mishi duka a wajen tana fad'in "na fama d'in, aiga irinta nan, jiya mena fad'a maka akan maganar nan? amma baka saurareni ba kai mai taurin kai, saina shek'eka da hannuna, hamago kawai kana so mu rasaka gaba d'aya, ya kake so muyi to, me zamu gayama yaranka idan sun tambayemu."
Duk maganar da take tana zubar da hawaye ne, shi kuma hawayen nata yake kallo yanda suke zuba da k'arfi, hannu ya mik'a mata da nufin ta taho, buge hannun tayi da k'arfi tana fad'in "Bana so, bana sonka mugu kawai, saina kasheka da hannuna."
Sake bata hannun yayi ya marairaice kamar zai fashe da kuka yace "dan Allah baby, kizo mana ko naji sauqin ciwon dake damuna, nayi kuskure amma ki yafe min."
Ganin qwalla sun taru a idonshi ne yasa ta fad'a jikinshi da k'arfi har yana shirin fad'uwa tana tsananta kukanta tana fad'in "me yasa Faruk, me yasa zaka sa mana kanka a had'ari, kasan fa muna buqatarka musamman a wannan yanayin."
A hankali ya kai hannunshi kan cikinta ya shafa yana fad'in "ki gafarceni, ina hakane saboda farin cikinki da iyayenki, Khairat na kasa samun sukuni ganin halin da iyayenki ke ciki, dolena ne nayi saboda farin cikinku ya d'ore."
Goge hawayenta tayi tace "Amma ai ina farin cikin kasancewata da kai, kuma su Mamie ma suna farin cikin samun suruki kamarka, farin cikinmu zai gushene idan kasa kanka a had'ari, dan Allah karka sake irin haka, Faruk ba zan juri rasaka ba wallahi, nasan mutuwa zanyi nima idan na rasaka, dan Allah ka zauna tare dani."
Abbakar ne yace "to Roméo da Juliette ku wuce mu shiga ciki kowa ya shiga."
Dariya sukayi suka wuce ciki suka zazzauna, su Musa kam idone ya sake raina fata musamman abubuwan da suke gani a hannun Umar Faruk, lawyer ne ya matso kusan Umar Faruk ya sunkuya yace "kawo hujjojin na fara dubawa kafin alqali ya shigo."
A wulaqance ya kalleshi yace "barshi kawai, aida hannayena nima Allah ya horemin, idan alqalin ya shigo na bayar a bashi."
Yana gama fad'a kuma alqali ya shigo, tsaye suka mi'ke harya zauna, bayan maganganun da alqali yayi ne ya tambayi ko hujjojin sun bayyana gaban kotu kamar yanda Umar Faruk ya nemi alfarma aka mishi, Umar Faruk ne ya mik'e yayi daidai da mik'ewar lawyensu, hararanshi yayi ya rab'ashi ya bawa maga takarda duka hujjojin, saida alqali ya gama dubawa duka sannan ya nisa ya gama ruubuce rubutunshi kafin ya fara magana,
"Bayan hujjojin da aka gabatar a gaban kotu, kotu ta samu Sani Saley Odette Asma'u dasu Musa da laifi dumu dumu, sai dai kuma babu matashi Salim a kotun nan, dan haka kotu ta bada umarnin da a gaggauta gurfanar da Salim a gabanta, dan shima mai laifine, sannan kotu na buqatar a gabatar mata da docteur Shehu, dan shima da nashi laifin abisa cin hanci dan gurb'ata sunan wani."
Tsaye Umar Faruk ya mik'e dan girmamawa yace " ya mai girma mai shari'a, ina so kotu ta sani cewa wad'annan matasan samarin dama fil'azal masu laifi ne, laifinsu kuwa shine fyad'e wa mata, muna da shaida akan hakan idan kotu na buqatara gabatar dasu a gabanta zamu iya, bayan fyad'e kuma ni kaina sun so su kasheni badan komai ba sai dan su karb'i hujjojin dana gabatar, amma da ikon ubangiji kuma Allah bai basu sa'a ba, da wannan nake roqon kotu mai alfarma data yanke ma wad'annan hukunci mai tsaurin gaske wanda ba zai bayar da damar da za'a sake fito dasu ba daga gidan yari, dan a cikin hujjojin dana gabatarwa da kotu akwai bellynsu da akayi ba tare da sun cika wa'adin da aka dib'ar musu ba, abin takaicin ace anci zarafin yar babban mutum kuma shugaba, amma su kasa samun adalci, wannan ne yasa wata matashiyar budurwa da Musa yaci zarafinta yasa iyayenta suka barshi da Allah, dan sun san ba zasu samu adalci ba, na gode ya mai shari'a."
Tsawon lokaci alqali na nazartar lamarin kafin ya fara da "bayan hujjojin da aka gabatarwa da kotu tare da dogon nazari da tayi, kotu ta samu wannan mutane da laifi dumu dumu, dan haka wannan kotu mai alfarma ta yanke wa su Musa hukunci kamar haka, dukansu zasuyi shekara.....a gidan yari, haka ma Odette da Asma'u da Sani Saley da kuma yaro Salim an yanke musu hukuncin d'aurin wata uku uku a gidan yari tare da horo mai tsanani saboda magud'i a cikin siyasa da b'ata sunan wani, sannan kotu na umartar su Musa da subiya tara ta 150 0000cfa ga Umar Faruk saboda rayuwarshi da suka nema, kuma zasuyi hakan ne a cikin sati d'aya tak, sannan kotu ta wanke Mani Bukar cike da girmamawa da mutuntawa, sauran a gurfanar da likita da Salim a gaban kotu, da wannan zaman kotu ya qare."
