zuba a hannu ya fara shafa mata a fuska, da qyar ta farfad'o sai dai da wani sabon ciwon kan, da kuka ta farka tare da saka hannaye biyu akai tana fad'in,
"Kaina zai fashe, ka taimaka dan Allah ka d'aure min, zai fashe, kaina zai tarwatse, ciwo yake min sosai, dan Allah ka d'aure minshi *Faruk*."
"Kanki ne ke ciwo?" ya tambaya cike da tausayi.
Itama cikin kuka tace "qirjina ma fashewa zaiyi, amma nafi jin ciwon kan nan, dan Allah ka taimaka min ka samo abu ka d'aure minshi."
Rufe ido yayi lokaci d'aya kuma ya bud'e ya saukesu a kanta, tsaye yayi tare da sungumarta ya rumguma a jikinshi, yanda ta kwantar da kanta a qirjinshiya yasa hankalinshi ya sake tsananta tashi, domin kuwa tsaf yake jiyo yanda jijiyoyin kanta ke harbawa, a hankali yake takawa da ita harya direta akan gado, ya qura mata ido yana ganin jijiyoyinta duk sun fito, alamu ne qarara suka bayyana masa irin wahalar da take ciki, haka kawai sai yaji inama ciwon ya koma kansa, koba komai zai fita juriya da hak'uri, gyara zamanshi yayi a kan gadon yasa hannayenshi biyu ya fara shafa kanta daga farkon inda take aza goshinta wajen sallah, har zuwa inda gashinta ya tsaya kusa da kunne, ya jima yana shafa mata kamar yana wasa jin haka kuma yasa Khairat shako wuyar rigarshi cikin azaba da rad'ad'i ta bud'e ido danta masa magana amma sai taga dishi dishin ma har yafi d'azu, dan haka ta d'ago kanta ta kai bakinta har saman hanshinshi sannan tace "ka d'aure min kaina nace, ko so kake na mutu? mugu kawai azzalumi."
Shidai baice qala ba harta saki wuyan rigarshi, yana cikin shafa mata ya matse daidai inda gashinta ya tsaya sosai da yatsa biyu, wata siririyar qara tare da zabura ta cakumi rigarshi ta shige qirjinshi tana rik'e hannunshi daya matse mata kai da k'arfi sosai, k'ok'arin k'wace hannunshi take dan ba qaramin matsa ya mata ba, shi kuma ya rik'e sosai hakan yasa ta kasa k'watar kanta, turmutsutsu kawai take a jikinshi tana zubar da hawaye, gashi tana rok'on ya saketa amma bata jin muryarta na fita, da qyar yayi dauriya ya k'arasa addu'o'in da yake karanta mata saboda yanda take had'a jikinshi da nata tana murzawa, ba tare daya d'auke yatsunshi ba yaja yatsun nashi da k'arfi har saida ya diresu akan inda take aza goshinta wajen sallah sannan ya saketa, tana jin wani sauk'i ya zirnyarceta ta fad'a saman pillow tana sauke numfashi amma idonta rufe, sai lokacin taji kan yana mata sauk'i sosai sai kuma taji qirjinta kamar zai tsage, hannaye ta d'ora akai tana murzawa, ganin haka yasa ya d'auke hannayenta yace "bara na taimaka miki, shima zai bari da yardar Allah."
Kallonta yake yana tunanin yanda zaiyi wannan taimakon, kiran sallah isha'i ne ya riske kunnuwanshi, a hankali ya fara k'ok'arin sauka daga kan gado amma sai yaga ta dunk'ule waje d'aya tana dafe qirjinta sosai, wani sauk'ak'ak'en numfashiya sauke sannan ya dawo ya zauna, gyara mata kwanciyarta yayi ta mik'e sosai kamar wata gawa sannan ya d'auke hannayenta daga qirjinta, "um um, Umar faruk, karka fara." cewar wani b'angare na zuciyarshi.
"Ba komai, matarka ce ai, ka d'auka yanzu ma wani *Jihadi* ne za kayi, domin tana cikin halin rayuwa ne da mutuwa."
"Hummmmmmm." cewar Umar Faruk.
A hankali ya kai hannu ya sab'ule d'aurin qirjin dake jikinta, wata 'yar k'aramar numfashi yaja tare da saka tafikan hannayenshi ya rufe fuskarshi, ba k'aramin rikita mashi lissafi sukayi ba, kasancewar Allah ya horesu gasu kuma b'ul b'ul dasu kamar na mai k'aramin ciki, jawur suke har sunfi fatarta haske uwa uba kuma kanπ, kamar wani abu ya cijesu saboda yanda suke jawur dasu kamar an sulb'esu, gasu giri giri suke babu alamar kunya a idonsuππ, bud'e idonshi yayi ya sauke a fuskarta sai dai idonta a rufe suke, da alama bata ma cikin hayyacinta, "k'uk'ut." ya had'iye yawu kafin ya kai hannunshi da tuni suka fara karkarwa ga gumi dake tsattsafo masa, dan tuni ya shiga masifa network kuma ya kawo service, awazarta duka biyu ya soka hannayenshi a qarqashi ya tallabosu, wata irin bank'arewa tayi ta tusa masa qirkinta a nashi qirjin saboda masifar zafin da taji, kwantar da ita yayi saita kuma tasowa tana kara 'kwak'umeshi, sake mayar da ita yayi yana fad'in "ki tsaya mana, bana son mugunta fa."
