fara durk'ushewa sakamakon yawan bani bani da take masa kuma bata bari ya fita ya nema, a hankali sai abubuwa suka fara canza musu har takai ya fara siyar da k'adarorinshi daya mallaka.
A lokacin kuma ciwo yaci qarfin mahaifiyarshi, amma babu kud'in da zai iya siya mata koda magani bare ya kaita asibiti, da qyar Asma'u ta bashi izinin zuwa yaga mahaifiyarshi bayan dogon rarrashin daya mata, yana zuwa kuma ya makara dan sai gawarta ya samu, ya girgiza sosai da mutuwar mahaifiyarshi, amma rashin imani na Asma'u bata barshi ya qarasa jimamin rashin mahaifiyarshi ba ta fara azabtar dashi ta wata sabuwar hanyar, a lokacin ta fito da wani sabon salo ta hanyar d'ora mishi duk aikin gida, saboda kawai yanzu ba yada komai, kuma duk abin nan da ake akan idon 'ya'yansu mata guda uku da Allah ya basu, ko sau d'aya bata tab'a tunanin yayanta mata bane kuma zasu iya koyi da ita, haka take azabtar dashi yaran kuma na gani kuma dukansu basu damu ba, dan dama tana d'orasu ne akan turbarta.
Kasancewar suna nesa da gida yasa iyayenta da 'yan uwanta basu riga sun fahimci halin da take ciki ba, a ranar da suka samu labari mahaufiyarsu tayi tattaki izuwa gidan, anan kuma idanta ya gane mata tabbas, danta samu Hamza ya tak'ark'are yana sharar gida, ran Fateema ya b'aci sosai kuma taji kunyar abinda ta gani, amma abin takaici shine, koda ta fara mata magana akan abinda take saita mik'e ta fara zuba rashin mutunci da fad'a, cike da quna Fateema tace,
"Yanzu Asma'u ni kike fad'awa wannan maganar, ni kike kallo kike fad'a min wai na takura miki?
Cike da rashin kunya tace "eh mana, na fad'a miki, gidana fa kika zo, kuma naga mijina ne ba mijinki ba, to miye a ciki? nifa ba zan iya wannan banzar rayuwar ba irin taku, kana zaune gidan miji bakin ciki da takaicin namiji ya kasheka , ai muna gani tun muna qanana irin rayuwar da kike a gidan mahaifinmu, hawan jinin da kike fama dashi ma ai duk shine sila, shine kike so nima na zauna ya qaqaba min, wannan da kike gani namiji shima, kuma dana bashi dama babu abinda zai hana yamin tsiyarsu irinta maza."
Cikin sanyin murya tace "naji, tunda haka kika zab'arwa kanki, ga hanyar nan, kuma duniya ta isheki riga da zanin d'aurawa."
Qarasa mata tayi da "harda d'an kwali ma."
"Haka kika ce? shikenan kije , amma ki sani akwai ranar qin dillanci, akwai ranar da za kiyi nadama, bansan ko zamu riski lokacin ba, amma dai nasan tabbas zata zo, kuma ki sani daga yau ba zan qara shiga sabgarki ba."
"To saime, nace saime dan baki shiga sabgar tawa ba? hakan ma yafi min dad'i, yanzu ne kuma zan sake watayawa yanda nake so, dan haka tafi nono fari, danni ko baki kika min ba kamani zaiyi ba." duk tayi maganar ne tana murgud'a baki.
"Haka kike gani, ai kuwa da zan miki wallahi ba zaki kai ko ina ba, amma ina jin tsoron karki qara lalacewa."
"Kiyi mana, wallahi babu abinda zai sameni, ina yin duk abinda nake so kamar yanda nake samun duk abinda nake so, dan haka babu abinda bakinki zaimin ."
"Haka ki kace?"
"Eh, haka nace."
"Shikenan kije , kije kya gani."
"Wallahi sai dai naga alkairi."
Juyawa tayi ta bar gidan rai b'ace tare da tunanin yaushe Asma'u ta zama haka, da wannan tunanin takai gida kuma ta kwanta bacci ba tare data fad'awa mahaifinsu ba, dan tasan inta fad'a masa toshi zai tsine mata ne ba tare da b'ata lokaci ba.
Babu wanda yasan me zai faru a gaba, badan haka ba da Fateema ta janye mugun bakin data ma Asma'u tun kafin ta kwanta bacci, domin kuwa wannan baccin data kwanta bacci ne na qarshe, baccin da babu tashi sai lokacin da aka busa qaho na biyu.
Haka lokaci yaja sosai babu abinda ya sauya a game da al'amarin Hamza, har suka aurar da *Salamatu* wacce suke kira da Uwani, da kuma Zulfa'u ya rage Zabba'u, lokacin kuma aka samu cikin Zuby amma sam Asma'u bata bari Hamza ya sani ba, domin kuwa cikin ba nashi bane na abokinshi ne, kuma hakan ta faru ne lokacin da abokin yazo gidan domin sanin meke faruwa ya daina fita, daga ranar suka qulla wannan alaqar kuma tana jin dad'in haka saboda yana sakar mata kud'i masu yawa, sai dai ta manta da ciki d'an dumane dole wata rana zai fito kuma ta haifeshi.
