saida kowa ya zauna mazauninshi harda secretaire d'inta ta zaune daga bayanta danta d'auki rahoton abinda zasu tattauna, sai lokacin kuma kallonta ya kai ga wata kujera da babu mazauninta, kallon habiba tayi tace,
"Wane sakarai ne anan da bai shigo ba?"
Cikin ladabi Habiba tace " *Umar Faruk* ne."
Za tayo magana suka ji an bud'e k'ofar wajen, ganin saurayin cikin hanzari yake yasa ta tashi tsaye cike da raini tace "sannu da zuwa yallab'ai."
Kallonta yayo ya kalli mutanen dake wajen, take ya fahimci abinda take nufi dan haka yace "je demande vos esxuze, je..."
Tsawar data masa yasa yayi shiru "yi mana shiru, kenan muna zaune nan dan ka zo ka bamu hak'uri, kai mahaukacin ina ne da baka san mahimmancin lokaci ba? kawai mutane jahilai daku babu abinda kuka iya sai tumasanci da banlag...."
"Ke, ya isheki haka."
Wannan maganar ita tasa tayi shiru bata shirya ba.....
Cikin b'acin rai ya ci gaba da cewa "me kika d'auki kanki? su waye jahilan? fad'a min matakin karatunki da har kike fad'a min haka, to bari kiji wallahi kika sake kirana jahilai saina fasa miki baki a wurin nan, ke in ba jahilce ke damunki ba me yasa zaki kira wasu da jahilai, kuma bari kiji aikine da nake a service d'inku zaisa kimin kallon banza ko? to na daina daga yau, saiki zauna ki cinye wurin idan zaki iya."
Yana fad'a ya juya ya barta nan tsaye sake da baki, a fusace ya bar wurin kayanshi ya had'a dake kan teburd'inshi yana shirin fita, ta baya yaji an dafa kafad'arshi, juyowa yayi ya sauke idonshi akan babban abokinshi....
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Bismmilahir-rahman-rahim_
_Manzo (S.A.W) yace "Imanin d'ayanku ba zai cika ba har saiya soma dan uwansa abinda yake so ma kansa."_ *Imamul Bukhari da muslim suka ruwaitoshi*
2β£
"Faruk lafiya na ganka rai a b'ace?"
Cikin masifa yace "ina fa lafiya, wannan 'yar rainin hankalin tana nema ta b'ata min rai kawai dan tana ganin nan mallakin mahaifinta ne, ni dama tunda naga yarinyar nan nasan ba za ayi abun k'warai a wurin nan ba."
Wani murmushi yayi yace "Faruk, to yanzu meya faru kenan?"
"Me kuwa ya faru, na baro mata wurin,kuma daga nan gidanmu nayi dan ba zan iya aiki a k'arkashin yarinyar nan ba."
Da sauri ya rik'e hannunshi daga shirin rataya jakar da yake shirin yi yana fad'in "me kace? Faruk kana da hankali kuwa? kasan me kake shirin aikatawa?"
"To bari kaji in fad'a maka kuskuren da kake shirin aikatawa, wannan aiki shekara hud'u mukayi muna neman abinyi amma bamu samu ba, ka sani kafin mu sameshi munsha wahala sosai, bama wannan ba Faruk me yasa ba kayi tunanin mutanen da suka ci suke sha ta dalilinka ba, ko ka manta da irin nauyin dake kanka ne, sannan ka sani wannan aikin da kake neman watsarwa a yanzun, to ka sani akwai dubbun nan mutanen dake qaunarshi kuma d'aruruwan mutane ne zasu so da burin samun kujerar daka tashi, dan haka kayi tunani kafin ka yanke hukunci."
Barinshi yayi tsaye yana tunanin abinda ya fad'a, ganin baida wata mafita data wuce ya zauna yasa ya ajiye jakar cikin sanyin jiki ya koma sale d'in bak'in, a hankali ya bud'e kofar yayi daidai da har sun gama tattauna abinda ya tarasu, kallonshi take sosai da mamakin abinda ya maidoshi, saida ta bawa bakin nata hannu sukayi musabaha sannan suka wuce, saida ta gama kallonshi shi kuma ya kasa cewa komai, wayarta ta dauka Habiba ta biyota da jakarta suka fita daga wajen, acessaire (lift) suka shiga Habiba na shirin rufewa ya kutsa kai ciki, tana ganin haka ta fito cikin zafin rai ta nufi matattakalar bene da sauri ta fara sauka, da sauri shima ya fito harda gudu gudu ya tari gabanta ya soma sauka ta baya yana kallonta yana fad'in "magana zamuyi dan Allah ki saurareni."
Bata saurareshi harta sauka suna kaiwa tsakiyar ma'aikatar ya sake tare gabanta yana fad'in "dan Allah ki saurareni, hak'uri zan baki...."
Marin daya sauka a kunci ne yasa yayi d'uf, dafe yake da kunci yana kallonta, itama shi d'in take kallo haka kuma duk mutanen wajen ita su suke kallo, kafin wani abu ya sake faruwa sai kuwa Faruk ya zabgeta da marin da yafi wanda ta mishi.
Dafe kuncinta tayi baki bud'e tana kallonshi saboda mamaki, kasa motsawa tayi daga wajen yayin da shi kuma ya d'ora mata da wani sabon bayani "wallahi ke baki isa ba kisa hannu ki mareni, akan me? saboda kawai muna k'asanki."
