Murmushi tayi da bakinta kad'ai ya motsa kafin tace "ta fad'a min komai a waya duk abinda ya shiga tsakaninki da 'yarsa, na yarda zan taimakeki ne a zahiri saboda kin samemu tsakiya da shirye shiryen zab'e, kuma akwai wani aiki da mai neman kujerar Mani Bukar ya biyani kud'ad'e danna kai Mani Bukar qasa kamar yanda ina d'aya daga cikin wanda suka sakashi yayi sama, dan haka karki damu zuwa gobe zan gama shirya komai, kuma zakisha mamakin abinda na shirya, tabbas Khairat zata ji ba dad'i itama."
Da farin ciki tanti tace "na gode sosai Hajia da wannan taimakon, kuma insha Allah Hajia za kiji babban biya."
D'an b'ata rai matar tayi ta kalli yar fara tace "yar fara ina fatan kin fad'a mata ba'a min wasa da maganar data shafi kud'i ko?"
"Ai karki damu Hajia, na fad'a mata komai a game dake, ba za'a tab'a samun matsala ba." cewar 'yar fara.
"To yayi kyau, zaku iya tafiya." tana fad'a ta tashita shiga wani d'aki ta barsu nan, tashi sukayi Mama na yaba matar tana ji inama ta zama ita, har saida 'yar fara tace "to ai matsalar kin tsufa ne, amma badan haka ba ai zaki iya hawa network kema."
Hararanta tayi tace "karki cimin mutunci mana, me kika d'aukeni?"
"Ba komai." cewar 'yar fara.
*Mamienmu amin afuwa*ππββ
****************
Umar Faruk na zaune daf da Khairat yana bata magani zazzab'i tana sha, Mammie na gefen Khairat sai Mamie da Papa dake d'aya kujerar suna kallonsu, duk da dare yayi yana so yaje gida amma ganin jikin nata ba sauqi yasa ya kasa tafiya, tana shan maganin ta koma ta kwanta tana sake dunqulewa cikin bargon da Mamie ta d'auko mata, a hankali take lumshe ido alamar tana so tayi bacci, a haka har baccin yayi gaba da ita, tashi Umar Faruk yayi ya musu sallama zai fita, da k'arfi sukaga Khairat ta fad'o daga kan kujerar, a zabure ta farka itama tana kallon mutanen wajen, da sauri Umar Faruk ya qarasa wajenta ya kamata ta tashi ta koma ta zauna, fuska ba annuri yace "kalleni nan."
Kallonshi tayi ya sake had'e rai yace "wallahi ku daina wahalar da ita haka in kuna son zaman lafiya, kunga ina binku a hankaline saboda ina so mu rabu lafiya daku, tab'ata da kuke shine kuskuren da kukeyi."
Qwafa yayi ya mik'e zai nufi hanyar fita Papa yace "Umar Faruk, me yake damunta ne?"
Juyowa yayi yace "karku damu Papa, komai zaiyi daidai na baku tabbacin hakan."
Yana fad'a ya juya ya kalli Khairat, hararan sama da qasa ta masa taja dogon tsaki, fita ranshi a b'ace ba tare daya damu da abinda tayi ba, sam yau ma basuyi bacci ba ko kad'an, daga wannan ciwo sai waccen a haka suka kwana.
**************
Tunda Zuby taga shiru bai dawo ba sai ranta ya fara b'aci ta fara tunanin abinda Mama ta fad'a mata, ta kuma yarda tabbas wata rana zaice zai tare can tare da Khairat indai har ana haka tun yanzu, ganin Ruk'ayya ta kawo abincinshi ta aje kawai saita tashi ta d'auko maganin data jefa qasan gado ta duba wanda zata saka a abinci ta mayar da sauran, tsautsayi ya kawo Umar Faruk a lokacin da take zuba maganin a abinci, komawa yayi da baya ya saita kansa tare da had'e b'acin ranshi sannan yayi sallama ya shiga, ko kad'an bai nuna mata wani abu ba ya share kawai, wanka yayi sannan ya zauna cin abinci, bismillah yayi yana shu'umin murmushi ya kai lomar bakinshi, saida ya cinye wanda ta zuba mishi duka saboda yunwar da yake ji, dan duk lokacin da zai kai abu bakinshi saiya tuna Khairat, hakan yasa shima bai cika ci yana qoshi ba kwanan nan, da farin ciki Zuby ta kwana sab'anin Umar Faruk daya kwana yana kallon fuskarta, tsanarta na sake mamayeshi, daga qarshe kuma tunanin Khairat ya maye gurbin tunaninta dashi har gari ya waye.
Hannu ya mik'a mata cike da qoqarin taushe qiyayyar da take mata yace "ina so zan gaisa da yarona."
Hannun ta mik' masa ta taso shi kuma ya bi cikinta da kallo wanda ya turo riga ya fito, shafar cikin yayi yace "nasan ka tashi lafiya, haka Papanka da mamanka, kuma nasan zaka kula min da kanka, ni zan tafi."