_To wai fan's, me Umar Faruk ke nufi da baya son mugunta, mema aka masa na muguntar?_
Nan ma dai addu'a ya mata ya tofa mata sannan ya rabu da ita yana ji yana gani jam'i ya wuceshi, sauka yayi daga gadon ya bud'a wajen kayanta ya d'auko wata rigar bacci da wandonta silip ya aje mata yana fad'in "ki tashi ki saka."
Sai dai bansan Khairat azabar ciwon kai yasa ji da ganinta sun d'auke ba na wucen gadi , ko alamar taji ma ba tayi ba hakan yasa ya d'auki kayan ya warware rigar yana kallo........
_Me kuka ce?π zai saka ne ko kuma dai yaya zaiyi?_π
πluv u my Meelat.π
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Sadaukarwa ga*
_Fateema_ momyn Dady
_Maman tasleem_
_Bismmilahir-rahman-rahim_
_Allahumma antas- salam, wa minkas-salam, tabarakta ya zuljalali wal-ikram._
*Astagfirullah wa atubu ilaikh.*
2β£5β£
Kamar zai fita daga d'akin kuma saiya kashe wutar d'akin ya dawo da rigar a hannunshi, duk da ba'a gani amma haka ya lalabata ya qarasa zame towel d'in, wandon ya d'auka ya fara saka mata sannan ya zura mata rigar, saida ya tabbatar komai yayi daidai sannan ya kunna hasken d'akin, daga inda yake ya kalleta ganin kayan sun mata d'as gwanin kyau, fita yayi daga d'akin danya tafi masallaci sai dai kuma yasan alwalarshi ta karye dole saiya d'anyi wankaπ ko sama sama neπ, haka kam akayi saida yayi wanka ya fito ya bud'a kayanshi zai ciro wasu kayan ya saka kawai yaga maganin da kakarta ta bashi, a hankali ya fara tuna maganganun iyayenta dama kakarta d'in, hakan yasa ya ya fad'a a fili "kenan wannan ne abinda ke damunta? to me yake janyo mata shi?"
Maganar kaka ya sake tarowa baya kawai sai yace "uhum, kenan b'acin rai da damuwa ne kamar yanda mahaifinta ya fad'a? ikon Allah."
"Ba wannan kayan bane jikina, waya canza min kayana?" ta tambaya tana kallonshi.
"Dank'ari." cewar Umar Faruk.
Da sauri ta sauka daga kan gadon tana fad'in "waya canza min kayan jikina, ka fad'a min gaskiya Faruk, kaine? yanzu kenan ka kalleni saboda kaga bana cikin hayyacina? kamin adalci kenan? saboda kawai kana mijina."
"Kinga dan Allah, bafa abinda kike tunani bane, ba..ni ba...bane ba sauya miki kaya."
Kafeshi tayi da ido tace "kalleni."
Kallonta kam yayi sai dai gaba d'aya gabansu dukan uku uku yake, a hankali tace "ka rantse ba kai bane, ni kuma saina yarda."
Shiru ya d'anyi kafin yace "kiyi hak'uri, ni na canza miki, amma...."
"Amma me? baka kalleni ba za kace?"
Kuka ta saka da k'arfin gaske harda bubbuga qafafu tana fad'in "shikenan ya gama dani wallahi, ace kamar wannan yaron ne zai saka min kaya a jikina, shikenan ta qare miki Khairat, baki da bakin magana kuma tunda haka ta faru, nan gaba kuma kusantarki zaiyi daga nan kuma saiki d'auki cikinshi sannan ki haifeshi , bayan nan kuma saiya...."
Da sauri Umar Faruk ya janyo k'ugunta ya had'e da nashi ya d'ora yatsarshi akan labb'ata suna kallon juna, wani yanayi yake ji dashi kad'ai yasan me yake ji, dakewa yayi ya kama gashinta ya fara wasa dashi kamar gaske harda murmushi kafin yace mata "kiyi shiru, bana so mutanen dake waje su d'auka wani abu ne nake miki, dan haka kuskure ne, ki cire wannan tunanin a qwaqwalwarki dan haka ba zata faru ba, ni Umar Faruk ba zan iya had'a jikina da naki ba."
"Saboda me? ni karuwa ce? kaima haka kake gani? amma me yasa ka aureni to?"
Ganin hawaye sun cika idonta sai kuma ta bashi tausayi sosai, a hankali ba tare daya raba jikinshi ba yace "ni ba haka nake nufi ba, kawai dai ba zan iya had'a jikina da naki bane, saboda ina da matuk'ar kishi."
Qasa tayi da idonta tace "kenan yanzu da ice ka had'a jikinka? ko kuma kana nufin daga wannan had'awar da kayi yanzu ne ba zaka sake had'awa ba?"
Sakinta yayi yace "daga wannan ba zan sake ba."
Har zai wuce tace "baka ji mena fad'awa mahaifiyar matarka ba kenan? idan naso Faruk zaka zama nawa, idan nayi niyya zaka zama kamar raqumi da akala sai yanda nayi da kai, ka daina cika baki."
"Hummm, ba wani cika baki, ina da yarda da kaina ne shi yasa."
"Ka tabbata?"
"Qwarai ma kuwa."
"Ok, zamu gani, ni kuma zan ruguje wannan yarda da kai d'in."
