Yana kallonta yace "na shiga wajen k'anwarki ne, kinyi kewata har haka?"
Duk da taji wani abu ya soketa amma basarwa tayi tace "sosai ma, nifa bana son kana nisa dani sosai, sai naga kamar zan rasaka ne."
Tana fad'a ta janyo kanshi ta kwantar a saman cinyarta ta fara shafar kansa har zuwa qasumbarsa tana fad'in "yau ba zan fita aiki ba, amma zanje na siyowa su Mamie kayan da zasu tafi dashi, kaga daga nan nima saina siyo namu, dan nasan yanzu a Germany akwai sanyi, dan haka ina buk'atar ka bani aron motarka."
Shiru yayi yana kallonta yayin da zuciyarshi ke antayo mishi sink'i sink'in tambayoyi _"wai me yasa Khairat da Zubeida suka kasance ba d'aya ba? bayan kuma dukansu mata ne, me yasa Khairat tafi bashi farin ciki? sab'anin Zuby da sukayi soyayya, me yasa Khairat take son kusanci dashi sosai? ba kamar Zuby ba da bata ma son yana tab'a jikinta a koda yaushe, me yasa Khairat ta iya komai kuma cikin salo tare da iya takonta? shin wayewa ce tafi Zubeida? ko kuma ilimin bokon data fita ne? ko kuma bud'ewar ido?"_
_Bara na fan's Jihadi su baka amsar_π
Jin yayi shiru yasa ta shafi kumatunsa tace "baby." ta fad'a cikin shagwab'a.
Kallonta yayi yace "ina jinki."
"Au du baka ji me nace ba? me kake tunani?"
Tashi yayi daga cinyarta yace "naji, amma ai naji baki nemi izinin fitar ba."
Hararan wasa ta masa tana fad'in "wato kai mai iko ko? dama an fad'a namiji ko ka girmeshi in dai har aure ya shiga tsakaninku, to ka zama abin tausayi, dan iko kuke nunawa harna fitar hankali."
Da murmushi a fuskarsa yace "kuma hakan yayi ko?"
Gira ta d'aga sama tace "sosai ma, tunda hukuncine da yazo daga sama yankakke."
Harda gyaran murya tayi kafin ta langab'e kai tayi kalar tausayi tace "baby, dama ina neman izininka ne ina so zan fita dan na siyowa su Mamie kayan tafiyarsu, idan da hali ina so ka bani izini tare da aron makullin motarka?"
Janyota yayi jikinshi yana fad'in "kaji neman izini mai kyau, gaskiya daga yanzu haka zaki dinga yi idan zaki fita."
D'aga kanta tayi ta kalleshi amma wani kallo daya watsa mata yasa a hankali ta zura harshenta cikin bakinshi ta lumshe ido tare da kama harshen tana tsotsa......... saida ta gama rikirkitashi sannan ta mik'e tana gyara jikinta tace "bara na d'auko kayan karatu."
Hannunta ya rik'e hakan yasa ta juyo ta kalleshi, wani marayan kallo daya mata irin kizo ki taimakeni d'in nan yasa tayi murmushi ta matso kusanshi, kasancewar yana zaune hakan yasa ta manna kanshi a qirjinta a tsakiyar mamanta tana shafa kanshi, a hankali ta d'ago dashi ta kalleshi idonshi sunyi ja tace,
"Malam, lokacin karatu fa yayi." tana fad'a ta wuce d'auko litattafanta, ba yanda ya iya haka suka fara karatunsu kamar kullum.
Ruk'ayya ta kawo musu abin kari kamar yanda ta saba kuma yace ta kira Zubeida, da sallama ta shigo fuskar nan a had'e ba annuri, dogon hijabi ne a jikinta yama rufe kayan dake jikinta, zaune tayi inda tasan nan zaice ta zauna, ganin sun gaisa da asuba yasa ba tayi magana ba, Umar Faruk ne ya kalleta yace "ba gaisuwa?"
"Amma ai mun gaisa d'azu." ta fad'a ba tare data kalleshi ba.
"Ina nufin 'yar uwarki, nasan kin karanta a hadith, cewar idan kazo ka samu mutum a wuri kaine zaka fara gaisheshi."
A wulak'ance tace "ina kwana." tana hararan Khairat d'in.
Khairat da ita kanta haushinta take ji itama a wulak'ance ta amsa da "lafiya lau."
A haka suka fara cin abincin babu mai magana, Khairat kam yau kishinta take ji sosai, haka ma Zuby kamar zata mutu saboda ganin wai yau Umar Faruk ne ya zama nasu su biyu.
Zuby da masifa ke gurgurarta ce tace "idan ba damuwa zan iya magana?"
Kallonta yayi da murmushi yace "Zubeida, a zamanin 'yanci muke fa, zaki iya magana mana kina da damar hakan."
"Sai nake ganin kamar hakan bai dace ba kullum a dinga dafawa ana bamu, me zai hana ka raba mana girki, kaga kenan duk lokacin da kwanan d'aya daga cikinmu ya zagayo itace da girkin ranar."
Tabbas Zuby tayi gaskiya dan abinda ya kamata kenan, saida ya gyara zamansa kafin yace "gaskiya ne Zubeida, kin fad'i abinda dama dole zanyi magana akai koba yanzu ba."
