Cikin kunnenta ya rad'a mata " ai Umar Faruk mallakar Khairat ne, sai yanda taso za tayi dashi, kinga kuwa ai dani da hannayena na karb'ar kyauta daga gareki duk naki ne."
Dariya ta sake yi tace "na ganoka fa, kana nufin dani da abinda na mallaka duka naka ne, shi yasa ma ka karb'a."
Kumatunta yaja yace "mai basira kenan."
Da qyar suka rabu ya tafi wajen aiki, ita kuma ta koma ta kwanta bacci danya tabbatar mata ba zai dawo da rana ba, aikinshi yake hankali kwance cike da farin ciki da nutsuwa, bayan sallah azahar saiga wani babban kira a wayarshi, ya zai gani inba Papa ba, da girmamawa ya d'auka suka gaisa, nan Papa yace yana son ganinshi inba damuwa, nan ya aje komai dake gabanshi ya tafi kiran mai gida kuma suruki.
*Bayan yaje gidan* Papa yake sanar dashi wani compagnie a qasar *Las vegas* dake *America* suna neman zakakurin matashin mai aikin zane irinshi, dan haka in yana son aiki toya shirya zuwa qarar Las vegas domin tattaunawa dasu, kuma tattaunawar ba zata wuce gobe ba, dan haka idan ya amince compagnie ya d'auki nauyin tafiyarshi da dawowarshi, wannan shine sharad'in farko, Umar Faruk ya d'auka kawai alfarma ce Papa ya mishi kasancewarshi surukinshi, hakan yasa ya amince kuma ya kama hanyar gida cike da zumud'in fad'awa Khairat abinda ake ciki, sai dai baisan ita tayi silar samun wannan aikin nashi ba.
Su Mama ya samu a tsakar gidan dukansu suna d'an tab'a hira sama sama, saida ya zauna ya fad'a musu komai dake faruwa, mahaifiyarshi dai kam tayi farin ciki, amma banda sauran iyayen nasu da suke ganin ci gabanshi na qara kusantoshi, addu'a Mama ta mishi kafin ya tashi ya nufi d'akin Khairat yana sake kallon k'ofar Zuby dake rufe, yana tunani a ranshi har yanzu bata dawo ba kenan, qwafa yayi a cikin ranshi kafi ya shiga d'akin da sallama, littafi ne a hannunta tana karatu tana ganinshi ta taso ta tarbeshi, "albishirinki?"
"Goro." ta fad'a a harshen zarma kamar yanda shima yayi.
A harshen zarma dai fad'a mata komai, rashin mamaki da tayi yasa yayi zargin wani abu, kallonta yayi yace "alkairina, kodai aikinki ne."
Zaunar dashi tayi tana kallonshi tace "kayi hak'uri Umar Faruk, ba lallai ina so na canza qaddarar ubangiji a kanka bane, amma ina so naga kaji dad'i kaima, ba dole sai kayi aiki da compagnien ba harna tsawon lokaci, amma idan ka samu wani abu mai tsoka kaima zaka iya tsayawa da qafafunka, wannan shine burina a kanka, ina so naga ka tsaya da qafarka saboda kana basira da ilimin daka wuce ka zauna qarqashin wani, amma ka yafe min idan nayi ba daidai ba."
"Shawara mai kyau, hakan kuma zai bani damar kin rattab'a hannu akan aiki dasu na dindindin."
"Hakane." ta fad'a tana murmushi.
Rumgumeta yayi yace "na gode Khairat." a zuciyarshi kuma cewa yayi " da farko na d'auka *Jihadi* nayi na aureki , amma yanzu komai na fitowa fili cewar, kece silar arzik'ina a duniya, kuma kece farin ciki da kwanciyar hankalina."
D'orawa da "ki shirya, dan tare zamu tafi dake ki nuna min gari."
Cikin dariya ta kalleshi tace "shirme."
"Allah kuwa nake fad'a miki." ya fad'a yana dariya.
_Wannan karan naga uban daya isa ya hana tafiyar nan._
*****************
Koda Zuby taje gida basu tsaya komai ba suka wuce wajen malam, nan Zuby ta fad'a mishi abinda ke faruwa, tambayarta yayi me take so a mata? cewa tayi asa Umar Faruk ya tsaneta harya saketa ma, nan yace msu "aikinku mai sauki ne, kuma zai yiwu, amma harsai kun samo wani abu daya zama na ita Khairat d'in ne, bi ma'ana abinda take sawa a jikinta koma menene, dashi za'a had'a laqanin da zai tsaneta, zaku iya?"
Mama ce ta karb'e da "zamu iya mana malam, aiba wuyane da aikin ba."
"A shikenan, kuyi qoqari ku kawo cikin kwana biyu ko uku, dan a gaggauta yin komai."
"To malam, kar kaji komai za'a kawo."
Da haka suka baro wajen malam Zuby tayi gida Mama ma tayi hanyar gida, da tunanin yanda za ayi ta samu abun Khairat taje gida, ganin motar Umar Faruk ba qaramin tsinkewa 'yan cikinta sukayi ba, da qyar ta shiga gidan tana d'an sunnewa, ganin baya tsakar gidan yasa ta fara gaggawar bud'a d'akinta ba tare data kula da mutanen tsakar gidan ba, suma babu wanda ya mata magana dan sunga abinta iskanci ne da raini, tana shiga tayi saurin cire kayanta tayi zaune gabanta na fad'uwa tana tunanin hukuncin da zai mata.