Sunkuyawa yayi ya sumbaci cikin sannan ya fice, saida ya gaishe da iyayensu sannan ya wuce gidansu Khairat, da shigarshi sallama kad'ai yayi ya samu duka mutan gidan tsaye akan Khairat dake ta birgima a qasa tana kuka tana cewar zuciyarta zata fashe zafi take mata, qarasowa yayi dan babu ma wanda ya amsa sallamar tashi, tsaye yayi shima yana kallonta idonta rufe sai hawaye dake fitowa, matsowa yayi da nufin zama kusa da ita kawai saita d'ago ta bulalo amai, duk da ta b'ata mishi jiki bai damu ba saida ya zauna ya fara taimaka mata da addu'a, a hankali a hankali ta fara samun nutsuwa da sauqi, bayan wani lokaci kuma sai bacci yayi gaba da ita, Mamie ce tace "Allah ka dubi yarinyar nan ka sassauta mata abinda yake damunta, Allah ka yafe mata kurakurenta badan mu ba." ta qarashe da fashewa da kuka.
Kallonta Umar Faruk yayi yace "dan Allah kuyi hak'uri ku daina kukan nan, insha Allah zata samu lafiya."
Cikin kuka Mamie tace "wallahi tausayi take bani, kwananta biyu yau a gidan nan amma har yanzu baccin da tayi baifi na awa biyu ba idan aka had'a, ace daga wannan ciwo sai waccen, da anji sauqin wannan kuma sai wani da danno kai, wallahi nidai ban tab'a ganin laulayi irin nata ba."
Gyara mata kwanciya yayi ya mik'e yace "ku kula da ita zanje na samo ganyen magarya, insha Allah zata samu lafiya da yardar Allah."
Yana fad'a ya fice daga gidan, zaune sukayi suna kallonta kafin ta farka kuma, ba dadewa kuwa ta farka tana dafe kai, Mamie ce ta kawo mata abinci taci amma sam tak'i ci, saida Papa ya lallab'ata ya rarrasheta kad'ai ta samu taci kad'an, tana gama ci ta tashi da gudu taje k'ofar shigowa falon ta fara amaye abinda taci, tana haka Umar Faruk ya shigo gidan, tsaye yayi yana kallonta da tausayawa saida ta gama ya rik'ota suka shigo, kallonta yake sosai duk da cikinta ya girmema na Zuby amma ko alamun fitowa baiyi ba, zaunar da ita yayi sannan ya bawa Mamie ledar hannunshi yace "ku jiqa wannan ku ajeshi a wuri mai kyau, zan nemeshi nan da kwana bakwai insha Allah."
"To shikenan." cewar Mamie tana karb'a.
****************
Misalin *09:30* na dare duk suna zaune a falon, Khairat na kwance akan cinyar Umar Faruk da yake so ya tashi ya tafi ta rik'eshi, hira suke sama sama wani jami'i ya shigo ba tare da sallama ba ya sarawa Papa alamar girmamawa yana fad'in,
"Yallab'ai, wata mata ce a qofar gida tace tana son ganinka, na tambayeta abinda ya kawota amma tace ita kai take son gani."
Shiru Papa ya d'anyi kafin yace "ok ba damuwa, kace ta shigo."
Juyawa jami'in yayi bayan ya amsa da "an gama yallab'ai."
Harsun fara tab'a hira sukaji ance "salam."
Kowa kallon qofar yayi dan ganin mai sallamar, zunbur Papa ya mik'e da tsananin mamaki yace " *Odette*, kece gidana, meya kawoki nan, kin manta rabuwarmu ne?"
Kowa dai da mamaki yake kallonsu harda Khairat da jikinta ya d'anyi dama, juyawa matar tayi ta kalli qofa tace " *Salim*, shigo mana."
Wani matashin saurayine da bazai wuce shekara sha shida ba zuwa sha bakwai fari sol dashi kamar matar, d'an gaye ne sosai irin matasa ne masu aji, turo yaron tayi gaba ya nufi Papa tace "kaje, yau dai na sauke wannan nauyi, kuma na huta da qorafinka kullum, kuma yanzu asirinmu zai rufu."
Daf da Papa yaron ya tsaya yana murmushi ba b'ata lokaci ya rumgume Papa yana fad'in "oh Babana, naji dad'in had'uwa da kai."
Papa daya kusa mtuwar tsaye da qyar ya raba jikinshi dana yaron yace "kai wace maganar banza ce wannan, waye uban naka?"
Hamshaqiyar matar ce tace "kunga na barku lafiya, saida safenku."
Cike da yabqi da yanga tace "oh yi hak'uri fa, wannan ai shine *Salim* danka dana jima ina boye maka, amma kwanakin nan yana addabata waishi dole na had'ashi da mahaifinshi danya gaji da ganinka a tv kullum, nace yayi hak'uri amma sai yace zai fad'a a gidan jaridu da tv cewar shi d'in danka ne, shi yasa naga zaifi ayi komai asiri rufe ba tare da anyi tone tone ba, kasan zab'e ke tafe."
"Wannan ai maganar banza ce ma, kin sani na sani lafiya lau muka rabu dake, karki yarda kice zaki b'ullomin ta wannan hanyar, dan wallahi ba zakiji dad'i ba, kuma ki gaggauta fita min da wannan d'an iskan yaron kafin nasa a fitar min dashi."
Rai b'ace tace "a'a Mani, karka sake zagar min yaro wallahi, kuma idan kace baka yarda ba kai ka sani bana abu babu hujja, kamar yanda kasan bana qarya ko kuma cuta."