(Ba lallai hukuncin dana yanke yama kowa dad'i ba, bana da ilimin shari'a, kuma wanda zai bani bayanin haka na rasa lambarshi a d'aya layin da aka min asararshi.)
Kallon tanti yayi yace "kiyi hak'uri tanti, banso haka ta faru ba kuma banji dad'in faruwar hakan ba, amma nasan zaki fahimceni." Yana fad'a yayi gaba abinshi Odette ta bishi da mugayen ashar, tanti kam bakinta ma ya mutu murus bata san me zata ce ba.
A wajen su Bello suka fara tuhumar Musa akan shiya lalata musu rayuwa, gashi yaja musu zasu qarar da rayuwar da basu da tabbacin zasu kaita a gidan yari, suna cike da wannan jimami da zulumi da kuka Umar Faruk dake rik'e da hannun Khairat ya tsaya gabansu yana murmushi, gemunshi ya shafo yana kallonsu yace "gashi a karo na biyu na sake antayaku gidan da kuka fito, amma wannan karan zanyi iya bakin qoqarina naga baku fito ba, kuma na muku alk'awarin ziyartarku kowane qarshen sati dan yin wa'azi wa yan gidan, aci gabza lafiya yan samari."
Wucewa sukayi Musa yayi saurin cewa "dama kai ka tona mana asiri a farko ma?"
Da wani shegen murmushi ya d'aga masa gira kawai suka wuce har saida suka shiga mota Khairat ta kalleshi tace "dama kai ka bayyana masu laifin a waccen lokacin?"
Shiru yayi sai Mamie dake baya ce tace "shine 'yata, haqiqa Umar Faruk ya mana taimakon da ba zamu iya biyanshi ba, sai dai kawai mu bishi da addu'a."
"Ita nafi buqata a wajenku Mama." ya fad'a yana kallon Mamie.
D'ora kanta tayi akan kafad'arshi ta rumgume hannunshi tana fad'in "ashe kaine ka taimakeni a waccen lokacin ma, na gode maka sosai baby, gaskiya kai na daban ne, kuma kasa naji kunya akan abinda na dinga yi maka a baya, da nasan kaine wanda ya taimakeni da banyi abinda nayi ba."
Shafa fuskarta yayi yace "karki damu, komai ai ya wuce, ba gashi kin zama tawa ba."
"Kuma nima ka zama nawa ba." ta fad'a tana qara qamqameshi.
6📓3📓
*A gurguje*
Saida Umar Faruk yayi jinya sosai kafin ya samu sauqi, a lokacin kuma cikin Zuby yana wata takwas, a lokacin kuma Allah ne yayi ikonsa, yayin da Zuby ke fuskantar rayuwar qansqanci a gidan mahaifinta da wulaqanci iri iri, kyara da zagi ga aiki babu tausayi haka suke sakata duk da tsohon cikinta, amma da zaran Umar Faruk ya shigo gidan da sunan yazo ganinta zasu dinga sakar mata fuska, amma kasancewar shi ba yaro bane yasa ya fahimci canji daga wajen Zuby a take ya fahimci halin da take ciki, amma abin takaici daya umarceta su koma gida sam sai tace gidan ubanta itama zata zauna, dole ya rabu da ita a haka yake d'awainiya da ita da abinda yake cikinta.
Khairat kuma yanzu lafiya ta samu, sam bata cika cin abinci ba sai kayan qwalam da maqulashe, Umar Faruk kuma kullum cikin kashe mata kud'i yake da faranta ranta, yayin da kullum suke maqale da juna bacci kad'ai ke rabasu, tayi nauyi sosai saboda cikinta na watan haihuwa ne, kunburin qafafu kuma shi yafi takurata sosai, sai nauyin jikin da tayi ko qwaqwaran motsi bata iya yi da kyau, hakan yasa har Papa yake tunanin ko za'a fitar da ita ne waje ta haihu a can, amma tace bata so.
Salim kam anyi nema amma shiru babu labarinshi, dama kuma tunda Umar Faruk ya qwamusheshi ya tsorata yasa suka bar garin shi da mahaifiyarshi, basu tsaya ko ina ba sai Maradi, anan suka fara wata sabuwar rayuwar a wani qauyen da ake kira *Madarunfa*.
**************
Wani bala'in ciwo ne ya addabi tanti a gidan yarin da suka rasa gane gabansa, da farko sun d'auka hawan jini ne amma sai suka fahimci abin ya wuce nan, gashi idan aka ce dare yayi to babu mai bacci saboda bala'in haukan da take tsurawa a wajen da hayaniya, a hankali kuma wani qurji ya fito mata a qafa, da sannu sannu saiya dinga girma har yakai matakin da yayi ruwa ya fashe ya fara wari, da qyar aka samu aka canza mata waje ita d'aya.