Ana sallah la'asar ya fito, koda d'akin bud'e bai kula da tsiyarta ba yayi alwala ya wuce masallaci, bai kuma dawo ba sai bayan sallah isha'i, lokacin Khairat ta sake daddaga abinci mai rai da lafiya, saida ta zubo min a babban kula tace na kawawa _Team Khairat_ amma na taho akan hanya nayi tuntube tuwon ya zube, daga nan na zaune na qarasa cinye wanda yayi saura tare da kazar dake samaπ kunsan dai akwai aminci tsakaninmu da kaza, yau ma kamar jiya sunci sunsha kuma sunyi farin ciki tare da raya darensu, yayin da Zuby haushi kamar zai kasheta, dan da yaje mata saida safe bai mata wata maganar kirki ba, hakan kuma ya qara b'ata mata rai, amma dai kuma ba zata iya bayar da hak'uri ba a tunaninta, shi kuma a nashi b'angaren yana ganin saita bashi hak'uri ta kuma gane kurenta sannan.
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Bismmilahir-rahman-rahim_
4β£7β£
Kamar kullum gaba d'aya sun taru a d'akin Baba inda yake musu nasiha akan kyautatawa, saida aka gama kamar kullum ana shirin tashi Umar Faruk yayi gyaran murya yace "am, ina da magana, dan Allah ku zauna."
Gyara zama kowa yayi Baba yace "muna jinka Umar Faruk."
"Dama akan maganar aikin dana samu ne, acan compagnie suna buk'atar naje gobe domin tattaunawa dani, kamar yanda na fad'a muku wannan aikin Khairat ce silar samar minshi, kuma ni babu inda na tab'a zuwa na qasar waje, kasancewarta wacce tasan wajen yasa nake tunanin tafiya tare da ita, amma shawara ce bansan ku me kuka gani ba?"
Baba ne yace "Umar Faruk, kaima fa yanzu magidanci ne, ba komai bane zaka nemi shawararmu akai, indai har kana ganin hakan ba matsala kuma shine daidai, ai saimu muku fatan alkairi."
"Na gode Baba." ya fad'a kafin ya d'ora da "dama wannan ce maganar, na gode."
Tashi kowa yayi zai fita Zuby kam ta kasa tashi, ganin Umar Faruk zai fita yasa Zuby kallon Baba tace "ina da magana nima."
Juyowa Umar Faruk yayi ya kalleta, kallonshi tayi itama tace "ka dawo ka zauna."
Zaunawa yayi Mama ma zata fice Zuby tace "Mama kema ki zauna."
Saida kowa ya fita Baba ya kalli Zuby yace "ina jinki Zubeida, ina fatan dai ba wata matsala bace?"
Tana kallon Umar Faruk tace "gaskiya ni ba'a min adalci ba, na fahimci yana son yin tafiya da ita, to ba komai su tafi, amma kafin su tafi ya fad'a min Γ wane matsayi nake, dan wallahi ba zan iya zaman gadi ba a gidan nan haka kawai."
Da mamaki duka suke kallonta kafin Umar Faruk yace "Zubeida wane irin rashin adalci nake miki?"
Shiru tayi harya sake maimaitawa da "Zubeida fad'a min, mena miki na rashin adalci."
Cikin turo baki tace "ai duk mai ido yasan baka adalci a tsakaninmu, domin kuwa ko ranar aikina ne idan ka shiga d'akinta saika jima kafin ka fito, kuma inhar ka shiga d'akinta to sai dai ka fito da fara'a da murmushi a fuskarka, sab'anin d'akina idan ka shigo sai kayi duk abinda za kayi ka b'ata min ran sannan kaima ka fito cikin b'acin rai, bugu da qari ita cikin kayan abincin su Mama take diba tana aiki dasu, ni kuma ka siyo min wanda basu kai basu kawo ba, dad'in dad'awa kuma duk da nasan ita yar mai kud'i ce, amma na tabbata daga cikin suturun da take sakawa akwai wanda kai ka matasu na lefenta, yah Umar idan nace zan dinga zayyano maka rashin adalcin da kake ba zai k'idayu ba."
Murmushin takaici yayi na gefen labb'a, dan yaso a kamashi da laifi danya b'ata hak'uri, amma kash ta kasa bayar da hujjar da zai d'auki laifin a kanshi, saida ya qara gyara zamanshi yace "da kin fad'i wani abu daban ba wannan ba, amma tunda haka ki kace bara na fad'a miki abinda yayi daidai da abinda kika fad'a."
