Zuby Allah yasa karki sake b'ata ran mazaje._
29/08/2019 Γ  14:33 - Meerahgee❀: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*JIHADI*
_Umar faruk_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


_Bismmilahir-rahman-rahim_


6⃣0⃣


"Halan yau mahaukaciyar ta keta maka kaya, dan nasan dai ba fyad'e zaka mata ba, kuma ma ko hakane ai ba kaine farau ba bare ta tashi hankalinta, hasali ma kai *jihadi* kayi."

Da wani irin matsanancin yanayin dashi kanshi baisan ya shiga ba yake kallonta, kasa cire belt d'in yayi ya matso kusanta yace "Zubeida, anya kina da hankali kuwa, kinsan me kika fad'a, Khairat d'ince kike kira da mahaukaciya? to bata haukace ba kamar yanda kuka shirya, kuma da yardar Allah duk abinda kuka shirya kanku zai dinga komawa, tunda har yanzu kun kasa gane itace gaba daku kuma ta muku nisan daba zaku tab'a kamata ba, to bara yau na fad'a miki abinda kullum nake dannar zuciyata da karta fad'a miki haka."

Sake matsowa yayi kusanta yace "kina cewa nayi jihadi ne na auri Khairat, to ki sani Zubeida kema a halin yanzu *jihadi* nake naci gaba da zama dake, kiyi tunani akan abinda na fad'a miki dan babu qarya a maganata, kuma ki sani akwai abubuwa da dama dana sani a game daku Zubeida amma na shanye, badan komai ba sai dan nasan Allah ma baya kama bayinsa da laifi d'aya tak, zaki ga bawa na laifi iya laifi amma sai Allah ya d'aga masa qafa, wala'Allah ya gyara a gaba ko kuma a mishi kamun kazar kuku, to akan me ni ba zan iya yi muku uzuri ba, amma kwata kwata kun kasa gane haka, to wallahi ba zan qara shiru ba, *Khairat ta fiki komai Zubeida, ta fiki zuciya mai kyau, ta fiki halaye masu kyau, ta fiki girma da matsayi ba'a wajena ba har a wajen mutane, kuma da yardar Allah babu abinda zai sake samunta ta sanadiyar jahilai irinku.*"

"Zubeida, ina son Khairat, ina mata son da ban tab'a ma kowa irinshi ba, kuma wallahi zamu zauna da ita muyi rayuwa a tare, ki sani wannan ne na qarshe da zan sake miki uzuri akan banzan quruciya da tab'argazarki, nasan dole zaki ji zafin kalamaina, amma Allah ma yaga zuciyata na kasa jura ne, kuma nayi iya qoqarina na b'oye duk abinda yake damuna."

A fusace ya fice daga d'akin ya nufi d'akin Khairat kamar yanda yake yi duk lokacin da ranshi ya b'ace, saida ya kai tsakiyar gidan ya tuna ko riga babu a jikinshi, bai damu ba haka ya ciro makullanshi ya bud'e d'akin ya shiga ciki, kwance yayi akan gado ya rufe ido yana tuno 'yar rayuwar da sukayi da Khairat da farin cikin daya samu a tare da ita, ya jima d'akin kafin ya shiga douche yayi wanka ya fito ya shirya, fita yayi baibi takan kowa ba bare wata Zuby.


Yana kan hanyarshi ta zuwa ma'aikatarshi yaga motar Salim a gabanshi, wani banzan kallo yama mota kafin ya fara binshi a baya zuciyarshi na raya mishi abubuwa da dama, yana binshi har saida ya shiga wata unguwa da babu mutane sosai, qofar gidan da yayi parking yasa Umar Faruk fitowa shima daga mota, yana kallo ya shiga cikin gidan sai dai bai iya binshi ba saboda yaga irin gidan nanne da an bud'e qofa za'a san wanda ya shigo, yana nan tsaye harya fito tare da mahaifiyarshi Odette, tare suka shiga mota suka d'auki hanya kuma, binsu yayi har suka sauka unguwarsu Khairat amma nesa da gidansu a gidan wani d'an siyasar mai neman kujerar Papa, murmushi yayi ya d'auki glass d'inshi mai baqaqen ido yasa, sake kallon qofar gidan yayi yace,

"Yanzu ainihin maganar zata fito fili, yanzu ne zanyi *jihadin* gaskiya, dan dole saina dawo da farin cikin masoyiyata da iyayenta."