************
Koda Zuby ta wayi gari ta tashi bata jin dad'i sai rik'ewar da bayanta keyi, sai dai babu wanda zata fad'a ma ya kalleta ma bare ya tausaya mata, tana cikin yanayin nan Hajia babba ta gidan ta fito mata da kayan wanki, duk qoqarin Zuby nasan ta fahimceta amma ina saida ta fara wankin tana kuka, tana gamawa ta d'ora girkin rana, tana idawa ne ta fara qoqarin shara ,amma ina bata kai ko ina ba ta fad'i wajen tana neman taimako, da taimakonsu suka d'auketa suka kaita asibiti sannan suka kira Umar Faruk dan yasan halin da ake ciki.
A lokacin Umar Faruk na zaune bakin gado d'akin Khairat yana kallonta tana kai da kawowa sai sharar gumi take, qafafunta yake kallo da sukayi sumtum dasu kamar zasu fashe, wata qaramar riga ce gareta mai siraren hannuwa, tsaye yayi ya nufi wajenta ya rik'o hannunta yana fad'in "zo ki zauna dan Allah ki huta, yawon ya isa haka."
Fincike hannunta tayi za tayi magana kuma tayi saurin dafe cikinta da qugu tace "washhh, wayyo Allah na, dan Allah ka kira min Mamie, wallahi bana jin dad'i."
Qara rik'eta yayi yace " jikin ne, bara na kirasu To."
Zai fita kenan ta fizgo rigarshi cike da azaba ta durqushe qasa tana kuka tana fad'in "wayyo Allah, Faruk da ciwo wallahi, dan Allah ka min addu'a, wallahi ji nake kamar zan mutu, wayyo Allah na Allah ka taimakeni."
Durqushewa yayi shima yana rik'e da hannunta yana kallon idonta dake rufe sai hawaye ke fitowa, janyo kanta yayi ya manna a qirjinshi ya kara bakinshi a kunnenta yace "kiyi hak'uri Khairat d'ina, ki yawaita anbaton sunan Allah a bakinki, a yanzun kina cikin wani hali ne da babu abinda zan iya yi miki sai dai addu'a, amma mahaliccinki shine ke tare dake a wannan halin, da ace idan nace ciwon nan ya dawo kaina zai dawo, haqiqa da zanyi addu'a a yanzun nan dan na d'auke miki wannan shan wahalar, amma kiyi hak'uri kinji ina tare dake insha Allah."
Sake qamqameshi tayita fashe da kuka, rarrashinta yake yana tofa mata addu'a yana so ya tashi ya kira Mamie amma ina, suna haka ta sake kwamtsa wata qara tare da cakumo rigarshi, a gigice ya d'auketa ya sauko da ita falo inda Mamie suke zauna, nan dai suka nufi asibiti, a hanyar zuwa ne kuma kiran Zuby ya shigo, koda ya d'auka Hajia babba ce, koda ta fad'a mishi sake rud'ewa yayi musamman daya tuna cikin Zuby ba watan haihuwarshi bane yanzun.
D'an magori ya kai Khairat, Zuby kuma asibitin da aka kaita daban itama, koda sukaje aka yi shirin yiwa Khairat aiki dan fito da abinda ke cikinta, cikin nasara kuma akayi sa'ar fito da kyakyawar yarinya sak mahaifiyarta bata bar komai ba dan gane da ita, a lokacin kuma Umar Faruk na wajen Zuby tare da Mama, tasha wahala sosai kafin ta haiho abin cikinta, namiji ne amma sai yazo babu rai saboda yana wata takwas ne, suna cikin wannan jimamin suka tafi ganin Khairat da yarta, nan kuma farin ciki sukayi sosai yayin da asibiti ya cika da mutane ana ta murna.
A hankali Khairat ta bud'a idonta daga baccin da take na hutu, wani irin ciwo taji yana taso mata da ba zata iya misaltashi ba, da qyar ta hango Umar Faruk rik'e da yarinyar yana kallonta sai wasar baki yake, jin abin na qara taso mata yasa ta tara mishi alamar yazo, duk mutanen dake d'akin kallonta suke suna tambayar ya jikinta, bawa Mama yarinyar yayi ya qaraso wajenta, sunkuyawa yayi tare da rik'e hannun nata, bud'a baki tayi tana magana amma baya jin me take fad'a dan haka ya kara kunnanshi wajen bakinta.
Murmushi ta masa tace "baby, ni kad'ai nasan me nake ji, bansan ko zan rayu ba, amma dai saida na tabbatar na baka wata babyn kafin zan barka, ka kula min da ita sannan ka tabbatar ta samu tarbiya wacce ban samu ba a lokacin yarintata, nasan kamin kyautar yarinyar nan tun tana ciki, amma yanzu ta zama taka, dan bata da wani gata daya fika a duniyar nan, alfarma d'aya nake nema a wajenka?"
Kallonta yayi yace "alkairina bana son irin maganganun nan fa, me yasa zaki fad'i haka a irin wannan lokacin, yanzu fad'a min wace alfarma kike nema a wajena?"
Murmushi ta masa tace "ina so ka sawa yarinyar nan suna Islam, ina so ta zama mai tsantsar addini da fahimtar sunna."
Qara matse hannunta yayi yace "zanyi Khairat, dan Allah kiyi shiru kinji."
"Ina....." shiru tayi ta kasa fad'a ta rik'e cikinta, rik'e hannunta yayi yana fad'in "lafiya, me kike jine?"