"Da farko kince idan na shiga d'akin Khairat nakan jima ban fito ba kuma ina fitowa da fara'a, ba zan iya ce miki komai ba, amma ina baki shawara ki samu wata qawarki da kika yarda da ita ki tambayeta me yake janyo hakan, na tabbata zata fad'a miki gaskiya, na biyu kuma maganar abinci, to kiji in fad'a miki, wannan kayan abincin da kika gani wallahi ko Baba baya da iko akansu kamar yanda Khairat take da iko akansu, kinsan me yasa? saboda itace ta siyesu, kuma bata tab'a kulasu ba sai ranar dake kika kawo shawarar kowace ta dinga girki da kanta, Zubeida idan akwai wanda akawa rashin adalci to Khairat ce, domin kuwa a lokacin dana siyo miki kayan abincin nan ita ban siyo mata ba, sannan na d'auki kud'i na qara muki dasu, duk da haka sisin kwabo ban bata ba dan nasan ba zata karb'a ba, tunda ta shigo gidan nan zan iya fad'a miki adadin da taci abincin gidan nan, kinga kenan ita akawa rashin adalci, na uku kuma kince sutura, to kijini da kyau Zubeida, ni banwa Khairat lefe ba kece nayiwa lefe, tunda nake da ita zani d'aya na atamfa bai shiga tsakani na da ita ba, kin ganni a matsayin mijin Khairat? wallahi har yanzu idan banda wurin kwanciya da ruwan gidan nan, banga wani abu da Khairat ke anfani dashi ba wanda zan iya cewa nawa ne, sannan atamfar da Khairat ke sawa a jikinta ma kad'ai tafi k'arfin arzik'ina, bare kuma kudin d'inkinta har azo ga shadda ko less, maganar sarka da d'an kunnai ma mu barta, har yanzu babu tsaiyar dana tsinanawa baiwar Allah nan a matsayina na mijinta, hasali ma nine ke qaruwa da ita tako ina, a yanzun burina bai wuce na samu hanyar da zan saka mata da alkairin data min ba, dan duk wanda zai bawa ahalinka abinda zasu ci ya kuma dinga kyautata musu, to tabbas shi masoyinka ne na gaskiya, musamman ita da bata damu da dukiyarta ba, ita dai burinta kawai ta kyautatawa wanda yake tare da ita, ba tayi dan gobe ta fad'a tayi maka, sannan idan tayi ba'a karb'a ba tana jin zafi, domin kuwa ita alheri a cikin jininta yake kamar yanda ma'anar sunanta yake, dan haka ina baki shawara Zubeida, ki cire komai a ranki ki rumgumi yer uwarki, wallahi babu komai a zuciyarta a game dake, ko sau d'aya bata tab'a nuna min kishinta a kanki ba, ina fatan za kiyi anfani da shawarata, kuma ki yafe min idan na fad'i abinda ya b'ata miki rai."
Mik'ewa yayi da fad'in "saida safenku." danshi baiga abinda zai sashi b'ata lokacinshi ba akan banzan shirmen Zuby.
Mama da Baba ma sun gamsu da abinda ya fad'a dan haka sukayi shiru harta tashi ta koma d'akinta, yana shiga d'aki Khairat ya sameta zauna tana tunani akan karatun da Baba ya musu, dan a cikin kyautatawar daya musu magana akai, akwai kyautatawa iyaye, ita kuma tana tunanin yanda ta zauna da nata iyayen, ji tayi tana so ta basu hak'uri akan yanda ta mu'mulancesu a baya, zaune yayi kusanta ya janyota jikinshi yana fad'in "yadai, meya faru."
"Ba komai." ta fad'a tana shafa jikinshi.
"Kin tabbata?"
"Um."
Dago kanta yayi ya kalli fuskarta, turo baki yayi gaba kamar yaro ya langab'e kai yace " ban yarda ba gaskiya, akwai wanda ya tab'a min baby, fad'a min meya faru.?
Qara langab'ewa tayi tace " ba komai fa."
"To indai hakane kiyi dariya na gani."
D'an murmushin yaqe tayi tace "nifa bacci nake ji."
Tana fad'a ta kwanta tare da jan zanin rufa, Umar Faruk a ranshi cewa yayi "baiwar Allah, ko tana tunanin abinda ya faru ne wanda ya tsayar dani? koma dai meye dole nima na saki farin ciki kamar yanda kema kike sakani farin ciki, wannan itace damar da nake da wajen saka miki da alkairi."
Hayeta yayi ya fara mata cakulkuli yana fad'in "ba zan iya komai ba sai naga dariyarki."
Ai kuwa dariya ta fara qyalqyalawa daga haka kuma suka lula duniyarsu ta maji dad'i......
**************
Tunda asuba koda Khairat tayi sallah ta fara shirya musu kayansu tare da shirya kanta , Umar Faruk kuma saida ya shiga d'akunan iyayensu suka gaisa tare da d'akin Zuby, haka yayi sallama har sau uku amma ko qala ba tace ba, sannan ya qara da "kin tashi lafiya?"
Ganin Khairat ta taho kuma ko Khairat ba zaiso ta rainashi ba yasa ya wurga mata wata harara, shiru tayi tana sauke numfashi ,wucewa yayi suka bi bayanshi amma abin mamaki, da hanzari Zuby ta zagaya ta zauna a gidan gaba, kallonta yayi zaiyi magana kawai yaga Khairat ta bud'a mazauninshi ta zauna, saida ta daidaita zamanta sannan ta fizgo makullin hannunshi fuskarta a had'e itama ba alamar wasa, jin tayiwa motar key yasa ya bud'a gidan baya ya zauna ya rufe yana fad'in "Allah gani gareka, ashe dama haka mata biyu suke, da zaran sun had'u sai an caza maka qwaqwalwa."