A ranar da Hamza yaga cikin kuwa, ya sameta ne d'akinta kwance da kayan bacci, anan yaga cikin dake jikinta d'an wata shida zuwa bakwai wanda take b'oyewa kullum,
"Me zan gani haka Asma'u?" ya fad'a yana sake kallon cikin gidan nata.
Cikin baccin daya fara d'aukarta taji muryarshi, a zabure ta tashi zaune tana d'aukar hijabin da take ajewa saboda gudun irin haka, cike da dakiya tace "mefa kake gani, miye haka zaka shigo min d'aki a wannan daren?"
"Asma'u, ciki fa nake gani a jikinki, ko kuma kina so kice min wannan ba cikin mutum bane?
"Ciki kuma, a ina?"
Da hannu ya nunata amma ya kasa fad'ar komai saboda yanda zuciyarshi ke bugawa, ya jima yana nuna hannun amma baice qala ba, daga haka kuma ya fad'i qasa wanwar , fashewa tayi da qara hakan yasa Zabba'u fitowa daga d'akinsu, nan dai aka samu aka kaishi asibiti amma ina lokaci yayi Hamza, shima nan aka tabbatar musu da zuciyarshi ce ta buga, Asma'u bata ji mutuwarshi ba saboda lasisi ne ya bata ci gaba da harkarta, bayan wattani kuma ta haifi Zuby kuma samu kulawar mahaifinta wanda mutane sukewa kallon aminin mahaifinta, sai dai tunda akayi arba'in d'in Zuby shima Alhaji *Bala* ya fita sabgarta, da farko tayi yunkurin tona musu asiri, amma sai Bala ya nuna mata ya fita zama d'an iska, domin kuwa cewa yayi taje ta fad'a, shi namiji ne bai gudun abinda mutane zasu ce, bayan tunani da tayi saita fahimci ita zata jefa kanta rijiya, dan haka taja bakinta tayi shiru.
Sai dai rayuwar ta sauya musu sosai, dan abinda zasu ci wani lokacin wuya yake musu, wani lokacin ma saita d'an kula maza kafin ta samu abinda zata ciyar da Zuby da kanta, rufi asiri d'aya shine su Zulfa'u suna taimaka musu wani lokacin, a haka rayuwa ta tafi har girma ya risketa tare da yarta Zubeida.
Ba tayi qasa a gwiwa ba wajen zuwa wajen malam tare da fad'a mishi abinda ya kaita, bud'ar bakin malam cewa yayi "tabbas, wannan yaron zaiyi arzik'i, kuma arzik'in zaizo ta sanadiyar matarshi ne ta farko."
"Ban gane matarshi ta farko ba, kana nufin ba yata kad'ai zai aura ba, kuma wacce zai aura farko itace silar arzik'inshi, to wacece ita.?"
Rarraba ido yayi, dan na farko ma yayi qarfin hali ne ya fad'a da d'an abinda shed'anu suka nuna mishi, duk da yasan ba lallai gaskiya bane, amma saboda ita d'in abokiyar harka ce ba zaiso mutuncinshi ya zube ba, dan haka yace "haba Ma'u, ai 'yar taki nake nufi."
A wulak'ance tace "ka tabbata?"
"K'warai ma kuwa, ai kisan yanda za ayi ki hadasu, dan arzik'inshi na tattare da ita, yarinyar akwai qashin arzik'i."
"Gado tayi gaba da baya." ta fad'a tana yamutsa fuska.
A lokacin da taje ma iyayen Umar Faruk da maganar basu ce komai ba sai fatan alkairi, haka ma Umar Faruk da aka fad'a mishi, bud'ar bakinshi cewa yayi "Allah ya sanya alkairi."
"Ameen, Allah ya maka albarka." cewar Mama
"Ameen."
Daga wannan rana ne sai Asma'u take turo Zuby gidan tazo har takanyi sati biyu wani lokacin, shakuwa ta shiga tsakaninsu duk da dai Umar Faruk baya jin komai a zuciyarshi a game da ita, amma a lokacin da girma ya qara zuwa masa ya sake mallakar hankalin kanshi, a lokacin yana da shekara *30* sai buk'atar aure ta kamashi, amma sam Zuby tak'i amincewa tace saita samu certificat d'inta na (BEPC) sannan suyi aure, dole ya hak'ura tunda baida wacce yake so kuma baya da ra'ayin yin mata biyu a cikin qananin lokaci da kuma qarancin shekarunshi.
*Wannan* ne dalilin da yasa tanti ta tsani Khairat ba tare da wani dalili ba, ta yarda d'ari bisa d'ari akan abinda malam ya fad'a ,musamman da tasan Khairat 'yar babban mutum ce, tasan ba makawa sai yayi kud'i ta silarta, hakan yasa ma tayi gaggawar shigo da Zuby gidan.
*WANNAN KENAN*
πππππ
*_CIGABAN LABARI_*
Tana d'auka yace " ina kika je?"
Cikin gunaguni da harare tace "ina gida wajen Mama."
"Da izinin wa kika je?"
"Toh , wajen mahaifiyar tawa ma da zanzo saina fad'a maka? to da izinina nazo."
Da qyar ya taushi zuciyarshi yace "naji, na miki uzuria karo na farko, amma ki sani kika sake maimaita irin haka, wallahi ranki idan yayi dubu zai b'ace, sannan, ki gaggauta dawowa gida nan da minti talatin ina jiranki."