Wani murmushin ya sakeyi saboda ganin Salim ya fito ya shiga mota yayi gaba, cewa yayi "da sannu kai zaka warware min komai."

Binshi yayi ya kira wayar Aliyu, yana d'auka ya fad'a mishi inda yake yace ya sameshi, ba b'ata lokaci Aliyu ya sameshi saboda yana da abin hawa, sauka yayi daga motanshi ya shiga motar Umar Faruk, kallonshi yayi yace "yah Umar lafiya kace na sameka nan?"

Nuna mishi motar Salim yayi yace "kaga wannan motar?"

"Eh na gani."

Nuna mishi Salim yayi dake cin abinci a restaurant d'in yace "kaga mai ita can, ina so ne daga yanzu ka fara bibiyarshi, kuma ina so na dinga sanin duk inda ya kasance."

"Shikenan yah Umar, insha Allah zanyi yanda kace."

Nan ya bar Aliyu shi kuma ya koma unguwar da Odette take, kasancewar yana da kati hakan yasa ya wanke mutanen unguwar ta hanyar tambayarsu wacece Odette, cikin tsoro suke fad'a mishi duk abinda suka sani a kanta, daga nan ma komawa yayi gidan *Alhaji Sani Saley* ya kasa ya tsare har saida yaga fitowar Odette.

Ganin a qasa take tafiya yasa ya d'an jira yaga inda zatayi, yana kallonta kuma sai yaga mota biyu sun fito daga cikin gidan, mai gadi ya gani ya rufe qofar ya zauna qofar gidan akan kujera, saida yaga b'acewarsu sannan ya fita daga motar ya nufi wajen mai gadin, sallama ya mishi suka gaisa kafin ya kalli hanyar da Odette tabi yace,

"Abokina dan Allah tambaya nake, wannan matar data fita ba Odette bace kuwa?"

Ya rik'e sunan ne tun ranar da Papa ya fad'a, kasancewar mai gadin mai hankaline yasa yace "itace, lafiya, ka santa ne?"

Ganin bazai bada matsala ba yasa Umar Faruk gyara tsayuwa yace "sosai ma na santa, tana zuwa harnan kenan?"

"Eh, tana zuwa nan, ai mutuniyar mai gida ce sosai."

"Ok na gane, na gode sosai, amma naga mai gidan ya fita, shin kasan inda yayi?"

"A'a, ban sani ba gaskiya."

"Shikenan na gode."

Hannu ya bashi kafin ya wuce, wani abokinshi ya kira mai sunan *RB* ya nemi sani akan *SS* wato Sani Saley.......


*Yanzu fa Umar Faruk zai fara nashi wasan*


Kwana ma wuya yakewa Umar Faruk yanzu sobada binciken da yasa gaba, kuma cikin ikon ubangiji ya tara hujjoji masu yawan gaske akan Sani Saley da Odette, dan ko rintsawa bayayi sai bincike da tambaya, ya samu masaniya tun daga yanda Odette ta fara harkarta har zuwa yanzu, kuma komai rubutashi yake yana copie d'inshi a wayarshi.

*Yau* ma kamar kullum tafe yake cikin sabuwar motar daya siya izuwa wani gida da wajen bincikenshi a fad'a mishi zai samu masaniya akan duk abinda suke shiryawa game da maganar Salim, yana zuwa daidai kwatancen ya fito daga mota ya nufi gidan, a hankali ya tura qofar sai yajita a rufe, tsaye yayi yana d'an kalle kalle ya hango wani yaro, qarasawa yayi yana fad'in "sannu yan samari, dan Allah masu gidan nan basa nan ne?"

Kallonshi yaron yayi yace "ai duka mazane ba mata."

Da mamaki ya kalli yaron amma saiya share, shafa kan yaron yayi ba tare da yayi magana ba ya koma qofar gidan, d'aga kai yayi ya kalli katangar yaga bata da tsayi sosai, yar dariya yayi a ranshi ya tuna ranar daya ma su Musa kutse a cikin gidansu, kallon unguwar yayi yaga ba hayaniya sosai, tsalle yayi ya rik'e katangar ya haura ciki, yana direwa ya tsaya yana kallon gidan, idonshi ne ya sauka kan takalmin dake qofar d'akin, da sauri ya qarasa jikin bishiya ya b'uya yana jiyo tashin muryoyi, cikin sand'a da dubara ya dinga takawa har ya kai bakin window ya leqa, abinda ya gani shi yasa shi saurin yin qasa yana waro ido waje da tsananin mamaki.....

