifa bana son haka."
"Allah sarki, yo mijinki ko mijina? kaji min yarinya kai, kawai dan na ara mikishi saiki wani zak'e dayawa."
Kallon Umar Faruk tayi ta kalli Mammie tace "zak'ewa ma nake? to ai mijin naki ne ke rawar qafa a kaina."
"Kaji wani d'aurin duniya kuma, to nidai ban gani ba, kuma nasan yafi sona."
"To ai gashi nan ki tambayeshi kiji." Khairat ta fad'a tana nunashi da hannu
"Ba buk'ata, danni zai zab'a, bana so kiji kunya a gaban mutane."
Cikin taushin murya cike da jin kunya Umar Faruk yace " gaskiya ne, za tasha a wajenki."
Mammie kam bushewa tayi da dariya had'e da yiwa Khairat gwalo, turo baki tayi tana kallon Umar Faruk, shi kam kasa kallonta yayi saboda wutar tartsatsin da yake ji a kanta, haka suka mik'e gaba d'ayansu zasu tafi, bayan sunyi sallama Mammie tace "nasan dai sai mun had'u a lokacin tafiyarmu ko?
"Insha Allah." ya fad'a kawai.
"To Allah ya nuna mana."
"Ameen." suka amsa.
A hankali Khairat ta taka musu har zuwa k'ofar d'aki sannan suka tsaya, sumbatar bakinshi tayi tare da kumatunshi kafin ta kalleshi tace "Allah ya tsare, saika zo."
Su Mamie dake hangensu yasa ya d'an shafi fuskarta kawai yayi gaba, suna fita suka d'auki hanya saida ya aje Abbakar gida ko shiga baiyi ba ya juya ma'aikata dan lokaci yayi sosai, sai dai zuciyarshi ta qara narkewa da tsananin son Khairat, haka ya koma duk baijin dad'in aikin saboda manyan kayan dake jikinshi, ga kuma motsi da k'amshin Khairat daya isheshi duk sanda ya motsa, ji yake kamar tana jikinshi ko kuma tana sumbatartashi, a haka dai ya gama aikin a daddafe har aka tashi.
Bai wuce gida ba har saida ya tsaya ya siyawa Zuby kayan data buk'ata kafin ya wuce gida, yana isa ana kiran sallah magrib hakan yasa yana shiga d'akinta ya aje mata kayan ya fito yayi alwala cikin gaggawa ya tafi masallaci, bai dawo gidan ba har saida akayi sallah isha'i saboda lokacin qurarre ne kuma suna tare da Ishaq suna hira, suna gamawa ya shigo gidan saida ya fara shiga wajen Baba suka gaisa kafin ya shiga d'akin Mama da sauran iyayen, yana fitowa ya wuce d'akin Zuby.
Ya samu tana nad'e sallayar da tayi sallah, abinda ya qona masa rai da haushi shine, d'akin dai tsaf dashi sai kamshin turaren wuta amma kayan jikinta, tun atamfar safe ce daya fita ya barta da ita ya kuma dawo ya sameta da ita, kuma yanzu ma ita dai ce, ya d'auka kafin ya dawo daga masallaci zai samu ta canza, amma ina alamu dai na ba tayi wanka ba tun na safe, zaune yayi a kukerar robar dake fuskantar gadon ya kalleta fuska ba yabo ba fallasa yace, cike da ladabi tace "sannu da zuwa."
"Yawwa, sannu? ya gida?"
"An gode Allah."
Aje sallayar tayi ta tsaya tana kallonshi, a d'an dak'ile yace "zauna mana."
Zaune tayi bakin gadon tana kallonshi shima wuyanta yake kallo dake tsattsafo da zufa , a shak'e yace "kin duba kayan?"
"Eh yah, na duba."
"To miye babu a ciki?"
Cikin sanyin murya tace "eh to, kusan abinda babu kad'an ne gaskiya."