Yana fad'a ya kashe wayar ita kuma ta kalli Mama tace "kiji rainin wayo."
Shiru Mama ta mata ganin haka yasa ta tashi ta kimtsa nata yanata sukayi sallama ta kama hanya, dan nisan dake tsakani ma zai iya d'aukarta minti talatin d'in, da qyar ta samu taxi ta hau, koda taje bata samu Umar a gidan ba, hakan kuma ya mata dad'i sosai.
*************
B'angaren Khairat kuma tana babban shagon siyayya , kud'i kawai take kashewa yayin da take tuna iya mutanen dake cikin qwaqwalwarta take siya musu kaya, ta jima sosai kafin ta fita ta d'auki hanyar komawa masaukinsu, tana zuwa su Mammie ita suke jira , dan haka basu b'ata lokaci ba wajen isa filin jirgi kuma suka tashi da izinin Allah suka sauka lafiya.
_Me kuma zai faru yanzu? my Hajja fa ta dawo._
*Kamar yanda na fad'a, babu abinda zai tsayar dani rubutu idan harna fara rubutawa,amma fa akwai yiwuwar na dakatar da rubuta _Jihadi_ na d'an wani lokaci, danna lura kamar kun fara gajiya da comment, comment bawai yana nufin a turo makaπ tsalle koπ€Έββtalar qafafu ba, ko striker dake cinye data, tabbas muna jin dad'in addu'a, amma mutum yayi sharhi akai shine zai baka tabbacin an karanta abinda ka rubuta d'in, so idan kun gyara zanci gaba, idan ba haka baπbana da matsala, zan sawake ma kaina ta hanyar ajiyeshi gefe ko kuma na dinga turawa masu so na fita daga duk grp d'in da basa comment.*
_Ina muku barka da sallah, Allah ya nuna mana ta bad'i, Allah ya karb'i ibadunmu , Allah ya gafarta mana zunabanmu, Allah yasa muna cikin bayin da aka 'yanta._π *Ameen ya Hayyu ya Qayyum.*
14/08/2019 Γ 15:32 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Sufa iyaye girmane dasu, samun Zuby bata hanyar aure ba yana d'aya daga cikin kamun da bakin mahaifiyar Asma'u ya fara mata, kuma wannan ba abun mamaki bane danni naga irin haka da idona.*π
_Muje zuwa masoya masu fahimta_π
_Bismmilahir-rahman-rahim_
4β£3β£
Driven gida ne ya kawo Khairat saboda shiya d'aukosu daga filin jirgi, saida ya shigar mata da kayan cikin gidan kafin ya wuce, nanfa yara suka mata ca suna mata sannu da zuwa, haka ma manya sannu suke mata cikin murna, jin ana sallah isha'i a masallaci yasa Khairat kallon duka mutanen wajen cikin farin ciki tace "zanje nayi sallah, amma kumin alk'awarin ba zaku fad'awa Faruk ba."
Fateema da Zeinab ne suka amsa da "munyi aunty."
Kumatunsu ta shafa tace "da kyau 'yan mata, zan wuce, idan na fito zan baku tsarabarku."
Wucewa tayi Ruk'ayya tabi bayanta da kayanta, tana shiga d'akin taga yasha gyara, kallon Ruk'ayya tayi tace "kece ko?"
Cikin dariya tace "eh aunty, ai naga bakya son k'azanta, shi yasa nake shigowa ina gyarawa duk da ba kya nan."
"Kin kyauta." ta fad'a tana shirin fitowa yin alwala.
"Amma fa aunty naga sai farin ciki kike, kodai da wani abu ne?" cewar Ruk'ayya.
Cak Khairat ta tsaya amma bata juyo ba, ajiyar zuciya ta sauke mai nauyin gaske, ita kanta haka take ji tana farin ciki, kuma baya rasa nasaba da kusanto da kanta da tayi wajen Umar Faruk, ba tare data juyo ba kuma ta wuce ta fad'a 'yar qaramar toilet d'insu, koda ta fito bata samu Ruk'ayya ba, a haka ta kabbara sallah kuma harta kammala Umar Faruk basu shigo ba.
Jakar data zuba tsarabara ciki ta janyo ta fito da ita tsakar gidan, fitowarta yayi daidai da fitowar Zuby daga d'aki itama, kallon juna sukayi Zuby kuma ta bita da harara, Khairat kuma binta tayi da kallon zan kamaki a hannuna, wajensu Mama ta nufa inda suke zaune akan tabarma, zaune tayi itama tana cire hijab d'in jikinta danya d'an takurata sannan ta bud'e jakar, kayan kanti ne masu kyau da qualitie wanda ta siyowa Zeinab, Fateema, Yusuf, Ubaidullah, Bilal, Abdul rahaman, bawa kowa tayi sai lokacin ta fahimci ba kowa ya samu ba, dan dama ba wani sanin yaran tayi ba tayi anfani da ganinsu ne yau da gobe, kallon sauran tayi tace "ayya, kuyi hak'uri kunji, insha Allah kuma zan siyo muku naku."
Mama Sa'a kuma cewa tayi "haba, aiba komai ba, wannan ma an gode wallahi, Allah yashi albarka."