"Kinga maganinki nan ki d'auka kisha yafi miki mahimmanci."
Juyawa tayi inda ya nuna mata ta kalla, maido kallonta tayi gareshi tace "ina ka samu magani na?"
"Matata ce ta bani."
Wani irin murd'awar kayan ciki taji lokaci d'aya kuma zuciyarta ta turnuk'o, a dake tace "wace matar taka? ba dai wannan d'iyar masifafiyar matar ba?"
Dariya ce ta kama Umar Faruk, karo na farko da Khairat taga dariyarshi, kafeshi tayi da ido harya tsagaita yace "wannan ta dabance , duk cikin matan nawa babu mai qaunata kamar ita, shi yasa nima na mata waje na musamman a zuciyata."
Duk da Khairat ta fahimci Umar faruk zaiyi dad'in zama kuma kamar yanda Ruk'ayya tace ta fad'a ne, amma kuma wani bala'i da taji ne a zuciyarta yasa ta rasa meke damunta, haka kawai taji bata so yana danganta kanshi da kowace mace a duniya, ba tare daya ankara ba Khairat ta kai masa duka a qirji harda fad'in "aisai kaje gaka gata ku cinye junanku."
Juyawa tayi zata haye gado tana fad'in "aikin banza kawai, ni gidanmu ma zan koma."
Da k'arfi taji ya janyota har saida ta fad'a qirjinshi, kafe juna sukayi da ido na d'an lokaci kafin yayi k'arfin halin cewa "meye wannan nake gani a idonki?"
Tsaki tayi mai k'arfi ta janye kanta daga jikinshi, fizgota yayi niyyar yin sai kuma,
"Assalama alaikum." sallamar Ruk'ayya ta katsesu.
"Shigo Ruk'ayya." cewar Umaririπ.
Shigowa tayi tana aje kwanukan Khairat tace "kina zuwa a lokacin da bai dace ba fa."
Ruk'ayya dai sakin ido tayi tana kallonta, har zata fita kuma tace "kina ji? ki dafa min."
A hankali Ruk'ayya ta tako ta zo ta d'auki indomien inda ta d'auka d'azu sannan ta fita tana guna guni, kwance tayi akan gado ta d'auki wayarta ta fara kiran lambar Mamie, muryarshi taji yace "ki daure ki dinga suturta jikinta koda gaban mace ne 'yar uwarki."
Hannu d'aya ta rumgume a qirji ta mike qafafunta tana girgizawa tana murmushi tace "to meye a ciki, naga jikina ne ba bana ka ba, kuma kace baka qaunarshi ba zaka tab'a had'ashi da jikinka ba, to miye na damuwa?"
Muryar Mamie ta daki kunnuwanta dan haka tace "Mamie ya kike, shine kun manta dani ko kirana ba kuyi ba?"
Shiru tayi kafin tace "ba wani nan, kudai kuna can kuna soyayyarku da Papa, tunda yanzu babu kowa a gabanku, dama nice kuma kun kawar dani."
Turo baki tayi cikin shagwab'a tace "wallahi Mamie nayi kewar Papa, nan fa gaba d'aya ba dad'i, yau fa har zazzab'i ya kamani, amma dai da sauki."
Nan suka dinga hira har Ruk'ayya ta shigo ta kawo mata sannan ta kashe wayar, sauka tayi daga kan gadon ta zauna kujerar da Umar Faruk ke cin abinci harda turashi take da k'ugu tana fad'in "duk kabi ka matse waje kai kad'ai."
Plate d'in imdomin ta ta aza ta fara ci itama, satar kallon hannunta yake wanda suka sha jan lalle, tana ci tana kallonshi ta wutsiyar ido tana kuma tunanin abubuwan da matar nan ta fad'a mata, alwashi taci saita saka matar nan tayi nadamar abinda ta mata, to amma tayaya? dole saita samu kusanci da Umar Faruk, to shima tayaya? abu mai sauk'i, namiji neshi ke kuma macce, kawai ki samu kusanci dashi, a hankali ta juya ta kalleshi, caraf idonsu suka had'u, kallon baka da hankali ta masa yayin da shi kuma ya bita da harara, tunawa da plan d'inta yasa ta turo baki gaba cikin sigar shagwab'a ta d'an mangareshi da kanta, hannu tasa ta debo lomar indomie ta nufi bakinshi da ita, ganin yana mata kallon rashin fahimta yasa ta sake langab'e kai tace "bud'a bakinka mana."
Kai ya gurgiza mata alamar a'a, a bakinta ta saka lomar ba tare data kallesa ba tace "hum, kama daina kallona haka."
Wata sallamar ce ta katsesu daga k'ofar kewayen nasu, Umar faruk ne ya fita jim kad'an ya dawo, tsaye yayi a kanta yace "ki canza kaya Baba nasan ganinmu."
"Meya faru?" ta tambaya.
"Ki tashi, duk litinin ana zama wajenshi da wannan lokacin."
"Me ake tattaunawa?"
"Oh, Khairat, kiyi abinda nace mana."
"To bari na gama cin abinci na."
Ba yanda ya iya saida ta gama sannan ta wanke hannu ta d'auki doguwar riga tasa ta d'auki kallabi ta yafa, yana kallonta yace "hijab zaki saka."
"A'a, nifa bana iya zama dashi, kuma ba kace wajen Baba ne zamu ba."