Da d'an k'arfi yace "to yanzu kamar nawa zai isheki ki siyo abinda babun?"
Nanma a ladabce tace "eh to, ko nawa ka bayar ma zai isa."
D'aga gira yayi sama ya d'an zame daga kan kujerar yasa hannu aljihu ya fito da kud'i, jikka biyar biyar guda biyu ya bata yace "gashi, sai kiyi manage dashi dan kinsan nauyi dayawa ne a kaina."
"An gode Allah ya saka da alkairi." ta fad'a a sanyaye.
Sauran canjin ya mayar aljihu kafin ya sake gyara zama ya kalleta sosai yace "ina son yin wata muhimmiyar magana dake, ina fatan zaki bani hankalinki kuma ki fahimceni?"
"Ina ji yah Umar."
"Zubeida, akwai wani babban taro da aka shirya a Germany, taro ne na manyan mutane wanda zai had'a da iyalensu, mahaifin Khairat na d'aya daga ciki, kuma ya gayyaceni a matsayina na surukinsa, tafiyar zata iya d'aukanmu kwana biyu zuwa uku, shi yasa nake neman alfarmarki kwanan d'ayan, domin zai iya yiwuwa na shiga cikin kwananki domin kinsan tafiyar hali, kosu Mama basu sani ba domin ina so na kammala daku iyalina, ina fatan zaki min wannan alfarmar ki bani kwananki d'aya tak."
Cikin mamakin kalamansa tace "tafiya kuma, har qasar waje, amma kuma kai yaya ka amince ka tafi? ba ka tsoron ko wani abu aka shirya maka."
"Me kuma za'a shirya min? tare fa da Khairat zamu tafi."
"Darammm." taji gabanta ya fad'i, cike da kasa b'oye abinda ke ranta ta mik'e tsaye tace "uhum, yanzu naji magana, kace dai tare da karuwarka zaku tafi, wato harta bud'e maka idon da har kake tunanin fara biyarta a duk inda tayi ko? yah Umar wai yaushe ka zama haka ne? gaba d'aya ka canza kamar ba kai ba, to wallahi in dai izinina ne ake nema ban yarda ba."
Wata wawura daya ma hannunta har yayi qara cikin d'aga murya yace "Zubeida , akan miye ina magana dake har zaki mik'e tsaye kina min ihu, rainani ne ki kayi kome, me yasa zaki d'aga muryarki akan tawa? wai tambaya ma kike yaushe na canza? to a ranar da kika canza na canza nima, akan miye zan zaunar dake ina miki magana cikin nutsuwa ke kuma zaki d'aga min hankali, waye ya koyar dake wannan d'abi'ar? nace waye yace kizo nan ki dinga min abinda ranki yake so, waye." ya qarashe da d'aga murya tare da hankad'ata saman gado.
D'orawa yayi da "kina tunanin izininki nake nema? to baki fahimta daidai ba, ni alfarma na nema kimin ta kwana d'aya wanda shima qila waqala na yishi a can, da har zaki wani ce wai baki yarda ba, to karki yarda mana saime? naga idan zamanki nake a gidan."
"Ba dai alfarmar dana nema bace har tasa kika min haka, to bari ki gani yanzu zanyi maganin abin."
Wayarshi ya ciro daga aljihu ya danna kira, daga d'aya b'angaren ana d'auka cike da karsashi da kashe murya tace "hello baby."
Saida ya lumshe ido saboda yanda yaji har tsikar jikinshi ta tashi, saita nutsuwarsa yayi tare da sauke ajiyar zuciya kafin yace "hello, ya kike?"
Cikin shagwab'a da wata shegiyar kissa tace "ba dad'i, ka tafi ka barni inata jiranka, duk da ina kewar gida amma har kasa naji gidan ya gundureni saboda kayi nesa dani, a gaskiya Faruk sai yanzu nake qara tabbatarwa cewa soyayya *had'in Allah ce*, yanzu fad'a min yaushe zaka taho?"
