wannan karan aljanu sun raina masa hankali, dan lokacin farko daya fara taimakawa Bala sai suka nuna sun tafi, amma ganin hakan a yanzu ya nuna mishi suna cikin jikinshi kuma sun mishi raunin da harya tab'a zuciyarshi, da qyar Bala ya rik'e hannun Umar Faruk ya fara magana cikin rawar jiki yana fad'in "ka ka....ya femin.....ka roqar min..."

Bai qarasa ba ya fara da "Ashhadu an la'ilaha illalah.....tare da taimakon Umar Faruk ya qarasa karlmar shahada.

Koke koke iyalinshi suka fara amma dole dai ayi hak'uri.

😭😭😭😭😭😭 *Zuby anyi rashin uba*


Dare ne dan haka suka d'aukeshi izuwa asibiti dan a ajeshi wajen ajiyar gawa, tun a hanya Aliyu ya kira ya fad'a masa Salim na kan hanyar zuwa wajen, dan haka koda ya ajesu ya taka mota da k'arfi ya isa wajen, kuma zuwanshi yayi daidai da isar Salim wajen yana kiran lamba da Aliyu ya kirashi, Aliyu na ganin motar Umar Faruk ya fito daga wajen daya b'uya danya kalli drama, fitowa yayi daga mota ya tunkari motar Salim, shima yana ganinshi fitowa yayi da niyyar yi mishi magana, da fara'a Umar Faruk ya bashi hannu suka gaisa yana fad'in,

"Petit frère (qanena), yana ganka nan?"

Jin Umar Faruk bai saki hannunshi ba kuma yana nufa dashi wani kango yasa yace "ina jiran wani ne anan."

A lokacin har sun shiga ciki, sakin hannunshi yayi ya tsaya bayanshi, juyowar da zaiyi ya d'aukeshi da mahaukacin marin da yasa ya fad'i kwance kamar sumamme....


_Hhhhhhhhhhh, akwaita fa_

A firgice Salim ya tashi zaune yana dafe da kunci yana ja da baya yana kallon Umar Faruk dake matsowa kusanshi, "kai, meye haka, kana da hankali kuwa, kasan me kayi, ni ka mara? wallahi zaka....." bai qarasa ba Umar Faruk ya matso kanshi ya shaqo wuyan rigashi, jayoshi yayi qiiiii a qasa har saida ya kaishi gaban wani dakali sannan ya zauna ya sashi gaba yana qara had'e rai, kukan da Salim keyi ne yasa daka mishi tsawa yana fad'in "yimin shiru."

Tsaf Salim yayi shirun yana kama baki, a kausashe yace "tambayarka zanyi, kuma ina buqata sanin gaskiyar al'amarin, idan kuma kamin qarya, wallahi saika gwamaci kid'a da karatu."

Kai kawai Salim ke d'agawa alamar toh, cikin daga murya yace "kana jina?"

"Eh, ina jinka, wallahi ba zan maka qarya ba."

"Da kyau." Umar Faruk ya fad'a yana shafar fuskarshi da hannu d'aya, d'aya hannun kuma ya ciro wayarshi ya dannan wajen records d'in murya kafin ya d'ora da "naje har gidanku, kuma na gana da mahaifiyarka ta fad'a min komai, dan haka abinda nake son sani daga gareka shine, ya akayi ka shirya duk abinda aka shirya, sannan su waye masu hannu a ciki?"

Gyara zama yayi yana shafar kuncinshi dake mishi zugin zafin masifa ya fara da "wallahi son kud'ina ne ya jamin nayi duk abinda nayi, mun fara had'uwa da Odette ne a unguwarmu taje gidan wata qawarta 'yar fara, itace ta fara min magana tace wankana ya birgeta, na nuna mata jin dad'ina saita d'auki kud'i ta bani, daga nan duk lokacin da tazo saita nemeni mun gaisa, shine wata biyu daya wuce tazo min da maganar tana so ta sani wani aiki, nan ta fad'a min zanje gidan Mani Bukar a matsayin d'an da suka haifa bata hanyar aure ba, amincewar da nayi yasa ta fara kaini asibiti aka min gwajin da ake so yazo d'aya dana Mani Bukar, cikin ikon Allah sai jininmu yazo d'aya amma sauran qwayoyin hallitarmu sunsha banban, nan ta sanya likitan ya rubuta duk wani gwaji ya zama iri d'aya tsakaninmu ta yanda zan zama kamar d'an cikinshi, kuma bata tsaya nan ba saida ta ziyarci asibiti har hud'u wanda tasan Mani Bukar zai iya tuntub'a idan har bai yarda da abinda muka zo mishi dashi ba, daga cikin likitocin da Papa ke huld'a dasu harda likitanshi na gida daya yarda dashi fiye da kima, hakan yasa ta had'a takardu na qarya da zasu nuna ni d'anta ne kuma jinin Mani Bukar, kuma koda aka kawoni ma muka je asibiti wannan sakamakon qaryar aka fad'a mishi da yasa na zama d'anshi."