Mama kuma dad'i taji sosai saboda ganin anyi daidai, dan Bilal d'ane ga Mama Maimuna kuma ya samu, Abdul rahaman d' ga Mama Sa'a kuma shima ya samu, Zeinab kuma 'yarta ce itama kuma ta samu, sai Fateema da Yusuf yayan Abbakar, suna cikin godiya kuma saiga takalma ta fiddo ta bawa Mama Sa'a Mama Maimuna da kuma Mama, suna da kyau kuma basu da tudu ko kad'an, nanma godiyar suka fara sai kuma ga wasu kayan masu kyau tabawa Ruk'ayya har kala uku, wata agogo ta fito da ita mai shegen kyau qirar rolex ta bawa Mama Sa'a da tafi kusa da ita tace "wannan na Baba ne."
Kafin tayi magana Khairat ta fito da wata agogon qirar gucci ta fata tabawa Saratu tace "na mijinki ne wannan."
Sannan ta bita da wasu had'add'un turare kala uku tace naki ne wannan."
"Kai, amma na gode sosai yer uwa, irin wannan tsaraba haka."
Sallamar Aliyu da Usman ce ta katsesu, 'karasowa sukayi Usman na fad'in "matar yaya, yaushe garin?"
A harshen zarma ta amsa mishi da "ana sallah na shigo."
"Sannu da zuwa, ya hanya?" cewarsu gaba d'aya.
"Lafiya lau." ta fad'a tana mika musu wasu kwalaye wanda ko a cikin bacci aka basu zasu san na miye, Aliyu ne ya waro ido yace " Iphone7, ta mece aunty?"
"Naku ne." ta fad'a ba tare data kallesu ba.
Su kuma mamaki ne ya hanasu karb'a, saida ta juyo tace "baku sone?"
Da sauri Aliyu ya karb'a yana fad'in "ah haba aunty, mu mun isa? mun gode Allah saka da alkairi."
Karb'a yayi duka ya mik'awa Usman d'aya, amma sai Usman yace "na gode, amma gaskiya ni bana so, wannan ma ta isheni."
Ba tare da damuwa ba Khairat ta kalli Aliyu tace "ok , ka bawa maiso ko cikin abokanka."
Mamaki ne ya cika kowa dake wajen, Usman d'in ne yace "kud'i fa kika saka kika siyo saboda ni, me yasa ba zaki aje ba koki siyar?"
Wani d'an murmushi tayi mai sauti tace "ba wakai ba na siyo, na siyo ne wa mutanen da nake rayuwa dasu, tunda baka so ai ba za'a rasa maiso ba."
Gyara zama tayi tana kallonshi tace "da farko na shigo gidan nan ne a matsayin bana son d'an uwanku , duk da haka kuma zan iya sadaukar da komai nawa dominku, yanzu kuma da nake son Faruk, ina ji zan iya taimaka muku da k'arfina ma ba iya dukiyata ba kad'ai, ko zaku kasheni ba zan daina muku alkairi ba domin kuwa a jinina yake, haka ma kome za'a fad'a ba zan daina taimakawa mutane ba."
Tana fad'a ta tashi zata wuce d'aki Mama Sa'a tace "dan Allah yata kiyi hak'uri, karki bi ta abinda ya fad'a."
Juyowa tayi za tayi magana idonta ya sauka akan Zuby dake k'ofar d'akinta zaune, shiru tayi ta wuce d'aki tana ji kamar bata kyauta ba da bata bawa Zuby komai ba, domin kuwa kishiya aina mak'iya bace, coiffeuse d'inta ta kalla, da sauri ta qwala kiran sunan Ruk'ayya, tana shigowa ta d'auki wasu turaruka wanda suke birgeta har guda biyu ta bata tace "ki kaiwa Zubeida."
Da mamaki Ruk'ayya tace "amma aunty sai naga kamar naki, me yasa zaki batasu?"
Cikin d'an murmushi tace "Ruk'ayya, wannan ba komai bane danna bawa Zubeida wannan, itafa kishiyata ce bawai mak'iyata ba, zan iya bata fiye da wannan ma musamman idan ta buqata ko kuma naga buqatar hakan ta kamata."
"To aunty." ta fad'a tare da fita daga d'akin.
Tana bud'a labulen suka ci karo da Umar Faruk wanda labarin zuwanta ya sameshi tun a tsakar gidan, rab'awa tayi ta wuceshi shi kuma ya shiga ciki, Khairat na ganinshi ta daka tsalle tare da qara ta nad'e a jikinshi,shima rumgumeta yayi sosai a jikinshi yana juyi da ita a tsakiyar d'akin yana dariya, cikin murna take fad'in "nayi kewarka sosai baby, nayi kewarka, nayi farin cikin ganinka sosai."