Numfashi ta fara ja amma ta kasa mayar dashi, ga maganar da take so ta fad'a amma ta maqale mata, nan dai aka kira lokitoci aka koma da ita wani d'akin aka fara dubata, da qyar da sud'in goshi aka ceto Khairat, Umar Faruk yayi farin ciki sosai a lokacin kuma koda akayi sallah la'asar aka kauda yaron da Zuby ta haifa, Zuby tayi kuka sosai gashi yan uwanta ne kad'ai tare da ita babu mahaifiya babu wani babba sai Mama kawai.
6📓4📓
Dukansu sun koma gida, Zuby ta koma gidan mahaifinta Khairat kuma dasu Mama da sauran yan gidan sun tare a sabon gidansu, a ranar Khairat tayi kuka sosai tare da qara godewa Allah da kuma Umar Faruk, dan sak sashin daya mata irin sashinta ne na gida, musamman d'akinta da toilet d'inta, haka ma kayan daya zuba mata irin na d'akinta ne duka, lallai dukiya ta kwanta sosai sai dai ace alhamdulillah, babban abin farin ciki shine, islamiyya daya bud'e dake liqe a gidan, wacce malaman ciki suka kasance, shi, Ruk'ayya, Usman, Aliyu da kuma babban yaya Abbakar, kuma tuni suka fara koyarwa a ciki, mutane na zarya zuwa gidan kuma suna samun kulawa sosai, kasancewar su Uwani na wuni gidan kullum yasa Zuby ke farin ciki dan babu wannan aikin da muzgunawar mutan gidan, bayan kwana biyu sunje su fad'awa Mama Zuby ta haihu, amma sai hankalinsu ya tashi saboda ganin yanda Mama ta koma, a mutanen dake kusa da ita suka samu labarin cewa ko bacci ba tayi yanzu sai surutai da sambatu, sun tsorata sosai musammanma da tayi kamar bata sansu ba, haka suka dawo Zulfa'u dake da tsoro cewa tayi ba zata sake komawa ba sai an sallameta.
Ranar suna anyi bidiri da shagalin da babu wanda yayi tsammanin za ayi, dan Umar Faruk cewa yake walima kawai zaiyi, amma saiya shammaci Khairat ya mata duk abinda tayi burin yi, yarinya kuma taci sunan Islam, sai dai abin mamaki shine Umar Faruk yana kiranta da qaramar Khairat, kullum ya kira sunan sai Khairat ta kalleshi tayi murmushi, a haka aka gama sabga suka fara jego cikin kulawar Mammie da Mama dasu Mama Sa'a, ga kuma tururuwar da har yanzu mutane keyi a gidan, kuma a wannan lokacin ne Khairat ta fahimci kyautatawa nada anfani sosai, a haka suka yi Arba'in cike da qoshin lafiya, sai dai Khairat naci gaba da samun kulawa saboda ita aikine aka mata, kuma jikinta da sauqi sosai.
*BAYAN WATA BIYAR*
A lokacin Khairat ta tayar da rigima sai dai Umar Faruk ya dawo da Zuby, da farko bai amince ba, amma data saka mishi kuka tace zata fad'awa malam dole ya yarda, da kanshi yaje danya dawo da ita, amma saboda tasan ba sonta yake ba yasa tak'i amincewa, ganin irin rayuwar da take yasa yace to su koma can gidansu ta zauna, shima da qyar ta yarda ta bishi suka koma gidan ta fara rayuwar 'yanci.
Sai dai sauyawar rayuwa yasa Zuby yin biyayya wa Khairat tunda itace shugabar gidan, wani abun al'ajabi shine soyayyar Islam da Allah ya sawa Zuby a zuciyarta, kullum ta kalli yarinyar sai taga da yaronta na rayé da yanzu yana kamarta shima, hakan yasa Zuby rainon Islam kullum tana tare da yarinyar, tun tana aika yara su d'aukota mata ita har wani lokacin ta kanje da kanta ta d'aukota musamman in yara na school ko islamiyyar dare, yarinya ce mai shiga rai saboda yar qibartada kyawunta ga kuma gashinta da kullum Zuby ke kan mata gyaranshi duk da uwarta na mata.
Hakan nawa Khairat dad'i sosai danta samu damar zuwa islamiyya hankali kwance ba tare da damuwa ba, kuma kullum cikin kyautatawa Zuby take ko abinci ita ke fidda mata sutura kam ba'a magana, karatu kuma sosai ta mayar da hankalinta kanshi, a islamiyya Umar Faruk malamine, a gida kuma miji, wani lokacin yakan takurata sosai, hakan yasa har bata fata ranar shigarshi ajinsu yayi, tafi son Ruk'ayya kullum dake musu Bulugul Maram.
***********
Tunda al'amarin Mama ya girmama bayan ta fito malam ya duqufa wajen gane meye matsalarta, amma duk qoqarinshi bai gane komai ba, hakan yasa ya tuntub'i malaman da yake ganin sune manyanshi, amma a cewar wasu matsalarta kawai sai dai a tayata da addu'a, amma abun kam ba'a magana kamar wacce bakin uwa ya tab'a, haka itama Umar Faruk ya ware mata d'aki a gidan ta fara rayuwa amma kullum cikin matsalarta suke, qoqarin fita daga gida sambatu iri iri, babu sambatun da suka fi daga hankalinsu kamar idan tana fad'in "eh wallahi, nice nan da kaina nayi sanadiyar mutuwar mijina,
Showing 174001 words to 177000 words out of 186119 words
Duk maganar da take tana zubar da hawaye ne, shi kuma hawayen nata yake kallo yanda suke zuba da k'arfi, hannu ya mik'a mata da nufin ta taho, buge hannun tayi da k'arfi tana fad'in "Bana so, bana sonka mugu kawai, saina kasheka da hannuna."