Hijab d'inta da take sallah ya d'auka ya matso kusanta ya gyarashi , bai b'ata lokaci ba wajen saka mata, k'ok'arin 'kwacewa tayi ya mata wani jan kallo dole ta tsaya, gaba ya sata suka fita daga d'akin bayan ya rufe, suna daf da shiga d'akin Baba inda gaba d'aya mutanen gidan suke, hannunta Umar Faruk ya kama ya gyarawa yatsunsu waje d'aya tare da murzawa har suka shiga yayin da yayi sallama, amma suna shiga ya saki hannunta suka samu wuri suka zauna, tunda ya rik'e hannunta taji wani *baqon yanayi* a tare da ita da bata tab'a jin irinshi ba, kamar yanda shima abubuwan da yaji sunfi k'arfin wasa, dan saida ya tuna da maganar Ishaq cewar *wataqila yanzu ne ya fara soyayar gaskiya.*
Kallon kowa take yayin da su kuma suke sauraran nasihar da Baba ke musu akan rik'o da zumunci, sun jima sosai kafin Baba yaba Zeinab damar rufe musu taron da addu'a, sosai yarinyar ta shiga ran Khairat saboda ganinta bata fi yar shekara bakwai ba, amma sink'i sink'i addu'o'i na fitowa daga bakinta, haka suka tashi suka fito, kowa makwancinshi ya nufa sai Umar Faruk daya kalli Khairat yace "muje kiga Mama."
Binshi kawai tayi suka nufi d'akin Mama, da sallama ya shiga ita kuma tun k'ofar d'akin take kalle kalle har suka shiga, zaune yayi kusa da Mama dake kwance amma ganinsu tare yasa ta tashi zaune tana fad'in "ah, ashe tare kuke da 'yata."
Sai lokacin ta d'anyi zaune akan kujera tana kallon d'akin da kyau, k'aramar panka take kallo a ganinta ba zata musu komai ba, muryar Umar Faruk ce ta katse yana fad'in "ya jikin Mama?"
Kallon Mama tayi tace "dama baku da lafiya ne?"
"A'a 'yata, ai nama ji sauk'i."
Umar Faruk ta kalla dan haka yace "hawan jininsu ne ya tashi, amma sunsha maganinsu."
"Wane irin magani, kuma baku kaita asibiti ba?"
"Eh, akwai maganin da aka rubuta musu, to shine suke anfani dashi." cewar Ruk'ayya dake gyara shinfid'a.
"Amma ai hakan bai dace ba, me zai hana ku dinga kaita asibiti duk lokacin da bata jin dad'i? amma zama da ciwo ana shan magani barkatai."
Tsam ta mik'e daga kujerar ta durk'usa kusan Mama ta tallabota ta zauna daidai, kallon Ruk'ayya tayi tace "ki bani hijab d'insu."
Ba tace komai ba sai hijab d'in data mik'o mata, saka mata tayi sannan tayi tsaye tana ciccib'ar Mama tana fad'in "muje asibiti Mama, lafiyarki tafi komai mahimmanci, kuma suma kansu yayanki nasan sun san da haka, amma babu mai fasahar kaiki asibiti, sai sun rasaki kuma za kiga sunfi kowa damuwa da kuka."
Kallonta kawai Umar Faruk da Ruk'ayya da sauran yaran suke, tsaye yayi yana fad'in "ba wai bamu damu bane, muma muna...."
"Dan Allah kayi shiru, ni ba tambayarka nayi ba."
Mama ce tace "'yata dama kin barshi wallahi, naji sauk'i ai da dama jikin ba kamar d'azu ba."
"A'a Mama muje kawai, sai dai kuma ko kina so ki nuna min ni ba 'yarki bace."
Suna fitowa farfajiyar gidan ta kalli Umar Faruk tace "ka rik'e Mama, zan d'auko makullin mota."
Tana fitowa kuma da makullin da post d'inta ta kuwa haka ta rik'e Mama har suka fita inda Baba ya fito da su tafi tare amma Khairat tace kawai yayi zamanshi, tare da Umar Faruk suka tafi suna gaba ita dashi tana tuk'i, Mama na baya in banda addu'a da qaunar Khairat babu abinda take ji, bata san kuma me yasa ba amma taji daga haka son sarakuwar tata ya kamata, suna zuwa asibitin da taje da safe docteur Sadiya ta tafi sai wani docteur d'in, cikin qwarewa ya duba Mama kuma ya fad'a musu jininta ya hau, allura aka mata na saukar da hawan jinin sannan aka rubuta wasu magunguna masu matuk'ar tsadar gaske, ita ta biya kud'in sannan suka kamo hanyar gida, saida ta tsaya babban pharmacie ta siyo duka magungunan sannan suka tafi gida dare yayi sosai lokacin.
Har d'aki suka kai Mama ta kwanta Khairat taja zanin rufa ta rufeta, gefen fuskar Mama ta shafa tace "kiyi bacci Mama, dan Allah banda damuwa da tunani, ki more baccinki babu mai takuraki."
Mik'ewa tayi tana fad'in "saida
Showing 66001 words to 69000 words out of 186119 words
"Kaina zai fashe, ka taimaka dan Allah ka d'aure min, zai fashe, kaina zai tarwatse, ciwo yake min sosai, dan Allah ka d'aure minshi *Faruk*."
"Kanki ne ke ciwo?" ya tambaya cike da tausayi.