Da d'an k'arfi ya furta "su Musa, taya hakan zata faru, mutane dake kurkuku me zai kawosu nan, ko dai anyi bellynsu ne?"


Sake leqawa yayi ya tabbatar sune dan haka kawai ya qarasa qofar ya bud'e sakatar qofar a hankali ya fita, da hanzari ya bar unguwar yana tunanin abinda ya gani, Khairat ya kira wacce ke zaune gaban Mamie ta aje mata farfesun kaji tana ci😭(ina ci my Hajiata), koda ta d'auka yace ta taimaka mishi da lambar wannan gendarme d'in daya qwamushe su Mama, yarda da kanta yasa ba tayi tunanin komai ba ta aika mishi da lambar.


Cikin sa'a ya samu lambar Abdul waid, koda ya fad'a mishi wanene shi ya samu tarba ta musamman, tambayarshi ya fara yi ko yasan wanda sukawa Khairat fyad'e? amsar dai itace "eh, lokacin dana dawo nan da aiki ake nuna min su." nan ya tambaye ko zai iya sanin shekara nawa aka yankewa su Musa, nanma fad'a mishi yayi yaji ko shekara basuyi ba a cikin shekarun da aka d'iba musu, d'orawa yayi da "amma kuma taya za'a sakesu bayan basu cika wa'adinsu ba, taya za ayi irin haka?"

Nan Abdul waid ya fad'a mishi basu da laifi a ciki daga samane aka yanke hukuncin a sakesu saboda wani babbane yazo bellynsu, tambayarshi yayi "wa yayi bellynsu?"

"Sani Saley ne." cewar Abdul waid.

Suna gama waya yana ci gaba da tafiya kuma Aliyu ya kirashi, yana dauka nanma ya fad'a mishi yau ma gasu a gidan nan dake unguwar *Lazare*, da mamakin abinda ke kai Salim gidan Umar Faruk yace " kaci gaba da saka masa ido, an jima zaka kawoni gidan."


****************

Tafe suke a mota shi da Aliyu suna yar hira har suka isa wannan gidan, saida suka fito Aliyu ya nuna mishi sannan ya shiga gidan cikin baqaqen kaya, sallama yayi matar dake zaune ita kad'ai ta amsa mishi, sai dai a tsorace take sosai musamman da Umar Faruk yace "sannu Mama, sunana Faruk, kuma ni jami'in bincikene na farin kaya, nazo ne zan miki wasu tambayoyi, fatan zaki bani hadin kai ba saita kaimu ga tafiya dake ba offishinmu."

Cikin saurin kuka matar ta fashe da kuka tace "na shiga uku ni *Salmu*, dama nasan wata rana sai Salim ya jawo min magana, yallab'ai wallahi zan fad'a maka gaskiya, ba saika tafi dani ba."

Kujera Umar Faruk ya janyo ya zauna tare da fad'in "bismillah." a zuciyarshi kuma istigfari yake akan qaryar da yayi yanzun...


_Hummmm, ranar fa ta kusa zuwa._
29/08/2019 Γ  14:33 - Meerahgee❀: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*JIHADI*
_Umar faruk_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›

_My sweet and lovely Dotana *(Khadija Journaliste)*, ina tayaki murnar fara wannan novel mai sunan *Rayuwata ce*, a gaskiya na jinjina miki sosai musamman yanda kika d'auko yanda ya kamata iyaye su tarbiyanci yaransu, Allah ya baki ladar fad'akarwar daki kayi niyya._


_Bismmilahir-rahman-rahim_


6⃣1⃣


"Ina jinki Mama." ya fad'a yana fito da qaramin littafin ajiye muhimman bayanai a aljihunshi da alqalami.


"Ina so nasan meye tsakaninki da yaron nan Salim da yake yawan zuwa gidan nan?"