Sake bata hannun yayi ya marairaice kamar zai fashe da kuka yace "dan Allah baby, kizo mana ko naji sauqin ciwon dake damuna, nayi kuskure amma ki yafe min."
Ganin qwalla sun taru a idonshi ne yasa ta fad'a jikinshi da k'arfi har yana shirin fad'uwa tana tsananta kukanta tana fad'in "me yasa Faruk, me yasa zaka sa mana kanka a had'ari, kasan fa muna buqatarka musamman a wannan yanayin."
A hankali ya kai hannunshi kan cikinta ya shafa yana fad'in "ki gafarceni, ina hakane saboda farin cikinki da iyayenki, Khairat na kasa samun sukuni ganin halin da iyayenki ke ciki, dolena ne nayi saboda farin cikinku ya d'ore."
Goge hawayenta tayi tace "Amma ai ina farin cikin kasancewata da kai, kuma su Mamie ma suna farin cikin samun suruki kamarka, farin cikinmu zai gushene idan kasa kanka a had'ari, dan Allah karka sake irin haka, Faruk ba zan juri rasaka ba wallahi, nasan mutuwa zanyi nima idan na rasaka, dan Allah ka zauna tare dani."
Abbakar ne yace "to Roméo da Juliette ku wuce mu shiga ciki kowa ya shiga."
Dariya sukayi suka wuce ciki suka zazzauna, su Musa kam idone ya sake raina fata musamman abubuwan da suke gani a hannun Umar Faruk, lawyer ne ya matso kusan Umar Faruk ya sunkuya yace "kawo hujjojin na fara dubawa kafin alqali ya shigo."
A wulaqance ya kalleshi yace "barshi kawai, aida hannayena nima Allah ya horemin, idan alqalin ya shigo na bayar a bashi."
Yana gama fad'a kuma alqali ya shigo, tsaye suka mi'ke harya zauna, bayan maganganun da alqali yayi ne ya tambayi ko hujjojin sun bayyana gaban kotu kamar yanda Umar Faruk ya nemi alfarma aka mishi, Umar Faruk ne ya mik'e yayi daidai da mik'ewar lawyensu, hararanshi yayi ya rab'ashi ya bawa maga takarda duka hujjojin, saida alqali ya gama dubawa duka sannan ya nisa ya gama ruubuce rubutunshi kafin ya fara magana,
"Bayan hujjojin da aka gabatar a gaban kotu, kotu ta samu Sani Saley Odette Asma'u dasu Musa da laifi dumu dumu, sai dai kuma babu matashi Salim a kotun nan, dan haka kotu ta bada umarnin da a gaggauta gurfanar da Salim a gabanta, dan shima mai laifine, sannan kotu na buqatar a gabatar mata da docteur Shehu, dan shima da nashi laifin abisa cin hanci dan gurb'ata sunan wani."
Tsaye Umar Faruk ya mik'e dan girmamawa yace " ya mai girma mai shari'a, ina so kotu ta sani cewa wad'annan matasan samarin dama fil'azal masu laifi ne, laifinsu kuwa shine fyad'e wa mata, muna da shaida akan hakan idan kotu na buqatara gabatar dasu a gabanta zamu iya, bayan fyad'e kuma ni kaina sun so su kasheni badan komai ba sai dan su karb'i hujjojin dana gabatar, amma da ikon ubangiji kuma Allah bai basu sa'a ba, da wannan nake roqon kotu mai alfarma data yanke ma wad'annan hukunci mai tsaurin gaske wanda ba zai bayar da damar da za'a sake fito dasu ba daga gidan yari, dan a cikin hujjojin dana gabatarwa da kotu akwai bellynsu da akayi ba tare da sun cika wa'adin da aka dib'ar musu ba, abin takaicin ace anci zarafin yar babban mutum kuma shugaba, amma su kasa samun adalci, wannan ne yasa wata matashiyar budurwa da Musa yaci zarafinta yasa iyayenta suka barshi da Allah, dan sun san ba zasu samu adalci ba, na gode ya mai shari'a."
Tsawon lokaci alqali na nazartar lamarin kafin ya fara da "bayan hujjojin da aka gabatarwa da kotu tare da dogon nazari da tayi, kotu ta samu wannan mutane da laifi dumu dumu, dan haka wannan kotu mai alfarma ta yanke wa su Musa hukunci kamar haka, dukansu zasuyi shekara.....a gidan yari, haka ma Odette da Asma'u da Sani Saley da kuma yaro Salim an yanke musu hukuncin d'aurin wata uku uku a gidan yari tare da horo mai tsanani saboda magud'i a cikin siyasa da b'ata sunan wani, sannan kotu na umartar su Musa da subiya tara ta 150 0000cfa ga Umar Faruk saboda rayuwarshi da suka nema, kuma zasuyi hakan ne a cikin sati d'aya tak, sannan kotu ta wanke Mani Bukar cike da girmamawa da mutuntawa, sauran a gurfanar da likita da Salim a gaban kotu, da wannan zaman kotu ya qare."