Baisan sanda wani basaraken murmushi ya sub'uce masa ba, a hankali ya furta "zanzo, yanzu fad'a min tafiyar nan da zamuyi, kina ganin zamu iya dawowa a kwana biyu?"
"Eh baby , dan a ranar da za muje ma a ranar za'a gabatar da taron, kawai dai akwai gajiyar tafiya da kuma ganin gari da zai iya kaimu kwana ukun."
Yanda muryarta ke fita yasa yasa hannunshi yana shafar saitin zuciyarsa da yake jin bugunta yana canzawa , cikin basarwa yace "to a kwana biyu nake so mu dawo, ki shirya zanzo d'aukarki yanzu."
Cike da zumud'i da qwarin murya danta daki dodon kunnensa tace "an gama ranka shi dad'e."
Kashe wayar yayi ya maida kallonsa ga Zuby dake zaune tana sauraranshi, kallon sama da qasa ya mata yace "wai duk wanda ya samu dama ba zai tsaya wasa ba sai k'ok'arin ya dama damarsa, to in dan kwana d'aya ne ki rik'e na yafe miki bana buk'ata, zan tafi a ranar da kwanan Khairat zai zagayo, naga kuma mai hanani abinda naga dama."
Wucewa yayi ya barta a zaune yana fad'in "aikin banza kawai, yara da zaran sun ganka ba kaya a jikinka saisu nemi su rainaka."
Yana fita d'akin Khairat ya nufa ya bud'e da makullan wajensa ya shiga, kayansa ya cire ya shiga wanka, bai jima ba ya fito ya shirya cikin qananun kaya yayi wanka da turare kafin ya d'auki makullin mashin d'inshi dan dashi yake so ya d'auko gimbiyar.
_Yaufa my Khairat utu utu zata hau._😁
*****************
Duk da yaso ta fito amma saida tasa ya sake shiga ciki ya gaishe dasu Mamie kafin ta fito, cak ta tsaya saboda ganin Dream a maimakon Renge rover😂, matsowa tayi kusanshi tace "baby, ina motar take?"
Gemunshi ya tattaro ya had'e guri d'aya yana murmushi, a tunaninta so yake ya gwada soyayyar da take fad'in tana masa shi yasa ya taho da mashin d'in, ba zata bari shirinta ya watse ba dan haka ta saki murmushi ta rumgumeshi taré da sumbatar kumatunshi kafin tace,
"Karo na farko a rayuwata zan hau mashin, a gaskiya soyayya za tayi dad'i akan mashin."
Cikin dariya ya fara qoqarin hawa yana fad'in "saima kin hau zaki tabbatar."
Rik'e rigarsa tayi tace "ka taimaka min na hau kafin ka hau."
Hannun damansa ya mika mata ta rik'e sannan ta tattare rigarta kafin ta hau, yana hawa ya tayar suka d'auki hanya, tintserewa tayi da dariya ta fara masa cakulkuli tana fad'in,
"Ashe haka mashin yake? gaskiya daga yau ba zan sake hawa mota ba, nima mashin zan siya sabo."
"Ke ke, dan Allah ki bari, za kisa mu fad'i fa, ki bari mana, hhhhhhh." ya qarashe da dariya.
Saida suka hau titi kad'ai ta rabu dashi amma fa tana makale a bayanshi tayi luf kamar mai bacci, surutu kawai take zuba masa shi dai nishadi da farin ciki ma ya hanashi magana, da sauri ta nuna masa wata babban restaurant da zasu wuce ta gabanta tace ai saiya tsaya sunci abinci.
"Dan Allah me zamu tsaya muyi anan? idan yunwa kike ji muke gida sai kisa Ruk'ayya ta dafa miki duk abinda kike so." cewar Umar Faruk.
Cikin raha tace "a'a ni bana jin yunwa , kawai zamu je ne a matsayin masoya kuma muci abinci."