D'aukar kayanshi yayi ya bar ma'aikatar gaba d'aya, cikin fushi da ba zata iya misaltashi ba ta bar wajen, gudu take sosai a mota ba tare da tunanin wani abu ya sameta ba.
Tana shiga ko rufe motar ba tayi ba ta wuce cikin gidan da gudu, daf da k'ofar shiga ta fad'a saman mutum, kallon kallon suka tsaya yi tana gama gane waye ya rik'eta ta fizge jikinta tana tureshi baya, shi kuma murmushi kawai yake mata, cikin masifa da son sauke bala'inta a kanshi ta fara magana,
"Meye haka, kai mahaukacin ina ne? baka ganine da zaka bigeni harda wani tab'a jikina? to bari kaji wallahi yau duk uban daya tsaya maka a garin nan saika bar gidan nan, tunda bana ubanka bane."
Duk da maganganunta sun masa zafi amma daurewa yayi yace "bake kika kawoni ba, ba kuma zaki fitar dani ba idan banyi niyya ba."
Cike da gatsali tace "saboda uban kane ya gida gidan?"
Cike da hassala ya fizgo hannunta kamar zai had'ata da jikinshi yace "wai ke me yasa baki da wayo ne, me yasa duk abinda ya zo bakinki fad'inshi kike? ke dai kinsan ubana ba matsiyaci bane bare kice zaki min gorin da kike wa wasu."
Sake fizge hannunta tayi ta tureshi iya k'arfinta tace "banza kawai, wani arzik'i mahaifin naka yake da da har zaka fad'a min, to bari kaji yau dole ka bar gidan nan, dan ba zai yiyuba ka zauna kana kawo mana mata a gida ba bayan kasha giyarka."
Muryar Mamie ce suka ji tace "Khairat dama rashin mutuncin naki har ya kai haka? waike wace irin yarinya ce marar ganin girman na gaba da ita? me yasa kika zab'arwa kanki wannan kakkaussar rayuwar da ba zata kaiki ko ina ba a matsayinki na mace?"
K'arasa shigowa tayi cikin falo tana kallon uwar tace "nice ai ya kamata na miki wannan tambayar, me yasa kika auri mutumin da kinsan baya da hallaye masu kyau? sannan karki sake cemin bana da mutunci, dan inma hakane to gadone nayi"
Kafin tayi wata magana ta d'ora da "kinga, wallahi yaron nan ya bar gidan nan yau, idan kuma ba haka ba zansa Papa yayi rashin mutunci a gidan nan, idan kuma shiya kasa saboda yana tsoronki, toni da kaina zanyi kuma zaku sha mamaki."
A fusace ta rab'a uwar tayi d'akinta ta barsu nan, hawayen da suka fara taho mata ne tayi saurin saka hannu ta share tana kallon Mujahhid, murmushin yak'e ta masa tace "kana ji ko yarona, kayi hak'uri dan Allah k....."
Katseta yayi ya matso kusanta da sauri yana fad'in "karki damu Mamie, ba komai wallahi, zan tafi, amma ni ke nake tunani yanda zaki ci gaba da rayuwa a gidan nan cikin kad'aici."
Kallonshi tayi tace "a'a, karka damu dani, aini na saba, zan ci gaba da zama a haka, har lokacin da Khairat zata fitar da mijin aure, dan aurenta ne ya tsayar dani gidan nan."
"Shikenan Mamie, zan tafi, bara naje na had'a kayana."
Tana shiga d'aki ta jefar da jakarta ta k'arasa gaban coiffeuse tasa hannu tayi watsi da kayan dake wajen, matuk'a ranta a b'ace yake kuma tana so tayi abinda yafi wanda aka mata ciwo, a hankali ta fara zamewa a jikin bango tana sulalewa har takai qasa, fashewa tayi da kuka sosai, ta jima a gurin tana kuka har saida mai aiki ta bud'a d'akin zata shigo, cikin daka tsawa tace "ki fita ki bani wuri, bana son ganin kowa."
Abinda ba'a so ne ya faru, saboda tsananin damuwa da kuka yasa qirjinta ya fara matsanancin ciwo haka kuma kanta ya fara mata bala'en'en ciwon da tafi fatan mutuwarta a kanshi, jin haka yasa ta rarrafa ta bud'a coffre ta d'auki maganinta, duk da dishidishi take gani hakan ta duba amma bata ga ruwa ba ba a d'akin , k'arfin hali tayi ta tashi ta nufi k'ofa danta samu ruwan, tana kusa ga kaiwa kawai ta fad'i a guri numfashinta kad'an yake fita, hannayenta ne duk bisa kanta saboda yanda yake fizgarta, daga haka kuma bata sake sanin meya k'ara faruwa ba a gaba.
*Da misalin* 16:30 Papa ya shigo gidan, Mamie na zaune akan kujera cikin damuwa da tunanin halin da Khairat take ciki, ba tare da sallama ba kawai ya zauna kusa da ita yana fad'in "sannu da gida."
Cikin sanyin jiki da tabe baki tace "yawwa, sannu da shigowa?"
"Ba dai Khairat bata dawo ba?" ya fad'a yana cire hular kanshi.