Sauketa yayi da nufin ya mata magana amma saita had'e bakinsu waje d'aya, shima bai tsaya b'ata lokaci ba wajen biye mata suka
Showing 117001 words to 120000 words out of 186119 words
A lokacin kuma ciwo yaci qarfin mahaifiyarshi, amma babu kud'in da zai iya siya mata koda magani bare ya kaita asibiti, da qyar Asma'u ta bashi izinin zuwa yaga mahaifiyarshi bayan dogon rarrashin daya mata, yana zuwa kuma ya makara dan sai gawarta ya samu, ya girgiza sosai da mutuwar mahaifiyarshi, amma rashin imani na Asma'u bata barshi ya qarasa jimamin rashin mahaifiyarshi ba ta fara azabtar dashi ta wata sabuwar hanyar, a lokacin ta fito da wani sabon salo ta hanyar d'ora mishi duk aikin gida, saboda kawai yanzu ba yada komai, kuma duk abin nan da ake akan idon 'ya'yansu mata guda uku da Allah ya basu, ko sau d'aya bata tab'a tunanin yayanta mata bane kuma zasu iya koyi da ita, haka take azabtar dashi yaran kuma na gani kuma dukansu basu damu ba, dan dama tana d'orasu ne akan turbarta.
Kasancewar suna nesa da gida yasa iyayenta da 'yan uwanta basu riga sun fahimci halin da take ciki ba, a ranar da suka samu labari mahaufiyarsu tayi tattaki izuwa gidan, anan kuma idanta ya gane mata tabbas, danta samu Hamza ya tak'ark'are yana sharar gida, ran Fateema ya b'aci sosai kuma taji kunyar abinda ta gani, amma abin takaici shine, koda ta fara mata magana akan abinda take saita mik'e ta fara zuba rashin mutunci da fad'a, cike da quna Fateema tace,
"Yanzu Asma'u ni kike fad'awa wannan maganar, ni kike kallo kike fad'a min wai na takura miki?
Cike da rashin kunya tace "eh mana, na fad'a miki, gidana fa kika zo, kuma naga mijina ne ba mijinki ba, to miye a ciki? nifa ba zan iya wannan banzar rayuwar ba irin taku, kana zaune gidan miji bakin ciki da takaicin namiji ya kasheka , ai muna gani tun muna qanana irin rayuwar da kike a gidan mahaifinmu, hawan jinin da kike fama dashi ma ai duk shine sila, shine kike so nima na zauna ya qaqaba min, wannan da kike gani namiji shima, kuma dana bashi dama babu abinda zai hana yamin tsiyarsu irinta maza."
Cikin sanyin murya tace "naji, tunda haka kika zab'arwa kanki, ga hanyar nan, kuma duniya ta isheki riga da zanin d'aurawa."
Qarasa mata tayi da "harda d'an kwali ma."
"Haka kika ce? shikenan kije , amma ki sani akwai ranar qin dillanci, akwai ranar da za kiyi nadama, bansan ko zamu riski lokacin ba, amma dai nasan tabbas zata zo, kuma ki sani daga yau ba zan qara shiga sabgarki ba."
"To saime, nace saime dan baki shiga sabgar tawa ba? hakan ma yafi min dad'i, yanzu ne kuma zan sake watayawa yanda nake so, dan haka tafi nono fari, danni ko baki kika min ba kamani zaiyi ba." duk tayi maganar ne tana murgud'a baki.
"Haka kike gani, ai kuwa da zan miki wallahi ba zaki kai ko ina ba, amma ina jin tsoron karki qara lalacewa."
"Kiyi mana, wallahi babu abinda zai sameni, ina yin duk abinda nake so kamar yanda nake samun duk abinda nake so, dan haka babu abinda bakinki zaimin ."
"Haka ki kace?"
"Eh, haka nace."
"Shikenan kije , kije kya gani."
"Wallahi sai dai naga alkairi."
Juyawa tayi ta bar gidan rai b'ace tare da tunanin yaushe Asma'u ta zama haka, da wannan tunanin takai gida kuma ta kwanta bacci ba tare data fad'awa mahaifinsu ba, dan tasan inta fad'a masa toshi zai tsine mata ne ba tare da b'ata lokaci ba.
Babu wanda yasan me zai faru a gaba, badan haka ba da Fateema ta janye mugun bakin data ma Asma'u tun kafin ta kwanta bacci, domin kuwa wannan baccin data kwanta bacci ne na qarshe, baccin da babu tashi sai lokacin da aka busa qaho na biyu.
Haka lokaci yaja sosai babu abinda ya sauya a game da al'amarin Hamza, har suka aurar da *Salamatu* wacce suke kira da Uwani, da kuma Zulfa'u ya rage Zabba'u, lokacin kuma aka samu cikin Zuby amma sam Asma'u bata bari Hamza ya sani ba, domin kuwa cikin ba nashi bane na abokinshi ne, kuma hakan ta faru ne lokacin da abokin yazo gidan domin sanin meke faruwa ya daina fita, daga ranar suka qulla wannan alaqar kuma tana jin dad'in haka saboda yana sakar mata kud'i masu yawa, sai dai ta manta da ciki d'an dumane dole wata rana zai fito kuma ta haifeshi.
A ranar da Hamza yaga cikin kuwa, ya sameta ne d'akinta kwance da kayan bacci, anan yaga cikin dake jikinta d'an wata shida zuwa bakwai wanda take b'oyewa kullum,
"Me zan gani haka Asma'u?" ya fad'a yana sake kallon cikin gidan nata.
Cikin baccin daya fara d'aukarta taji muryarshi, a zabure ta tashi zaune tana d'aukar hijabin da take ajewa saboda gudun irin haka, cike da dakiya tace "mefa kake gani, miye haka zaka shigo min d'aki a wannan daren?"