Jakarta ta bud'a ta ciro da takardu ta jefa mishi a qirji tace "wannan suna dauke da duk wasu bayanai tun daga lokacin dana d'auki cikin Salim har haihuwarshi, sannan akwai gwajin da asibiti sukayi na qwayoyin hallitunshi iri d'aya ne da naka, idan kuma baka yarda ba zaka iya sakawa a maka sabon gwaji."
Tana fad'a ta juya ta fita daga gidan, yaron kuma zaune yayi kusa da Mamie yana kallonta yace "bonsoir (ina wuni)."
Da sauri Mamie ta shige d'akinta tana hawaye, maida kallonshi yayi ga Khairat data tashi zaune tana kallon ikon Allah, da azama yaje wajenta ya zauna yana kallonta yace "wannan itace auntyna ko?"
Kafin ayi magana kuma ya kamo hannun Khairat yana maqalewa da nashi, badan rashin lafiya da matar nan ta gane kurenta cewar Khairat a zuciyarta, amma duk da haka cikin zafin rai ta d'aga hannu ta wanke yaron da mari ta nunashi tace "karka sake tab'ani dan kai ba d'an uwana bane."
Dafe kunci yayi yana murmushi yace "ke kuma haka kike tarban bak'inku, ba komai ke yayata ce zaki iya yimin komai."
Tashi tayi danta bar wajen amma saita zube saboda qafafunta da suka rik'e, Umar Faruk ne ya tashi ya d'auketa ya kaita d'akinta ya kwantar da ita, addu'a ya mata ya rufeta sannan ya fito ya bar d'akin dan tak'i kallonshi ma, yasan badan rashin lafiya ba da gidan nan ya hargitse yau.
Papa ya samu tsaye yana duba takardun nan har yanzu, indai har zaiyi anfani da abinda ya gani a takardun to tabbas Salim d'ansa ne, amma ba zai yarda ba dan haka Umar Faruk na musu sallama ya fita ya kira docteur d'inshi yace gobe zaizo, d'akin Mamie ya shiga ya samu tana kuka, zaune yayi ya fara magana da "Na'ima, dan Allah..."
D'aga mishi hannu tayi ta tashi tana share hawayenta tace "kar kaba kanka wahala wajen rarrashina, nima ba hushi nayi da kai ba, kawai dai banji dad'i bane saboda ban tab'a tunanin ka haihu a waje ba, amma inhar ina da hankali aibai kamata nayi hushi da haka ba saboda nasan komai a game da rayuwarka ta baya."
"Na gode da kika fahimceni Na'ima, amma wallahi nima ban tab'a sanin inada wannan yaron ba, kuma har yanzu ma ban yarda d'ana bane harsai Allah ya tashemu gobe munje asibiti an sake mishi wani gwajin."
*Wata sabuwa*
*Barka da Ranar Hausa ta duniya, Allah ya d'aukaka matan hausawa.*
29/08/2019 Γ 14:33 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Haka kawai sai kaga Allah ya had'a zuqatan bayinsa, ba gari d'aya ba bare unguwa, amma haka Allah ya had'amu har muke qaunar junanmu, Allah ubangiji ya baki lafiya my Meerahgee *(Maryam Gital)*, Allah yasa zakkar jikina kuma sanadin yake zunubanki, your Meerahgee again._ππ
_Dan Allah ki daina wahalar da zuciyata ki fito ki naganki ko naji sanyi, Allah ya qara miki lafiya dawamammiya, *My BK* i love you_.
Ba'a b'ata lokaci ba Papa ya d'auki Salim suka je aka sake mishi gwaji, ba yanda ya iya tunda gwajin ya bayyana d'anshi ne na cikinshi, daga nan kuma sai yaji yaron ya shiga ranshi, ashe shima Allah ya bashi namiji.
*Hummmmmmmm*
Koda suka zo gida Papa yasa aka gyara mishi d'aya daga cikin d'akuna, ana cikin haka ya had'a yaron tare da masu gadinshi suka je babban boutique aka siyo mishi kaya masu kyau da tsada, sabuwar rayuwa kenan wa Salim.
*Wacece Odette???*
Odette shahararriya kuma 'yar duniya ta gidan gaba, sun jima tare da Mani Bukar saboda gogewarta da kuma iya bariki da soyayya, tun kafin ya fara siyasa suke tare da ita, kuma tana d'aya daga cikin wanda suka bashi gudummuwa sosai harya hau kujerar da yake yanzun, a waccen lokacin zai iya cewa bayan mahaifiyar Khairat ita macen da yake so, amma a lokacin da shiriya tazo mishi saiya fad'a mata ya shiryu kuma itama ta tuba ga Allah, sam tace shi dai yaje amma ita tana nan har yanzu, saida mata babbar sallama sannan suka rabu cikin mutunci, amma shine yau tazo mishi da maganar yaro d'an shekara sha bakwai, wanda baisan dashi ba sai yanzu.
Bata jira amsarshi ba ta bud'a jakarta ta fiddo ledar awarar data siya ta bud'e, ba tare da kama hannun yaro ba ta fara gaigayar awarar ko kallonshi ba tayi, shi kuma kallonta yake da gani kasan yunwa take ji sosai, yanda take cin awarar sai yaji ta birgeshi yana ji kuma inama Khairat itama haka take cin komai, murmushi kawai yake mata har suka d'auki wata hanyar ta daban, sai lokacin ta kalleshi tace "yah ina zamu je kuma nan?"