Shiru yayi yana zare ido yana kallon Umar Faruk, ganin yana kallonshi yasa yace "ina jinka, baka fad'a min masu hannu a ciki ba."

"Odette, itace alhakin shirya komai, amma dai nasan tana aiki da Sani Saley."

"Bayansu baka san wasu da take mu'amula dasu ba?"

"Gaskiya ban sani ba, amma dai akwai wata mata da suke zuwa tare da 'yar fara, ranar ma dana kai Odette gidan Sani Saley na tarar da wannan matar tare da 'yar fara, sai kuma wasu samari guda hud'u, naji da kunnuwana suna magana akan wani shiri da zasuyi akan Mani Bukar, amma bansan ko menene ba."

"Kenan baka san waya tura maganar kai d'an Mani Bukar bane a social media?" cewar Umar Faruk.

"Na sani, wannan samarin ne, kuma naji suna cewa zasu tattaro sauran matan da Mani Bukar yayi alaqa dasu."

Hararanshi Umar Faruk yayi yace "kar kamin qarya fa."

"Wallahi ba qarya bace, basa doguwar magana idan ina wurin."

"Kenan su sukace ka dingawa iyalenshi iskanci da shaqiyanci?"

"Eh, saboda suna so na baqantawa matarshi rai da Khairat, kuma wannan matarce tace na dinga yin haka, amma duk kud'ad'en da nake amsa nine keyin gaban kaina saboda na samu na fitar da kaina kafin ta kwab'eme mumu."

"Wacece matar?" ya tambaya a daqile.

Shiru yayi alamar tunani kamar kuma an tsokaleshi sai yace "yawwa na tuna, sunan *Asma'u*."

Wani bazawarin murmushi yayi na gefen labb'a, tsayar da d'aukar yayi a wayarshi sannan ya tashi tsaye yana fad'in "bansan ko zan iya taimakonka ba idon doka tazo hawa kanka, dan haka kayi ta kanka."

Ficewa yayi ya samu Aliyu suka d'auki hanyar gida, kiran Khairat ne ya shigo wayarshi ya d'auka,

"Ka kyauta baby, wuni d'aya har ana shirin kwanciya bacci amma ka kasa zuwa gaka matarka da yaronka."

Cike da kasala yace "ayyah baby, kiyi hak'uri ki yafe wa wannan hamagon mijin naki, yanzu haka a hanya nake zanje gida, abubuwa sun faru da dama yau d'in nan, amma dai zuwa gobe da safe nasan zakiji wasu labarai marasa dad'i."

"Subhanallah, meye faru baby?"

"Um um, ba yau ba, saida safe zan fad'a miki insha Allah."

Cikin kukan shagwab'a tace "yanzu kenan ba zaka zo ka ganni ba, nifa ina son ganinka."

Cikin rikitaciyar murya yace "na fiki son na ganki, kin manta yaushe rabon damu had'u ne? aiki shirya kawai, amma idan na kamaki wallahi dole yarona ya samu ingantanccen abincinshi yaci koya samu kuzari."

"Kai baby , wane irin abinci kuma?"

Saida ya d'an cije lips kamar yana gabanta yace "wannan sirri ne, amma idan na daukoki kika dawo gidana, to zaki sani."

Cikin wani kukan shagwab'ar tace "hum hum, wallahi ni har kasa na fara jin tsoron had'uwarmu, dan kasan fa ba 'yar qaramar jarumta nake yi ba wajen d'aukarka, amma yanzu nasan zaka sausauta min saboda abinda ke cikina."

Darayi yayi yace "ashe ana jin maza dauriya kawai akeyi, to karki damu, jarumin mijinki zai dinga sassauta miki, kiji dad'i abinki *maini*."

"Yawwa yaron kirki, ina sonka."

"Nima ina sonki alkairina, saida safe."

Yana kashe wayar ya kalli Aliyun da yake kallonshi kamar wani gunki, maida hankalinshi yayi ga tuqi yana fad'in "yadai Aliyu, da matsala ne?"

Ajiyar zuciya ya sauke yace "gaskiya da matsala."

"Tame?" ya fad'a yana kallonshi.

