take zuwa kuma wannan kuma ban sani ba, dan tana zuwa club da dama daga manya har qanana, yau kuma nasan zata fita saiku had'u acan."

Da mamaki Faruk ya kalleshi yace "malam, mufa a ma'aikatarta muke aiki, ba wani abu bane a tsakaninmu da ita ba, amma ta yaya zamu sameta a wannan wajen kuma fa sai cikin dare."

D'aure fuska mutumin yayi yace "kunga dan Allah kubar nan, taimako kuka ce kuma shi nayi muku."

Yana fad'a ya koma mazauninshi ya barsu tsaye, mashin d'insu suka hau akan hanya suna tunanin wata shawarar, amma Faruk yace shi bai tab'a zuwa gidan rawa ba ba kuma zai fara zuwa yau ba.


Suna zuwa gida suka fad'awa Baba yanda ake ciki, fafur Baba ya rufe ido yace bai yarda su tashi su koma, ganin basu son tafiya yasa Baba ya tisa k'eyar Umar faruk gaba yace su tafi, haka kuwa akayi akan mashin d'inshi suka tafi, amma wannan karan suna zuwa mai gadin yace musu an tafi da ita likita babu lafiya, da alama ma kamar babu rai a tare da ita, tabbas Umar faruk yaji ba dad'i kuma yana tsoron ace abinda ya faru tsakaninsu ne ya janyo faruwar hakan, likitar aka fad'a musu suka nufi can shi da Baba.


_Faruk ni dai a ganina da kun hak'ura da son ganinta kawai._πŸ˜‰


Cikin sa'a kuwa suna zuwa sukaga masu tsaron mahaifinta a kusa da d'akin da aka shigar da ita cikin gaggawa, kusa da d'akin suka tsaya amma ba suyi magana ba saboda ganin mahaifin nata nata kai komo a wajen ya gagara nutsuwa, duk da baisan mahaifiyarta ba amma da gani yasan ita ta haifeta saboda tsananin kamar da suke, kuma dama tun daga fatar jiki zaka san uwace tayi ba mahaifinta ba dake tillik'ik'e kuma bak'i wulik dashi,🀣 had'in gambiza ba, duk da akwai damuwa sosai a fuskarta amma dai babu alamun hawaye a tare da ita.

D'auke kai sukayi kamar ba wajensu suka zo ba, amma abin mamaki shine muryar Baba da sukaji yace "kina zaune hankali kwance, da alama so kike ta mutu ki huta ko? to ta Allah ba taki ba wallahi."

Tsaye ta mik'e cikin jin zafi tace "eh, so nake ta mutu na huta, kai a ganinka idan ta mutu ba zan samu salama ba? idan da abinda ya janyo mata wannan halin bai wuce kai ba, wallahi duk kai kaja mana halin da muke ciki saboda bak'in halinka, yarinyar nan tun tana k'arama ta fara fahimtar halayenka, amma hakan baisa ka daina ba, me kake so ta zama? wallahi ka sani alhakin lalacewar rayuwarta yana wuyanka ne, addu'a d'aya nake mata yanzu shine, kar Allah yasa ta fara shaye shaye da bin maza kamar yanda kake lalata 'ya'yan wasu."

Fizgota yayi daf dashi cikin hassala yace "ke ya isa haka, ke me yasa baki da kunya ne? a cikin mutane zaki nime tozarta ni, kuma ni ai nasan 'yata, wallahi ba zata tab'a bin maza ba."

Fizge hannunta tayi tasa gyalenta ta share hawayen idonta tayi murmushin takaici tace "kenan baka so ta fara bin maza ko, ka manta da fad'ar Manzo (S.A.W) ne, _cewar duk abinda kayi sai an maka_? kayi gaggawar aurar da ita, idan kuma ba haka ba to wallahi ni zan barka na koma wajen iyayena, dan ba zan iya supporter naji kona ga wani abu ya sameta ba."


"Ke marar mutunci, wallahi zai karyaki a warin nan, shashashar banza kawai."

Duk maganar nan yayita ne da d'aga hannu kamar zai mareta, zaburowa tayi tace "ka dakeni mana, ina jin tsorone ? dukanka wane irine ban gani ba ai sai dai kuma na gaba."