Saida ta sauke ajiyar zuciya tace "bata wuce awa d'aya ba da fita ta dawo, tana d'akinta."
"Bacci take?"
A sanyaye tace "gaskiya ban sani ba, ta shigo kamar ranta a bace yake, harma suka samu matsala da Mujahhid wanda yayi sanadiyar komawarsa gida, amma tunda ta shiga d'aki bata fito ba, kuma mai aiki taje ta dubo halin da take ciki ta korota."
Jin tayi shiru yasa ya kalleta yace "ina jinki, sai akayi yaya?"
"Ba komai, har yanzu tana ciki."
Tsaye ya mik'e yana girgiza kai yace "ban san me yasa kike nuna mata rashin kulawarki ba kamar ba 'yar da kika haifa ba, da bake kika haifeta ba sai nace ba kya sonta, kinfi kowa sanin duk baccin da Khairat za tayi ba zata kai wannan lokacin tana bacci ba, amma ki kasa duba halin da take ciki."
Yana bud'e k'ofar ya k'arasa a guje yana fad'in "oh mon Dieu, Khairat, Khairat!!!."
Maida kallonshi yayi ga Mamie wacce ta shigo yanzu, cikin b'acin rai yace "kin gani ko, kin gani abinda kika jawo mana, wai me yasa kike nunawa yarinyar nan rashin kulawa ne? ki dubi sakacinki abinda yake nema yaja mana."
Mamie da bata san meya faru ba itama cikin fad'a tace "to miye anfanin kulawar da zan dinga nuna mata, naga kaima da kake nuna mata kulawar ba wani girmanka take gani ba, bare kuma ni Γ banza...."
Duk da ta kai k'arshen aya amma saida ta dire kalmar ba daidai ba saboda tsawar daya mata, cikin d'aga murya yace "dallah ki min shiru, zaki kama min ita ne ko kuma burinki ta mutu?"
Qafafunta ta kama shi kuma ya d'auki duka rabin jikinta suka nufo da ita waje, ma'aikatan gidan na ganin haka suka fara tambayar lafiya meya sameta, biyarsu suke a baya har chauffeur ya bud'e musu k'ofar mota suka kwantar da ita a baya sannan suka shiga suka bar gidan, ma'aikatan kowa jini kan akaifa , ba zasu ce suna jin dad'i ba saboda rashin lafiyarta , amma dai sun san sun d'an samu hutu na wani d'an lokaci.
********************
*Faruk* ne zaune akan taburma shi da abokinshi *Ishaq*, yayin da wata dattijuwar mata mai kamala ke gefensu akan kujera yar tsugunno, sai kuma babban malamin dake tsaye ya tisasu a gaba yana fad'a akan aikinshi daya baro, cikin fad'a ya sake cewa,
"Kai yanzu badan baka da hankali ba, daga k'aramin abu sai kawai kayi hushi, kai gaka uban zuciya ko? to bari kaji wallahi wannan aikin idan har ka bari ya kubuce maka, to wallahi za kayi nadama da daka sani, kai kafi kowa sanin kaine kusan rabin k'arfin gidan nan, to idan kace ka daina aikin kenan duk yayanka ne zai had'a ya d'auki har nauyinka.?"
D'ago kanshi yayi yace "Baba bafa k'aramin abu bane, marina fa tayi a fuska, wallahi ko k....."
Tsawar da Baba ya masa yana fad'in "ta mareka d'in, nace ta mareka saime? idan baka rama ba mutuwa za kayi, kuma tun farko ai kai kaja komai."
"Dan haka ka jini da kyau, ka tashi yanzun nan ga Ishaq nan ya rankaka kuje ka sameta ka bata hak'uri, karka yarda ka rasa wannan aikin, in kuma kayi sake to ka sani, wallahi abincin gidan nan ma ka daina ci tunda kai sarkin zuciya ne, waika gaka *Umar Faruk* ko?"
Sake d'ago kai yayi yace "Baba, cewa fa kake naje na...."
"K'warai haka nake nufi, dole sai kaje ka bata hak'uri, in kuma ba haka ba to duk matakin dana d'auka kanka, kai ka siyo da kud'inka."
Sai lokacin mahaifiyarshi tace "in banda abin Umar faruk ma, kaida maganar aure ka keyi amma kake k'ok'arin aje aikin da shine gatanka."
"To, fad'a masa dai, tunda naga shi baya da hankali zuciya ce kawai yasa a gaba."
Ishaq ne yace "kaga, ba wani abin damuwa bane, yanzu ya tashi mu tafi mu koma service d'in mu samu manager, nasan insha Allah zai taimaka mana kamar yanda ya taimaka mana muka samu aikin nan da farko."
Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi kafin ya kalli Baba yace " kuyi hak'uri Baba, insha Allah zanje na bata hak'uri kamar yanda kuka ce."
Addu'a Mama ta bishi da ita da fatan samun dacewa, Baba kuma na sake jaddada masa ya tabbatar ya bata hak'uri sosai harta hak'ura, haka suka fito da niyyar tafiya ma'aikatar wajen manager.