Gyara zama yayi yace "yanda naji kuna farin ciki kai da aunty Khairat, saiya qara min son aure a zuciyata wallahi."

Murmushi kawai yayi suka ci gaba da tafiya, saida suka kusan kaiwa gida sannan yace "kana son aure kenan?"

"Ina so, amma kasan ba lallai malam yamin ba."

"Me yasa?"

"Saboda nayi qarami."

Daga gira yayi sama yace "a hakan, kana shakara ashirin da d'aya ne za ace kayi qarami, gashi kuma soyayyar wasu ma na birgeka, kaga indai kana so ni zanyiwa malam magana, kuma kaima kasan zai fahimta, fatana kawai Allah ya had'a da mace ta gari mai tsoron Allah, faqat."

"Ameen yah Umar, ai yama had'a insha Allah."

"Toh , wacece wannan?" ya tambaya cikin 'yar dariya.

Shima cikin dariyar yace "wannan yarinyar mana, qanwar aunty Saratu, *Firdaussi*, gaskiya ina sonta, kuma tana da hankali sosai."

Shiru Umar Faruk yayi yana tuna kullum tazo gidan nan to ranar gidansu saiya shaida tazo saboda hidimar da take mishi, bugu da qari inhar zata gaishe dana sama da ita to zata sunkuya har qasa, da haka suka isa gida Aliyu ya nufi makwancinshi sai Umar Faruk daya shiga d'akin Baba ya fad'a mishi rasuwar Bala, fitowa yayi ya baroshi yana jimamin abin, d'akin Zuby ya kalla yaga amma yaga alamun tana ciki, tab'e baki yayi ya wuce d'akin Khairat, dan iba tilastashi za ayi ba ba zai tab'a maido da ita ba cikin sauk'i haka.


*Washe gari* da safe duka mazan gidan malam ya had'a kansu suka tafi wajen jana'izar Bala, Zubeida na d'aki bata san wainar da ake toyawa ba tanata had'a kaya, su kuma basu fad'a mata ba saboda ganin halin da take ciki, sun jima zaune acan kafin suka taso suka dawo gida, sai lokacin Zuby tayi niyyar barin gidan saboda tunanin malam ba zai bari ba, Umar Faruk na shirin shiga d'akin Mama Zubyta fito da kaya da ciki, Mama ce tayi saurin cewa "Ina zuwa haka Zubeida?"

Tana kallon Mama saita fashe da kuka, hankali tashe Mama tayi kanta da sauran matan gidan suna tambayar lafiya, durqushewa tayi a wajen tana ci gaba da kuka, haushi ne yasa Umar Faruk qarasa shiga d'akin ya zauna yasa kwanan abinci gaba yana jiran a kirashi, cikin kuka tace "sakina yayi."

"Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." shine abinda uwayen suka fad'a a tare.

Baba ne yace "saki fa, Umar Faruk d'in?"

"Kai Umar." cewar Baba cikin d'aga murya.

Da "na'am" ya amsa yana fitowa daga d'akin, yana zuwa gabansu ya durqusa yana sauraronsu, "me yarinyar nan ta maka da zaka saketa a wannan halin, me yake damunka ne?"

Ba tare daya kalli Baban ba yace "Baba ku gafarceni, nasan hakan ba zai muku dad'i ba dama, amma nasan kunsan haka kawai ba zan d'auki wannan matakin ba ba tare da wani dalili ba, a gaskiya zamana da Zubeida ba zaici gaba da yiwuwa ba a haka, shi yasa na kawo qarshen abin."

"Meta maka, wane irin laifi ta maka da zaka yanke wannan hukuncin a kanta, kasan abinda zai iya biyo baya a dalilin abinda kayi?" cewar Mama cikin hushi.

"Babu abinda zai faru Mama, kuma fa Allah ne ya hallata aure ya kuma hallata saki, amma gata nan ku tambayeta idan nayi mata rashin adalci a wannan lamarin."

Maida kallonsu sukayi gareta Mama tace "me kika mishi ke kuma?"

Shiru tayi sai goge hawaye take, Baba ne ya qara "me kika mishi Zubeida?"

Kallon Umar Faruk tayi da tace bata mishi komai ba, amma ganin shima ita yake kallo, dan haka tayi shiru daga abinda taso fad'a, ganin ta kasa magana yasa ya mike yana fad'in "bance ki fita daga d'akinki ba ai, ki zauna anan harki haihu." yana fad'a ya fita daga gidan, hanya ta kama zata fita Mama tace "a'a babu inda zaki je, ki zauna kiyi iddarki kamar yanda yace."