Gyara madubi Khairat tayi ta kalleshi tace "baby ka shirya?"
Gintse dariyarshi yayi ya sunne kai qasa, Zuby kuma qoqarin bud'ewa ta farayi danta fita, Khairat na ganin haka ta fizgi motar da iya k'arfinta a zuciyarta tana fad'in "uban daya kawoki gidan gaba."
Titi suka hau Umar Faruk na kallon kowace daga baya, Khairat na tuk'i hankali kwance Zuby kuma tayi tsaki yafi dubu , amma jin sun qyaleta yasa tace "aikin banza, barewa ai ba tayi gudu ba d'anta yayi rarrafe, an gada wajen uba dole a nuna hali."
Ba tare data kalleta ba tace "na fad'a miki ki daina saka iyaye a maganar data shafemu , bai zama lallai abinda zai fito a bakina ya miki dad'i ba, amma kika b'ata min rai yanzun nan saina had'a motar nan da bango."
Sai lokacin ta kalleta duk da tana tuki tace "bana tsoron mutuwa, dan Mama tace ni yar aljanna ce, bugu da qari ina tare da babyna, zanyi farin ciki mu mutu tare, idan kin shirya biyarmu to."
"To an fad'a miki ina tsoron mutuwa ne? ai gwara na mutu ma da zama dake a matsayin kishiya wallahi, inkin fasa hadamu da bango bakya tsoron Allah daya halicceki."
"Kin shirya mutuwa kenan?" cewar Khairat.
"Shege ka fasa, d'an halak sai yanka."
Da sauri Khairat ta kalleta tace "a'a malama, ki daina sako mana wannan kalmar anan, ni dai 'yar halak ce."
"Kenan nice shegiyar?"
"To ai ba kama garesu ba, kuma ba'a rubuta a goshinki ba bare na karanta, kinga kenan ba zan iya sani ba."
"In haka kike tunani, toki d'auka ni yar babanki ce."
Umar Faruk ne yayi saurin cewa "ya isa haka to, karna sake jin bakinku, inba haka ba rai zai b'ace."
Khairat kuma gani tayi aita kaita qasa, dan haka tace "ina aiki na masu hankali, amma idan haukana ya motsa to akwai matsala, ki kiyaye bakinki kafin kiji abinda zai iya tarwatsa miki lissafi."
Tsaki Zuby tayi ta rumgume hannaye har suka isa ecole d'insu, saida ta juya ta kalli Umar Faruk sannan ta kalli Khairat tace "na gode Allah, ni ba 'yar d'an giya bace."
Tana fad'a ta fita ta bar motar, Khairat binta tayi da kallo lokaci d'aya hawaye suka soma zubo mata, fitowa Umar Faruk yayi ya bud'e inda take zaune, saida ya kama hannunta ya fito da ita sannan ta zagaya ta zauna inda Zuby ta tashi, saida suka fara tafiya jin tana shashek'ar kuka yasa ya fara tausarta da kalamai masu sanyi, ba tayi shiru ba har saida taga yayi parking a k'ofar gidansu sannan, zata fita ya rik'e hannunta suka kalli juna, d'aure fuska yayi yace,
"Ki maye fara'a a gurbin d'aure fuskar nan."
Cikin muryar kuka tace "amma fa kaji abinda yarinyar nan ta fad'a min."
"Naji, kuma kamar yanda ki kace kina da hankali, to ina so ki nuna min ke mai ilimi ce, kuma naji dad'i da kika qyaleta."
Share fuskarta tayi kafin suka fita suka nufi cikin gidan, sun samu Papa da Mamie suna hira a falo, da gudu Khairat ta fad'a jikin Papa tana dariya, saida suka gama murnar ganin juna sannan Papa yace "shalelen Papa, ashe har yanzu baki girma ba? na dauka kin girmi hakan yanzu."
Turo baki tayi gaba tace "Papa wane irin girma kuma, nifa kamar autace a gareku, babu wani gabana kuma babu bayana, to in banyi ba wa zai muku."
Mamie ce ta juyo da fuskarta ta kama kumatunta tana fad'in "banga laifinka ba, kiyi yanda kike so shalelen Papanta."
Murmushi tayi tace "Mamie ina kwana?"
"Lafiya lau Khairat, ina mai gidan naki?"
Kallon kofar da suka shigo tayi danta nuna musu Umar Faruk, ganinshi tayi durk'ushe yana gaishe da Papa, ajiyar zuciya tayi ta tashi ta kama Umar Faruk ta zaunar dashi kan kujerar da dukansu suke tana fad'in "kaifa yanzu d'an gidane, bamu da wani dangi
Showing 126001 words to 129000 words out of 186119 words
Cikin kunnenta ya rad'a mata " ai Umar Faruk mallakar Khairat ne, sai yanda taso za tayi dashi, kinga kuwa ai dani da hannayena na karb'ar kyauta daga gareki duk naki ne."
Dariya ta sake yi tace "na ganoka fa, kana nufin dani da abinda na mallaka duka naka ne, shi yasa ma ka karb'a."