Hannu ya d'aga kam da nufin kai mata mari sai kawai ya tsaya cak saboda ganin Khairat d'in da aka shiga da ita ranga ranga amma ta fito da k'afafunta, kamar dai yanda suka taho da ita haka ta fito babu takalmi ba kallabi, kallon iyayen nata kawai take sai huci take saukewa, takowa ta farayi gabansu docteur kuma ya biyo bayanta yana neman ta tsaya dan farfad'owarta kenan taji hayaniyar iyayenta, saida ta tsaya gabansu ta kallesu da kyau sannan ta kalli drivensu tace "muje ka mayar dani gida."

Wucewa tayi mahaifin nata ya rik'e hannunta yana fad'in "gimbiyata, ina kuma zaki je ya jikin naki?"

Da iya k'arfinta ta fizgo hannunta tana mashi jan kallo tace "lache moi ma main." ta k'arashe da d'aga murya.

Wucewa tayi suka bi bayanta Papa na kiran sunanta harta shiga mota ta rufe, haka suka shiga motar ba tare da kowa yayi magana ba har suka kai gidan.

Faruk kam da Babanshi mutuwar tsaye sukayi, mamaki ya gama kashesu a wurin, tabbas akwai wasu abubuwa a cikin rayuwar gidan, da alama arzik'i ne Allah ya musu amma babu kwanciyar hankali.


_Wallahi da auren wani mai kud'in gwara auren talaka in dai da kwanciyar hankali, Allah ka k'ara mana kwanciyar hankali da ni'ima a qasarmu dama sauren qasashe baki d'aya._

*********************

Gida suka koma dan sunga babu alamun nasara, amma duk da haka Baba bai hak'ura ba yace koma da safe ya shirya ya tafi gurin aikinshi kamar yanda ya saba, watak'ila idan da rabo ma ba zata masa magana.


*Luv you guy's*😍
06/08/2019 Γ  00:06 - Meerahgee❀: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*JIHADI*
_Umar faruk_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_

_My BK, kiyi sauri ki dawo fa._

_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


_Bismmilahir-rahman-rahim_


*Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a garesa yace* " _Kaji tsoron Allah a duk inda kake_"
*Rawahu muslim*


3⃣

Tunda ta shiga d'aki wanka tayi ta saka kayan data saba sakawa wato k'aramin wando iya cinya da k'aramar riga, zaune tayi akan gado tana tunanin abinyi, har akayi sallah magrib da isha amma bata tashi daga in da take ba, wani tunani da tayi yasa ta tashi ta fito daga d'akin, duk da duka iyayen nata na zaune a falon amma babu wanda ta kula bare ta masa magana, farfajiyar gidan ta fita, masu tsaron mahaifinta ne zaune a kusa da mai gadi suna hira, tsaye tayi nesa dasu cike da raini tace "kuzo nan."

Kallon juna sukayi cike da raini suka tashi a kasalance suka nufi wajenta, tsaye sukayi kowa ya d'auke kai babu mai kallonta, cikin jin haushi ta daka musu tsawa "kai, ni kuke wa wannan kallon? to ku saurareni da kyau kuji aiki zan saku."

Shirun da sukayi yasa ranta ya sake b'aci , a harrzuk'e ta shak'o uwan rigar d'aya daga cikinsu tana fad'in "kai matsiyacin banza, ku har kun isa ina magana daku kuna wani d'auke kai, ko kun manta k'ark'ashin mahaifina kuke, kufa ba komai bane face maqasqanta wanda suke wuni dare da rana a bayan iyayenmu domin tsare lafiyarsu, yaushe kuka fara tunanin kuna da matsayi da har zaku rainani?"

Mai sauk'in cikin sune yace "kiyi hak'uri Hajia, ki fad'i aikin da zamu miki."

Tureshi tayi yayi baya baya kamar zai fad'i sannan ta kalli wanda yayi maganar tace "ku nutsu ku jini da kyau, akwai wani saurayi da nake so ku d'auko min shi gobe, ina so ku kaishi d'aya daga cikin gidajen Papa, idan kun d'aukoshi saiku kirani zan sameku acan, amma kafin nazo ku tabbatar kun canzamin kammaninshi ta yanda ba zai iya gane kanshi ba bare kuma wani."