Duk da cikin kuka take saida tace "Allah ya sawaqe, kenan ni gani marar zuciya, ya sakeni kuma yace na zauna nayi idda anan, to ba zai yiwu ba wallahi, ai nima da gidanmu, kuma kunfi kowa sanin inda ya d'aukoni, dan haka banga wanda ya isa ya rik'eni ba wallahi."

Zata wuce Baba yace "kash Zubeida, banji dad'in fitar wannan kalma daga bakinki ba, abinda muka fad'a miki yanzu ba fad'armu bane, wannan fad'ar ubangijinmu ne wanda shi yafi sanin daidai yake kuma tsara mana rayuwarmu, karki bijerewa umarnin Allah da manzonsa, hakan zai iya jefaki cikin hushin ubangiji, amma in kinga hakan bai miki ba to ga hanya nan ki wuce."

Suna kallo itama ta sulalata fita daga gidan tana kuka, Mama kuma haushin Zubeida ne ya kamata sosai, sai taji koba komai d'anta zai iya tsira daga sharrin 'yar uwarta.

***************

Koda taje gida ta fad'awa tanti tashin hankali da masifa kam ta shasu, zagi kuma ba Umar Faruk ba har malam ya samu rabonshi, haka dai ta gaji da masifa Zuby na sauraranta harta d'auki gyalenta ta fita daga gidan.

_Hmmm, yanzu ma kika fara gani._


*****************

Shima koda ya fita daga gidan gidansu habibiyarshi ya nufa, da sallamarshi kuwa suka amsa mishi suna zaune falo, kamar yanda yanzun ya fara zama jiki a wajen Papa zaman gida, zaune yayi suna gaisa har Salim ya fito daga d'aki, kallonshi kawai Umar Faruk keyi wanda Salim kad'ai yasan ma'anarhi, saida ya zo tsakiyar falon ya sunkuya yana kallon Umar Faruk yace "Ina kwananku."

Papa da Mamie basu amsa ba saboda mamaki, sake fad'in "ya tashin asuba?"

"La...fi.....ya lau." cewar Papa yana mamaki.

Murmushi Umar Faruk ya kalli Mammie yace "Hajiata ina d'aya Hajiar tawa?"

Turo baki tayi da kawar da kai tana fad'in "ban sani ba."

Mikewa yayi tsaye ya matsa kusanta yace "ran gimbiya ya huce, kinsan bana son hushinki, fad'a min inda zan ganta ko hankalina ya kwanta?"

D'an dukan damtsenshi tayi tana fad'in "hankalin sarki ya kwanta, sarauniyar tana d'aki."

Da dariya ya nufi d'akin ya bar Salim durqushe anan, yana ganin Umar Faruk ya shige d'akin Khairat ya mik'e tsaye da sauri ya bar gidan gabanshi na fad'uwa yana tunanin ta yanda zai bar gidan nan cikin sauqi, bai zame ko ina ba sai gidansu wajen mahaifiyarshi, da shigarshi ya fad'a d'akin nasu daba kayan kirki, tana kwance ya fara kiran sunan "Ma, Ma, tashi dan Allah zama bai kamamu ba."

Tashi tayi zaune tana kallonshi, "Maa , ki tashi fa."

"Meya faru, ka sake jangwalo wata tsiyar ko? anya Salim kana tuna waye kai?" duk tayi maganar ne tana tashi tsaye.

Kallonta yayi yace "Maa, ba lokacin wannan nasihar taki , yanzu ki had'a mana kayanmu gaba d'aya ki kimtsasu, daga yanzu zuwa ko wane lokaci zanzo mu wuce *Maradi*, tunda can danginmu suke."

Yana fad'a bai tsaya jin ta bakinta ba ya fita a guje, ita kuma da kallo ta bishi har saida ya fita, fashewa tayi da kuka tana fad'in "Salim wace irin rayuwa ka jefa kanka cikinta ka jefani , me zan fad'awa dangin mahaifinka yanzu idan wani abu ya sameka?"

Ganin bata da wani zab'i yasa ta fara had'a musu kayansu, dan ita kanta tayi farin ciki da hakan idan suka bar garin.

**************

Yana shiga ya sameta kwance tana bacci, zaune yayi kusanta yana kallon fuskarta ganin kyawunta harya fara dawowa, ya jima yana kallonta kafin ya tasheta, da taimakonshi ya cire mata kaya ya kaita bayi dan wanka, harya ajeta a cikin bahon wanka yana kallon tanqamemiyar douche d'in, a zuciyarshi kuma yana sake jinjina hak'uri da sadaukarwar da Khairat tayi domin aurenshi, kallon ko ina yake yana ganin tsabagen tsagwaron kud'in da aka narka wa bayan gida kad'ai, wannan idan ka shigo ai awa d'aya ba zata saka ka fita ba *(inaga fa wannan shine dalilin da yakesa Khairat bata fitowa da wuri)*, ganin yanda yake kallon wurin yasa tace "baby ya dai?"