Kumatunta yaja yace "mai basira kenan."
Da qyar suka rabu ya tafi wajen aiki, ita kuma ta koma ta kwanta bacci danya tabbatar mata ba zai dawo da rana ba, aikinshi yake hankali kwance cike da farin ciki da nutsuwa, bayan sallah azahar saiga wani babban kira a wayarshi, ya zai gani inba Papa ba, da girmamawa ya d'auka suka gaisa, nan Papa yace yana son ganinshi inba damuwa, nan ya aje komai dake gabanshi ya tafi kiran mai gida kuma suruki.
*Bayan yaje gidan* Papa yake sanar dashi wani compagnie a qasar *Las vegas* dake *America* suna neman zakakurin matashin mai aikin zane irinshi, dan haka in yana son aiki toya shirya zuwa qarar Las vegas domin tattaunawa dasu, kuma tattaunawar ba zata wuce gobe ba, dan haka idan ya amince compagnie ya d'auki nauyin tafiyarshi da dawowarshi, wannan shine sharad'in farko, Umar Faruk ya d'auka kawai alfarma ce Papa ya mishi kasancewarshi surukinshi, hakan yasa ya amince kuma ya kama hanyar gida cike da zumud'in fad'awa Khairat abinda ake ciki, sai dai baisan ita tayi silar samun wannan aikin nashi ba.
Su Mama ya samu a tsakar gidan dukansu suna d'an tab'a hira sama sama, saida ya zauna ya fad'a musu komai dake faruwa, mahaifiyarshi dai kam tayi farin ciki, amma banda sauran iyayen nasu da suke ganin ci gabanshi na qara kusantoshi, addu'a Mama ta mishi kafin ya tashi ya nufi d'akin Khairat yana sake kallon k'ofar Zuby dake rufe, yana tunani a ranshi har yanzu bata dawo ba kenan, qwafa yayi a cikin ranshi kafi ya shiga d'akin da sallama, littafi ne a hannunta tana karatu tana ganinshi ta taso ta tarbeshi, "albishirinki?"
"Goro." ta fad'a a harshen zarma kamar yanda shima yayi.
A harshen zarma dai fad'a mata komai, rashin mamaki da tayi yasa yayi zargin wani abu, kallonta yayi yace "alkairina, kodai aikinki ne."
Zaunar dashi tayi tana kallonshi tace "kayi hak'uri Umar Faruk, ba lallai ina so na canza qaddarar ubangiji a kanka bane, amma ina so naga kaji dad'i kaima, ba dole sai kayi aiki da compagnien ba harna tsawon lokaci, amma idan ka samu wani abu mai tsoka kaima zaka iya tsayawa da qafafunka, wannan shine burina a kanka, ina so naga ka tsaya da qafarka saboda kana basira da ilimin daka wuce ka zauna qarqashin wani, amma ka yafe min idan nayi ba daidai ba."
"Shawara mai kyau, hakan kuma zai bani damar kin rattab'a hannu akan aiki dasu na dindindin."
"Hakane." ta fad'a tana murmushi.
Rumgumeta yayi yace "na gode Khairat." a zuciyarshi kuma cewa yayi " da farko na d'auka *Jihadi* nayi na aureki , amma yanzu komai na fitowa fili cewar, kece silar arzik'ina a duniya, kuma kece farin ciki da kwanciyar hankalina."
D'orawa da "ki shirya, dan tare zamu tafi dake ki nuna min gari."
Cikin dariya ta kalleshi tace "shirme."
"Allah kuwa nake fad'a miki." ya fad'a yana dariya.
_Wannan karan naga uban daya isa ya hana tafiyar nan._
*****************
Koda Zuby taje gida basu tsaya komai ba suka wuce wajen malam, nan Zuby ta fad'a mishi abinda ke faruwa, tambayarta yayi me take so a mata? cewa tayi asa Umar Faruk ya tsaneta harya saketa ma, nan yace msu "aikinku mai sauki ne, kuma zai yiwu, amma harsai kun samo wani abu daya zama na ita Khairat d'in ne, bi ma'ana abinda take sawa a jikinta koma menene, dashi za'a had'a laqanin da zai tsaneta, zaku iya?"
Mama ce ta karb'e da "zamu iya mana malam, aiba wuyane da aikin ba."
"A shikenan, kuyi qoqari ku kawo cikin kwana biyu ko uku, dan a gaggauta yin komai."
"To malam, kar kaji komai za'a kawo."
Da haka suka baro wajen malam Zuby tayi gida Mama ma tayi hanyar gida, da tunanin yanda za ayi ta samu abun Khairat taje gida, ganin motar Umar Faruk ba qaramin tsinkewa 'yan cikinta sukayi ba, da qyar ta shiga gidan tana d'an sunnewa, ganin baya tsakar gidan yasa ta fara gaggawar bud'a d'akinta ba tare data kula da mutanen tsakar gidan ba, suma babu wanda ya mata magana dan sunga abinta iskanci ne da raini, tana shiga tayi saurin cire kayanta tayi zaune gabanta na fad'uwa tana tunanin hukuncin da zai mata.