"Asma'u, ciki fa nake gani a jikinki, ko kuma kina so kice min wannan ba cikin mutum bane?
"Ciki kuma, a ina?"
Da hannu ya nunata amma ya kasa fad'ar komai saboda yanda zuciyarshi ke bugawa, ya jima yana nuna hannun amma baice qala ba, daga haka kuma ya fad'i qasa wanwar , fashewa tayi da qara hakan yasa Zabba'u fitowa daga d'akinsu, nan dai aka samu aka kaishi asibiti amma ina lokaci yayi Hamza, shima nan aka tabbatar musu da zuciyarshi ce ta buga, Asma'u bata ji mutuwarshi ba saboda lasisi ne ya bata ci gaba da harkarta, bayan wattani kuma ta haifi Zuby kuma samu kulawar mahaifinta wanda mutane sukewa kallon aminin mahaifinta, sai dai tunda akayi arba'in d'in Zuby shima Alhaji *Bala* ya fita sabgarta, da farko tayi yunkurin tona musu asiri, amma sai Bala ya nuna mata ya fita zama d'an iska, domin kuwa cewa yayi taje ta fad'a, shi namiji ne bai gudun abinda mutane zasu ce, bayan tunani da tayi saita fahimci ita zata jefa kanta rijiya, dan haka taja bakinta tayi shiru.
Sai dai rayuwar ta sauya musu sosai, dan abinda zasu ci wani lokacin wuya yake musu, wani lokacin ma saita d'an kula maza kafin ta samu abinda zata ciyar da Zuby da kanta, rufi asiri d'aya shine su Zulfa'u suna taimaka musu wani lokacin, a haka rayuwa ta tafi har girma ya risketa tare da yarta Zubeida.
Ranar wata *litinin* Zuby ta taso daga Γ©cole, a qasa take tafiya ga rana ga yunwa, Umar Faruk ne ya b'illo akan hanyar da take, nan dai suka gaisa kuma ya d'auketa ya rage mata hanya, suna zuwa gida kamar yanda ya zama saban Mama zama k'ofar gida a bakin bishiya, yauma nan take zaune daga ita sai kallabin dake kanta, saida ya sauka daga kan mashin d'in ya gaisheta sosai kafin ya tashi ya tafi, Zuby kuma tuni dama tayi cikin gida bata ko kulata ba, bin kowannensu tayi da kallo tana girgiza kai, har zuciyarta taji sun birgeta kuma sun dace da juna, hakan yasa tayi tunanin had'a aurensu, sai dai kuma Umar Faruk talaka ne haka ma mahaifinshi, amma ba zata aiwatar da komai ba har saita nemi shawarar malam sannan.
Ba tayi qasa a gwiwa ba wajen zuwa wajen malam tare da fad'a mishi abinda ya kaita, bud'ar bakin malam cewa yayi "tabbas, wannan yaron zaiyi arzik'i, kuma arzik'in zaizo ta sanadiyar matarshi ne ta farko."
"Ban gane matarshi ta farko ba, kana nufin ba yata kad'ai zai aura ba, kuma wacce zai aura farko itace silar arzik'inshi, to wacece ita.?"
Rarraba ido yayi, dan na farko ma yayi qarfin hali ne ya fad'a da d'an abinda shed'anu suka nuna mishi, duk da yasan ba lallai gaskiya bane, amma saboda ita d'in abokiyar harka ce ba zaiso mutuncinshi ya zube ba, dan haka yace "haba Ma'u, ai 'yar taki nake nufi."
A wulak'ance tace "ka tabbata?"
"K'warai ma kuwa, ai kisan yanda za ayi ki hadasu, dan arzik'inshi na tattare da ita, yarinyar akwai qashin arzik'i."
"Gado tayi gaba da baya." ta fad'a tana yamutsa fuska.
A lokacin da taje ma iyayen Umar Faruk da maganar basu ce komai ba sai fatan alkairi, haka ma Umar Faruk da aka fad'a mishi, bud'ar bakinshi cewa yayi "Allah ya sanya alkairi."
"Ameen, Allah ya maka albarka." cewar Mama
"Ameen."
Daga wannan rana ne sai Asma'u take turo Zuby gidan tazo har takanyi sati biyu wani lokacin, shakuwa ta shiga tsakaninsu duk da dai Umar Faruk baya jin komai a zuciyarshi a game da ita, amma a lokacin da girma ya qara zuwa masa ya sake mallakar hankalin kanshi, a lokacin yana da shekara *30* sai buk'atar aure ta kamashi, amma sam Zuby tak'i amincewa tace saita samu certificat d'inta na (BEPC) sannan suyi aure, dole ya hak'ura tunda baida wacce yake so kuma baya da ra'ayin yin mata biyu a cikin qananin lokaci da kuma qarancin shekarunshi.
*Wannan* ne dalilin da yasa tanti ta tsani Khairat ba tare da wani dalili ba, ta yarda d'ari bisa d'ari akan abinda malam ya fad'a ,musamman da tasan Khairat 'yar babban mutum ce, tasan ba makawa sai yayi kud'i ta silarta, hakan yasa ma tayi gaggawar shigo da Zuby gidan.
*WANNAN KENAN*
πππππ
*_CIGABAN LABARI_*
Tana d'auka yace " ina kika je?"