Nunfasawa tayi yace "Ina kallon ikon Allah ne, ashe haka douche d'inki take da kyau da girma, shi yasa ranarki ta farko a gidana kika kasa shiga tawa douche d'in, gaskiya bayan ganin wannan kyakyawar douche d'in taki sai naji kunyar kaina."

Ruwan cikin bahon ta d'iba ta watsa mishi tana fad'in "ka ganka ko, ni kuma yanzu nafi jin dad'in wacce qaramar."

"Hum, wasu shashashu na cewa wai *jihadi* nayi na aureki, amma basu san cewa Khairat ce tayi *jihadi* ba data zauna da Umar Faruk."

Hannu yasa cikin bahon ya fara zuba mata ruwa a jikinta, da kanshi ya mata wanka ta fito daga bahon ya b'oyeta cikin towel sannan ya kaita d'aki, kafin ya gama shiryata ya jima sosai da saida ya rage zafi sannan, a lokacin kuma suka fito falo tare ya fad'a musu rasuwar Baban Zuby, sunyi jimami sosai musamman Khairat sai taji kamar wani babanta ne ya rasu, shiryawa sukayi suma suka tafi wajen rasuwar.


****************

Sai yamma tanti taji rasuwar nan sannan Zubyma taji, uba ubane, saida Zuby tayi kuka sosai tayi jimamin mutuwarshi, tanti ce tace ta shirya taje amma ita ba zata je ba, dan haka Zuby ta nemi rankiyar Zabba'u kuma ta samu.


*Da safe* Zabba'u tazo suka wuce, Zuby taji inama bata je ba, dan matanshi ne suka dinga fad'in ita d'in yarshi ce amma basu san taya ta zama ba, nan aka fara tsurfa iri iri har zuwa ake ganin Zuby, wasu na tambayar wacece mahaifiyarta wasu na tambayar taya ta zama yarshi, saida ta gaji Zabba'u ta janyota suka koma gida.


**************

*Kwana biyu* Umar Faruk ya qarasa had'a duk wasu hojjoji da suke nuna Salim ba dansa bane, kuma shirene na yan adawa tare da hadin gwiwar wasu tsofaffin masu laifi, abinda ya mishi dad'i sosai shine sake binciko mishi wani laifin Musa da Abdul Waid yayi, an sake kama shi da laifin yiwa wata budurwar fyade a wani qauyen *Agadez* da ake kira *Adarbisa* , babban abin farin cikin shine saida Abdul waid yasa wani jami'i dake can garin ya samo mishi cikakkiyar hujja a kan hakan, kuma anyi nasarar samun abinda ake nema, dan haka yau koda ya tashi da kanshi ya ziyarci offishin lawyer Papa.

Bayan gaisuwa ya fad'a mishi abinda ya kawoshi, nan ya nuna mishi jin dad'inshi kuma ya mishi alk'awarin za'a shigar da qara nan bada jimawa ba, amma zaije a nemi amincewar Papa dasa hannunshi, alfarma Umar Faruk ya nema kan baya so asan da hannunshi a ciki, kuma ya amince da duk abinda ya fad'a, a haka suka rabu shi kuma ya kama hanyar auwa gidan Papa.

***************


Koda yaje da maganar ta girgiza Papa sosai, Khairat kuma tace "ai dama na fad'a muku, wannan yaron ba zai tab'a zama danka ba kawai raina maka hankali sukayi."

Da mamaki cikin rud'ewa Papa yace "taya haka zata kasance, docteur *Shehu* fa da kanshi ya mana gwaji kuma ya tabbatar."

Lawyer ne yace "ka kwantar da hankalinka Alhaji, muna da duk wasu hujjoji a hanunmu , koma miye dai zaka ji."

Umarni Papa ya bayar aka shigar da qarar, take aka kai magnar babbar kotu, kamar yanda aka sallama gidan Sani Saley aka bashi takardar sammaci, haka su Musa da sukaga takardar sukayi mamaki, dan a ganinsu babu wanda yasan da fitowasu bare mafakarsu, Odette ma na tsaka da jin dad'in rayuwarta aka kawo mata wannan takarda da tasata gudawa tsawon wannan yinin , tanti
Showing 168001 words to 171000 words out of 186119 words