Ba tare daya kalleta ba yace "zanje na siyar daku ne, ko baki san mace mai ciki tsadane da ita ba?"
"Hum, aiba zaka fara ba, dan nasan ko ka siyar dani ba zaka yarda ka siyar da magajinka ba."
Dariya yayi yace "gaskiyarki kam, amma taya zan siyar da uwar bayan itace mai haifawar? abune da ba zai yiwu ba ai a wajen Umar Faruk."
Kallonshi tayi ta cika baki da awara tace "kana sona ne har yanzu?"
Kallon qwayar idonta yayi amma ya kasa cewa komai, maida kallonshi yayi ga tuqinsa ita kuma tace "basai ka fad'a ba nasan baka sona."
Kallonta yayi yace "Zuby, kina so na b'ata lokacina wajen fad'a miki abinda kika sani, ko kuma kina sone dole saina ce miki ina qaunarki fiye da tunaninki, nasan kema kinsan da haka."
Ganin dai suna shiga wani wajen yasa tace "wai ina zamu ne?"
Kashe mata ido yayi hankali nutsu yace "ki yarda dani mana, ba zan cutar dake ba."
K'ofar wani matashin gida suka paka, shine ya fara fita kafin ta fito itama, goge maiqon dake hannunta tayi a hijabinta sannan tabi bayanshi suka shiga ciki, babu hayaniya gidan sosai hakan yasa sai wata dattijuwar mata ta musu iso ciki, suna shiga falon Zuby ta tsaya cak saboda ganin babanta Bala zaune da alama bashi da lafiya, saida Umar Faruk ya d'an ja hijabinta sannan suka samu wuri suka zauna, gaisawa sosai Umar Faruk yayi da mutanen Zuby na kallonshi dan yanda taji suna gaisawa alama ce ta yana zuwa gidan, kallon da Umar Faruk ya mata yasa ta kalli Bala tace "ina kwana?"
"Ina kwana yanzu?" cewar Umar Faruk.
"Ina wuni?" ta fad'a tana cika baki.
"Lafiya lau Zubeida, ya makarantar?"
"Lafiya lau."
D'aya daga cikin matance tace "wannan matarka ce?"
"Eh, amaryar ba." cewar Umar Faruk cike da kunya.
Bala ne ya d'ora da "kuma 'yata ba."
Da mamaki matan suka kalleshi yayin da Zuby ta kalleshi, babbarce tace " 'yarka kuma Alhaji, taya ta zama 'yarka kuma?"
"Eh, haka nace, 'yata ce kuma ta cikina, zaku iya bamu wuri." ya fad'a a kausashe.
"Allah ya qara sauqi, insha Allah zata samu sauqi, dan bata da haqqin kowa a kanta, hasali ma zuciyarta fara ce, taimakon mutane shine aikinta, kuma Allah yayi alk'awarin ba zai kunyartar da mai irin wannan hali ba."
Yatsa yasa ya share qwallar dake idonshi yana ci gaba da cewa "baiwar Allah, wallahi da inada maganin cutarta dana batashi, da ace kuma nasan inda zan samo mata maganin da zanje na samo mata koda kuwa zansha wahala ne, sai kash muna ji muna gani yarinyar kirki tana wahala babu yanda muka iya, alhalin ita bata jurar ganin talaka a cikin wani hali."
Cikin sanyin jiki Umar Faruk yace " sai dai muyi hak'uri kawai, Allahn daya d'ora mata shi zai yaye mata insha Allah."
Kallon Umar Faruk Bala yayi yace "shin kasan wacece Hajia Khairat a wajena, shin kasan taimakon da tayi mana a rayuwa? nasan zaka sani tunda matarka ce."
Katseshi Umar Faruk yayi da "a'a wallahi Baba, ko sau d'aya Khairat bata tab'a fad'a min wani abu daya danganceta ba."
Murmushi Bala yayi yace "kaji yar arzik'i, to Hajia Khairat da kake gani a yanzu haka nida iyalina muna rayuwa ne da taimakon da tayi mana, *wasu shekaru da suka gabata* na kasance mai munanan halaye, ta sanadiyar haka na rasa komai nawa saboda almubazzaranci, a lokacin da muka fara rasa abinda zamu ci nida iyalina sai hankalina ya sake tashi, a hankali sai rayuwa taci gaba da garani yanda ya kamata, nasan kuma hakan nada alaqa da cin amanar da nayiwa abokina wato Hamza, wata rana mun tashi gidan nan babu yara ma zasu saka
Showing 159001 words to 162000 words out of 186119 words
Murmushi tayi da bakinta kad'ai ya motsa kafin tace "ta fad'a min komai a waya duk abinda ya shiga tsakaninki da 'yarsa, na yarda zan taimakeki ne a zahiri saboda kin samemu tsakiya da shirye shiryen zab'e, kuma akwai wani aiki da mai neman kujerar Mani Bukar ya biyani kud'ad'e danna kai Mani Bukar qasa kamar yanda ina d'aya daga cikin wanda suka sakashi yayi sama, dan haka karki damu zuwa gobe zan gama shirya komai, kuma zakisha mamakin abinda na shirya, tabbas Khairat zata ji ba dad'i itama."