Sun samu manager kuma Ishaq ya fad'a masa komai daya faru, yayi mamaki sosai dan baisan wainar da aka toya ba, yayi jimami sosai tare da k'ara tsorata Faruk akan karma ya fara tunkararta ya jira hukuncin da mahaifinta zai d'auka a kanshi ko kuma ita da kanta, baiji shakka ko d'ard'ar ba akan matakin da zasu d'auka, matsalarshi d'aya shine yanda mahaifinshi ya d'auka da zafi sosai, ganin baice komai ba yasa manager cewa,
"A gaskiya *Umar Faruk* ba zan yarda a dalilinka na rasa nawa aikin ba, kayi hak'uri, amma taimakon da zan iya maka na riga da nayi maka shi, shawara d'aya da zan baka kawai shine, idan har ta dawo d'aukar fansa to ka qasqantar da kanka, ka nuna mata kayi nadama kuma a bisa kuskuren rashin sanin ko wacece ita ka mareta, idan kayi sa'a ta iya yafe maka, amma gaskiya bana tunanin zata hak'ura, dan wallahi yarinyar nan rashin mutuncinta ya kai mak'ura, bata kallon kowa da idon daraja babu tausayi ko imani a zuciyarta, kuma tun ranar da mahaifinta ya mallaka mata masana'antar nan na fad'a muku dukanmu sai munyi hak'uri da ita, saboda kaushinta yayi yawa."
A sanyaye Umar faruk yace "zan jaraba na gani, bara naje bureau d'in nata."
Murmushi manager yayi yace "ta yaya kake tunanin zata zauna a wajen nan, ina jin a lokacin da naga tafiyarta to a lokacin ne abun ya faru."
"Kenan yanzu tana gida?" cewar Faruk d'in.
"Ina tunanin haka."
"Shikenan, zamu je har gidan, watak'ila ma tafi saurarenmu." cewar Ishaq
Faruk ne yace "a'a fa Ishaq, gaskiya bana so naje gidansu, idan taga haka zata san nadamu sosai, zata d'auka gaba d'aya na bada rayuwata wa aikin nan, hakan kuma zaisa ta qara wani rashin mutuncin."
"Muji ta d'auka a hakan in har ba zata koreka ba, meye a ciki?"
Kai Faruk ya girgiza yace "waiku me yasa ne kuke shakkarta har haka? mutum ce fa kamarku kuma mace mai rauni a kanku, me yasa zaku dinga tsoronta har haka, nifa wallahi bana son irin haka gaskiya, dan wannan ai bayar da maza kuke, yarinyar da da zaku bud'e mata ido sau d'aya dole zata fara shakkarku itama, amma duk kubi kuna wani tsoronta kamar ita ta halliceku."
Fuskar manager d'auke da murmushi yace "bawai muna jin tsoronta bane, sai dai ka sani kowane d'an adam a rayuwa yana buqatar ci da sha kafin ya rayu, to tamu k'addarar ta damka cin mu da shanmu ta sanadiyarta ne, ita kuma bata da kirki duk da bata jima a garin nan ba, amma na samu labarinta sosai kamar wanda yayi rayuwa a gidansu, dan ba tun yau muke tare da mahaifinta ba, kaga dole mubi a sannu."
Faruk ne ya tashi tsaye yace "zamu je gidan, ina fatan ta amince kodan saboda Baba."
Cikin tsokana Ishaq daya mik'e shima yace "da kana so amma kake wani nuna baka damu ba."
"Amma ai kaji me nace, ina fata ta amince saboda Baba." ya fad'a ba tare daya kalleshi ba.
Suna fita akan mashin d'in Faruk suka kama hanyar zuwa gidansu Khairat......
_Shin kuna ganin za suyi nasara kuwa? to wai zama su samu ganin Khairat d'in ko kuwa dai...???_
*********************
Suna zuwa k'ofar gidan suka tsaya suka sauka akan mashin d'in suka nufi k'ofar gidan, mai gadin gidan ne mai sanye da kaki irin na sojawa ya taresu yana fad'in "yadai malamai, daga ina, wa kuke nema?"
Ishaq ne yace "sannun ko, dan Allah munzo ganin Hajia Khairat ne."
Kallon tuhuma ya musu yace " Hajia Khairat? to tasan da zuwanku ne?"
Kallon juna sukayi tare da yin shiru na 'yan dak'ik'u kafin Ishaq ya sake cewa "gaskiya bata san da zuwanmu, mu daga service d'inta muke, manager ne ya turo mu saboda wani aiki daya d'an taso."
Kallonshi Faruk yayi saboda jin abinda ya fad'a , mai gadin ne yace "kuyi hak'uri mazaje, duk wanda ku kaga ya shiga gidan nan to an san da zuwanshi koda kuwa d'an uwane, kunsan gidan manyan mutane."
"Yanzu kenan babu wata dama da zata saka mu ganinta?" cewar Faruk.
"Gaskiya babu, dan Hajia Khairat ko tasan da zuwan mutun ma zata iya tsayar dashi a k'ofar gidan nan na tsawon awa uku, idan na barku kuka shiga zan iya rasa aikina."
Faruk ne yace "yanzu dan Allah to ya zamuyi muganta?"
Mai gadin ne yace "in dai abu mai mahimmaci ne, to zan iya fad'a muku wurin da zaku sameta, yanzu dai kunga ta shiga gida, kuma da alama ranta a b'ace ta shigo."
"To kenan ina zamu sameta?"