Kallon Khairat yayi yace "abinda ya dace ayi kenan, dan haka yanzu zaku fara girki da kanku."
Waro masa ido tayi tayi magana qasa qasa sai dai baiji me tace ba saboda na kurame ne tayi, ganin Zuby ta tashi tare da fad'in "alhamdulillah, aci lafiya." tana fad'a ta bar d'akin domin kuwa burinta ya cika.
Khairat na ganin haka ta gyara zama da kyau ta cire hannunta daga plate d'in tace masa "me kayi haka Faruk, so kake kaci mutuncina a gaban yarinya qarama, dan kasan ban iya komai ba shi yasa zaka amince da abinda ta fad'a? to kama sake tsari dan wallahi ba zan yarda ba, dan babu abinda zai sani yin girki koda ma na iya."
"Khairat, miye abun d'aga hankali a cikin nan? kinyi sakaci tun farko kasancewarki na 'ya mace kika kasa koyan aiyukan da kinsan dole zaki yisu in dai har kinyi aure, amma duk da haka ba wata matsala tunda zaki iya koya."
"Kana haukane? nice zanje koyan girki saboda kawai waccen yarinyar, nifa ba zan iya wannan wahalar ba ta girki danko a gidanmu banyi ba, kuma kai shaidane."
Kallon da yake watsa mata ba tare da magana ba yasa ta mik'e ta cire rigar baccinta ta shiga wanka, tana fitowa shima ya shiga cikin sauri ya fito ya fara shiri, saida ya gama shi da ita babu mai kula wani harya d'auki jakarshi zai fita ya d'auko makullin motar ya mik'a mata, karb'a tayi ba tare data kulashi ba kafin ya fice daga gidan.
Saida ya fita kuma tana shirin tana tambayar kanta me yasa tayi haka? ita da take burin ganin ta mallakeshi ta hanya mai kyau, ji tayi kuma ta kasa hak'ura kawai ta d'auki wayarta ta danna masa kira, k'in d'aga kiran yayi saboda yana kan hanya cinkoso yayi yawa, har ya kai bata daina kira ba koda yaga itace kawai saiya share yana tunanin me zata fad'a masa, da sauri ya shiga ma'aikatar ya tarar an fara taro, kamar ko wane ma'aikaci shima tsayawa yayi yana sauraron abinda manager ke fad'a, ya jima yana jawabi kafin ya gabatar da abinda ya tarasu.
Nan aka fara duba sunayen mutum uku wanda zanensu yafi na kowa, na farko shine *Umar Faruk Ahmad* na biyu kuma *Abdullahi Salis* ta uku *Surayya Balarabe*, nan aka kira kowa aka bashi kyautarshi tare da musu fatan alkairi sannan aka qarfafa musu gwiwa tare ma da wanda nasu samu nasara ba, damar tafiya aka basu ba tare da sunyi aikin wannan ranar ba.
*****************
Umar Faruk baya raba d'ayan biyu kan cewar aikin Khairat ne, dan shi dai yasan a tarihin masana'antar babu wanda akace an tab'a bawa kyautar mota, wannan mamakin ya hanashi tuk'a motar sai Ishaq ne ya tuk'ota shi kuma yazo a mashin d'inshi, a k'ofar gida aka paka motar su kuma suka shiga ciki Ishaq na shaidawa mutanen, murna dai ba kowa ke yi ba daga ciki harda Umar Faruk, a haka aka kira Khairat da Zuby dansu gani, suma dai babu wacce ta fito da farin cikinta a fili, Zuby tunaninta shine Khairat ce ta bashi motar raina mata hankali kawai zasuyi, Khairat kuma haushin ta kira bai d'aga bane yake damunta.
Sake fita sukayi da Ishaq Umar Faruk ya goyashi a mashin ya mayar dashi ma'aikatar shi kuma ya dawo amma a hanya saida ya tsaya ya s gas guda biyu 5kl kafin ya dawo gida.
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Sorry fan's abisa rashin amsa comment d'inku, jikin ne sai a hankali._
_Dan Allah ku tayamu da addu'a Allah ya bawa my *BK* lafiya, ina so ta dawo muci gaba da kodimoπ, my masoyiyar BK nayi kewarki sosai, rashinki yasa nima bana jin dad'i._
_Bismmilahir-rahman-rahim_
3β£6β£
Tunda yaga baiga mota a k'ofar gidan ba ya tabbatar ta fita, koda ya shigo Aliyu ne ya tarbeshi ya karb'i tukunyar gas d'in, d'aya ya bawa Zuby d'aya kuma ya aje a kewayen Khairat, shiga yayi ya rage kayan jikinshi sannan ya kwanta akan gado, wayarshi ya ciro ya fara kiran Khairat, Khairat kuma data bar wayar a mota tana cikin babban kanti tana siyayya, hakan yasa Umar Faruk cewa ta rama ne itama.
***************
Har *12:40* Khairat bata dawo ba, ganin haka yasa Zuby girki d'an sassauk'an abinci ta zuba a plate ta rufe da d'aya tare da cokali ta tunkari d'akin Khairat.
Bud'a labulen tayi ta zura qafafunta ta shiga, ganin Zuby yasa ya tashi zaune dan baiyi tsammanin ita bace saboda murayar daya ji, "Zubeida, kece dama?"