Da farin ciki tanti tace "na gode sosai Hajia da wannan taimakon, kuma insha Allah Hajia za kiji babban biya."
D'an b'ata rai matar tayi ta kalli yar fara tace "yar fara ina fatan kin fad'a mata ba'a min wasa da maganar data shafi kud'i ko?"
"Ai karki damu Hajia, na fad'a mata komai a game dake, ba za'a tab'a samun matsala ba." cewar 'yar fara.
"To yayi kyau, zaku iya tafiya." tana fad'a ta tashita shiga wani d'aki ta barsu nan, tashi sukayi Mama na yaba matar tana ji inama ta zama ita, har saida 'yar fara tace "to ai matsalar kin tsufa ne, amma badan haka ba ai zaki iya hawa network kema."
Hararanta tayi tace "karki cimin mutunci mana, me kika d'aukeni?"
"Ba komai." cewar 'yar fara.
*Mamienmu amin afuwa*ππββ
****************
Umar Faruk na zaune daf da Khairat yana bata magani zazzab'i tana sha, Mammie na gefen Khairat sai Mamie da Papa dake d'aya kujerar suna kallonsu, duk da dare yayi yana so yaje gida amma ganin jikin nata ba sauqi yasa ya kasa tafiya, tana shan maganin ta koma ta kwanta tana sake dunqulewa cikin bargon da Mamie ta d'auko mata, a hankali take lumshe ido alamar tana so tayi bacci, a haka har baccin yayi gaba da ita, tashi Umar Faruk yayi ya musu sallama zai fita, da k'arfi sukaga Khairat ta fad'o daga kan kujerar, a zabure ta farka itama tana kallon mutanen wajen, da sauri Umar Faruk ya qarasa wajenta ya kamata ta tashi ta koma ta zauna, fuska ba annuri yace "kalleni nan."
Kallonshi tayi ya sake had'e rai yace "wallahi ku daina wahalar da ita haka in kuna son zaman lafiya, kunga ina binku a hankaline saboda ina so mu rabu lafiya daku, tab'ata da kuke shine kuskuren da kukeyi."
Qwafa yayi ya mik'e zai nufi hanyar fita Papa yace "Umar Faruk, me yake damunta ne?"
Juyowa yayi yace "karku damu Papa, komai zaiyi daidai na baku tabbacin hakan."
Yana fad'a ya juya ya kalli Khairat, hararan sama da qasa ta masa taja dogon tsaki, fita ranshi a b'ace ba tare daya damu da abinda tayi ba, sam yau ma basuyi bacci ba ko kad'an, daga wannan ciwo sai waccen a haka suka kwana.
**************
Tunda Zuby taga shiru bai dawo ba sai ranta ya fara b'aci ta fara tunanin abinda Mama ta fad'a mata, ta kuma yarda tabbas wata rana zaice zai tare can tare da Khairat indai har ana haka tun yanzu, ganin Ruk'ayya ta kawo abincinshi ta aje kawai saita tashi ta d'auko maganin data jefa qasan gado ta duba wanda zata saka a abinci ta mayar da sauran, tsautsayi ya kawo Umar Faruk a lokacin da take zuba maganin a abinci, komawa yayi da baya ya saita kansa tare da had'e b'acin ranshi sannan yayi sallama ya shiga, ko kad'an bai nuna mata wani abu ba ya share kawai, wanka yayi sannan ya zauna cin abinci, bismillah yayi yana shu'umin murmushi ya kai lomar bakinshi, saida ya cinye wanda ta zuba mishi duka saboda yunwar da yake ji, dan duk lokacin da zai kai abu bakinshi saiya tuna Khairat, hakan yasa shima bai cika ci yana qoshi ba kwanan nan, da farin ciki Zuby ta kwana sab'anin Umar Faruk daya kwana yana kallon fuskarta, tsanarta na sake mamayeshi, daga qarshe kuma tunanin Khairat ya maye gurbin tunaninta dashi har gari ya waye.
Tana zaune harya gama shirinshi zai fita, juyowa yayi ya kalleta yace "ni zan wuce, babu komai?"
"Ba komai."
Hannu ya mik'a mata cike da qoqarin taushe qiyayyar da take mata yace "ina so zan gaisa da yarona."
Hannun ta mik' masa ta taso shi kuma ya bi cikinta da kallo wanda ya turo riga ya fito, shafar cikin yayi yace "nasan ka tashi lafiya, haka Papanka da mamanka, kuma nasan zaka kula min da kanka, ni zan tafi."
Sunkuyawa yayi ya sumbaci cikin sannan ya fice, saida ya gaishe da iyayensu sannan ya wuce gidansu Khairat, da shigarshi sallama kad'ai yayi ya samu duka mutan gidan tsaye akan Khairat dake ta birgima a qasa tana kuka tana cewar zuciyarta zata fashe zafi take mata, qarasowa yayi dan babu ma wanda ya amsa sallamar tashi, tsaye yayi shima yana kallonta idonta rufe sai hawaye dake fitowa, matsowa yayi da nufin zama kusa da ita kawai saita d'ago ta bulalo amai, duk da ta b'ata mishi jiki bai damu ba saida ya zauna ya fara taimaka mata da addu'a, a hankali a hankali ta fara samun nutsuwa da sauqi, bayan wani lokaci kuma sai bacci yayi gaba da ita, Mamie ce tace "Allah ka dubi yarinyar nan ka sassauta mata abinda yake damunta, Allah ka yafe mata kurakurenta badan mu ba." ta qarashe da fashewa da kuka.