"Duk kwana uku takan je wajen casu, amma takamaimai wajen da
Showing 3001 words to 6000 words out of 186119 words
"Wane sakarai ne anan da bai shigo ba?"
Cikin ladabi Habiba tace " *Umar Faruk* ne."
Za tayo magana suka ji an bud'e k'ofar wajen, ganin saurayin cikin hanzari yake yasa ta tashi tsaye cike da raini tace "sannu da zuwa yallab'ai."
Kallonta yayo ya kalli mutanen dake wajen, take ya fahimci abinda take nufi dan haka yace "je demande vos esxuze, je..."
Tsawar data masa yasa yayi shiru "yi mana shiru, kenan muna zaune nan dan ka zo ka bamu hak'uri, kai mahaukacin ina ne da baka san mahimmancin lokaci ba? kawai mutane jahilai daku babu abinda kuka iya sai tumasanci da banlag...."
"Ke, ya isheki haka."
Wannan maganar ita tasa tayi shiru bata shirya ba.....
Cikin b'acin rai ya ci gaba da cewa "me kika d'auki kanki? su waye jahilan? fad'a min matakin karatunki da har kike fad'a min haka, to bari kiji wallahi kika sake kirana jahilai saina fasa miki baki a wurin nan, ke in ba jahilce ke damunki ba me yasa zaki kira wasu da jahilai, kuma bari kiji aikine da nake a service d'inku zaisa kimin kallon banza ko? to na daina daga yau, saiki zauna ki cinye wurin idan zaki iya."
Yana fad'a ya juya ya barta nan tsaye sake da baki, a fusace ya bar wurin kayanshi ya had'a dake kan teburd'inshi yana shirin fita, ta baya yaji an dafa kafad'arshi, juyowa yayi ya sauke idonshi akan babban abokinshi....
*Luv you guy's*π
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Bismmilahir-rahman-rahim_
_Manzo (S.A.W) yace "Imanin d'ayanku ba zai cika ba har saiya soma dan uwansa abinda yake so ma kansa."_ *Imamul Bukhari da muslim suka ruwaitoshi*
2β£
"Faruk lafiya na ganka rai a b'ace?"
Cikin masifa yace "ina fa lafiya, wannan 'yar rainin hankalin tana nema ta b'ata min rai kawai dan tana ganin nan mallakin mahaifinta ne, ni dama tunda naga yarinyar nan nasan ba za ayi abun k'warai a wurin nan ba."
Wani murmushi yayi yace "Faruk, to yanzu meya faru kenan?"
"Me kuwa ya faru, na baro mata wurin,kuma daga nan gidanmu nayi dan ba zan iya aiki a k'arkashin yarinyar nan ba."
Da sauri ya rik'e hannunshi daga shirin rataya jakar da yake shirin yi yana fad'in "me kace? Faruk kana da hankali kuwa? kasan me kake shirin aikatawa?"
"To bari kaji in fad'a maka kuskuren da kake shirin aikatawa, wannan aiki shekara hud'u mukayi muna neman abinyi amma bamu samu ba, ka sani kafin mu sameshi munsha wahala sosai, bama wannan ba Faruk me yasa ba kayi tunanin mutanen da suka ci suke sha ta dalilinka ba, ko ka manta da irin nauyin dake kanka ne, sannan ka sani wannan aikin da kake neman watsarwa a yanzun, to ka sani akwai dubbun nan mutanen dake qaunarshi kuma d'aruruwan mutane ne zasu so da burin samun kujerar daka tashi, dan haka kayi tunani kafin ka yanke hukunci."
Barinshi yayi tsaye yana tunanin abinda ya fad'a, ganin baida wata mafita data wuce ya zauna yasa ya ajiye jakar cikin sanyin jiki ya koma sale d'in bak'in, a hankali ya bud'e kofar yayi daidai da har sun gama tattauna abinda ya tarasu, kallonshi take sosai da mamakin abinda ya maidoshi, saida ta bawa bakin nata hannu sukayi musabaha sannan suka wuce, saida ta gama kallonshi shi kuma ya kasa cewa komai, wayarta ta dauka Habiba ta biyota da jakarta suka fita daga wajen, acessaire (lift) suka shiga Habiba na shirin rufewa ya kutsa kai ciki, tana ganin haka ta fito cikin zafin rai ta nufi matattakalar bene da sauri ta fara sauka, da sauri shima ya fito harda gudu gudu ya tari gabanta ya soma sauka ta baya yana kallonta yana fad'in "magana zamuyi dan Allah ki saurareni."
Bata saurareshi harta sauka suna kaiwa tsakiyar ma'aikatar ya sake tare gabanta yana fad'in "dan Allah ki saurareni, hak'uri zan baki...."
Marin daya sauka a kunci ne yasa yayi d'uf, dafe yake da kunci yana kallonta, itama shi d'in take kallo haka kuma duk mutanen wajen ita su suke kallo, kafin wani abu ya sake faruwa sai kuwa Faruk ya zabgeta da marin da yafi wanda ta mishi.
Dafe kuncinta tayi baki bud'e tana kallonshi saboda mamaki, kasa motsawa tayi daga wajen yayin da shi kuma ya d'ora mata da wani sabon bayani "wallahi ke baki isa ba kisa hannu ki mareni, akan me? saboda kawai muna k'asanki."