Da hannu ta nunasu tace "kun fahimta?"

D'aya daga cikine yace "amma ta yaya zamu iya ganeshi kenan?"

Sai lokacin ta tuna da hakan, a wulak'ance ta kallesu tace "ku jirani anan, yanzun nan zan samo photonshi."

Binsu tayi da harara tare da fad'in "banzaye kawai marasa anfani."

Tana wucewa wanda ta shak'e ma wuyan riga yayi wani huci tare da rik'e gudu yana kallonta, a hassale yace "wallahi saina ma yarinyar nan rashin mutunci ta yanda gobe ba zata sake sha'awar wulak'anta wani ba, dan muna aiki qasan mahaifinta bashi ke nuna maqasqanta bane kamar yanda take d'auka, wallahi na gaji dan abinda take mana ko wannan banzan mashayin uban nata bai isa ya mana ba bare kuma ita banza."

D'aya daga cikine yayi dariya yace "toya zamuyi tunda Allah ya d'orasu akanmu, kuma da kake cewa zaka mata rashin mutunci, ita fa 'yar akuya kai kasan haka, kenan me kake tunanin yi mata?"

Da sauri ya bashi amsa da "dukan tsiya zan mata wallahi har saina sab'a mata kammaninta."

Shak'iyin cikin ne ya lashe baki tare da d'an cije leb'e yace "ku naku duk wasa ne, irin yaran nan ai duka baya gyarasu, karfa ku manta gatane ta gani shi yasa take abinda take so, ni wallahi ban tab'a jin wai na daketa ba, dan duka ba shine mafita ba."

"Miye mafita to? danni dai na gaji da rainin hankalin yarinyar nan."

Saida ya kalleshu yana murmushi kafin yace "kona fad'a ma ba zaku iya ba, dan haka ku barni kawai ni zanji da komai."

"Kamar ya ba zamu iya ba? ka fad'a in dai har za muyi maganinta wallahi za muyi."

Sake kafesu yayi da ido yace "kun tabbata?"

"Eh, ka fad'a kawai."

Ajiyar zuciya yayi yace "kullum tana cikin qananan kaya, hakan kuma na tayar min da sha'awata, abinda za muyi kawai mu takurata ta hanyar samun biyan buk'atarmu, ta hakane kad'ai zamu iya huce abinda ta mana."

Tuni d'aya daga ciki har shaid'an ya k'awata masa abin, cewa yayi "kuma fa hakane wallahi, dan shi fyad'e idan kayiwa mace ba zata tab'a mantawa ba har abada, kaga zamu tashi 1-1 mu da ita ,ita ba zata manta ba muma ba zamu manta irin wannan cin kashin data mana ba."

Hannu ya bashi suka bige suna dariya yace "da kyau mutumina ka fahimceni daidai, kuma ma wannan yarinyar ai da gani kasan ba mune zamu fara ba, da alama wasu sun rigamu kai da gani kasan ba budurwa bace, a idone kawai muke ganin haka."

"Gaskiya ne kuma."

"To amma ni gaskiya ina d'an jin tsoro, gaskiya ban tab'a yi ba tunda nake, kuma kaga za ayi binciki akan lamarin nan idan aka ganemu, kunga fa shikenan munyi asarar rayuwarmu mun b'ata k'uruciyarmu a banza."

"Bama za'a ganemu ba, ai za muyi anfani ne da kasancewarmu sojiji miyi aiki da ilimi, insha Allah komai zai wuce babu abinda zai faru, kuma muma ai bamu tab'a yi ba."

"To ya zamuyi kenan?"

"Abu mai sauk'i, kawai za muyi anfani da gidan rawar da take zuwa duk kwana uku sai muyi komai acan, kunga ta haka zamu fita daga zargi kuma babu wani bincike, domin kuwa cikin biyu dole suyi tunanin d'aya."

"Kamar me dame kenan?"

"Na farko za suyi tunanin kodai ita da samarinta ne da suka saba shek'e ayarsu, ko kuma dai tunda wajen rawa na b'ata garine , kaga za'a ce ta had'u da marasa jine kawai suka mata fyad'e wannan shine."