Cikin muryar kuka tace "Salim, Salim dai d'ana ne, ni na haifeshi, kuma maraya ne mahaifinshi ya rasu, matsalar Salim rashin jin maganata, a lokacin da yazo min da maganar zaije a matsayin d'an wani babban mutum saida na hanashi, amma sam yaron nan yak'i jin maganata, amma bansan komai ba wallahi."

Shiru tayi haka ma Umar Faruk yana rubutun basaja kamar gaske, jin shiru yasa ta marairaice tace "dan Allah yallabai ka taimakeni kamar yanda Allah ya taimakeka, ka rufa min asiri karka kama yaron nan dan Allah, wallahi shi kad'ai gareni kuma shima ni kad'ai gareshi, idan ka taimaka mana wallahi zanja mishi kunne, kai har garin ma zamu bari na mayar dashi wajen dangin mahaifinshi, dan Allah ka taimaka."

Kallonta Umar Faruk yayi yace "Mama, kinsan girman laifin da d'anki ya aikata kuwa? ya yarda ya zama d'an wanda baiji ba bai gani ba, hakan ya ruguza rayuwar wannan bawan Allah, ya kuma dagula farin cikinshi dana iyalinshi, taya kike tunanin zai samu sassauci?"

"Dan Allah ka taimaka ka min rai, wallahi ba zai sake ba, kuma talauci na daga cikin abinda yasashi aika hakan."

Saboda yanda take kuka yasa yace "shikenan Mama daina kukan, insha Allah zamu duba al'amarin muga yanda za ayi."

"Na gode yaro, na gode sosai, Allah ya saka maka da alkairinsa."

Kiran daya shigo wayarshi ne yasa yaja "ameennn." d'in, fito da wayar yayi ganin lambar babanshi na uku ne ya kira (Bala) yasa ya tashi tsaye tare da d'aukar kiran, abun mamaki muryar macece tace "Hello Umar Faruk ne?"

"Eh nine."

"Dan Allah kayi sauri kazo, Alhaji ne yace a kiraka kazo."

"Ince dai lafiya ko?"

"Ba lafiya, jikinshi ne yayi qamari, kuma ruwan addu'a daka bayar ma ana bashi sam yau yak'i ya karb'a."

"To shikenan, gani nan zuwa."

Yana fad'a ya kashe wayar ya fita ya manta ma da inda yake, da azama ya shiga motar yaja suka d'auki hanya, Khairat ya kira tana d'auka yace "baby, Salim yana gidane?"

"Salim kuma, lafiya?" ta tambaya da mamaki.

"Lafiya lau, ki duba min dan Allah.

Mamie ta kalla dake gefenta ta tambayeta, "yana d'akinshi har yanzu." cewar Mamie.

Maida mishi tayi da "yana d'akinshi bai fita ba, lafiya dai ko?"

"Lafiya lau, dan Allah zaki iya samo min lambarshi?"

"Baby, lafiya, me yake faruwa ne?"

"Babyyyy, kiyi abinda nake fad'a miki mana."

"To naji." Mamie ta sake kalla tace "kina da lambarshi wai?"

"A'a, me zanyi da lambarshi ni kam, sai dai ki tambayi mahaifinki."

"Babu mai lambarshi a gidan nan sai wada yake zaune dominshi, bara na tambayar maka."

"Yawwa 'yar aljannata, ina jiranki."

Cikin mintuna qalilan ta tura mishi lambar bayan ta karb'a daga wajen Papa, yana ganin lambar yasa Aliyu ya d'auketa a wayarshi sannan yace "kasan dubara da za kayi mishi irin taku ta matasa da za tasa ya kai kanshi wannan sabon filin dana siya wanda ke *Yantala*."

Akan titi ya tsaya ya saukeshi Aliyu na mamaki da tunanin yanda zaiyi ya kaishi wajen, da qyar ya samu dubara ya kira lambar, ba jimawa ya d'aga Aliyu ne yace "yane Baabaa, ka fita ko kana gida?"

Fad'uwa kawai gabanshi keyi, cike da qasaita Salim yace "waye kai kuma?"

Cikin murd'awar 'yan ciki Aliyu ya dake yace "kana nufin baka d'auki muryata ba kome?"

Cikin d'an sakin fuska Salim yace " *Rabilou* kaine?"

Cike da dakiya Aliyu ya nuna mishi shima matashin zamani ne yace "shege baabaa, nine mana, dan Allah kazo ka d'aukeni ina nan yantala."