Saida ta tsaya gabanshi tace "eh, kona koma ne baka buk'atar ganina?"
"Ah haba, ni na isa."
Ganin tayi zaune a bakin gadon kusa da qafafunshi tana wani yamutsa fuska yasa ya d'an qara gyara nutsuwarsa yace "ina jinki, magana zamuyi ne?"
"Abinci na kawo maka, dan nasan kana jin yunwa, tunda naga ita har yanzu bata dawo daga walagigin ba." ta fad'a tana bud'a plate d'in.
"Me kike nufi da abinda kika fad'a?" ya tambaya.
Cikin had'e fuska tace "ka fini sani mana."
Qara gyara zama yayi yace "Zubeida, ku matana ne, kuma nine mai alhakin kare mutuncin kowace daga cikinku, ya kamata kisan me zaki dinga fad'a akan Khairat, duk cin zarafin da zaki mata kamar ni kikawa , haka itama idan ta miki ni tawa, tunda kika zo gidan nan kike kiranta da sunan da bai dace ba, na miki shiru ne kawai amma naga baki gani ba, to daga yanzu bana so na sake jin kin kirata da sunan karuwa, dan ita ba karuwa bace kamar yanda kike fad'a, dan haka ki kiyaye, idan kuma abincin kika zo bani zaki iya ajewa ki tafi na gode."
Cike da makirci ta fashe da kuka tana fad'in "ni dama sani baka sona yanzu, wallahi banyi tunanin haka daga gareka ba yah Umar, gaba d'aya ka canza saboda waccen matar, shine ba komai ba anfanin zamana a gidan nan in dai har baka sona."
Tsaye ta mike ta fara tafiya taji ya rik'e hannunta, saukowa yayi daga kan gadon ya rumgumota jikinshi yana shafa kanta, cikin rarrashi ya fara fad'in, kiyi hak'uri, baki fahimceni bane Zubeida, ina so ki gane cewa, ke da Khairat ba zan bari wani ya cutar da d'aya ba, ko itace take fad'a miki haka abinda zanyi kenan, ke da ita duka Allah zai tsayar dani ranar gobe kuma ya tambayeni yanda na shugabanceku, Zubeida na zama mutum azzulumi da baya iya adalci tsakanin matanshi, da farko naci amanar Khairat ta hanyar kusantarki a kwananta, dan Allah ki taimaka karna sake aikata wani laifi, banyi adalci ba idan nayi shiru ina ji kina kiranta da karuwa, amma kiyi hak'uri kinji."
D'ago da kanta yayi yana kallon fuskarta yace "kiyi shiru to, yanzu kije d'akinki ki zauna zanci abincin, bana son mai d'akin ta sameki anan, dan nasan yanzu tana kan hanyarrrr."
Bai k'arasa ba kuma Khairat ta bud'a labulen d'akin ta shigo, daram dam, shine tsinkewar da gaban Khairat yayi ganin Zuby a qirjin Umar Faruk, bugun zuciyarta ne ya qaru ta yanda ba zata iya saisaita kanta ba, sauke idonta tayi akan Zuby ta fara takowa cikin d'akin, itama Zuby d'in ita take kallo harta aje plate d'in hannunta akan center tebur d'in d'akin, ganin yanda suke kallon juna yasa Umar Faruk cewa "Zuby ki wuce d'akinki."
Saida ta gama hararan Khairat sama da qasa sannan taja dogon tsaki ta nufi hanyar fita, aikam dama zuciyar Khairat a wuya take hakan yasa ta finciko rigar Zuby ta shake sosai ta zubar da kayan hannunta harda wayarta ta mata wani jan kallo tace "dawa kike, ni Khairat ki kewa tsaki, ni kike wa tsaki? dake nake magana."
Ta qarashe maganar da d'aga murya, matsowa Umar Faruk yayi da nufin magana Khairat ta daga masa hannu tace "dakata min dallah, bari na gama da ita sannan, kana kallo qaramar yarinya zata nemi taci mutunci na, akan miye zata min tsaki?bayan nice ke daidai nayi mata tunda ni na sameta a d'akina, koda yake ba laifinta bane laifinka ne, da baka kirata ba aiba zata zo, shine har zata dinga min kallon raini da iskanci, wallahi sai naji wanda ya d'aure miki gindi a gidan nan."
Ta qarasa tana jinjigar Zuby dake hannunta, Zuby kam tuni idonta suka fara kawo qwalla, cikin gunguni ta rik'e hannun Khairat tace "dallah sakeni malama."
Wani murmushin rainin hankali Khairat ta mata ta sake shak'ar rigarta ta jinjina tace "ki k'wace mana idan kina ganin k'arfinki yakai, tabbas gata da shagwab'a ne suka raini ne, amma ki sani ina da k'warin k'ashi da tsabagen tsagwaron k'arfi, ta yanda idan na rik'i kamarki wallahi ba zaki iya k'watar kanki ba, amma idan kinyi musu toki gwada ki gani."
Qara qoqarin qwaqwale hannun Khairat tayi amma tajita jim a hannunta, sake maqale murya tayi tace "dallah nace ki sakeni ko."