(Ba lallai hukuncin dana yanke yama kowa dad'i ba, bana da ilimin shari'a, kuma wanda zai bani bayanin haka na rasa lambarshi a d'aya layin da aka min asararshi.)
Kallon tanti yayi yace "kiyi hak'uri tanti, banso haka ta faru ba kuma banji dad'in faruwar hakan ba, amma nasan zaki fahimceni." Yana fad'a yayi gaba abinshi Odette ta bishi da mugayen ashar, tanti kam bakinta ma ya mutu murus bata san me zata ce ba.
A wajen su Bello suka fara tuhumar Musa akan shiya lalata musu rayuwa, gashi yaja musu zasu qarar da rayuwar da basu da tabbacin zasu kaita a gidan yari, suna cike da wannan jimami da zulumi da kuka Umar Faruk dake rik'e da hannun Khairat ya tsaya gabansu yana murmushi, gemunshi ya shafo yana kallonsu yace "gashi a karo na biyu na sake antayaku gidan da kuka fito, amma wannan karan zanyi iya bakin qoqarina naga baku fito ba, kuma na muku alk'awarin ziyartarku kowane qarshen sati dan yin wa'azi wa yan gidan, aci gabza lafiya yan samari."
Wucewa sukayi Musa yayi saurin cewa "dama kai ka tona mana asiri a farko ma?"
Da wani shegen murmushi ya d'aga masa gira kawai suka wuce har saida suka shiga mota Khairat ta kalleshi tace "dama kai ka bayyana masu laifin a waccen lokacin?"
Shiru yayi sai Mamie dake baya ce tace "shine 'yata, haqiqa Umar Faruk ya mana taimakon da ba zamu iya biyanshi ba, sai dai kawai mu bishi da addu'a."
"Ita nafi buqata a wajenku Mama." ya fad'a yana kallon Mamie.
D'ora kanta tayi akan kafad'arshi ta rumgume hannunshi tana fad'in "ashe kaine ka taimakeni a waccen lokacin ma, na gode maka sosai baby, gaskiya kai na daban ne, kuma kasa naji kunya akan abinda na dinga yi maka a baya, da nasan kaine wanda ya taimakeni da banyi abinda nayi ba."
Shafa fuskarta yayi yace "karki damu, komai ai ya wuce, ba gashi kin zama tawa ba."
"Kuma nima ka zama nawa ba." ta fad'a tana qara qamqameshi.
6📓3📓
*A gurguje*
Saida Umar Faruk yayi jinya sosai kafin ya samu sauqi, a lokacin kuma cikin Zuby yana wata takwas, a lokacin kuma Allah ne yayi ikonsa, yayin da Zuby ke fuskantar rayuwar qansqanci a gidan mahaifinta da wulaqanci iri iri, kyara da zagi ga aiki babu tausayi haka suke sakata duk da tsohon cikinta, amma da zaran Umar Faruk ya shigo gidan da sunan yazo ganinta zasu dinga sakar mata fuska, amma kasancewar shi ba yaro bane yasa ya fahimci canji daga wajen Zuby a take ya fahimci halin da take ciki, amma abin takaici daya umarceta su koma gida sam sai tace gidan ubanta itama zata zauna, dole ya rabu da ita a haka yake d'awainiya da ita da abinda yake cikinta.
Khairat kuma yanzu lafiya ta samu, sam bata cika cin abinci ba sai kayan qwalam da maqulashe, Umar Faruk kuma kullum cikin kashe mata kud'i yake da faranta ranta, yayin da kullum suke maqale da juna bacci kad'ai ke rabasu, tayi nauyi sosai saboda cikinta na watan haihuwa ne, kunburin qafafu kuma shi yafi takurata sosai, sai nauyin jikin da tayi ko qwaqwaran motsi bata iya yi da kyau, hakan yasa har Papa yake tunanin ko za'a fitar da ita ne waje ta haihu a can, amma tace bata so.
Salim kam anyi nema amma shiru babu labarinshi, dama kuma tunda Umar Faruk ya qwamusheshi ya tsorata yasa suka bar garin shi da mahaifiyarshi, basu tsaya ko ina ba sai Maradi, anan suka fara wata sabuwar rayuwar a wani qauyen da ake kira *Madarunfa*.
**************
Wani bala'in ciwo ne ya addabi tanti a gidan yarin da suka rasa gane gabansa, da farko sun d'auka hawan jini ne amma sai suka fahimci abin ya wuce nan, gashi idan aka ce dare yayi to babu mai bacci saboda bala'in haukan da take tsurawa a wajen da hayaniya, a hankali kuma wani qurji ya fito mata a qafa, da sannu sannu saiya dinga girma har yakai matakin da yayi ruwa ya fashe ya fara wari, da qyar aka samu aka canza mata waje ita d'aya.