Kallonta Umar Faruk yayi yace "dan Allah kuyi hak'uri ku daina kukan nan, insha Allah zata samu lafiya."
Cikin kuka Mamie tace "wallahi tausayi take bani, kwananta biyu yau a gidan nan amma har yanzu baccin da tayi baifi na awa biyu ba idan aka had'a, ace daga wannan ciwo sai waccen, da anji sauqin wannan kuma sai wani da danno kai, wallahi nidai ban tab'a ganin laulayi irin nata ba."
Gyara mata kwanciya yayi ya mik'e yace "ku kula da ita zanje na samo ganyen magarya, insha Allah zata samu lafiya da yardar Allah."
Yana fad'a ya fice daga gidan, zaune sukayi suna kallonta kafin ta farka kuma, ba dadewa kuwa ta farka tana dafe kai, Mamie ce ta kawo mata abinci taci amma sam tak'i ci, saida Papa ya lallab'ata ya rarrasheta kad'ai ta samu taci kad'an, tana gama ci ta tashi da gudu taje k'ofar shigowa falon ta fara amaye abinda taci, tana haka Umar Faruk ya shigo gidan, tsaye yayi yana kallonta da tausayawa saida ta gama ya rik'ota suka shigo, kallonta yake sosai duk da cikinta ya girmema na Zuby amma ko alamun fitowa baiyi ba, zaunar da ita yayi sannan ya bawa Mamie ledar hannunshi yace "ku jiqa wannan ku ajeshi a wuri mai kyau, zan nemeshi nan da kwana bakwai insha Allah."
"To shikenan." cewar Mamie tana karb'a.
****************
Misalin *09:30* na dare duk suna zaune a falon, Khairat na kwance akan cinyar Umar Faruk da yake so ya tashi ya tafi ta rik'eshi, hira suke sama sama wani jami'i ya shigo ba tare da sallama ba ya sarawa Papa alamar girmamawa yana fad'in,
"Yallab'ai, wata mata ce a qofar gida tace tana son ganinka, na tambayeta abinda ya kawota amma tace ita kai take son gani."
Shiru Papa ya d'anyi kafin yace "ok ba damuwa, kace ta shigo."
Juyawa jami'in yayi bayan ya amsa da "an gama yallab'ai."
Harsun fara tab'a hira sukaji ance "salam."
Kowa kallon qofar yayi dan ganin mai sallamar, zunbur Papa ya mik'e da tsananin mamaki yace " *Odette*, kece gidana, meya kawoki nan, kin manta rabuwarmu ne?"
Kowa dai da mamaki yake kallonsu harda Khairat da jikinta ya d'anyi dama, juyawa matar tayi ta kalli qofa tace " *Salim*, shigo mana."
Wani matashin saurayine da bazai wuce shekara sha shida ba zuwa sha bakwai fari sol dashi kamar matar, d'an gaye ne sosai irin matasa ne masu aji, turo yaron tayi gaba ya nufi Papa tace "kaje, yau dai na sauke wannan nauyi, kuma na huta da qorafinka kullum, kuma yanzu asirinmu zai rufu."
Daf da Papa yaron ya tsaya yana murmushi ba b'ata lokaci ya rumgume Papa yana fad'in "oh Babana, naji dad'in had'uwa da kai."
Papa daya kusa mtuwar tsaye da qyar ya raba jikinshi dana yaron yace "kai wace maganar banza ce wannan, waye uban naka?"
Hamshaqiyar matar ce tace "kunga na barku lafiya, saida safenku."
"Ke, wai miye haka, wanene wannan yaron?" cewar Papa.
Cike da yabqi da yanga tace "oh yi hak'uri fa, wannan ai shine *Salim* danka dana jima ina boye maka, amma kwanakin nan yana addabata waishi dole na had'ashi da mahaifinshi danya gaji da ganinka a tv kullum, nace yayi hak'uri amma sai yace zai fad'a a gidan jaridu da tv cewar shi d'in danka ne, shi yasa naga zaifi ayi komai asiri rufe ba tare da anyi tone tone ba, kasan zab'e ke tafe."
"Wannan ai maganar banza ce ma, kin sani na sani lafiya lau muka rabu dake, karki yarda kice zaki b'ullomin ta wannan hanyar, dan wallahi ba zakiji dad'i ba, kuma ki gaggauta fita min da wannan d'an iskan yaron kafin nasa a fitar min dashi."
Rai b'ace tace "a'a Mani, karka sake zagar min yaro wallahi, kuma idan kace baka yarda ba kai ka sani bana abu babu hujja, kamar yanda kasan bana qarya ko kuma cuta."