D'aukar kayanshi yayi ya bar ma'aikatar gaba d'aya, cikin fushi da ba zata iya misaltashi ba ta bar wajen, gudu take sosai a mota ba tare da tunanin wani abu ya sameta ba.
Tana shiga ko rufe motar ba tayi ba ta wuce cikin gidan da gudu, daf da k'ofar shiga ta fad'a saman mutum, kallon kallon suka tsaya yi tana gama gane waye ya rik'eta ta fizge jikinta tana tureshi baya, shi kuma murmushi kawai yake mata, cikin masifa da son sauke bala'inta a kanshi ta fara magana,
"Meye haka, kai mahaukacin ina ne? baka ganine da zaka bigeni harda wani tab'a jikina? to bari kaji wallahi yau duk uban daya tsaya maka a garin nan saika bar gidan nan, tunda bana ubanka bane."
Duk da maganganunta sun masa zafi amma daurewa yayi yace "bake kika kawoni ba, ba kuma zaki fitar dani ba idan banyi niyya ba."
Cike da gatsali tace "saboda uban kane ya gida gidan?"
Cike da hassala ya fizgo hannunta kamar zai had'ata da jikinshi yace "wai ke me yasa baki da wayo ne, me yasa duk abinda ya zo bakinki fad'inshi kike? ke dai kinsan ubana ba matsiyaci bane bare kice zaki min gorin da kike wa wasu."
Sake fizge hannunta tayi ta tureshi iya k'arfinta tace "banza kawai, wani arzik'i mahaifin naka yake da da har zaka fad'a min, to bari kaji yau dole ka bar gidan nan, dan ba zai yiyuba ka zauna kana kawo mana mata a gida ba bayan kasha giyarka."
Muryar Mamie ce suka ji tace "Khairat dama rashin mutuncin naki har ya kai haka? waike wace irin yarinya ce marar ganin girman na gaba da ita? me yasa kika zab'arwa kanki wannan kakkaussar rayuwar da ba zata kaiki ko ina ba a matsayinki na mace?"
K'arasa shigowa tayi cikin falo tana kallon uwar tace "nice ai ya kamata na miki wannan tambayar, me yasa kika auri mutumin da kinsan baya da hallaye masu kyau? sannan karki sake cemin bana da mutunci, dan inma hakane to gadone nayi"
Kafin tayi wata magana ta d'ora da "kinga, wallahi yaron nan ya bar gidan nan yau, idan kuma ba haka ba zansa Papa yayi rashin mutunci a gidan nan, idan kuma shiya kasa saboda yana tsoronki, toni da kaina zanyi kuma zaku sha mamaki."
A fusace ta rab'a uwar tayi d'akinta ta barsu nan, hawayen da suka fara taho mata ne tayi saurin saka hannu ta share tana kallon Mujahhid, murmushin yak'e ta masa tace "kana ji ko yarona, kayi hak'uri dan Allah k....."
Katseta yayi ya matso kusanta da sauri yana fad'in "karki damu Mamie, ba komai wallahi, zan tafi, amma ni ke nake tunani yanda zaki ci gaba da rayuwa a gidan nan cikin kad'aici."
Kallonshi tayi tace "a'a, karka damu dani, aini na saba, zan ci gaba da zama a haka, har lokacin da Khairat zata fitar da mijin aure, dan aurenta ne ya tsayar dani gidan nan."
"Shikenan Mamie, zan tafi, bara naje na had'a kayana."
Tana shiga d'aki ta jefar da jakarta ta k'arasa gaban coiffeuse tasa hannu tayi watsi da kayan dake wajen, matuk'a ranta a b'ace yake kuma tana so tayi abinda yafi wanda aka mata ciwo, a hankali ta fara zamewa a jikin bango tana sulalewa har takai qasa, fashewa tayi da kuka sosai, ta jima a gurin tana kuka har saida mai aiki ta bud'a d'akin zata shigo, cikin daka tsawa tace "ki fita ki bani wuri, bana son ganin kowa."
Abinda ba'a so ne ya faru, saboda tsananin damuwa da kuka yasa qirjinta ya fara matsanancin ciwo haka kuma kanta ya fara mata bala'en'en ciwon da tafi fatan mutuwarta a kanshi, jin haka yasa ta rarrafa ta bud'a coffre ta d'auki maganinta, duk da dishidishi take gani hakan ta duba amma bata ga ruwa ba ba a d'akin , k'arfin hali tayi ta tashi ta nufi k'ofa danta samu ruwan, tana kusa ga kaiwa kawai ta fad'i a guri numfashinta kad'an yake fita, hannayenta ne duk bisa kanta saboda yanda yake fizgarta, daga haka kuma bata sake sanin meya k'ara faruwa ba a gaba.
*Da misalin* 16:30 Papa ya shigo gidan, Mamie na zaune akan kujera cikin damuwa da tunanin halin da Khairat take ciki, ba tare da sallama ba kawai ya zauna kusa da ita yana fad'in "sannu da gida."
Cikin sanyin jiki da tabe baki tace "yawwa, sannu da shigowa?"
"Ba dai Khairat bata dawo ba?" ya fad'a yana cire hular kanshi.
Saida ta sauke ajiyar zuciya tace "bata wuce awa d'aya ba da fita ta dawo, tana d'akinta."