************
Koda Zuby ta wayi gari ta tashi bata jin dad'i sai rik'ewar da bayanta keyi, sai dai babu wanda zata fad'a ma ya kalleta ma bare ya tausaya mata, tana cikin yanayin nan Hajia babba ta gidan ta fito mata da kayan wanki, duk qoqarin Zuby nasan ta fahimceta amma ina saida ta fara wankin tana kuka, tana gamawa ta d'ora girkin rana, tana idawa ne ta fara qoqarin shara ,amma ina bata kai ko ina ba ta fad'i wajen tana neman taimako, da taimakonsu suka d'auketa suka kaita asibiti sannan suka kira Umar Faruk dan yasan halin da ake ciki.
A lokacin Umar Faruk na zaune bakin gado d'akin Khairat yana kallonta tana kai da kawowa sai sharar gumi take, qafafunta yake kallo da sukayi sumtum dasu kamar zasu fashe, wata qaramar riga ce gareta mai siraren hannuwa, tsaye yayi ya nufi wajenta ya rik'o hannunta yana fad'in "zo ki zauna dan Allah ki huta, yawon ya isa haka."
Fincike hannunta tayi za tayi magana kuma tayi saurin dafe cikinta da qugu tace "washhh, wayyo Allah na, dan Allah ka kira min Mamie, wallahi bana jin dad'i."
Qara rik'eta yayi yace " jikin ne, bara na kirasu To."
Zai fita kenan ta fizgo rigarshi cike da azaba ta durqushe qasa tana kuka tana fad'in "wayyo Allah, Faruk da ciwo wallahi, dan Allah ka min addu'a, wallahi ji nake kamar zan mutu, wayyo Allah na Allah ka taimakeni."
Durqushewa yayi shima yana rik'e da hannunta yana kallon idonta dake rufe sai hawaye ke fitowa, janyo kanta yayi ya manna a qirjinshi ya kara bakinshi a kunnenta yace "kiyi hak'uri Khairat d'ina, ki yawaita anbaton sunan Allah a bakinki, a yanzun kina cikin wani hali ne da babu abinda zan iya yi miki sai dai addu'a, amma mahaliccinki shine ke tare dake a wannan halin, da ace idan nace ciwon nan ya dawo kaina zai dawo, haqiqa da zanyi addu'a a yanzun nan dan na d'auke miki wannan shan wahalar, amma kiyi hak'uri kinji ina tare dake insha Allah."
Sake qamqameshi tayita fashe da kuka, rarrashinta yake yana tofa mata addu'a yana so ya tashi ya kira Mamie amma ina, suna haka ta sake kwamtsa wata qara tare da cakumo rigarshi, a gigice ya d'auketa ya sauko da ita falo inda Mamie suke zauna, nan dai suka nufi asibiti, a hanyar zuwa ne kuma kiran Zuby ya shigo, koda ya d'auka Hajia babba ce, koda ta fad'a mishi sake rud'ewa yayi musamman daya tuna cikin Zuby ba watan haihuwarshi bane yanzun.
D'an magori ya kai Khairat, Zuby kuma asibitin da aka kaita daban itama, koda sukaje aka yi shirin yiwa Khairat aiki dan fito da abinda ke cikinta, cikin nasara kuma akayi sa'ar fito da kyakyawar yarinya sak mahaifiyarta bata bar komai ba dan gane da ita, a lokacin kuma Umar Faruk na wajen Zuby tare da Mama, tasha wahala sosai kafin ta haiho abin cikinta, namiji ne amma sai yazo babu rai saboda yana wata takwas ne, suna cikin wannan jimamin suka tafi ganin Khairat da yarta, nan kuma farin ciki sukayi sosai yayin da asibiti ya cika da mutane ana ta murna.
A hankali Khairat ta bud'a idonta daga baccin da take na hutu, wani irin ciwo taji yana taso mata da ba zata iya misaltashi ba, da qyar ta hango Umar Faruk rik'e da yarinyar yana kallonta sai wasar baki yake, jin abin na qara taso mata yasa ta tara mishi alamar yazo, duk mutanen dake d'akin kallonta suke suna tambayar ya jikinta, bawa Mama yarinyar yayi ya qaraso wajenta, sunkuyawa yayi tare da rik'e hannun nata, bud'a baki tayi tana magana amma baya jin me take fad'a dan haka ya kara kunnanshi wajen bakinta.
Murmushi ta masa tace "baby, ni kad'ai nasan me nake ji, bansan ko zan rayu ba, amma dai saida na tabbatar na baka wata babyn kafin zan barka, ka kula min da ita sannan ka tabbatar ta samu tarbiya wacce ban samu ba a lokacin yarintata, nasan kamin kyautar yarinyar nan tun tana ciki, amma yanzu ta zama taka, dan bata da wani gata daya fika a duniyar nan, alfarma d'aya nake nema a wajenka?"
Kallonta yayi yace "alkairina bana son irin maganganun nan fa, me yasa zaki fad'i haka a irin wannan lokacin, yanzu fad'a min wace alfarma kike nema a wajena?"
Murmushi ta masa tace "ina so ka sawa yarinyar nan suna Islam, ina so ta zama mai tsantsar addini da fahimtar sunna."
Qara matse hannunta yayi yace "zanyi Khairat, dan Allah kiyi shiru kinji."
"Ina....." shiru tayi ta kasa fad'a ta rik'e cikinta, rik'e hannunta yayi yana fad'in "lafiya, me kike jine?"