"Hum, bari kiji na fad'a miki, dama nasan dole za kiyi rawar kai dan tunda naga mahifiyarki na tabbatar da haka, tun ranar da kika shigo gidan nan kike min kallon bi aho amma na miki shiru, to ki sani qyaleki nake ba dan komai ba sai dan canjin da aka samu, idan kuma kika kuskura kika tayar da qwanqwanman Khairat harna dawo asalin Khairat d'ita, tofa akwai matsala dan ba lallai gidan nan su iya dani ba, kashedi na qarshe, karki bari na sake ganin qafarki cikin d'akina dan ban yarda dake ba, kamar yanda ban yarda da mahaifiyarki ba."
Da kai ta mata alamar ta wuce kawai, ficewa tayi da sauri saboda hawayen dake son taho mata, kai tsaye d'akinta ta wuce ta fad'a saman gado ta fashe da kuka, duk da zuciyarta naso ta qaryata abinda take ji, amma dai tabbas ta tsorata da Khairat yau d'in nan, dan tasan gaminta da ita ba zai mata kyau ba, saida taci kukanta ta koshi sannan ta kira Mama ta fad'a mata abinda yake faruwa, fad'a sosai Mama ta mata tare da zaginta gaba da baya kafin ta sake jaddada mata tayi aiki da magungunan nan.
Bud'ar bakinta cewa tayi "ai Mama maganin ne nasa a abinci nakai masa, shine fa tsinannar ta shigo."
"Toki kwantar da hankalinki, nasan ai zaici abinci, da yaci kuma magana ta qare."
"To Mama, sai an jima."
***************
Tana fita Khairat ta wurga masa harara tana hango Zuby a qirjinshi, ta gabanshi taso wucewa amma saiya tareta, kallonshi tayi tace "matsa min a hanya."
"Ba zan iya ba, saboda kina hushi dani."
"Ka matsa min nace ko, inba so kake na huce a kanka ba."
"In dai zaki huce na amince ki huce a kaina."
K'arfinta tasa ta tureshi gefe hakan yasa yayi baya da k'arfi, amma jarumta tasa bai fad'i qasa ba, tsaye yayi sosai a gabanta a hankali ya rik'o hannunta tare da zube gwiwoyinshi a qasa ya marairaice kafin ya fara magana,
"Kiyi hak'uri, nasan ke mai hak'uri ce, ki yafe min domin nasan kin yafe min laifin da yafi wannan ma, kimin uzuri danna fahimci ke mai ilimi ce, my *Khairiri* ki yafewa wannan hamagon mijin naki mana, ke alkairi ce a gareshi kamar yanda fassarar sunanki yake, duk da dai bana da laifi, amma ina neman gafararki matata, idan baki yafe min ba zan shiga tashin hankalin da nake da yak'inin ban tab'a shiga irinsa ba, domin kuwa Khairat ta zama wani b'angare na sassan jikin Umar Faruk, a yanzun yafiyarki ce zata zata tabbatar da ci gaba da farin cikin mijinki ko akasin haka, domin kuwa ba Umar Faruk in dai har ba Khairat, hushinki na second d'aya, tamkar hushin duka mutanen duniya ne a wajen Umar Faruk, ki tausaya kuma agazawa wannan bawan Allah wanda rayuwarsa ta kasance kece mahad'inta, kuma nasan ko Khairat ce ta b'atawa Umar Faruk rai, zata sunkuya har qasa sannan ta nemi afuwarsa, a lokacin kuma Umar Faruk zai rumgumo Khairat jikinsa sannan yace na yafe miki my Khairat."
_Kaji mai wayo, wato ya fad'a mata abinda ya kamata tayi cikin dubara._
Inhar Khairat tace kalaman nan basu shiga sassa da b'argo da jijiyarta suka ratsa zuciyarta ba, to qarya ta fad'a hakan yasa ta sunkuya itama ta rumgumeshi tace "na yafe to, amma me yasa zata shigo min har d'aki kuma ta raina min wayo?"
K'eya ya d'an sosa yace "kiyi hak'uri, abinci kawai ta kawo min."
Sai lokacin ta juya ta kalli plate d'in dake aje, takawa tayi ta d'auki plate d'in ta dauka ta bud'a, tsaki tayi tare da fad'in "aikin banza kawai, inba munafirci ba meye na kawo maka abinci? bayan ba ranar girkinta bace, to ba zaka ci ba danni ban yarda da ita ba."
Tana fad'a ta fita da plate d'in ta aje akan gajerar katangarsu sannan ta dawo ta fara cire kayanta, bayanta ya tsaya ya fara cire mata bras yana fad'in "naji dad'i da kika yafe min, nan gaba zan kiyaye b'acin ranki."
Tana d'aure kitsonta tace "kayi nasara akan Khairat, dama wannan kalaman kad'ai Khairat take buk'ata kuma gashi ta samu maiyi mata."
Da haka ta shiga wanka shi kuma ya nufi masallaci, yana dawowa kuma ya samu tana sallah, kayan data barbaza ya fara tattarewa, wanda ta cire kuma ya ninkesu ya mayar drower, tana gamawa ta taso ta sumbaci goshinshi tare da qarasa addu'arta ta fad'a a fili cewa "Allah ya dawwamar maka da farin ciki
Showing 99001 words to 102000 words out of 186119 words
Yana kallonta yace "na shiga wajen k'anwarki ne, kinyi kewata har haka?"