"Bacci take?"
A sanyaye tace "gaskiya ban sani ba, ta shigo kamar ranta a bace yake, harma suka samu matsala da Mujahhid wanda yayi sanadiyar komawarsa gida, amma tunda ta shiga d'aki bata fito ba, kuma mai aiki taje ta dubo halin da take ciki ta korota."
Jin tayi shiru yasa ya kalleta yace "ina jinki, sai akayi yaya?"
"Ba komai, har yanzu tana ciki."
Tsaye ya mik'e yana girgiza kai yace "ban san me yasa kike nuna mata rashin kulawarki ba kamar ba 'yar da kika haifa ba, da bake kika haifeta ba sai nace ba kya sonta, kinfi kowa sanin duk baccin da Khairat za tayi ba zata kai wannan lokacin tana bacci ba, amma ki kasa duba halin da take ciki."
Yana bud'e k'ofar ya k'arasa a guje yana fad'in "oh mon Dieu, Khairat, Khairat!!!."
Maida kallonshi yayi ga Mamie wacce ta shigo yanzu, cikin b'acin rai yace "kin gani ko, kin gani abinda kika jawo mana, wai me yasa kike nunawa yarinyar nan rashin kulawa ne? ki dubi sakacinki abinda yake nema yaja mana."
Mamie da bata san meya faru ba itama cikin fad'a tace "to miye anfanin kulawar da zan dinga nuna mata, naga kaima da kake nuna mata kulawar ba wani girmanka take gani ba, bare kuma ni Γ banza...."
Duk da ta kai k'arshen aya amma saida ta dire kalmar ba daidai ba saboda tsawar daya mata, cikin d'aga murya yace "dallah ki min shiru, zaki kama min ita ne ko kuma burinki ta mutu?"
Qafafunta ta kama shi kuma ya d'auki duka rabin jikinta suka nufo da ita waje, ma'aikatan gidan na ganin haka suka fara tambayar lafiya meya sameta, biyarsu suke a baya har chauffeur ya bud'e musu k'ofar mota suka kwantar da ita a baya sannan suka shiga suka bar gidan, ma'aikatan kowa jini kan akaifa , ba zasu ce suna jin dad'i ba saboda rashin lafiyarta , amma dai sun san sun d'an samu hutu na wani d'an lokaci.
********************
*Faruk* ne zaune akan taburma shi da abokinshi *Ishaq*, yayin da wata dattijuwar mata mai kamala ke gefensu akan kujera yar tsugunno, sai kuma babban malamin dake tsaye ya tisasu a gaba yana fad'a akan aikinshi daya baro, cikin fad'a ya sake cewa,
"Kai yanzu badan baka da hankali ba, daga k'aramin abu sai kawai kayi hushi, kai gaka uban zuciya ko? to bari kaji wallahi wannan aikin idan har ka bari ya kubuce maka, to wallahi za kayi nadama da daka sani, kai kafi kowa sanin kaine kusan rabin k'arfin gidan nan, to idan kace ka daina aikin kenan duk yayanka ne zai had'a ya d'auki har nauyinka.?"
D'ago kanshi yayi yace "Baba bafa k'aramin abu bane, marina fa tayi a fuska, wallahi ko k....."
Tsawar da Baba ya masa yana fad'in "ta mareka d'in, nace ta mareka saime? idan baka rama ba mutuwa za kayi, kuma tun farko ai kai kaja komai."
"Dan haka ka jini da kyau, ka tashi yanzun nan ga Ishaq nan ya rankaka kuje ka sameta ka bata hak'uri, karka yarda ka rasa wannan aikin, in kuma kayi sake to ka sani, wallahi abincin gidan nan ma ka daina ci tunda kai sarkin zuciya ne, waika gaka *Umar Faruk* ko?"
Sake d'ago kai yayi yace "Baba, cewa fa kake naje na...."
"K'warai haka nake nufi, dole sai kaje ka bata hak'uri, in kuma ba haka ba to duk matakin dana d'auka kanka, kai ka siyo da kud'inka."
Sai lokacin mahaifiyarshi tace "in banda abin Umar faruk ma, kaida maganar aure ka keyi amma kake k'ok'arin aje aikin da shine gatanka."
"To, fad'a masa dai, tunda naga shi baya da hankali zuciya ce kawai yasa a gaba."
Ishaq ne yace "kaga, ba wani abin damuwa bane, yanzu ya tashi mu tafi mu koma service d'in mu samu manager, nasan insha Allah zai taimaka mana kamar yanda ya taimaka mana muka samu aikin nan da farko."
Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi kafin ya kalli Baba yace " kuyi hak'uri Baba, insha Allah zanje na bata hak'uri kamar yanda kuka ce."
Addu'a Mama ta bishi da ita da fatan samun dacewa, Baba kuma na sake jaddada masa ya tabbatar ya bata hak'uri sosai harta hak'ura, haka suka fito da niyyar tafiya ma'aikatar wajen manager.