Cikin dariya d'aya ya bashi hannu yana fad'in "gaskiya Musa kanka naja sosai, wannan tsarin fa yayi."

Cikin dariyar mugunta yace "ko baiyi ba dole zan fito da wani, dan burina kawai buk'atata ta biya a kanta."

Musa ne yace " ku zama cikin shiri , dan ko yau bata fita saboda abinda ya faru, watak'ila kwana uku mai zuwa ta fita."

Da wannan shawara suka tsaya akai.

_Allah ya kiyaye_πŸ‘

Tana shiga d'aki wayarta ta d'auka a saman gado k'irar IPhone XMax, kira ta aikawa manager yana d'auka cike da salon bada umarni tace "ina so cikin 5 minute ka aiko min da adreshin gidansu yaron nan tare da photonshi."

Tana gama fad'a ta kashe wayar, zaune tayi tsakiyar gadon tana jiran shigowar sak'on manager, 2 minute saiga sak'on ya shigo adreshi da kuma photonshi, a hankali ta furta sunan unguwar tasu " *Bassora*"

Take ta tuna marin daya mata, bata san lokacin data goge photon ba daga wayar saboda b'acin rai, ajiye wayar tayi a gefenta ta fara sauke nunfarfashi ita kad'ai, jin qirjinta ya fara nauyi yasa ta tashi ta bud'a coffre ta d'auki maganinta tasha sannan ta koma gado ta kwanta, bacci harya fara d'aukarta wayarta ta fara k'ara, tana dubawa taga sunan *Macho* ya fito, d'auka tayi ta d'ora a kunne tare da jan zanin rufarta ta rufe tace "hello macho."

Daga d'aya b'angaren tace "yane macho? naganki shiru, yau kin fito ne?"

"A'a macho ba zan fito ba, kawai ki tafi kuji dad'inku."

"Haba macho, me yasa to ba zaki je ba? kin ganni fa harna shirya."

"Ba zanje ba macho, kije kawai, sai gobe naje."

"To in dai hakane, nima saina bari har goben sai muje kawai."

A daqile tace "wannan kuma matsalarki ce."

Tana gam fad'a ta kashe wayarta gaba d'aya ta koma baccinta, a cikin bacci taji kamar ana tab'ata, bud'a ido tayi taga mahaifiyarta ce ke shafar kanta sai kuma mahifinta daga gefenta a tsaye, cike da masifa ta tashi zaune tace....

"Meya kawoku nan kuma a wannan dar....."

Da sauri Mama ta rufe mata baki tace "kiyi hak'uri Khairat, na yarda nayi kuskure, amma ki sani mufa iyayenki ne dole mu damu da halin da kike ciki, mun kasa bacci saboda tunanin damuwar dake damunki."

A raunane ta kalleta tana shirin fashewa da kuka tace "Mamie, ya kike so nayi? kince na daina shiga harkarki kuma na daina, yanzu me kike so nayi to?"

Shiru sukayi kafin ta sake cewa "Mamie, ki fad'a min tunda muke dake kin tab'a nuna min soyayyarki, kullum hantara kike da yimin fad'a tare da kokarin aibatani, ban tab'a yin daidai ba a wajenki idan nayi ma bakya yabawa, babu abinda kuka koya min babu abinda kuke koya min wanda zai anfane ni, da fadanku na bud'e idona kune kullum cikin fad'a da aibata junanku, duk da kunsan matsalar da hakan ya janyo min amma baku daina ba, shin so kuke sai ranar da kuka bud'e ido baku ganni a duniya sannan zaku daina?"

Kuka Mamie ta fashe dashi tace "a'a Khairat, wallahi ina sonki, kinsan babu yanda uwa za tak'i yar data haifa, ni ina so ki zama yarinyar kirki amma mahaifinki bai damu da rayuwarki ba, ina damuwa da halin da kike ciki, kawai dai akwai dalilin da suka sakani nuna miki rashin kulawa, amma ki yafe min kinji yata ba zan sake nesantarki ba."

Ta fad'a tana rumgumeta, itama rumgumeta tayi cikin kuka tace "Mamie na riga dana b'ata rayuwata."