Duk da taji wani abu ya soketa amma basarwa tayi tace "sosai ma, nifa bana son kana nisa dani sosai, sai naga kamar zan rasaka ne."
Tana fad'a ta janyo kanshi ta kwantar a saman cinyarta ta fara shafar kansa har zuwa qasumbarsa tana fad'in "yau ba zan fita aiki ba, amma zanje na siyowa su Mamie kayan da zasu tafi dashi, kaga daga nan nima saina siyo namu, dan nasan yanzu a Germany akwai sanyi, dan haka ina buk'atar ka bani aron motarka."
Shiru yayi yana kallonta yayin da zuciyarshi ke antayo mishi sink'i sink'in tambayoyi _"wai me yasa Khairat da Zubeida suka kasance ba d'aya ba? bayan kuma dukansu mata ne, me yasa Khairat tafi bashi farin ciki? sab'anin Zuby da sukayi soyayya, me yasa Khairat take son kusanci dashi sosai? ba kamar Zuby ba da bata ma son yana tab'a jikinta a koda yaushe, me yasa Khairat ta iya komai kuma cikin salo tare da iya takonta? shin wayewa ce tafi Zubeida? ko kuma ilimin bokon data fita ne? ko kuma bud'ewar ido?"_
_Bara na fan's Jihadi su baka amsar_π
Jin yayi shiru yasa ta shafi kumatunsa tace "baby." ta fad'a cikin shagwab'a.
Kallonta yayi yace "ina jinki."
"Au du baka ji me nace ba? me kake tunani?"
Tashi yayi daga cinyarta yace "naji, amma ai naji baki nemi izinin fitar ba."
Hararan wasa ta masa tana fad'in "wato kai mai iko ko? dama an fad'a namiji ko ka girmeshi in dai har aure ya shiga tsakaninku, to ka zama abin tausayi, dan iko kuke nunawa harna fitar hankali."
Da murmushi a fuskarsa yace "kuma hakan yayi ko?"
Gira ta d'aga sama tace "sosai ma, tunda hukuncine da yazo daga sama yankakke."
Kafin yayi magana ta gyara zama tana fuskantarshi tace "to naji zan nemi izinin."
Harda gyaran murya tayi kafin ta langab'e kai tayi kalar tausayi tace "baby, dama ina neman izininka ne ina so zan fita dan na siyowa su Mamie kayan tafiyarsu, idan da hali ina so ka bani izini tare da aron makullin motarka?"
Janyota yayi jikinshi yana fad'in "kaji neman izini mai kyau, gaskiya daga yanzu haka zaki dinga yi idan zaki fita."
D'aga kanta tayi ta kalleshi amma wani kallo daya watsa mata yasa a hankali ta zura harshenta cikin bakinshi ta lumshe ido tare da kama harshen tana tsotsa......... saida ta gama rikirkitashi sannan ta mik'e tana gyara jikinta tace "bara na d'auko kayan karatu."
Hannunta ya rik'e hakan yasa ta juyo ta kalleshi, wani marayan kallo daya mata irin kizo ki taimakeni d'in nan yasa tayi murmushi ta matso kusanshi, kasancewar yana zaune hakan yasa ta manna kanshi a qirjinta a tsakiyar mamanta tana shafa kanshi, a hankali ta d'ago dashi ta kalleshi idonshi sunyi ja tace,
"Malam, lokacin karatu fa yayi." tana fad'a ta wuce d'auko litattafanta, ba yanda ya iya haka suka fara karatunsu kamar kullum.
Ruk'ayya ta kawo musu abin kari kamar yanda ta saba kuma yace ta kira Zubeida, da sallama ta shigo fuskar nan a had'e ba annuri, dogon hijabi ne a jikinta yama rufe kayan dake jikinta, zaune tayi inda tasan nan zaice ta zauna, ganin sun gaisa da asuba yasa ba tayi magana ba, Umar Faruk ne ya kalleta yace "ba gaisuwa?"
"Amma ai mun gaisa d'azu." ta fad'a ba tare data kalleshi ba.
"Ina nufin 'yar uwarki, nasan kin karanta a hadith, cewar idan kazo ka samu mutum a wuri kaine zaka fara gaisheshi."
A wulak'ance tace "ina kwana." tana hararan Khairat d'in.
Khairat da ita kanta haushinta take ji itama a wulak'ance ta amsa da "lafiya lau."
A haka suka fara cin abincin babu mai magana, Khairat kam yau kishinta take ji sosai, haka ma Zuby kamar zata mutu saboda ganin wai yau Umar Faruk ne ya zama nasu su biyu.
Zuby da masifa ke gurgurarta ce tace "idan ba damuwa zan iya magana?"
Kallonta yayi da murmushi yace "Zubeida, a zamanin 'yanci muke fa, zaki iya magana mana kina da damar hakan."
"Sai nake ganin kamar hakan bai dace ba kullum a dinga dafawa ana bamu, me zai hana ka raba mana girki, kaga kenan duk lokacin da kwanan d'aya daga cikinmu ya zagayo itace da girkin ranar."
Tabbas Zuby tayi gaskiya dan abinda ya kamata kenan, saida ya gyara zamansa kafin yace "gaskiya ne Zubeida, kin fad'i abinda dama dole zanyi magana akai koba yanzu ba."
Kallon Khairat yayi yace "abinda ya dace ayi kenan, dan haka yanzu zaku fara girki da kanku."