Sun samu manager kuma Ishaq ya fad'a masa komai daya faru, yayi mamaki sosai dan baisan wainar da aka toya ba, yayi jimami sosai tare da k'ara tsorata Faruk akan karma ya fara tunkararta ya jira hukuncin da mahaifinta zai d'auka a kanshi ko kuma ita da kanta, baiji shakka ko d'ard'ar ba akan matakin da zasu d'auka, matsalarshi d'aya shine yanda mahaifinshi ya d'auka da zafi sosai, ganin baice komai ba yasa manager cewa,
"A gaskiya *Umar Faruk* ba zan yarda a dalilinka na rasa nawa aikin ba, kayi hak'uri, amma taimakon da zan iya maka na riga da nayi maka shi, shawara d'aya da zan baka kawai shine, idan har ta dawo d'aukar fansa to ka qasqantar da kanka, ka nuna mata kayi nadama kuma a bisa kuskuren rashin sanin ko wacece ita ka mareta, idan kayi sa'a ta iya yafe maka, amma gaskiya bana tunanin zata hak'ura, dan wallahi yarinyar nan rashin mutuncinta ya kai mak'ura, bata kallon kowa da idon daraja babu tausayi ko imani a zuciyarta, kuma tun ranar da mahaifinta ya mallaka mata masana'antar nan na fad'a muku dukanmu sai munyi hak'uri da ita, saboda kaushinta yayi yawa."
A sanyaye Umar faruk yace "zan jaraba na gani, bara naje bureau d'in nata."
Murmushi manager yayi yace "ta yaya kake tunanin zata zauna a wajen nan, ina jin a lokacin da naga tafiyarta to a lokacin ne abun ya faru."
"Kenan yanzu tana gida?" cewar Faruk d'in.
"Ina tunanin haka."
"Shikenan, zamu je har gidan, watak'ila ma tafi saurarenmu." cewar Ishaq
Faruk ne yace "a'a fa Ishaq, gaskiya bana so naje gidansu, idan taga haka zata san nadamu sosai, zata d'auka gaba d'aya na bada rayuwata wa aikin nan, hakan kuma zaisa ta qara wani rashin mutuncin."
"Muji ta d'auka a hakan in har ba zata koreka ba, meye a ciki?"
Kai Faruk ya girgiza yace "waiku me yasa ne kuke shakkarta har haka? mutum ce fa kamarku kuma mace mai rauni a kanku, me yasa zaku dinga tsoronta har haka, nifa wallahi bana son irin haka gaskiya, dan wannan ai bayar da maza kuke, yarinyar da da zaku bud'e mata ido sau d'aya dole zata fara shakkarku itama, amma duk kubi kuna wani tsoronta kamar ita ta halliceku."
Fuskar manager d'auke da murmushi yace "bawai muna jin tsoronta bane, sai dai ka sani kowane d'an adam a rayuwa yana buqatar ci da sha kafin ya rayu, to tamu k'addarar ta damka cin mu da shanmu ta sanadiyarta ne, ita kuma bata da kirki duk da bata jima a garin nan ba, amma na samu labarinta sosai kamar wanda yayi rayuwa a gidansu, dan ba tun yau muke tare da mahaifinta ba, kaga dole mubi a sannu."
Faruk ne ya tashi tsaye yace "zamu je gidan, ina fatan ta amince kodan saboda Baba."
Cikin tsokana Ishaq daya mik'e shima yace "da kana so amma kake wani nuna baka damu ba."
"Amma ai kaji me nace, ina fata ta amince saboda Baba." ya fad'a ba tare daya kalleshi ba.
Suna fita akan mashin d'in Faruk suka kama hanyar zuwa gidansu Khairat......
_Shin kuna ganin za suyi nasara kuwa? to wai zama su samu ganin Khairat d'in ko kuwa dai...???_
*********************
Suna zuwa k'ofar gidan suka tsaya suka sauka akan mashin d'in suka nufi k'ofar gidan, mai gadin gidan ne mai sanye da kaki irin na sojawa ya taresu yana fad'in "yadai malamai, daga ina, wa kuke nema?"
Ishaq ne yace "sannun ko, dan Allah munzo ganin Hajia Khairat ne."
Kallon tuhuma ya musu yace " Hajia Khairat? to tasan da zuwanku ne?"
Kallon juna sukayi tare da yin shiru na 'yan dak'ik'u kafin Ishaq ya sake cewa "gaskiya bata san da zuwanmu, mu daga service d'inta muke, manager ne ya turo mu saboda wani aiki daya d'an taso."
Kallonshi Faruk yayi saboda jin abinda ya fad'a , mai gadin ne yace "kuyi hak'uri mazaje, duk wanda ku kaga ya shiga gidan nan to an san da zuwanshi koda kuwa d'an uwane, kunsan gidan manyan mutane."
"Yanzu kenan babu wata dama da zata saka mu ganinta?" cewar Faruk.
"Gaskiya babu, dan Hajia Khairat ko tasan da zuwan mutun ma zata iya tsayar dashi a k'ofar gidan nan na tsawon awa uku, idan na barku kuka shiga zan iya rasa aikina."
Faruk ne yace "yanzu dan Allah to ya zamuyi muganta?"
Mai gadin ne yace "in dai abu mai mahimmaci ne, to zan iya fad'a muku wurin da zaku sameta, yanzu dai kunga ta shiga gida, kuma da alama ranta a b'ace ta shigo."
"To kenan ina zamu sameta?"
"Duk kwana uku takan je wajen casu, amma takamaimai wajen da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2 Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63