dai, ya azumin?"

Baiko kulashi ba sai Khairat da yake kallo yana fad'in "aunty Mama na ciyanki."

Cikin dariya ta aje kud'in hannunta akan gado ta tara hannu ta amsheshi duk da ba qarami bane tana fad'in "Mama ke kirana?"

"Eh." ya fad'a, hanyar fita ta nufa tana fad'in "to muje."

Umar Faruk ma bayansu yabi shima, suna fita suka samu Papa ne yanzu ma yayi aike, naman jajibir ne mai tarin waya da kuma kud'in cefane na sallah, yaron da aka aikone ya kalli Khairat ya bata enveloppe biyu yace "Alhaji ne yace abaki keda yar uwarki."

Bata tankasa ba harya fita su Umar Faruk yabi bayanshi dan bashi tukuici, kallon enveloppe d'in tayi taga d'aya sunanta ne a baya da signature d'in mahaifinta, d'aya kuma sunan Zuby ne nanma da sa hannun Papa, tasan akwai dalilin da yasa ya saka suna, ba kuma zai wuce adadin kud'in ne ya banbanta ba shi yasa ya raba musu, da Yusuf a jikinta ta qarasa inda su Zuby ke aiki ita dasu Saratu ta mik'a mata ba tare data mata magana ba, a wulaqance ta kalleta tace,

"Miye wannan d'in?"

Itama a daqile tace "ki karb'a mana saiki duba ki gani."

Saida taja tsaki ta karb'a tana kallon sunan da aka rubuta, kallonta tayi tace "wai miye wannan iskancin?"

A hassale Khairat tace "ba iskanci bane, mahaifina ne yace a baki, kuma na tabbata yayi hakane saboda yana kallonki a matsayin 'yarsa kamar ni."

Wani tsaki tayi kafin tayi dariya irinta daba tace "kiji wani rainin hankali, to an fad'a miki bana da hankali ne ko kuma sakara ce ni? to bari kiji wallahi asirinku ba zaiyi tasiri a kaina ba, kuma koba komai Allah ya kiyayeni naci kud"'in haram kud'in da bansan ta wace hanya aka samesu ba."

Muryar Umar Faruk ce ta katsesu yana fad'in "waike me yasa baki da hankali ne, le kullum inba tsokano abinda za ayi tashin hankali ki kayi ba hankalinki baya kwantawa, gidan nan sai kace ni kad'ai ne mai mata kullum a masifa nake kuma duk saboda ke, ko kad'an ke baki d'auki iyaye a wata tsiya ba shi yasa baka jin kunyar aibata na kowa, to wallahi na gaji da wannan iskancin naki, nakai maqura ta qarshe dan haka ba zan sake yarda ba, ya zama karo na qarshe da zan sake jin kina mata rashin kunya, ke inma banda raina mutane da ki kayi ba itace gaba dake ba a komai, amma kuma tana hak'uri dake bata miki cin kashin dake kike mata, to wallahi kashedi ne na qarshe wannan, in baki ji bari ba zaki ji a jikinki ma ba hoho ba, yar rainin hankali kawai."

Yana fad'a ya juya ya fita daga gidan, Khairat ma da yau takai maqura matsowa tayi kusan Zuby tace "ina da yaqini akan mahaifina cewa baya tab'a anfani da dukiyar daba tasa ba, sanin kowa ne da arziqinshi ya shiga siyasa, bawai yayi kud'i bane bayan ya fara siyasa, kin jima kina cin zarafina amma ina d'aga miki qafa, ki sani yau kin kaini qarshen da ba zan iya hak'ura ba, ya zama dole na nuna miki kuskurenki Zubeida, dole ki gane baki da wayo a duniyar nan, wallahi saina nuna miki banbancin dake tsakanina dake, Zubeida inhar bansa kinji kunyar mutanen gari ba ki canza min suna, Zubeida inhar gobe bansan kin kasa kallon kowa na gidan nan ba kice ni ba yar Na'ima bace, Zubeida inhar bansa kika kika tuhumi mahaifiyarki ba kice da zina Mani Bukar ya haifeni, wallahi gobe i warhaka ba zaki gane halin da kike ciki ba wannan alk'awarina ne."