Jakarta ta bud'a ta ciro da takardu ta jefa mishi a qirji tace "wannan suna dauke da duk wasu bayanai tun daga lokacin dana d'auki cikin Salim har haihuwarshi, sannan akwai gwajin da asibiti sukayi na qwayoyin hallitunshi iri d'aya ne da naka, idan kuma baka yarda ba zaka iya sakawa a maka sabon gwaji."
Tana fad'a ta juya ta fita daga gidan, yaron kuma zaune yayi kusa da Mamie yana kallonta yace "bonsoir (ina wuni)."
Da sauri Mamie ta shige d'akinta tana hawaye, maida kallonshi yayi ga Khairat data tashi zaune tana kallon ikon Allah, da azama yaje wajenta ya zauna yana kallonta yace "wannan itace auntyna ko?"
Kafin ayi magana kuma ya kamo hannun Khairat yana maqalewa da nashi, badan rashin lafiya da matar nan ta gane kurenta cewar Khairat a zuciyarta, amma duk da haka cikin zafin rai ta d'aga hannu ta wanke yaron da mari ta nunashi tace "karka sake tab'ani dan kai ba d'an uwana bane."
Dafe kunci yayi yana murmushi yace "ke kuma haka kike tarban bak'inku, ba komai ke yayata ce zaki iya yimin komai."
Tashi tayi danta bar wajen amma saita zube saboda qafafunta da suka rik'e, Umar Faruk ne ya tashi ya d'auketa ya kaita d'akinta ya kwantar da ita, addu'a ya mata ya rufeta sannan ya fito ya bar d'akin dan tak'i kallonshi ma, yasan badan rashin lafiya ba da gidan nan ya hargitse yau.
Papa ya samu tsaye yana duba takardun nan har yanzu, indai har zaiyi anfani da abinda ya gani a takardun to tabbas Salim d'ansa ne, amma ba zai yarda ba dan haka Umar Faruk na musu sallama ya fita ya kira docteur d'inshi yace gobe zaizo, d'akin Mamie ya shiga ya samu tana kuka, zaune yayi ya fara magana da "Na'ima, dan Allah..."
D'aga mishi hannu tayi ta tashi tana share hawayenta tace "kar kaba kanka wahala wajen rarrashina, nima ba hushi nayi da kai ba, kawai dai banji dad'i bane saboda ban tab'a tunanin ka haihu a waje ba, amma inhar ina da hankali aibai kamata nayi hushi da haka ba saboda nasan komai a game da rayuwarka ta baya."
"Na gode da kika fahimceni Na'ima, amma wallahi nima ban tab'a sanin inada wannan yaron ba, kuma har yanzu ma ban yarda d'ana bane harsai Allah ya tashemu gobe munje asibiti an sake mishi wani gwajin."
*Wata sabuwa*
*Barka da Ranar Hausa ta duniya, Allah ya d'aukaka matan hausawa.*
29/08/2019 Γ 14:33 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Haka kawai sai kaga Allah ya had'a zuqatan bayinsa, ba gari d'aya ba bare unguwa, amma haka Allah ya had'amu har muke qaunar junanmu, Allah ubangiji ya baki lafiya my Meerahgee *(Maryam Gital)*, Allah yasa zakkar jikina kuma sanadin yake zunubanki, your Meerahgee again._ππ
_Dan Allah ki daina wahalar da zuciyata ki fito ki naganki ko naji sanyi, Allah ya qara miki lafiya dawamammiya, *My BK* i love you_.
_Bismmilahir-rahman-rahim_
*Idan nayi magana dubannin rayuka zasu b'ace, dan haka nayi shiru.*π
5β£9β£
Ba'a b'ata lokaci ba Papa ya d'auki Salim suka je aka sake mishi gwaji, ba yanda ya iya tunda gwajin ya bayyana d'anshi ne na cikinshi, daga nan kuma sai yaji yaron ya shiga ranshi, ashe shima Allah ya bashi namiji.
*Hummmmmmmm*
Koda suka zo gida Papa yasa aka gyara mishi d'aya daga cikin d'akuna, ana cikin haka ya had'a yaron tare da masu gadinshi suka je babban boutique aka siyo mishi kaya masu kyau da tsada, sabuwar rayuwa kenan wa Salim.
*Wacece Odette???*
Odette shahararriya kuma 'yar duniya ta gidan gaba, sun jima tare da Mani Bukar saboda gogewarta da kuma iya bariki da soyayya, tun kafin ya fara siyasa suke tare da ita, kuma tana d'aya daga cikin wanda suka bashi gudummuwa sosai harya hau kujerar da yake yanzun, a waccen lokacin zai iya cewa bayan mahaifiyar Khairat ita macen da yake so, amma a lokacin da shiriya tazo mishi saiya fad'a mata ya shiryu kuma itama ta tuba ga Allah, sam tace shi dai yaje amma ita tana nan har yanzu, saida mata babbar sallama sannan suka rabu cikin mutunci, amma shine yau tazo mishi da maganar yaro d'an shekara sha bakwai, wanda baisan dashi ba sai yanzu.
****************
Kamar yanda Umar Faruk ya kai Zuby Γ©cole, haka ma yanzu duk da abinda ke gabanshi ajeshi yayi saboda lokacin tashinsu yayi, koda yaje ta taso daga inda take zaune harta shigo ta zauna yana kallon cikin dake maqale jikinta, saida ta rufe motar sannan ta kalleshi tace "sannu."