Itama cikin kuka tace "qirjina ma fashewa zaiyi, amma nafi jin ciwon kan nan, dan Allah ka taimaka min ka samo abu ka d'aure minshi."
Rufe ido yayi lokaci d'aya kuma ya bud'e ya saukesu a kanta, tsaye yayi tare da sungumarta ya rumguma a jikinshi, yanda ta kwantar da kanta a qirjinshiya yasa hankalinshi ya sake tsananta tashi, domin kuwa tsaf yake jiyo yanda jijiyoyin kanta ke harbawa, a hankali yake takawa da ita harya direta akan gado, ya qura mata ido yana ganin jijiyoyinta duk sun fito, alamu ne qarara suka bayyana masa irin wahalar da take ciki, haka kawai sai yaji inama ciwon ya koma kansa, koba komai zai fita juriya da hak'uri, gyara zamanshi yayi a kan gadon yasa hannayenshi biyu ya fara shafa kanta daga farkon inda take aza goshinta wajen sallah, har zuwa inda gashinta ya tsaya kusa da kunne, ya jima yana shafa mata kamar yana wasa jin haka kuma yasa Khairat shako wuyar rigarshi cikin azaba da rad'ad'i ta bud'e ido danta masa magana amma sai taga dishi dishin ma har yafi d'azu, dan haka ta d'ago kanta ta kai bakinta har saman hanshinshi sannan tace "ka d'aure min kaina nace, ko so kake na mutu? mugu kawai azzalumi."
Shidai baice qala ba harta saki wuyan rigarshi, yana cikin shafa mata ya matse daidai inda gashinta ya tsaya sosai da yatsa biyu, wata siririyar qara tare da zabura ta cakumi rigarshi ta shige qirjinshi tana rik'e hannunshi daya matse mata kai da k'arfi sosai, k'ok'arin k'wace hannunshi take dan ba qaramin matsa ya mata ba, shi kuma ya rik'e sosai hakan yasa ta kasa k'watar kanta, turmutsutsu kawai take a jikinshi tana zubar da hawaye, gashi tana rok'on ya saketa amma bata jin muryarta na fita, da qyar yayi dauriya ya k'arasa addu'o'in da yake karanta mata saboda yanda take had'a jikinshi da nata tana murzawa, ba tare daya d'auke yatsunshi ba yaja yatsun nashi da k'arfi har saida ya diresu akan inda take aza goshinta wajen sallah sannan ya saketa, tana jin wani sauk'i ya zirnyarceta ta fad'a saman pillow tana sauke numfashi amma idonta rufe, sai lokacin taji kan yana mata sauk'i sosai sai kuma taji qirjinta kamar zai tsage, hannaye ta d'ora akai tana murzawa, ganin haka yasa ya d'auke hannayenta yace "bara na taimaka miki, shima zai bari da yardar Allah."
Kallonta yake yana tunanin yanda zaiyi wannan taimakon, kiran sallah isha'i ne ya riske kunnuwanshi, a hankali ya fara k'ok'arin sauka daga kan gado amma sai yaga ta dunk'ule waje d'aya tana dafe qirjinta sosai, wani sauk'ak'ak'en numfashiya sauke sannan ya dawo ya zauna, gyara mata kwanciyarta yayi ta mik'e sosai kamar wata gawa sannan ya d'auke hannayenta daga qirjinta, "um um, Umar faruk, karka fara." cewar wani b'angare na zuciyarshi.
"Ba komai, matarka ce ai, ka d'auka yanzu ma wani *Jihadi* ne za kayi, domin tana cikin halin rayuwa ne da mutuwa."
"Hummmmmmm." cewar Umar Faruk.
A hankali ya kai hannu ya sab'ule d'aurin qirjin dake jikinta, wata 'yar k'aramar numfashi yaja tare da saka tafikan hannayenshi ya rufe fuskarshi, ba k'aramin rikita mashi lissafi sukayi ba, kasancewar Allah ya horesu gasu kuma b'ul b'ul dasu kamar na mai k'aramin ciki, jawur suke har sunfi fatarta haske uwa uba kuma kanπ, kamar wani abu ya cijesu saboda yanda suke jawur dasu kamar an sulb'esu, gasu giri giri suke babu alamar kunya a idonsuππ, bud'e idonshi yayi ya sauke a fuskarta sai dai idonta a rufe suke, da alama bata ma cikin hayyacinta, "k'uk'ut." ya had'iye yawu kafin ya kai hannunshi da tuni suka fara karkarwa ga gumi dake tsattsafo masa, dan tuni ya shiga masifa network kuma ya kawo service, awazarta duka biyu ya soka hannayenshi a qarqashi ya tallabosu, wata irin bank'arewa tayi ta tusa masa qirkinta a nashi qirjin saboda masifar zafin da taji, kwantar da ita yayi saita kuma tasowa tana kara 'kwak'umeshi, sake mayar da ita yayi yana fad'in "ki tsaya mana, bana son mugunta fa."
_To wai fan's, me Umar Faruk ke nufi da baya son mugunta, mema aka masa na muguntar?_
Nan ma dai addu'a ya mata ya tofa mata sannan ya rabu da ita yana ji yana gani jam'i ya wuceshi, sauka yayi daga gadon ya bud'a wajen kayanta ya d'auko wata rigar bacci da wandonta silip ya aje mata yana fad'in "ki tashi ki saka."