Waro masa ido tayi tayi magana qasa qasa sai dai baiji me tace ba saboda na kurame ne tayi, ganin Zuby ta tashi tare da fad'in "alhamdulillah, aci lafiya." tana fad'a ta bar d'akin domin kuwa burinta ya cika.
Khairat na ganin haka ta gyara zama da kyau ta cire hannunta daga plate d'in tace masa "me kayi haka Faruk, so kake kaci mutuncina a gaban yarinya qarama, dan kasan ban iya komai ba shi yasa zaka amince da abinda ta fad'a? to kama sake tsari dan wallahi ba zan yarda ba, dan babu abinda zai sani yin girki koda ma na iya."
"Khairat, miye abun d'aga hankali a cikin nan? kinyi sakaci tun farko kasancewarki na 'ya mace kika kasa koyan aiyukan da kinsan dole zaki yisu in dai har kinyi aure, amma duk da haka ba wata matsala tunda zaki iya koya."
"Kana haukane? nice zanje koyan girki saboda kawai waccen yarinyar, nifa ba zan iya wannan wahalar ba ta girki danko a gidanmu banyi ba, kuma kai shaidane."
Kallon da yake watsa mata ba tare da magana ba yasa ta mik'e ta cire rigar baccinta ta shiga wanka, tana fitowa shima ya shiga cikin sauri ya fito ya fara shiri, saida ya gama shi da ita babu mai kula wani harya d'auki jakarshi zai fita ya d'auko makullin motar ya mik'a mata, karb'a tayi ba tare data kulashi ba kafin ya fice daga gidan.
Saida ya fita kuma tana shirin tana tambayar kanta me yasa tayi haka? ita da take burin ganin ta mallakeshi ta hanya mai kyau, ji tayi kuma ta kasa hak'ura kawai ta d'auki wayarta ta danna masa kira, k'in d'aga kiran yayi saboda yana kan hanya cinkoso yayi yawa, har ya kai bata daina kira ba koda yaga itace kawai saiya share yana tunanin me zata fad'a masa, da sauri ya shiga ma'aikatar ya tarar an fara taro, kamar ko wane ma'aikaci shima tsayawa yayi yana sauraron abinda manager ke fad'a, ya jima yana jawabi kafin ya gabatar da abinda ya tarasu.
Nan aka fara duba sunayen mutum uku wanda zanensu yafi na kowa, na farko shine *Umar Faruk Ahmad* na biyu kuma *Abdullahi Salis* ta uku *Surayya Balarabe*, nan aka kira kowa aka bashi kyautarshi tare da musu fatan alkairi sannan aka qarfafa musu gwiwa tare ma da wanda nasu samu nasara ba, damar tafiya aka basu ba tare da sunyi aikin wannan ranar ba.
*****************
Umar Faruk baya raba d'ayan biyu kan cewar aikin Khairat ne, dan shi dai yasan a tarihin masana'antar babu wanda akace an tab'a bawa kyautar mota, wannan mamakin ya hanashi tuk'a motar sai Ishaq ne ya tuk'ota shi kuma yazo a mashin d'inshi, a k'ofar gida aka paka motar su kuma suka shiga ciki Ishaq na shaidawa mutanen, murna dai ba kowa ke yi ba daga ciki harda Umar Faruk, a haka aka kira Khairat da Zuby dansu gani, suma dai babu wacce ta fito da farin cikinta a fili, Zuby tunaninta shine Khairat ce ta bashi motar raina mata hankali kawai zasuyi, Khairat kuma haushin ta kira bai d'aga bane yake damunta.
Sake fita sukayi da Ishaq Umar Faruk ya goyashi a mashin ya mayar dashi ma'aikatar shi kuma ya dawo amma a hanya saida ya tsaya ya s gas guda biyu 5kl kafin ya dawo gida.
_Bara nima na tab'a turancin nan._π
_I need you prayers fan's._πππ
_Me zai faru to_π€
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Sorry fan's abisa rashin amsa comment d'inku, jikin ne sai a hankali._
_Dan Allah ku tayamu da addu'a Allah ya bawa my *BK* lafiya, ina so ta dawo muci gaba da kodimoπ, my masoyiyar BK nayi kewarki sosai, rashinki yasa nima bana jin dad'i._
_Bismmilahir-rahman-rahim_
3β£6β£
Tunda yaga baiga mota a k'ofar gidan ba ya tabbatar ta fita, koda ya shigo Aliyu ne ya tarbeshi ya karb'i tukunyar gas d'in, d'aya ya bawa Zuby d'aya kuma ya aje a kewayen Khairat, shiga yayi ya rage kayan jikinshi sannan ya kwanta akan gado, wayarshi ya ciro ya fara kiran Khairat, Khairat kuma data bar wayar a mota tana cikin babban kanti tana siyayya, hakan yasa Umar Faruk cewa ta rama ne itama.
***************
Har *12:40* Khairat bata dawo ba, ganin haka yasa Zuby girki d'an sassauk'an abinci ta zuba a plate ta rufe da d'aya tare da cokali ta tunkari d'akin Khairat.
πππhumm, zaki jawa kanki.
"Assalama alaikum." tayi sallama cikin taushin murya.
"Wa'alaiki salam, shigo." ya fad'a.