Cikin gunaguni da harare tace "ina gida wajen Mama."
"Da izinin wa kika je?"
"Toh , wajen mahaifiyar tawa ma da zanzo saina fad'a maka? to da izinina nazo."
Da qyar ya taushi zuciyarshi yace "naji, na miki uzuria karo na farko, amma ki sani kika sake maimaita irin haka, wallahi ranki idan yayi dubu zai b'ace, sannan, ki gaggauta dawowa gida nan da minti talatin ina jiranki."
Yana fad'a ya kashe wayar ita kuma ta kalli Mama tace "kiji rainin wayo."
Shiru Mama ta mata ganin haka yasa ta tashi ta kimtsa nata yanata sukayi sallama ta kama hanya, dan nisan dake tsakani ma zai iya d'aukarta minti talatin d'in, da qyar ta samu taxi ta hau, koda taje bata samu Umar a gidan ba, hakan kuma ya mata dad'i sosai.
*************
B'angaren Khairat kuma tana babban shagon siyayya , kud'i kawai take kashewa yayin da take tuna iya mutanen dake cikin qwaqwalwarta take siya musu kaya, ta jima sosai kafin ta fita ta d'auki hanyar komawa masaukinsu, tana zuwa su Mammie ita suke jira , dan haka basu b'ata lokaci ba wajen isa filin jirgi kuma suka tashi da izinin Allah suka sauka lafiya.
_Me kuma zai faru yanzu? my Hajja fa ta dawo._
*Kamar yanda na fad'a, babu abinda zai tsayar dani rubutu idan harna fara rubutawa,amma fa akwai yiwuwar na dakatar da rubuta _Jihadi_ na d'an wani lokaci, danna lura kamar kun fara gajiya da comment, comment bawai yana nufin a turo makaπ tsalle koπ€Έββtalar qafafu ba, ko striker dake cinye data, tabbas muna jin dad'in addu'a, amma mutum yayi sharhi akai shine zai baka tabbacin an karanta abinda ka rubuta d'in, so idan kun gyara zanci gaba, idan ba haka baπbana da matsala, zan sawake ma kaina ta hanyar ajiyeshi gefe ko kuma na dinga turawa masu so na fita daga duk grp d'in da basa comment.*
_Ina muku barka da sallah, Allah ya nuna mana ta bad'i, Allah ya karb'i ibadunmu , Allah ya gafarta mana zunabanmu, Allah yasa muna cikin bayin da aka 'yanta._π *Ameen ya Hayyu ya Qayyum.*
14/08/2019 Γ 15:32 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Sufa iyaye girmane dasu, samun Zuby bata hanyar aure ba yana d'aya daga cikin kamun da bakin mahaifiyar Asma'u ya fara mata, kuma wannan ba abun mamaki bane danni naga irin haka da idona.*π
_Muje zuwa masoya masu fahimta_π
_Bismmilahir-rahman-rahim_
4β£3β£
Driven gida ne ya kawo Khairat saboda shiya d'aukosu daga filin jirgi, saida ya shigar mata da kayan cikin gidan kafin ya wuce, nanfa yara suka mata ca suna mata sannu da zuwa, haka ma manya sannu suke mata cikin murna, jin ana sallah isha'i a masallaci yasa Khairat kallon duka mutanen wajen cikin farin ciki tace "zanje nayi sallah, amma kumin alk'awarin ba zaku fad'awa Faruk ba."
Fateema da Zeinab ne suka amsa da "munyi aunty."
Kumatunsu ta shafa tace "da kyau 'yan mata, zan wuce, idan na fito zan baku tsarabarku."
Wucewa tayi Ruk'ayya tabi bayanta da kayanta, tana shiga d'akin taga yasha gyara, kallon Ruk'ayya tayi tace "kece ko?"
Cikin dariya tace "eh aunty, ai naga bakya son k'azanta, shi yasa nake shigowa ina gyarawa duk da ba kya nan."
"Kin kyauta." ta fad'a tana shirin fitowa yin alwala.
"Amma fa aunty naga sai farin ciki kike, kodai da wani abu ne?" cewar Ruk'ayya.
Cak Khairat ta tsaya amma bata juyo ba, ajiyar zuciya ta sauke mai nauyin gaske, ita kanta haka take ji tana farin ciki, kuma baya rasa nasaba da kusanto da kanta da tayi wajen Umar Faruk, ba tare data juyo ba kuma ta wuce ta fad'a 'yar qaramar toilet d'insu, koda ta fito bata samu Ruk'ayya ba, a haka ta kabbara sallah kuma harta kammala Umar Faruk basu shigo ba.
Jakar data zuba tsarabara ciki ta janyo ta fito da ita tsakar gidan, fitowarta yayi daidai da fitowar Zuby daga d'aki itama, kallon juna sukayi Zuby kuma ta bita da harara, Khairat kuma binta tayi da kallon zan kamaki a hannuna, wajensu Mama ta nufa inda suke zaune akan tabarma, zaune tayi itama tana cire hijab d'in jikinta danya d'an takurata sannan ta bud'e jakar, kayan kanti ne masu kyau da qualitie wanda ta siyowa Zeinab, Fateema, Yusuf, Ubaidullah, Bilal, Abdul rahaman, bawa kowa tayi sai lokacin ta fahimci ba kowa ya samu ba, dan dama ba wani sanin yaran tayi ba tayi anfani da ganinsu ne yau da gobe, kallon sauran tayi tace "ayya, kuyi hak'uri kunji, insha Allah kuma zan siyo muku naku."