Ana sallah la'asar ya fito, koda d'akin bud'e bai kula da tsiyarta ba yayi alwala ya wuce masallaci, bai kuma dawo ba sai bayan sallah isha'i, lokacin Khairat ta sake daddaga abinci mai rai da lafiya, saida ta zubo min a babban kula tace na kawawa _Team Khairat_ amma na taho akan hanya nayi tuntube tuwon ya zube, daga nan na zaune na qarasa cinye wanda yayi saura tare da kazar dake samaπ kunsan dai akwai aminci tsakaninmu da kaza, yau ma kamar jiya sunci sunsha kuma sunyi farin ciki tare da raya darensu, yayin da Zuby haushi kamar zai kasheta, dan da yaje mata saida safe bai mata wata maganar kirki ba, hakan kuma ya qara b'ata mata rai, amma dai kuma ba zata iya bayar da hak'uri ba a tunaninta, shi kuma a nashi b'angaren yana ganin saita bashi hak'uri ta kuma gane kurenta sannan.
_Me kuka ce mutanena?_
πππ
17/08/2019 Γ 20:13 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Bismmilahir-rahman-rahim_
4β£7β£
Kamar kullum gaba d'aya sun taru a d'akin Baba inda yake musu nasiha akan kyautatawa, saida aka gama kamar kullum ana shirin tashi Umar Faruk yayi gyaran murya yace "am, ina da magana, dan Allah ku zauna."
Gyara zama kowa yayi Baba yace "muna jinka Umar Faruk."
"Dama akan maganar aikin dana samu ne, acan compagnie suna buk'atar naje gobe domin tattaunawa dani, kamar yanda na fad'a muku wannan aikin Khairat ce silar samar minshi, kuma ni babu inda na tab'a zuwa na qasar waje, kasancewarta wacce tasan wajen yasa nake tunanin tafiya tare da ita, amma shawara ce bansan ku me kuka gani ba?"
Baba ne yace "Umar Faruk, kaima fa yanzu magidanci ne, ba komai bane zaka nemi shawararmu akai, indai har kana ganin hakan ba matsala kuma shine daidai, ai saimu muku fatan alkairi."
"Na gode Baba." ya fad'a kafin ya d'ora da "dama wannan ce maganar, na gode."
Tashi kowa yayi zai fita Zuby kam ta kasa tashi, ganin Umar Faruk zai fita yasa Zuby kallon Baba tace "ina da magana nima."
Juyowa Umar Faruk yayi ya kalleta, kallonshi tayi itama tace "ka dawo ka zauna."
Zaunawa yayi Mama ma zata fice Zuby tace "Mama kema ki zauna."
Saida kowa ya fita Baba ya kalli Zuby yace "ina jinki Zubeida, ina fatan dai ba wata matsala bace?"
Tana kallon Umar Faruk tace "gaskiya ni ba'a min adalci ba, na fahimci yana son yin tafiya da ita, to ba komai su tafi, amma kafin su tafi ya fad'a min Γ wane matsayi nake, dan wallahi ba zan iya zaman gadi ba a gidan nan haka kawai."
Da mamaki duka suke kallonta kafin Umar Faruk yace "Zubeida wane irin rashin adalci nake miki?"
Shiru tayi harya sake maimaitawa da "Zubeida fad'a min, mena miki na rashin adalci."
Cikin turo baki tace "ai duk mai ido yasan baka adalci a tsakaninmu, domin kuwa ko ranar aikina ne idan ka shiga d'akinta saika jima kafin ka fito, kuma inhar ka shiga d'akinta to sai dai ka fito da fara'a da murmushi a fuskarka, sab'anin d'akina idan ka shigo sai kayi duk abinda za kayi ka b'ata min ran sannan kaima ka fito cikin b'acin rai, bugu da qari ita cikin kayan abincin su Mama take diba tana aiki dasu, ni kuma ka siyo min wanda basu kai basu kawo ba, dad'in dad'awa kuma duk da nasan ita yar mai kud'i ce, amma na tabbata daga cikin suturun da take sakawa akwai wanda kai ka matasu na lefenta, yah Umar idan nace zan dinga zayyano maka rashin adalcin da kake ba zai k'idayu ba."
Murmushin takaici yayi na gefen labb'a, dan yaso a kamashi da laifi danya b'ata hak'uri, amma kash ta kasa bayar da hujjar da zai d'auki laifin a kanshi, saida ya qara gyara zamanshi yace "da kin fad'i wani abu daban ba wannan ba, amma tunda haka ki kace bara na fad'a miki abinda yayi daidai da abinda kika fad'a."