"A'a Khairat, kar kice haka, wallahi......"

Kafin ta k'arasa uban dake tsaye yace "wato kullum laifina ne ko, kullum burinki shine ki d'ora min laifi ni kad'ai ko? to wallahi baki isa ki rabani da yata ba muguwa kawai."

Kallonshi Mamie tayi tace "eh naji, in ni muguwa ce kai kuma fa? ai kaine babban mugu tunda duk kaine ka jefamu halin da muke ciki, kuma wallahi in har baka tuba zuwa ga Allah ba sai kayi *nadama*."

Matsowa yayi kusanta a hassale yace "wallahi kika sake magana a wajen nan saina tattakaki, saboda kin rainani ina fad'a kina fad'a ko?"

"Allah yana gani bai rainaka ba kaine dai ka raina kanka, kuma nasan Allah ma ba zai kamani da laifi ba."

"Ke..." wata k'ara da Khairat tayi yasa suka maida hankalinsu kanta, saukowa tayi daga kan gadon ta kama hannayen iyayen nata ta tisa k'eyarsu suka fita daga d'akin, saida ta kallesu kafin ta rufe k'ofar tace "ba zaku tab'a gyaruwa ba, wannan shine babbar damuwata, baku damu daku tozartani ba ko a dinga yayatani ba, a duk in da kuka samu kanku fad'a ku keyi da junanku."

Tana fad'a ta rufe k'ofarta ta koma gado ta dinga kuka da takaicin rayuwar iyayenta.

_Novel hausa akace, dan haka kuyi hak'uri 'yan uwa, ba zan sake saka muku wani harshe ba insha Allah domin kowa ya fahimta._

*Shin su musa za suyi nasara akan Khairat kuw*?

*Wai me yasa iyayen Khairat suke haka*?

*Meye matsalar da Khairat ke ciki?*

_Kafin sanin amsoshin bara mu koma baya mu fara sanin tushen labarin._

_Ku biyoni😍_
06/08/2019 Γ  00:06 - Meerahgee❀: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*JIHADI*
_Umar faruk_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


_Bismmilahir-rahman-rahim_


4⃣


*TUSHEN LABARIN*

*Alhaji Mani Bukar* babban mutum kuma mai babban dangi, asalinshi haifaffan garin *Maradi* ne kasuwancine ya kaishi *niamey* daga nan kuma harya tsunduma siyasa, mahaifinsu mutum ne daya sha boko sosai ya k'oshi, hakan yasa yake da kula da takatsantsan da yaranshi, matan mahaifinshi biyu amma gaba d'aya yaranshi guda biyar saboda tazara da ake sawa, mahaifinsu irin tsofaffin masu kud'in nan ne, hakan yasa bayan rasuwarsa yaransa suka kwashi rabonsu bayan rabon gado.

Bayan rasuwar mahaifin sai kowa ya fara abinda yaga dama, haka ma Alhaji Ousmane wanda sukafi kiranshi da *Mani*, bana ce muku mutumin kirki ne ba amma dai yana da wasu manyan halaye wanda muke da tabbacin duk mai aikatasu, to tabbas babu abinda zai iya gagararsa kuma zai iya yin komai, wannan halaye kuwa sune *zina* da shan *giya*, duk da wannan halayen amma ubangiji ya masa talala ta hanyar k'ara sakawa dukiyarsa albarka, yana cikin holewarsa tare da abokai kuma sai Allah ya had'ashi da *Na'ima*.

*Na'ima Bilal Abdallah*, yarinya mai hankali nutsuwa da kuma tarbiya, ta samu duk wannan ne a wajen iyayenta saboda yanda suke tsaye a kanta, asalinsu mutanen *Arlit* ne amma aiki ya kai mahaifinta qasashe da dama tun kafin aurenshi da kuma lokacin da yayi auren harda cikinta ma, wanda daga qarshe dai a *India* aka haifeta, bayan wasu shekaru sai mahaifin nata ya rasu, kasancewar a ma'aikatar ana kula da ma'aikatan da kuma iyalensu yasa basu bari mahaifiyar da yarinyar sunsha wahala ba, sunci
Showing 6001 words to 9000 words out of 186119 words