Aje Yusuf tayi tasa hannu ta share hawayen da suka taho mata masu zafi tana kallon Zubyn, da k'arfi ta fizge enveloppe d'in dake hannnunta ta nunata da ita tace "saina sa kin fahimci haramcinki tafi haramcin da kike tunanin kud'in nan na d'auke dashi insha Allah, wallahi zaki gani za kuma ki gane kurenki, daga gobe zaki fara tunani kafin ki zagi asalin mutum ko ki masa rashin kunya, banza kawai da baki san inda duniya tasa gaba ba."

Tana fad'a ta juya ta shiga d'aki, aje enveloppe d'in hannunta tayi ta d'auki wayarta ta dannawa Bala kira, yana d'auka cike da girmamawa yace "ranki shi dad'e, barka da warhaka."

A tak'aice tace "barka Bala."

"Hajia ya hidima damu , ya k'ishin ruwa?"

"Alhaji Bala magana nake so muyi da kai."

"To to Hajia, ai lokacina gaba d'ayansa naki ne, ina jinki."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "kullum kana fad'a min girma da matsayin da nake dashi a wajenka, wani aiki ne nake so kamin a matsayin alfarma idan zaka iya."

"Hajia, aiba alfarma tsakaninmu, ki bada umarni kawai aikina cikawa ne."

"Na gode, Bala kasan me nake so dakai?"

"A'a Hajiata sai kin fad'a."

Juyawa tayi ta kalli kanta a madubi tace masa " lokaci yayi da ya kamata ka waiwayi ajiyarka da kayi shekarun baya, ina so ka amshi 'yarka dake hannun Asma'u."

Jim yayi kafin yace "Hajia hakan nada alaqa da alfarman da zan miki ne?"

"Hakan da za kayi taimakone bawai alfarma ba, Bala yarka na takura min sosai ta hanyar aibata min mahaifina kullum, ba wai burina na muzguna mata ba, danni ina da tabbacin nafi soyuwar a zuciyar mijinmu , idan so samu nane ina so mu zauna lafiya da ita, amma ita kullum cin zarafin iyayena ne burinta, kuma abinda za kayi bawai zaisa tabar gidan nan bane, kawai ina so ne ka fito a matsayin mahaifinta na gaskiya."

Shiru ya sake yi sannan yace "Hajia wannan ba matsala bane, a gaskiya bata kyauta ba kuma banji dad'i ba, kuma na tabbata hakan na faruwa ne ta sanadiyar mahaifiyarta, dan Asma'u ba mutumci ne da ita ba, amma karki damu Hajia zanyi abinda ki kace bawai a matsayin taimako ba, a'a sai dan na taimaki kaina da kuma ita yarinyar, lokaci ne yayi da zan tono shukar dana binne tsawan lokaci, kuma lokaci ne yayi da zan sadata da yan uwanta su san juna, kawai ki fad'i lokacin da kike so Hajiata."

Da wani mugun murmushi a fuskarta tace "gobe nake so."

"An gama Hajia, Allah ya kaimu goben."

"Ameen, zan fad'a maka lokaci da kuma kwatancin gidan."

Tana fad'a ta kashe wayar, dan ita dama bata bari ku dindige take kashe waya , yana daga cikin ikonta da take nunawa, wasu matasa ta kira su uku tace su sameta gida, suna zuwa ta basu wannan kudaden wanda Umar Faruk ya bata dana wajen Papa harda na Zubyn duk ta lissafa musu inda zasu kai, gida na farko data fad'a musu shine gidan Alhaji Bala, sannan sauran gidajen mutane, dama kuma yaran sune ke taimaka mata kowace shekara, suna girmamata ta yanda kiran Allah dana iyayensu ne kad'aizai hanasu amsa kiranta.


Tunda Umar Faruk ya fita bai dawo ba kasancewar daren sallah ne kowa baiyi bacci ba, mutanen gidan nata hayaniya Khairat kuma na d'aki tana tunanin hanyar da zata tara yan uwan Zuby da mahaifiyarsu a gobe, yayin da Zuby ma ke nata d'akin tana tunanin abinda Khairat ta fad'a, ganin ta kasa fahimtar komai yasa ta kira Mama ta fad'a mata, Mama ma hankalinta ya tashi sosai dan tana tunanin abinda zatayi, da tsoro da fargaba bacci ya d'auketa.