"Da farko kince idan na shiga d'akin Khairat nakan jima ban fito ba kuma ina fitowa da fara'a, ba zan iya ce miki komai ba, amma ina baki shawara ki samu wata qawarki da kika yarda da ita ki tambayeta me yake janyo hakan, na tabbata zata fad'a miki gaskiya, na biyu kuma maganar abinci, to kiji in fad'a miki, wannan kayan abincin da kika gani wallahi ko Baba baya da iko akansu kamar yanda Khairat take da iko akansu, kinsan me yasa? saboda itace ta siyesu, kuma bata tab'a kulasu ba sai ranar dake kika kawo shawarar kowace ta dinga girki da kanta, Zubeida idan akwai wanda akawa rashin adalci to Khairat ce, domin kuwa a lokacin dana siyo miki kayan abincin nan ita ban siyo mata ba, sannan na d'auki kud'i na qara muki dasu, duk da haka sisin kwabo ban bata ba dan nasan ba zata karb'a ba, tunda ta shigo gidan nan zan iya fad'a miki adadin da taci abincin gidan nan, kinga kenan ita akawa rashin adalci, na uku kuma kince sutura, to kijini da kyau Zubeida, ni banwa Khairat lefe ba kece nayiwa lefe, tunda nake da ita zani d'aya na atamfa bai shiga tsakani na da ita ba, kin ganni a matsayin mijin Khairat? wallahi har yanzu idan banda wurin kwanciya da ruwan gidan nan, banga wani abu da Khairat ke anfani dashi ba wanda zan iya cewa nawa ne, sannan atamfar da Khairat ke sawa a jikinta ma kad'ai tafi k'arfin arzik'ina, bare kuma kudin d'inkinta har azo ga shadda ko less, maganar sarka da d'an kunnai ma mu barta, har yanzu babu tsaiyar dana tsinanawa baiwar Allah nan a matsayina na mijinta, hasali ma nine ke qaruwa da ita tako ina, a yanzun burina bai wuce na samu hanyar da zan saka mata da alkairin data min ba, dan duk wanda zai bawa ahalinka abinda zasu ci ya kuma dinga kyautata musu, to tabbas shi masoyinka ne na gaskiya, musamman ita da bata damu da dukiyarta ba, ita dai burinta kawai ta kyautatawa wanda yake tare da ita, ba tayi dan gobe ta fad'a tayi maka, sannan idan tayi ba'a karb'a ba tana jin zafi, domin kuwa ita alheri a cikin jininta yake kamar yanda ma'anar sunanta yake, dan haka ina baki shawara Zubeida, ki cire komai a ranki ki rumgumi yer uwarki, wallahi babu komai a zuciyarta a game dake, ko sau d'aya bata tab'a nuna min kishinta a kanki ba, ina fatan za kiyi anfani da shawarata, kuma ki yafe min idan na fad'i abinda ya b'ata miki rai."
Mik'ewa yayi da fad'in "saida safenku." danshi baiga abinda zai sashi b'ata lokacinshi ba akan banzan shirmen Zuby.
Mama da Baba ma sun gamsu da abinda ya fad'a dan haka sukayi shiru harta tashi ta koma d'akinta, yana shiga d'aki Khairat ya sameta zauna tana tunani akan karatun da Baba ya musu, dan a cikin kyautatawar daya musu magana akai, akwai kyautatawa iyaye, ita kuma tana tunanin yanda ta zauna da nata iyayen, ji tayi tana so ta basu hak'uri akan yanda ta mu'mulancesu a baya, zaune yayi kusanta ya janyota jikinshi yana fad'in "yadai, meya faru."
"Ba komai." ta fad'a tana shafa jikinshi.
"Kin tabbata?"
"Um."
Dago kanta yayi ya kalli fuskarta, turo baki yayi gaba kamar yaro ya langab'e kai yace " ban yarda ba gaskiya, akwai wanda ya tab'a min baby, fad'a min meya faru.?
Qara langab'ewa tayi tace " ba komai fa."
"To indai hakane kiyi dariya na gani."
D'an murmushin yaqe tayi tace "nifa bacci nake ji."
Tana fad'a ta kwanta tare da jan zanin rufa, Umar Faruk a ranshi cewa yayi "baiwar Allah, ko tana tunanin abinda ya faru ne wanda ya tsayar dani? koma dai meye dole nima na saki farin ciki kamar yanda kema kike sakani farin ciki, wannan itace damar da nake da wajen saka miki da alkairi."
Hayeta yayi ya fara mata cakulkuli yana fad'in "ba zan iya komai ba sai naga dariyarki."
Ai kuwa dariya ta fara qyalqyalawa daga haka kuma suka lula duniyarsu ta maji dad'i......
**************
Tunda asuba koda Khairat tayi sallah ta fara shirya musu kayansu tare da shirya kanta , Umar Faruk kuma saida ya shiga d'akunan iyayensu suka gaisa tare da d'akin Zuby, haka yayi sallama har sau uku amma ko qala ba tace ba, sannan ya qara da "kin tashi lafiya?"
Nanma shiru ba amsa, fita kawai yayi daga d'akin, yana zuwa shima shiryawa yayi a lokacin kuma Khairat ta gama abin karyawa, suna gama break suka fito cikin shirinsu, duka iyayen nasu na zaune dan haka suka qarasa suka musu sallama, sun tashi kenan zasu wuce Zuby ta fito tana rufe d'aki itama zata wuce Γ©cole, ganin ko kallon kowa ba tayi ba ta kama hanyar fita yasa Umar Faruk binta da sauri, a soro ya sameta ya rik'e yana fad'in "ki jira mu saukeki."
Fizge hannunta tayi tace "rabu dani bana so."