Bata jira amsarshi ba ta bud'a jakarta ta fiddo ledar awarar data siya ta bud'e, ba tare da kama hannun yaro ba ta fara gaigayar awarar ko kallonshi ba tayi, shi kuma kallonta yake da gani kasan yunwa take ji sosai, yanda take cin awarar sai yaji ta birgeshi yana ji kuma inama Khairat itama haka take cin komai, murmushi kawai yake mata har suka d'auki wata hanyar ta daban, sai lokacin ta kalleshi tace "yah ina zamu je kuma nan?"
Ba tare daya kalleta ba yace "zanje na siyar daku ne, ko baki san mace mai ciki tsadane da ita ba?"
"Hum, aiba zaka fara ba, dan nasan ko ka siyar dani ba zaka yarda ka siyar da magajinka ba."
Dariya yayi yace "gaskiyarki kam, amma taya zan siyar da uwar bayan itace mai haifawar? abune da ba zai yiwu ba ai a wajen Umar Faruk."
Kallonshi tayi ta cika baki da awara tace "kana sona ne har yanzu?"
Kallon qwayar idonta yayi amma ya kasa cewa komai, maida kallonshi yayi ga tuqinsa ita kuma tace "basai ka fad'a ba nasan baka sona."
Kallonta yayi yace "Zuby, kina so na b'ata lokacina wajen fad'a miki abinda kika sani, ko kuma kina sone dole saina ce miki ina qaunarki fiye da tunaninki, nasan kema kinsan da haka."
Ganin dai suna shiga wani wajen yasa tace "wai ina zamu ne?"
Kashe mata ido yayi hankali nutsu yace "ki yarda dani mana, ba zan cutar dake ba."
K'ofar wani matashin gida suka paka, shine ya fara fita kafin ta fito itama, goge maiqon dake hannunta tayi a hijabinta sannan tabi bayanshi suka shiga ciki, babu hayaniya gidan sosai hakan yasa sai wata dattijuwar mata ta musu iso ciki, suna shiga falon Zuby ta tsaya cak saboda ganin babanta Bala zaune da alama bashi da lafiya, saida Umar Faruk ya d'an ja hijabinta sannan suka samu wuri suka zauna, gaisawa sosai Umar Faruk yayi da mutanen Zuby na kallonshi dan yanda taji suna gaisawa alama ce ta yana zuwa gidan, kallon da Umar Faruk ya mata yasa ta kalli Bala tace "ina kwana?"
"Ina kwana yanzu?" cewar Umar Faruk.
"Ina wuni?" ta fad'a tana cika baki.
"Lafiya lau Zubeida, ya makarantar?"
"Lafiya lau."
D'aya daga cikin matance tace "wannan matarka ce?"
"Eh, amaryar ba." cewar Umar Faruk cike da kunya.
Bala ne ya d'ora da "kuma 'yata ba."
Da mamaki matan suka kalleshi yayin da Zuby ta kalleshi, babbarce tace " 'yarka kuma Alhaji, taya ta zama 'yarka kuma?"
"Eh, haka nace, 'yata ce kuma ta cikina, zaku iya bamu wuri." ya fad'a a kausashe.
Tashi sukayi suna kallon Zuby, Bala kuma kallon Umar Faruk yayi yace "ya jikin Hajia Khairat?"
Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace "jiki da dama."
"Allah ya qara sauqi, insha Allah zata samu sauqi, dan bata da haqqin kowa a kanta, hasali ma zuciyarta fara ce, taimakon mutane shine aikinta, kuma Allah yayi alk'awarin ba zai kunyartar da mai irin wannan hali ba."
Yatsa yasa ya share qwallar dake idonshi yana ci gaba da cewa "baiwar Allah, wallahi da inada maganin cutarta dana batashi, da ace kuma nasan inda zan samo mata maganin da zanje na samo mata koda kuwa zansha wahala ne, sai kash muna ji muna gani yarinyar kirki tana wahala babu yanda muka iya, alhalin ita bata jurar ganin talaka a cikin wani hali."
Cikin sanyin jiki Umar Faruk yace " sai dai muyi hak'uri kawai, Allahn daya d'ora mata shi zai yaye mata insha Allah."
Kallon Umar Faruk Bala yayi yace "shin kasan wacece Hajia Khairat a wajena, shin kasan taimakon da tayi mana a rayuwa? nasan zaka sani tunda matarka ce."
Katseshi Umar Faruk yayi da "a'a wallahi Baba, ko sau d'aya Khairat bata tab'a fad'a min wani abu daya danganceta ba."
Murmushi Bala yayi yace "kaji yar arzik'i, to Hajia Khairat da kake gani a yanzu haka nida iyalina muna rayuwa ne da taimakon da tayi mana, *wasu shekaru da suka gabata* na kasance mai munanan halaye, ta sanadiyar haka na rasa komai nawa saboda almubazzaranci, a lokacin da muka fara rasa abinda zamu ci nida iyalina sai hankalina ya sake tashi, a hankali sai rayuwa taci gaba da garani yanda ya kamata, nasan kuma hakan nada alaqa da cin amanar da nayiwa abokina wato Hamza, wata rana mun tashi gidan nan babu yara ma zasu saka
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54 Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63