Khairat ma haka saida tayi bacci Umar Faruk ya shigo gidan, bai kuma tasheta ba sai sumbatarta da yayi ya kwanta gefenta badan yana jin bacci ba.....


*Gobe sallah, kuma gobe tonon...*😜
23/08/2019 Γ  12:51 - Meerahgee❀: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*JIHADI*
_Umar faruk_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


_Bismmilahir-rahman-rahim_


*Ina alfahari daku*πŸ’•πŸ’ž


5⃣4⃣

Kiran sallah asuba ne yasa Khairat bud'a ido, dan yanzu tana jin kiran sallah take tashin kanta, sauke idonta tayi akan Umar Faruk dake zaune yana kallonta shima, zaune ta tashi tana murza ido tana masa murmushi, cikin muryar bacci tace " kai kuma haka ake saika kasa tashina?"

A shagwab'e yace "kema kuma haka ake sai kiyi bacci ba tare da kin jira mijinki ba?"

Dariya tayi wacce bata da sauti tace "ka gafarci wannan sakaryar matar taka, har yanzu quruciya na damunta ne."

Dariya yayi yace "nadai fahimci yanzu babyna yasa kin rage bani kulawa, amma ba komai girmanshi ne ai."

Kamar zata fashe da kuka tace "baby, na fad'a maka fa banda komai, me yasa kake son tsokanata ne? ina so ko zan fara haifa maka yara sai mun qarasa cinye amarcinmu."

Yanda take maganar yasa ya janyota jikinshi ya rumgume yana fad'in "ina laifi wanda muka ci ma, ai kawai ki fara antayo minsu a shirye nake."

D'agowa tayi ta kalleshi tace "ko 'yan uku uku ne ka shirya?"

"Ai ko 'yan shida shida ne zan karb'a."

Dariya tayi ta fara qoqarin sauka daga kan gadon, da sauri ya rik'ota yana fad'in "bara na cajeki na gani, dan naga baki yarda kina da ciki ba."

Saida ta sauka da qafafunta qasa ta juyo saboda ya rik'e qugunta ita kuma ta zagaya hannayenshi a wuyanshi suna kallon juna, kallon qirjinta yake da yaga ya mishi wani b'ulb'ul ya cika sai walqiya yake kamar ta shafeshi da man gyad'a, bakinshi yasa ya janye rigarta ya cabko kan nononta ya fara tsutsa har yana lumshe ido, itama rufe idon tayi tana qara danna kanshi tana shafar kanshi, jin yana tutsa hannayenshi cikin rigar yasa ta janye tana fad'in "baby."

Kallonta yayi yace "ki tsaya mana na nuna miki kina d'auke da cikina."

"Um um." ta fad'a tana maqale kafad'a.

Hararanta yayi yace "kinsan zan gano gaskiya kenan."

"Indai ba coge kake son min ba kamar yanda ka fara min wayo a farkon zamanmu ta hanyar samun kusanci da jikina, to ka fad'a min baki da baki kawai."

Hannu ya mik'a mata yace "naji to zo kiji."

Matsowa tayi tace "ina jinka to."

Cikin wani irin kallo ya fara da "da farko dai na lura da sabon canji daga jikinki, saboda wannan kayan sun qara fitowa suna cika min ido sosai yayin da kullum suke min qwalele, sun cika fiye da baya kuma sai sheqi suke." duk yayi maganar ne yana shafarsu.

"Na biyu kuma yawan bacci da kike yanzu, ke baki fahimci hakan ba amma ni uban yaro tuni na fahimta, na uku kuma baki son cin abinci yanzu."

Dangware masa kai tayi tace "hamagon uba kawai."

Cikin dariya ya sake kamo hannunta yace "ya kuma had'u da hamagiyar uwa ba."

Tashi sukayi dukansu suka fita, alwala sukayi shiya wuce masallaci ita kuma ta dawo d'aki.....