"Um um , nifa bana son shiga irin guraren nan." ya fad'a cikin shagwab'a.
"Ai tare zamu shiga, in dai kana sona kawai muje."
Saida ya rank'wafo bayanta ya kwantota yace "an gama ranki shi dad'e."
Tsayawa yayi kamar yanda take so suka shiga babban restaurant d'in, d'aya daga cikin ma'aikatan ne suka tarbesu da kyakyawar mu'amula har suka samar musu da wajen zama, ana aka basu takardar da zasu duba abinda suke so, Khairat ce ta zaba Umar Faruk kuma yace abinda take so shi zaici, cikin k'ank'anin lokaci aka wadata gabansu da kayan tab'awa, suna ci suna hira kamar masoyan tun a ranar farko, suna daf da gamawa ma'aikacin ya dawo ya basu bill d'insu, ganin kudin da zasu biya yasa Khairat kallon Umar Faruk, shima kallonta yayi saita bawa ma'aikacin takardar ta nuna Umar Faruk tace "kaba baby zai biya." tana fad'a ta bud'a post d'inta ta d'auko kud'i ko dubawa ba tayi ba cikin dubara ba tare da kowa ya gani ba.
Nufa wajen Umar Faruk ma'aikacin yayi amma sai Khairat ta rigashi isa ta sunkuya kamar ta mishi sumba ta kamo hannunshi ta dank'a masa kud'in kafin ta dago ta kalli ma'aikacin cikin harshen frensh tace "dan Allah ina zan samu douche?"
Kwatanta mata yayi ta nufi wajen Umar Faruk kuma ya kalli a hannunshi yaga kud'i, karb'ar takardar bill d'in yayi sai yaga kud'in da aka rubuta ko kasheshi za ayi ba zai iya biyansu ba, sai lokacin ya fahimci abinda Khairat tayi, murmushi kawai yayi yayi kamar ya fito da kud'in daga aljihunshi ya bawa ma'aikacin, godiya yayi ya wuce Umar Faruk kuma ya maida kallonshi ta inda habibiyar zata fito.
Ai kuwa sai gata dama ba abinda taje tayi kawai dan tabar wurin ne, tana zuwa ya mik'e itama post d'inta ta d'auka sannan suka wuce, suna fita waje ya kalleta yace "me yasa zaki biya? bayan nine ya dace na biya."
"Ni kuma? biyan me?"
Kallonta yayi yaga raina masa wayo kawai za tayi dan haka yace "daga yau bana so ki sake shiga aikin daba naki ba, wannan ba huruminki bane, yin hakan kamar kina nuna ba zan iya d'aukar nauyinki bane."
Saida suka hau mashin d'in tace "duk da bana da ilimin addini, amma nasan abune mai kyau mata ta taimakawa mijinta, nice nace muzo nan badan kana so ba, taya zan bari kayi asarar mak'odan kud'ad'e har haka."
Jin yayi shiru yasa ta bishi da wata kissar ta hanyar rumgumeshi ta baya tana sauke numfashi tace "kayi hak'uri to idan ranka ya b'ace, zan kiyaye anan gaba, amma ban maka alk'awari ba."
Hannu ya zura ya shafi fuskarta yace "Allah ya miki albarka."
Da sauri ta d'aga daga jikinshi cikin daga murya kamar ta manta inda suke tace "wayyo Allah, yau mijina ne yake saka min albarka, gaskiya na gode baby, dan Allah kayi min alk'awarin kullum zaka dinga saka min albarka, kaji?"
"Nayi alk'awari." ya fad'a yana rik'e hannunta dake kan cinyarshi.
A haka suka kai gida cikin nishad'i da farin ciki, saida suka shiga wanka suka fito kafin ya saka doguwar riga ya shiga yiwa iyayensu saida safe, d'akin Zuby ne ya shiga qarshe ya tarar da ita kwance tana chat a
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32 Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63