Sai dai bansan Khairat azabar ciwon kai yasa ji da ganinta sun d'auke ba na wucen gadi , ko alamar taji ma ba tayi ba hakan yasa ya d'auki kayan ya warware rigar yana kallo........
_Me kuka ce?π zai saka ne ko kuma dai yaya zaiyi?_π
πluv u my Meelat.π
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Sadaukarwa ga*
_Fateema_ momyn Dady
_Maman tasleem_
_Bismmilahir-rahman-rahim_
_Allahumma antas- salam, wa minkas-salam, tabarakta ya zuljalali wal-ikram._
*Astagfirullah wa atubu ilaikh.*
2β£5β£
Kamar zai fita daga d'akin kuma saiya kashe wutar d'akin ya dawo da rigar a hannunshi, duk da ba'a gani amma haka ya lalabata ya qarasa zame towel d'in, wandon ya d'auka ya fara saka mata sannan ya zura mata rigar, saida ya tabbatar komai yayi daidai sannan ya kunna hasken d'akin, daga inda yake ya kalleta ganin kayan sun mata d'as gwanin kyau, fita yayi daga d'akin danya tafi masallaci sai dai kuma yasan alwalarshi ta karye dole saiya d'anyi wankaπ ko sama sama neπ, haka kam akayi saida yayi wanka ya fito ya bud'a kayanshi zai ciro wasu kayan ya saka kawai yaga maganin da kakarta ta bashi, a hankali ya fara tuna maganganun iyayenta dama kakarta d'in, hakan yasa ya ya fad'a a fili "kenan wannan ne abinda ke damunta? to me yake janyo mata shi?"
Maganar kaka ya sake tarowa baya kawai sai yace "uhum, kenan b'acin rai da damuwa ne kamar yanda mahaifinta ya fad'a? ikon Allah."
Maida kallonshi yayi gareta tana bacci hankali nutse, shiryawa yayi ya aje magungunan kusa da ita ya fita ya nufi masallaci, shi kad'ai yayi sallah shi sannan ya hau mashin d'inshi ya d'an fita, baifi awa d'aya ba kuma ya dawo, har yanzu bacci take dan haka ya fito da clΓ© USB daya siyo ya mak'ala a tv ya jona ya fara sauraren k'ira'o'in, wannan karatun ne ya tasheta yana ganin haka ya taso zunbur yayi kanta, tana dafe da kanta ta fara k'ok'arin bud'e idonta, a kanshi ta saukesu tana kallonshi, saida ta saisaita kanta sannan ta kalli d'akin da kyau ta kuma kalli jikinta, da sauri ta dafe qirjinta ta kalleshi a tsorace.
"Ba wannan kayan bane jikina, waya canza min kayana?" ta tambaya tana kallonshi.
"Dank'ari." cewar Umar Faruk.
Da sauri ta sauka daga kan gadon tana fad'in "waya canza min kayan jikina, ka fad'a min gaskiya Faruk, kaine? yanzu kenan ka kalleni saboda kaga bana cikin hayyacina? kamin adalci kenan? saboda kawai kana mijina."
"Kinga dan Allah, bafa abinda kike tunani bane, ba..ni ba...bane ba sauya miki kaya."
Kafeshi tayi da ido tace "kalleni."
Kallonta kam yayi sai dai gaba d'aya gabansu dukan uku uku yake, a hankali tace "ka rantse ba kai bane, ni kuma saina yarda."
Shiru ya d'anyi kafin yace "kiyi hak'uri, ni na canza miki, amma...."
"Amma me? baka kalleni ba za kace?"
Kuka ta saka da k'arfin gaske harda bubbuga qafafu tana fad'in "shikenan ya gama dani wallahi, ace kamar wannan yaron ne zai saka min kaya a jikina, shikenan ta qare miki Khairat, baki da bakin magana kuma tunda haka ta faru, nan gaba kuma kusantarki zaiyi daga nan kuma saiki d'auki cikinshi sannan ki haifeshi , bayan nan kuma saiya...."
Da sauri Umar Faruk ya janyo k'ugunta ya had'e da nashi ya d'ora yatsarshi akan labb'ata suna kallon juna, wani yanayi yake ji dashi kad'ai yasan me yake ji, dakewa yayi ya kama gashinta ya fara wasa dashi kamar gaske harda murmushi kafin yace mata "kiyi shiru, bana so mutanen dake waje su d'auka wani abu ne nake miki, dan haka kuskure ne, ki cire wannan tunanin a qwaqwalwarki dan haka ba zata faru ba, ni Umar Faruk ba zan iya had'a jikina da naki ba."
"Saboda me? ni karuwa ce? kaima haka kake gani? amma me yasa ka aureni to?"
Ganin hawaye sun cika idonta sai kuma ta bashi tausayi sosai, a hankali ba tare daya raba jikinshi ba yace "ni ba haka nake nufi ba, kawai dai ba zan iya had'a jikina da naki bane, saboda ina da matuk'ar kishi."
Qasa tayi da idonta tace "kenan yanzu da ice ka had'a jikinka? ko kuma kana nufin daga wannan had'awar da kayi yanzu ne ba zaka sake had'awa ba?"
Sakinta yayi yace "daga wannan ba zan sake ba."
Har zai wuce tace "baka ji mena fad'awa mahaifiyar matarka ba kenan? idan naso Faruk zaka zama nawa, idan nayi niyya zaka zama kamar raqumi da akala sai yanda nayi da kai, ka daina cika baki."