**************

Gaba d'aya akayi girki a gidan, hakan yaba kowa damar samun shirin tafiya Eid da wuri, kowa fitowa yayi cikin shirinshi mai ban sha'awa, Umar Faruk kam cikin dogon d'inki yake na shadda kalar ruwan zuma, hula takalma agogo duk wanda suka dace da kayanshi, Zuby ma na cikin shaddar daya siya mata da d'inki kalar data dace da ita, Khairat ma fitowa tayi cikin shaddarta baqa wulik wacce aka d'inke ko ina da kwalliya, idonka kad'ai zasu nuna maka d'inkin yaji kud'i ba kad'an ba, hijabin dake jikinta baqi da takalma baqaqe kalar kwalliyar kayanta ne, tunda ta fito sanyayyen qamshin turarenta ya bige Umar Faruk da sauran mutanen wajen ma, Zuby kuma d'inki da shaddar take kallo tana tunanin ita Umar Faruk ya raina ya siyawa wannan shaddar da bata banzan kud'in d'inkin da basu kai na Khairat ba.

A motarshi su Ruk'ayya da sauran yara da kula matanshiπŸ˜‚ suka tafi, banda tsaki da hararan mutane ba abinda Zuby keyi, Khairat kuma da angonta da sauran yara kowa zikiri ne a bakinshi kamar yanda sunna tazo dashi, a haka suka isa babban masallaci sukayi sallah, ana idawa kuma bayan taya juna murna suka d'auko hanyar dawowa gida, koda suka zo kowa ya samu waje ya zauna aka zubo abinci a manyan plate, gaba d'aya mutanen gidan ne aka taru maza daban mata daban aka ci abinci amma a waje d'aya.

Khairat kuma da tsarin ya birgeta kallonsu take cike da birgewa, Umar Faruk ma da kallonshi ke kanta suna had'a ido ya da hannun ya tambayeta lafiya, murmushi tayi ba tare da b'oyewa ba tace " ina kallonku ne, ganin kun taru gaba d'ayanku kuna farin ciki, sai naji inama ina da yan uwa nima, da yau zan tarasu gaba d'aya mu mori farin cikin wannan ranar, amma ni kad'ai, sai kuma ku dana samu a matsayin sabbin ahlina."

Mama ce ta dafa kafad'arta tace " 'yata, ki d'auka mu naki ne, dukanmu nan mun zama d'aya kinji ko."

Dariya tayi ta shafi kumatun Mama tace "na sani Mamana, nima ina kallonku kamar ahalina."

Suna haka dai aka gama cin abinci, a qa'ida mazan ma basa fita sai bayan sallah azahar, hakan yasa Umar Faruk da uwar gidansa Khairat suka shige d'aki suna lobayyarsu, saida akayi sallah azahar suka fita Khairat ta kira wayar Bala, yana d'auka tace " kana da lambar mahaifiyarta ne?"

"A'a Hajia, amma dai ina da wanda nake da tabbacin yana da lambarta."

"Ok to ka samu lambarta, idan ka kira ka fad'a mata zaka karb'i 'yarka ne." tana fad'a ta kashe wayar.

Baisha wahalar samun lambar Ma'u ba dan haka ya danna mata kira, cike da shaqiyanci yace "nasan ba zaki manta da muryar nan ba, dan haka ba buqatar fad'a miki waye ni."

A gigice Ma'u ta mik'e tsaye tace "Bala, kaine ka kirani, lafiya, me yasa ka kirani?"

"Kwantar da hankalinki ba abun damuwa bane, kawai dai ajiyar dana baki ce nake so ki maido min da ita saboda nine ubanta."

"Kai Bala ka kiyaye ni wallahi, kasan me kake fad'a kuwa? to kaji da kyau, wannan 'yar da kake magana akanta, itace 'yar daka kasa d'aukar nauyinta kuma ka manta da ita har wannan lokacin, shine yanzu dan rainin wayo zaka wani ce wai 'yarka kake so, to ka fita idona wallahi, dan dama a qufule nake da kai dan ba yanda zanyi ne na qyaleka , ka rasa wacce zaka fad'awa wannan sirrin sai kishiyar yata, wallahi ka cuceni ka cuci 'yarka mugu kawai."


"Bana kira bane danki fad'a min wannan banzar maganar, na kira ne danna fad'a miki zanje har gidan auren nata danna fad'a mata nine ubanta, kuma karki sake kirana da macuci, dan in kin kirani da wannan sunan bansan wane sunan za'a kiraki dashi ba, kuma ai kema mai laifince tunda kika aurar da 'yata ina raye, kuma da sunan wani uban bani ba."