Ganin Khairat ta taho kuma ko Khairat ba zaiso ta rainashi ba yasa ya wurga mata wata harara, shiru tayi tana sauke numfashi ,wucewa yayi suka bi bayanshi amma abin mamaki, da hanzari Zuby ta zagaya ta zauna a gidan gaba, kallonta yayi zaiyi magana kawai yaga Khairat ta bud'a mazauninshi ta zauna, saida ta daidaita zamanta sannan ta fizgo makullin hannunshi fuskarta a had'e itama ba alamar wasa, jin tayiwa motar key yasa ya bud'a gidan baya ya zauna ya rufe yana fad'in "Allah gani gareka, ashe dama haka mata biyu suke, da zaran sun had'u sai an caza maka qwaqwalwa."
Gyara madubi Khairat tayi ta kalleshi tace "baby ka shirya?"
Gintse dariyarshi yayi ya sunne kai qasa, Zuby kuma qoqarin bud'ewa ta farayi danta fita, Khairat na ganin haka ta fizgi motar da iya k'arfinta a zuciyarta tana fad'in "uban daya kawoki gidan gaba."
Titi suka hau Umar Faruk na kallon kowace daga baya, Khairat na tuk'i hankali kwance Zuby kuma tayi tsaki yafi dubu , amma jin sun qyaleta yasa tace "aikin banza, barewa ai ba tayi gudu ba d'anta yayi rarrafe, an gada wajen uba dole a nuna hali."
Ba tare data kalleta ba tace "na fad'a miki ki daina saka iyaye a maganar data shafemu , bai zama lallai abinda zai fito a bakina ya miki dad'i ba, amma kika b'ata min rai yanzun nan saina had'a motar nan da bango."
Sai lokacin ta kalleta duk da tana tuki tace "bana tsoron mutuwa, dan Mama tace ni yar aljanna ce, bugu da qari ina tare da babyna, zanyi farin ciki mu mutu tare, idan kin shirya biyarmu to."
"To an fad'a miki ina tsoron mutuwa ne? ai gwara na mutu ma da zama dake a matsayin kishiya wallahi, inkin fasa hadamu da bango bakya tsoron Allah daya halicceki."
"Kin shirya mutuwa kenan?" cewar Khairat.
"Shege ka fasa, d'an halak sai yanka."
Da sauri Khairat ta kalleta tace "a'a malama, ki daina sako mana wannan kalmar anan, ni dai 'yar halak ce."
"Kenan nice shegiyar?"
"To ai ba kama garesu ba, kuma ba'a rubuta a goshinki ba bare na karanta, kinga kenan ba zan iya sani ba."
"In haka kike tunani, toki d'auka ni yar babanki ce."
Umar Faruk ne yayi saurin cewa "ya isa haka to, karna sake jin bakinku, inba haka ba rai zai b'ace."
Khairat kuma gani tayi aita kaita qasa, dan haka tace "ina aiki na masu hankali, amma idan haukana ya motsa to akwai matsala, ki kiyaye bakinki kafin kiji abinda zai iya tarwatsa miki lissafi."
Tsaki Zuby tayi ta rumgume hannaye har suka isa ecole d'insu, saida ta juya ta kalli Umar Faruk sannan ta kalli Khairat tace "na gode Allah, ni ba 'yar d'an giya bace."
Tana fad'a ta fita ta bar motar, Khairat binta tayi da kallo lokaci d'aya hawaye suka soma zubo mata, fitowa Umar Faruk yayi ya bud'e inda take zaune, saida ya kama hannunta ya fito da ita sannan ta zagaya ta zauna inda Zuby ta tashi, saida suka fara tafiya jin tana shashek'ar kuka yasa ya fara tausarta da kalamai masu sanyi, ba tayi shiru ba har saida taga yayi parking a k'ofar gidansu sannan, zata fita ya rik'e hannunta suka kalli juna, d'aure fuska yayi yace,
"Ki maye fara'a a gurbin d'aure fuskar nan."
Cikin muryar kuka tace "amma fa kaji abinda yarinyar nan ta fad'a min."
"Naji, kuma kamar yanda ki kace kina da hankali, to ina so ki nuna min ke mai ilimi ce, kuma naji dad'i da kika qyaleta."
Share fuskarta tayi kafin suka fita suka nufi cikin gidan, sun samu Papa da Mamie suna hira a falo, da gudu Khairat ta fad'a jikin Papa tana dariya, saida suka gama murnar ganin juna sannan Papa yace "shalelen Papa, ashe har yanzu baki girma ba? na dauka kin girmi hakan yanzu."
Turo baki tayi gaba tace "Papa wane irin girma kuma, nifa kamar autace a gareku, babu wani gabana kuma babu bayana, to in banyi ba wa zai muku."
Mamie ce ta juyo da fuskarta ta kama kumatunta tana fad'in "banga laifinka ba, kiyi yanda kike so shalelen Papanta."
Murmushi tayi tace "Mamie ina kwana?"
"Lafiya lau Khairat, ina mai gidan naki?"
Kallon kofar da suka shigo tayi danta nuna musu Umar Faruk, ganinshi tayi durk'ushe yana gaishe da Papa, ajiyar zuciya tayi ta tashi ta kama Umar Faruk ta zaunar dashi kan kujerar da dukansu suke tana fad'in "kaifa yanzu d'an gidane, bamu da wani dangi
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43 Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63