Cike da isa Salim yace "kai ina motar taka take, mema ya kaika can unguwar?"

"Motarce ta bani matsala, yanzu haka ma da wayar makaniken ne na kiraka tawa ba caji, abinda ya kawoni kuma idan kazo na fad'a maka."

A gadarance yace "Ina kan hanyar kita daga gida, ka jirani kawai."

"Sai kazo." ya fad'a ya kashe wayar, wata ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, dan ba qaramin sauqi bane cika aikin Umar Faruk, da azama ya tari taxi ta kaishi can kafin shi ya isa wajen.


***************


Umar Faruk na barin nan gida ya wuce dan amsar wasu ruwan addu'a a wajen Baba, da karsashi ya shiga gidan da fad'in "assssss..."

Sallamar tashi ce ta maqale a maqoshi saboda ganin hasken fila a kewayen Khairat alamar akwai mutum a wajen, a hankali ya sulala yana takawa danshi gani yake Khairat ce zata masa bazata, leqawa yayi ta katanga sai yaga Zuby ce ke barbad'e a qofar d'akin, mamakinshi bai yawaita ba saboda ba yaune farkon ganinshi ba, dan haka ya qura mata ido yana kallo harta gama zata juyo yayi saurin cewa,

"Sannu da aiki 'yar gidan d'an me ganye."

πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚

Wani irin fad'uwa ne gabanta yayi had'e da kad'awar 'yan cikinta, tsabar tsoro ne yasa ta jefar da ledar maganin da wayar hannunta, kasa kallonshi tayi tunda tasan ko waye, a hankali ya zagayo yana kallonta harya sunkuya ya d'auki kayan data zubar, janyo hannunta yayi ya bata kayan yana ci gaba da kallon fuskarta, ganin dai ta kasa cewa komai yasa yace,

"Wannan itace damarki ta qarshe Zubeida, da ace a abinci nane na samu kina zubawa kamar yanda na tab'a gani, to da zan iya yafe miki kuma na zuba miki ido, danni yanzu ban damu da rayuwata ba kamar yanda na damu data wasu, wasun kuma ba kowa bane face iyalina, ba zan iya miki uzuri ba Zubeida dan kina qoqarin cutar da wacce tafi rayuwata mahimmanci ce, akanta kuma sai inda k'arfina ya qare, Zubeida ki gafarceni, amma dole zan d'auki matakin da nasan ba zai miki dad'i ba, na d'aga miki na miki uzuri duk saboda tunanin zaki shiryu wata rana, amma matsalar tana ga mahaifiyarki ne, ni kuma ban isa na rabaki da ita ba, saboda uwa uwa ce, dan haka zan saukewa kaina nauyin nan, kije *na sakeki saki d'aya*, ban sakeki saboda Khairat ba sai dan na fahimci babu Allah a tare dake, kuma ina neman alfarma da karki fad'awa kowa dalilin rabuwarmu, dan ke zaki fi cutuwa da hakan, Allah ya sadamu da alkairinsa, ki kula min da yarona ko yarinyata."

Juyawa yayi zai fita tayi saurin rik'e qafarshi ta zube qasa tana kuka tana fad'in "yah Umar kamin rai, dan Allah kar kamin haka, wallahi na tuba ba zan sake ba, wal....."

Rufe mata baki yayi ya sunkuya yace "zaifi miki kiyi shiru kar mutane suji, zaifi kyautuwa ki bar gidan nan ba tare da kowa yaji ba."

Fit ya fice ya koma d'akin Baba, sallama yayi shiru dan haka ya tura qofar, jin ta bud'e yasa ya leqa amma Baba baya ciki, da hanzari ya shiga ya nufi wajen ruwan addu'a da yake da tabbacin sune, dauka yayi ya fito ya rufe d'akin, motarshi ya hau kai tsaye ya nufi gidan Bala.


***************


Koda yaje ya samu jikin ya tsananta sosai, tallabo kanshi yayi da niyyar bashi ruwan, yana zuba mishi a baki ruwa suka dinga gangarowa suna fita daga bakinshi, aman da Bala ya fara tare da jini ne yasa Umar Faruk saduda ya kalleshi a matsayin gawa, danya tabbatar
Showing 165001 words to 168000 words out of 186119 words