"Hummm, ba wani cika baki, ina da yarda da kaina ne shi yasa."
"Ka tabbata?"
"Qwarai ma kuwa."
"Ok, zamu gani, ni kuma zan ruguje wannan yarda da kai d'in."
"Kinga maganinki nan ki d'auka kisha yafi miki mahimmanci."
Juyawa tayi inda ya nuna mata ta kalla, maido kallonta tayi gareshi tace "ina ka samu magani na?"
"Matata ce ta bani."
Wani irin murd'awar kayan ciki taji lokaci d'aya kuma zuciyarta ta turnuk'o, a dake tace "wace matar taka? ba dai wannan d'iyar masifafiyar matar ba?"
Dariya ce ta kama Umar Faruk, karo na farko da Khairat taga dariyarshi, kafeshi tayi da ido harya tsagaita yace "wannan ta dabance , duk cikin matan nawa babu mai qaunata kamar ita, shi yasa nima na mata waje na musamman a zuciyata."
Duk da Khairat ta fahimci Umar faruk zaiyi dad'in zama kuma kamar yanda Ruk'ayya tace ta fad'a ne, amma kuma wani bala'i da taji ne a zuciyarta yasa ta rasa meke damunta, haka kawai taji bata so yana danganta kanshi da kowace mace a duniya, ba tare daya ankara ba Khairat ta kai masa duka a qirji harda fad'in "aisai kaje gaka gata ku cinye junanku."
Juyawa tayi zata haye gado tana fad'in "aikin banza kawai, ni gidanmu ma zan koma."
Da k'arfi taji ya janyota har saida ta fad'a qirjinshi, kafe juna sukayi da ido na d'an lokaci kafin yayi k'arfin halin cewa "meye wannan nake gani a idonki?"
Tsaki tayi mai k'arfi ta janye kanta daga jikinshi, fizgota yayi niyyar yin sai kuma,
"Assalama alaikum." sallamar Ruk'ayya ta katsesu.
"Shigo Ruk'ayya." cewar Umaririπ.
Shigowa tayi tana aje kwanukan Khairat tace "kina zuwa a lokacin da bai dace ba fa."
Ruk'ayya dai sakin ido tayi tana kallonta, har zata fita kuma tace "kina ji? ki dafa min."
A hankali Ruk'ayya ta tako ta zo ta d'auki indomien inda ta d'auka d'azu sannan ta fita tana guna guni, kwance tayi akan gado ta d'auki wayarta ta fara kiran lambar Mamie, muryarshi taji yace "ki daure ki dinga suturta jikinta koda gaban mace ne 'yar uwarki."
Hannu d'aya ta rumgume a qirji ta mike qafafunta tana girgizawa tana murmushi tace "to meye a ciki, naga jikina ne ba bana ka ba, kuma kace baka qaunarshi ba zaka tab'a had'ashi da jikinka ba, to miye na damuwa?"
Muryar Mamie ta daki kunnuwanta dan haka tace "Mamie ya kike, shine kun manta dani ko kirana ba kuyi ba?"
Shiru tayi kafin tace "ba wani nan, kudai kuna can kuna soyayyarku da Papa, tunda yanzu babu kowa a gabanku, dama nice kuma kun kawar dani."
Turo baki tayi cikin shagwab'a tace "wallahi Mamie nayi kewar Papa, nan fa gaba d'aya ba dad'i, yau fa har zazzab'i ya kamani, amma dai da sauki."
Nan suka dinga hira har Ruk'ayya ta shigo ta kawo mata sannan ta kashe wayar, sauka tayi daga kan gadon ta zauna kujerar da Umar Faruk ke cin abinci harda turashi take da k'ugu tana fad'in "duk kabi ka matse waje kai kad'ai."
Plate d'in imdomin ta ta aza ta fara ci itama, satar kallon hannunta yake wanda suka sha jan lalle, tana ci tana kallonshi ta wutsiyar ido tana kuma tunanin abubuwan da matar nan ta fad'a mata, alwashi taci saita saka matar nan tayi nadamar abinda ta mata, to amma tayaya? dole saita samu kusanci da Umar Faruk, to shima tayaya? abu mai sauk'i, namiji neshi ke kuma macce, kawai ki samu kusanci dashi, a hankali ta juya ta kalleshi, caraf idonsu suka had'u, kallon baka da hankali ta masa yayin da shi kuma ya bita da harara, tunawa da plan d'inta yasa ta turo baki gaba cikin sigar shagwab'a ta d'an mangareshi da kanta, hannu tasa ta debo lomar indomie ta nufi bakinshi da ita, ganin yana mata kallon rashin fahimta yasa ta sake langab'e kai tace "bud'a bakinka mana."
Kai ya gurgiza mata alamar a'a, a bakinta ta saka lomar ba tare data kallesa ba tace "hum, kama daina kallona haka."
Wata sallamar ce ta katsesu daga k'ofar kewayen nasu, Umar faruk ne ya fita jim kad'an ya dawo, tsaye yayi a kanta yace "ki canza kaya Baba nasan ganinmu."
"Meya faru?" ta tambaya.
"Ki tashi, duk litinin ana zama wajenshi da wannan lokacin."
"Me ake tattaunawa?"
"Oh, Khairat, kiyi abinda nace mana."
"To bari na gama cin abinci na."