Bud'a labulen tayi ta zura qafafunta ta shiga, ganin Zuby yasa ya tashi zaune dan baiyi tsammanin ita bace saboda murayar daya ji, "Zubeida, kece dama?"
Saida ta tsaya gabanshi tace "eh, kona koma ne baka buk'atar ganina?"
"Ah haba, ni na isa."
Ganin tayi zaune a bakin gadon kusa da qafafunshi tana wani yamutsa fuska yasa ya d'an qara gyara nutsuwarsa yace "ina jinki, magana zamuyi ne?"
"Abinci na kawo maka, dan nasan kana jin yunwa, tunda naga ita har yanzu bata dawo daga walagigin ba." ta fad'a tana bud'a plate d'in.
"Me kike nufi da abinda kika fad'a?" ya tambaya.
Cikin had'e fuska tace "ka fini sani mana."
Qara gyara zama yayi yace "Zubeida, ku matana ne, kuma nine mai alhakin kare mutuncin kowace daga cikinku, ya kamata kisan me zaki dinga fad'a akan Khairat, duk cin zarafin da zaki mata kamar ni kikawa , haka itama idan ta miki ni tawa, tunda kika zo gidan nan kike kiranta da sunan da bai dace ba, na miki shiru ne kawai amma naga baki gani ba, to daga yanzu bana so na sake jin kin kirata da sunan karuwa, dan ita ba karuwa bace kamar yanda kike fad'a, dan haka ki kiyaye, idan kuma abincin kika zo bani zaki iya ajewa ki tafi na gode."
Cike da makirci ta fashe da kuka tana fad'in "ni dama sani baka sona yanzu, wallahi banyi tunanin haka daga gareka ba yah Umar, gaba d'aya ka canza saboda waccen matar, shine ba komai ba anfanin zamana a gidan nan in dai har baka sona."
Tsaye ta mike ta fara tafiya taji ya rik'e hannunta, saukowa yayi daga kan gadon ya rumgumota jikinshi yana shafa kanta, cikin rarrashi ya fara fad'in, kiyi hak'uri, baki fahimceni bane Zubeida, ina so ki gane cewa, ke da Khairat ba zan bari wani ya cutar da d'aya ba, ko itace take fad'a miki haka abinda zanyi kenan, ke da ita duka Allah zai tsayar dani ranar gobe kuma ya tambayeni yanda na shugabanceku, Zubeida na zama mutum azzulumi da baya iya adalci tsakanin matanshi, da farko naci amanar Khairat ta hanyar kusantarki a kwananta, dan Allah ki taimaka karna sake aikata wani laifi, banyi adalci ba idan nayi shiru ina ji kina kiranta da karuwa, amma kiyi hak'uri kinji."
D'ago da kanta yayi yana kallon fuskarta yace "kiyi shiru to, yanzu kije d'akinki ki zauna zanci abincin, bana son mai d'akin ta sameki anan, dan nasan yanzu tana kan hanyarrrr."
Bai k'arasa ba kuma Khairat ta bud'a labulen d'akin ta shigo, daram dam, shine tsinkewar da gaban Khairat yayi ganin Zuby a qirjin Umar Faruk, bugun zuciyarta ne ya qaru ta yanda ba zata iya saisaita kanta ba, sauke idonta tayi akan Zuby ta fara takowa cikin d'akin, itama Zuby d'in ita take kallo harta aje plate d'in hannunta akan center tebur d'in d'akin, ganin yanda suke kallon juna yasa Umar Faruk cewa "Zuby ki wuce d'akinki."
Saida ta gama hararan Khairat sama da qasa sannan taja dogon tsaki ta nufi hanyar fita, aikam dama zuciyar Khairat a wuya take hakan yasa ta finciko rigar Zuby ta shake sosai ta zubar da kayan hannunta harda wayarta ta mata wani jan kallo tace "dawa kike, ni Khairat ki kewa tsaki, ni kike wa tsaki? dake nake magana."
Ta qarashe maganar da d'aga murya, matsowa Umar Faruk yayi da nufin magana Khairat ta daga masa hannu tace "dakata min dallah, bari na gama da ita sannan, kana kallo qaramar yarinya zata nemi taci mutunci na, akan miye zata min tsaki?bayan nice ke daidai nayi mata tunda ni na sameta a d'akina, koda yake ba laifinta bane laifinka ne, da baka kirata ba aiba zata zo, shine har zata dinga min kallon raini da iskanci, wallahi sai naji wanda ya d'aure miki gindi a gidan nan."
Ta qarasa tana jinjigar Zuby dake hannunta, Zuby kam tuni idonta suka fara kawo qwalla, cikin gunguni ta rik'e hannun Khairat tace "dallah sakeni malama."
Wani murmushin rainin hankali Khairat ta mata ta sake shak'ar rigarta ta jinjina tace "ki k'wace mana idan kina ganin k'arfinki yakai, tabbas gata da shagwab'a ne suka raini ne, amma ki sani ina da k'warin k'ashi da tsabagen tsagwaron k'arfi, ta yanda idan na rik'i kamarki wallahi ba zaki iya k'watar kanki ba, amma idan kinyi musu toki gwada ki gani."
Qara qoqarin qwaqwale hannun Khairat tayi amma tajita jim a hannunta, sake maqale murya tayi tace "dallah nace ki sakeni ko."