Numfashi ta fara ja amma ta kasa mayar dashi, ga maganar da take so ta fad'a amma ta maqale mata, nan dai aka kira lokitoci aka koma da ita wani d'akin aka fara dubata, da qyar da sud'in goshi aka ceto Khairat, Umar Faruk yayi farin ciki sosai a lokacin kuma koda akayi sallah la'asar aka kauda yaron da Zuby ta haifa, Zuby tayi kuka sosai gashi yan uwanta ne kad'ai tare da ita babu mahaifiya babu wani babba sai Mama kawai.
6📓4📓
Dukansu sun koma gida, Zuby ta koma gidan mahaifinta Khairat kuma dasu Mama da sauran yan gidan sun tare a sabon gidansu, a ranar Khairat tayi kuka sosai tare da qara godewa Allah da kuma Umar Faruk, dan sak sashin daya mata irin sashinta ne na gida, musamman d'akinta da toilet d'inta, haka ma kayan daya zuba mata irin na d'akinta ne duka, lallai dukiya ta kwanta sosai sai dai ace alhamdulillah, babban abin farin ciki shine, islamiyya daya bud'e dake liqe a gidan, wacce malaman ciki suka kasance, shi, Ruk'ayya, Usman, Aliyu da kuma babban yaya Abbakar, kuma tuni suka fara koyarwa a ciki, mutane na zarya zuwa gidan kuma suna samun kulawa sosai, kasancewar su Uwani na wuni gidan kullum yasa Zuby ke farin ciki dan babu wannan aikin da muzgunawar mutan gidan, bayan kwana biyu sunje su fad'awa Mama Zuby ta haihu, amma sai hankalinsu ya tashi saboda ganin yanda Mama ta koma, a mutanen dake kusa da ita suka samu labarin cewa ko bacci ba tayi yanzu sai surutai da sambatu, sun tsorata sosai musammanma da tayi kamar bata sansu ba, haka suka dawo Zulfa'u dake da tsoro cewa tayi ba zata sake komawa ba sai an sallameta.
Ranar suna anyi bidiri da shagalin da babu wanda yayi tsammanin za ayi, dan Umar Faruk cewa yake walima kawai zaiyi, amma saiya shammaci Khairat ya mata duk abinda tayi burin yi, yarinya kuma taci sunan Islam, sai dai abin mamaki shine Umar Faruk yana kiranta da qaramar Khairat, kullum ya kira sunan sai Khairat ta kalleshi tayi murmushi, a haka aka gama sabga suka fara jego cikin kulawar Mammie da Mama dasu Mama Sa'a, ga kuma tururuwar da har yanzu mutane keyi a gidan, kuma a wannan lokacin ne Khairat ta fahimci kyautatawa nada anfani sosai, a haka suka yi Arba'in cike da qoshin lafiya, sai dai Khairat naci gaba da samun kulawa saboda ita aikine aka mata, kuma jikinta da sauqi sosai.
*BAYAN WATA BIYAR*
A lokacin Khairat ta tayar da rigima sai dai Umar Faruk ya dawo da Zuby, da farko bai amince ba, amma data saka mishi kuka tace zata fad'awa malam dole ya yarda, da kanshi yaje danya dawo da ita, amma saboda tasan ba sonta yake ba yasa tak'i amincewa, ganin irin rayuwar da take yasa yace to su koma can gidansu ta zauna, shima da qyar ta yarda ta bishi suka koma gidan ta fara rayuwar 'yanci.
Sai dai sauyawar rayuwa yasa Zuby yin biyayya wa Khairat tunda itace shugabar gidan, wani abun al'ajabi shine soyayyar Islam da Allah ya sawa Zuby a zuciyarta, kullum ta kalli yarinyar sai taga da yaronta na rayé da yanzu yana kamarta shima, hakan yasa Zuby rainon Islam kullum tana tare da yarinyar, tun tana aika yara su d'aukota mata ita har wani lokacin ta kanje da kanta ta d'aukota musamman in yara na school ko islamiyyar dare, yarinya ce mai shiga rai saboda yar qibartada kyawunta ga kuma gashinta da kullum Zuby ke kan mata gyaranshi duk da uwarta na mata.
Hakan nawa Khairat dad'i sosai danta samu damar zuwa islamiyya hankali kwance ba tare da damuwa ba, kuma kullum cikin kyautatawa Zuby take ko abinci ita ke fidda mata sutura kam ba'a magana, karatu kuma sosai ta mayar da hankalinta kanshi, a islamiyya Umar Faruk malamine, a gida kuma miji, wani lokacin yakan takurata sosai, hakan yasa har bata fata ranar shigarshi ajinsu yayi, tafi son Ruk'ayya kullum dake musu Bulugul Maram.
***********
Tunda al'amarin Mama ya girmama bayan ta fito malam ya duqufa wajen gane meye matsalarta, amma duk qoqarinshi bai gane komai ba, hakan yasa ya tuntub'i malaman da yake ganin sune manyanshi, amma a cewar wasu matsalarta kawai sai dai a tayata da addu'a, amma abun kam ba'a magana kamar wacce bakin uwa ya tab'a, haka itama Umar Faruk ya ware mata d'aki a gidan ta fara rayuwa amma kullum cikin matsalarta suke, qoqarin fita daga gida sambatu iri iri, babu sambatun da suka fi daga hankalinsu kamar idan tana fad'in "eh wallahi, nice nan da kaina nayi sanadiyar mutuwar mijina,
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59 Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63