Ba yanda ya iya saida ta gama sannan ta wanke hannu ta d'auki doguwar riga tasa ta d'auki kallabi ta yafa, yana kallonta yace "hijab zaki saka."
"A'a, nifa bana iya zama dashi, kuma ba kace wajen Baba ne zamu ba."
Hijab d'inta da take sallah ya d'auka ya matso kusanta ya gyarashi , bai b'ata lokaci ba wajen saka mata, k'ok'arin 'kwacewa tayi ya mata wani jan kallo dole ta tsaya, gaba ya sata suka fita daga d'akin bayan ya rufe, suna daf da shiga d'akin Baba inda gaba d'aya mutanen gidan suke, hannunta Umar Faruk ya kama ya gyarawa yatsunsu waje d'aya tare da murzawa har suka shiga yayin da yayi sallama, amma suna shiga ya saki hannunta suka samu wuri suka zauna, tunda ya rik'e hannunta taji wani *baqon yanayi* a tare da ita da bata tab'a jin irinshi ba, kamar yanda shima abubuwan da yaji sunfi k'arfin wasa, dan saida ya tuna da maganar Ishaq cewar *wataqila yanzu ne ya fara soyayar gaskiya.*
Kallon kowa take yayin da su kuma suke sauraran nasihar da Baba ke musu akan rik'o da zumunci, sun jima sosai kafin Baba yaba Zeinab damar rufe musu taron da addu'a, sosai yarinyar ta shiga ran Khairat saboda ganinta bata fi yar shekara bakwai ba, amma sink'i sink'i addu'o'i na fitowa daga bakinta, haka suka tashi suka fito, kowa makwancinshi ya nufa sai Umar Faruk daya kalli Khairat yace "muje kiga Mama."
Binshi kawai tayi suka nufi d'akin Mama, da sallama ya shiga ita kuma tun k'ofar d'akin take kalle kalle har suka shiga, zaune yayi kusa da Mama dake kwance amma ganinsu tare yasa ta tashi zaune tana fad'in "ah, ashe tare kuke da 'yata."
Sai lokacin ta d'anyi zaune akan kujera tana kallon d'akin da kyau, k'aramar panka take kallo a ganinta ba zata musu komai ba, muryar Umar Faruk ce ta katse yana fad'in "ya jikin Mama?"
Kallon Mama tayi tace "dama baku da lafiya ne?"
"A'a 'yata, ai nama ji sauk'i."
Umar Faruk ta kalla dan haka yace "hawan jininsu ne ya tashi, amma sunsha maganinsu."
"Wane irin magani, kuma baku kaita asibiti ba?"
"Eh, akwai maganin da aka rubuta musu, to shine suke anfani dashi." cewar Ruk'ayya dake gyara shinfid'a.
"Amma ai hakan bai dace ba, me zai hana ku dinga kaita asibiti duk lokacin da bata jin dad'i? amma zama da ciwo ana shan magani barkatai."
Tsam ta mik'e daga kujerar ta durk'usa kusan Mama ta tallabota ta zauna daidai, kallon Ruk'ayya tayi tace "ki bani hijab d'insu."
Ba tace komai ba sai hijab d'in data mik'o mata, saka mata tayi sannan tayi tsaye tana ciccib'ar Mama tana fad'in "muje asibiti Mama, lafiyarki tafi komai mahimmanci, kuma suma kansu yayanki nasan sun san da haka, amma babu mai fasahar kaiki asibiti, sai sun rasaki kuma za kiga sunfi kowa damuwa da kuka."
Kallonta kawai Umar Faruk da Ruk'ayya da sauran yaran suke, tsaye yayi yana fad'in "ba wai bamu damu bane, muma muna...."
"Dan Allah kayi shiru, ni ba tambayarka nayi ba."
Mama ce tace "'yata dama kin barshi wallahi, naji sauk'i ai da dama jikin ba kamar d'azu ba."
"A'a Mama muje kawai, sai dai kuma ko kina so ki nuna min ni ba 'yarki bace."
Suna fitowa farfajiyar gidan ta kalli Umar Faruk tace "ka rik'e Mama, zan d'auko makullin mota."
Tana fitowa kuma da makullin da post d'inta ta kuwa haka ta rik'e Mama har suka fita inda Baba ya fito da su tafi tare amma Khairat tace kawai yayi zamanshi, tare da Umar Faruk suka tafi suna gaba ita dashi tana tuk'i, Mama na baya in banda addu'a da qaunar Khairat babu abinda take ji, bata san kuma me yasa ba amma taji daga haka son sarakuwar tata ya kamata, suna zuwa asibitin da taje da safe docteur Sadiya ta tafi sai wani docteur d'in, cikin qwarewa ya duba Mama kuma ya fad'a musu jininta ya hau, allura aka mata na saukar da hawan jinin sannan aka rubuta wasu magunguna masu matuk'ar tsadar gaske, ita ta biya kud'in sannan suka kamo hanyar gida, saida ta tsaya babban pharmacie ta siyo duka magungunan sannan suka tafi gida dare yayi sosai lokacin.
Har d'aki suka kai Mama ta kwanta Khairat taja zanin rufa ta rufeta, gefen fuskar Mama ta shafa tace "kiyi bacci Mama, dan Allah banda damuwa da tunani, ki more baccinki babu mai takuraki."
Mik'ewa tayi tana fad'in "saida
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23 Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63