Yana fad'a ya kashe wayar tunda umarnin da aka bashi kenan, Khairat ya kira ya fad'a mata yanda sukayi tace mishi kawai yazo gidan yanzu, kwatanta mishi tayi kafin tayi kwance akan gado tana jiran zuwan Mama.

Ai kuwa baifi minti talatin ba saiga Bala ya paka yar motarshi data sha jiki, su Sa'ad na qofar gida yasa suka masa sallama da Baba, fitowa Baba yayi suka gaisa kafin Bala ya d'ora da " malam nasan baka sanni ba, to nidai sunana Alhaji Bala, kuma nazo ne ina son ganin sarakuwarka Zubeida."

"To, Zubeida kuma, meye had'inka da ita?"

"Eh to malam babbar magana ce ta kowani, kuma zanso kamin izinin shiga ciki danna ganta."

"Amma daka fad'a min abinda ke tsakaninku ai zaifi, tunda kaga matar aurene a gidan."

"To nidai mahaifin Zubeida, kuma mahaifiyarta tasan da zuwana."

😱😱😱😱😱😱


_Kuyi hak'uri da wannan._
23/08/2019 Γ  12:51 - Meerahgee❀: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*JIHADI*
_Umar faruk_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


_Bismmilahir-rahman-rahim_


5⃣5⃣



Kallon mahaukaci malam ya masa yace "uhum, malam ina jin dai kayi b'atan kaine ko? amma inba haka ba ya za kace haka."

Cewar Bala "malam, maganar nanfa tafi k'arfin tunaninka , ba kuma zaka tab'a fahimtar komai ba inba dama ka bani na shiga ciki ba."

Tsayar taxi a qofar gidan yasa suka kalli Ma'u dake fitowa a hargitse, duk da kayan sallah ne a jikinta shaddar da Umar Faruk ya bata amma yanda ta fito yasa ba zaka gane kan shirin nata ba, a harzuqe ta qaraso wajensu tana kallonsu, a d'arare tace "Bala, kenan saida kazo nan, wai me yasa kake haka, wannan wane irin tonon asiri ne dan Allah?"

"Kinga mushiga ciki ki fad'awa 'yata koni waye, inba haka ba wallahi anan zan tara miki Jama'a."

Bud'e baki tayi zatayi magana kuma sai tayi shiru, juyawa tayi ta kalli mutanen dake kai da kawowa sannan ta kalli malam daya kafesu da ido, saita nutsuwarta tayi tace "naji mu shiga ciki, amma dan Allah kamin alk'awarin ba zaka fad'a mata komai ba, zamu shiga ne kawai ka ganta."

Wata shed'aniyar dariya yayi yace " idan ganinta nake so nayi ai abune mai sauk'i, kinga fa lokacina kike b'ata min."

Malam ne ya kalleta yace "Asma'u, kiyi hak'uri da duk abinda zai faru ki d'auka yau itace ranar da dubunki ta cika, kaga malam mu shiga ciki dan ba zan yarda ku tara min jama'a ba anan."

Ganin sun shiga yasa dole tabi bayansu itama, abin haushin kuma kowa na tsakar gidan harda Zuby da kuma Khairat da bata jima da fitowa ba, gaisawa yake da mutanen yayin da malam ya janyo mishi kujera ya zauna, Bala kam ko kallon Khairat baiyi ba sai Zuby da yake kallo, a hankali yace " xyata, zo mana."

Wani kallo ta masa ta tab'e baki ta kawar da kai, murmushi yayi ya kalli Ma'u yace "ki fad'a mata nine babanta tazo wajena mana."

Mamaki ne ya fito kan fuskar kowa harda ita kanta Zubyn, Khairat kuma da farin ciki ta kalleshi tace "lah, ashe babanmu ne."

Da sauri ta taso daga inda take zaune tazo gabanshi ta mishi irin neman albarkar indiawa tana fad'in "Baba ka sama min albarka."

Jin abun yayi banbaraqwai,amma dan karya kwafsa
Showing 147001 words to 150000 words out of 186119 words