Mama Sa'a kuma cewa tayi "haba, aiba komai ba, wannan ma an gode wallahi, Allah yashi albarka."
Mama kuma dad'i taji sosai saboda ganin anyi daidai, dan Bilal d'ane ga Mama Maimuna kuma ya samu, Abdul rahaman d' ga Mama Sa'a kuma shima ya samu, Zeinab kuma 'yarta ce itama kuma ta samu, sai Fateema da Yusuf yayan Abbakar, suna cikin godiya kuma saiga takalma ta fiddo ta bawa Mama Sa'a Mama Maimuna da kuma Mama, suna da kyau kuma basu da tudu ko kad'an, nanma godiyar suka fara sai kuma ga wasu kayan masu kyau tabawa Ruk'ayya har kala uku, wata agogo ta fito da ita mai shegen kyau qirar rolex ta bawa Mama Sa'a da tafi kusa da ita tace "wannan na Baba ne."
Kafin tayi magana Khairat ta fito da wata agogon qirar gucci ta fata tabawa Saratu tace "na mijinki ne wannan."
Sannan ta bita da wasu had'add'un turare kala uku tace naki ne wannan."
"Kai, amma na gode sosai yer uwa, irin wannan tsaraba haka."
Sallamar Aliyu da Usman ce ta katsesu, 'karasowa sukayi Usman na fad'in "matar yaya, yaushe garin?"
A harshen zarma ta amsa mishi da "ana sallah na shigo."
"Sannu da zuwa, ya hanya?" cewarsu gaba d'aya.
"Lafiya lau." ta fad'a tana mika musu wasu kwalaye wanda ko a cikin bacci aka basu zasu san na miye, Aliyu ne ya waro ido yace " Iphone7, ta mece aunty?"
"Naku ne." ta fad'a ba tare data kallesu ba.
Su kuma mamaki ne ya hanasu karb'a, saida ta juyo tace "baku sone?"
Da sauri Aliyu ya karb'a yana fad'in "ah haba aunty, mu mun isa? mun gode Allah saka da alkairi."
Karb'a yayi duka ya mik'awa Usman d'aya, amma sai Usman yace "na gode, amma gaskiya ni bana so, wannan ma ta isheni."
Ba tare da damuwa ba Khairat ta kalli Aliyu tace "ok , ka bawa maiso ko cikin abokanka."
Mamaki ne ya cika kowa dake wajen, Usman d'in ne yace "kud'i fa kika saka kika siyo saboda ni, me yasa ba zaki aje ba koki siyar?"
Wani d'an murmushi tayi mai sauti tace "ba wakai ba na siyo, na siyo ne wa mutanen da nake rayuwa dasu, tunda baka so ai ba za'a rasa maiso ba."
Gyara zama tayi tana kallonshi tace "da farko na shigo gidan nan ne a matsayin bana son d'an uwanku , duk da haka kuma zan iya sadaukar da komai nawa dominku, yanzu kuma da nake son Faruk, ina ji zan iya taimaka muku da k'arfina ma ba iya dukiyata ba kad'ai, ko zaku kasheni ba zan daina muku alkairi ba domin kuwa a jinina yake, haka ma kome za'a fad'a ba zan daina taimakawa mutane ba."
Tana fad'a ta tashi zata wuce d'aki Mama Sa'a tace "dan Allah yata kiyi hak'uri, karki bi ta abinda ya fad'a."
Juyowa tayi za tayi magana idonta ya sauka akan Zuby dake k'ofar d'akinta zaune, shiru tayi ta wuce d'aki tana ji kamar bata kyauta ba da bata bawa Zuby komai ba, domin kuwa kishiya aina mak'iya bace, coiffeuse d'inta ta kalla, da sauri ta qwala kiran sunan Ruk'ayya, tana shigowa ta d'auki wasu turaruka wanda suke birgeta har guda biyu ta bata tace "ki kaiwa Zubeida."
Da mamaki Ruk'ayya tace "amma aunty sai naga kamar naki, me yasa zaki batasu?"
Cikin d'an murmushi tace "Ruk'ayya, wannan ba komai bane danna bawa Zubeida wannan, itafa kishiyata ce bawai mak'iyata ba, zan iya bata fiye da wannan ma musamman idan ta buqata ko kuma naga buqatar hakan ta kamata."
"To aunty." ta fad'a tare da fita daga d'akin.
Tana bud'a labulen suka ci karo da Umar Faruk wanda labarin zuwanta ya sameshi tun a tsakar gidan, rab'awa tayi ta wuceshi shi kuma ya shiga ciki, Khairat na ganinshi ta daka tsalle tare da qara ta nad'e a jikinshi,shima rumgumeta yayi sosai a jikinshi yana juyi da ita a tsakiyar d'akin yana dariya, cikin murna take fad'in "nayi kewarka sosai baby, nayi kewarka, nayi farin cikin ganinka sosai."
Sauketa yayi da nufin ya mata magana amma saita had'e bakinsu waje d'aya, shima bai tsaya b'ata lokaci ba wajen biye mata suka
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40 Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63