"Hum, bari kiji na fad'a miki, dama nasan dole za kiyi rawar kai dan tunda naga mahifiyarki na tabbatar da haka, tun ranar da kika shigo gidan nan kike min kallon bi aho amma na miki shiru, to ki sani qyaleki nake ba dan komai ba sai dan canjin da aka samu, idan kuma kika kuskura kika tayar da qwanqwanman Khairat harna dawo asalin Khairat d'ita, tofa akwai matsala dan ba lallai gidan nan su iya dani ba, kashedi na qarshe, karki bari na sake ganin qafarki cikin d'akina dan ban yarda dake ba, kamar yanda ban yarda da mahaifiyarki ba."
Da kai ta mata alamar ta wuce kawai, ficewa tayi da sauri saboda hawayen dake son taho mata, kai tsaye d'akinta ta wuce ta fad'a saman gado ta fashe da kuka, duk da zuciyarta naso ta qaryata abinda take ji, amma dai tabbas ta tsorata da Khairat yau d'in nan, dan tasan gaminta da ita ba zai mata kyau ba, saida taci kukanta ta koshi sannan ta kira Mama ta fad'a mata abinda yake faruwa, fad'a sosai Mama ta mata tare da zaginta gaba da baya kafin ta sake jaddada mata tayi aiki da magungunan nan.
Bud'ar bakinta cewa tayi "ai Mama maganin ne nasa a abinci nakai masa, shine fa tsinannar ta shigo."
"Toki kwantar da hankalinki, nasan ai zaici abinci, da yaci kuma magana ta qare."
"To Mama, sai an jima."
***************
Tana fita Khairat ta wurga masa harara tana hango Zuby a qirjinshi, ta gabanshi taso wucewa amma saiya tareta, kallonshi tayi tace "matsa min a hanya."
"Ba zan iya ba, saboda kina hushi dani."
"Ka matsa min nace ko, inba so kake na huce a kanka ba."
"In dai zaki huce na amince ki huce a kaina."
K'arfinta tasa ta tureshi gefe hakan yasa yayi baya da k'arfi, amma jarumta tasa bai fad'i qasa ba, tsaye yayi sosai a gabanta a hankali ya rik'o hannunta tare da zube gwiwoyinshi a qasa ya marairaice kafin ya fara magana,
"Kiyi hak'uri, nasan ke mai hak'uri ce, ki yafe min domin nasan kin yafe min laifin da yafi wannan ma, kimin uzuri danna fahimci ke mai ilimi ce, my *Khairiri* ki yafewa wannan hamagon mijin naki mana, ke alkairi ce a gareshi kamar yanda fassarar sunanki yake, duk da dai bana da laifi, amma ina neman gafararki matata, idan baki yafe min ba zan shiga tashin hankalin da nake da yak'inin ban tab'a shiga irinsa ba, domin kuwa Khairat ta zama wani b'angare na sassan jikin Umar Faruk, a yanzun yafiyarki ce zata zata tabbatar da ci gaba da farin cikin mijinki ko akasin haka, domin kuwa ba Umar Faruk in dai har ba Khairat, hushinki na second d'aya, tamkar hushin duka mutanen duniya ne a wajen Umar Faruk, ki tausaya kuma agazawa wannan bawan Allah wanda rayuwarsa ta kasance kece mahad'inta, kuma nasan ko Khairat ce ta b'atawa Umar Faruk rai, zata sunkuya har qasa sannan ta nemi afuwarsa, a lokacin kuma Umar Faruk zai rumgumo Khairat jikinsa sannan yace na yafe miki my Khairat."
_Kaji mai wayo, wato ya fad'a mata abinda ya kamata tayi cikin dubara._
Inhar Khairat tace kalaman nan basu shiga sassa da b'argo da jijiyarta suka ratsa zuciyarta ba, to qarya ta fad'a hakan yasa ta sunkuya itama ta rumgumeshi tace "na yafe to, amma me yasa zata shigo min har d'aki kuma ta raina min wayo?"
K'eya ya d'an sosa yace "kiyi hak'uri, abinci kawai ta kawo min."
Sai lokacin ta juya ta kalli plate d'in dake aje, takawa tayi ta d'auki plate d'in ta dauka ta bud'a, tsaki tayi tare da fad'in "aikin banza kawai, inba munafirci ba meye na kawo maka abinci? bayan ba ranar girkinta bace, to ba zaka ci ba danni ban yarda da ita ba."
Tana fad'a ta fita da plate d'in ta aje akan gajerar katangarsu sannan ta dawo ta fara cire kayanta, bayanta ya tsaya ya fara cire mata bras yana fad'in "naji dad'i da kika yafe min, nan gaba zan kiyaye b'acin ranki."
Tana d'aure kitsonta tace "kayi nasara akan Khairat, dama wannan kalaman kad'ai Khairat take buk'ata kuma gashi ta samu maiyi mata."
Da haka ta shiga wanka shi kuma ya nufi masallaci, yana dawowa kuma ya samu tana sallah, kayan data barbaza ya fara tattarewa, wanda ta cire kuma ya ninkesu ya mayar drower, tana gamawa ta taso ta sumbaci goshinshi tare da qarasa addu'arta ta fad'a a fili cewa "Allah ya dawwamar maka da farin ciki
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34 Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63