na d'aki aka sallama dan haka Zuby ta fita ta karb'o saqon , Zuby ta shiga d'akin ta samu tanti na waya, wayar da tasa cikin Zuby barazanar zubewa.....


_Me kuma taji???_


**Muje zuwa*😘


*Kuyi hak'uri da rashin jina , qanwar mijina ce tayi saukan Qur'ani yau.*


_Wanda suka kira ban d'auka ba kuyi hak'uri, duk kun kirane a lokacin da banawa ba, nasan dai kun fahimta saboda maganar ta manya ce, my Belle *(momyn khadija)*, naga kiranki kema, sorry, i love you all._


***************

6📓2📓
Cike da kwankwanto tanti tace "Malam anya kuwa baka ka kashe Bala ba? danni nasan dai mun baka aiki akanshi."

Jim tayi alamar tana sauraro, ta jima kafin tace "a'a wallahi babu ruwana ni, kai ka kasheshi, nidai kawai nace kasa su gane kurensu amma babu wanda nace ka kashe a ciki."

Nanma shiru tayi alamar tana sauraro sannan tace "yanzu ya kake so nayi in aka ganewa hnnuna a cikin kisanshi? nifa na fad'a maka babu ruwana wallahi." tana fad'a ta kashe wayar ta jefa kan gado, juyowa tayi da nufin fitowa sukayi karo da Zuby dake sauraronta.

Hawaye na zuba a idonta tace "Mama, dama ke kika kashe min mahaifi? lallai Mama kin wuce tunanina, wallahi ke shed'aniya ce ta qarshe, a gaskiya ba zan iya ci gaba da zama dake ba, wallahi gwara na fita ko akan titi ne na dinga kwanciya akan na zauna waje d'aya dake."

"Kinga Zuby ba abinda kike tunani bane, bab.."

"Ya isa haka." ta d'aga mata hannu, takardar sammacin ta jefa mata tana fad'in "ga wannan kad'an daga abinda kika shukane zaki fara girba."

Tana gama fad'a ta shige d'akinta dama kuma bata gama barbaza kayanta ba, dan haka ta tattara ta fito duk da maganar da da Mama ke mata bata saurara ba saida ta fita daga gidan, tunani take inda zata nufa, gidan Uwani ta nufa, amma ina ta samu itama da matsalar data sha mata kai, dan dole ta barnan ta nufi gidan Zulfa'u, itama dai ta samu yanzu ba kamar da ba, dan tana fuskarntar tsangwama ta miji, dan haka bata tafi gidan Zabba'u ba kawai ta wuce gidan mahaifinta kamar yanda Uwani ta bata shawara tun farko, kasancewar anyi sadakar uku hakan yasa bata samu mutane sosai ba, koda ta fad'a musu ta dawo gidan mahaifinta ne tijara wasu suka fara mata, yayin da wasu ke cewa gadone ya kawota, saida ta nuna musu ba shine a gabanta ba kuma ai bata cikin magada kad'ai ta samu lafiyarsu, babbar matar Bala ce tace su barta ta zauna koba komai zasu moreta.

**********

Hankalin SS ya tashi sosai, hakan yasa ya fita ya je ya samu malaminshi amma saiya fad'a mishi sune da nasara, badan komai ba saidan ya samu wani abu a wajenshi, bayan fitarshi kuma lawyern Papa yazo gidan SS amma bai sameshi ba, haka ya koma ba tare daya ganshi ba, yaso dawowa da dare amma bai samu dama ba, hakan yasa washe gari ya dawo ya sameshi, mai gadi ne ya mishi iso har cikin falon SS, kasancewar b'angarenshi daban ne yasa har mata na shigowa wajenshi ba tare da sanin iyalinshi ba, idan ma sun gani babu yanda sukeyi sai dai suyi shiru.

Su Musa ya samu wajen suna tattaunawa, kasancewar su Musa sun sankomai sa game da Papa yasa yanzu haka suke shiri akan yanda zasu had'o duka karuwan da Papa yayi mu'amula dasu dan gabatar dasu a gaban kotu, gaisawa sukayi nan ya fito da duka hujjojin da Umar Faruk ya bashi, da mamaki yasa hannu zai karb'a kawai ya janye takardun da qaramar recorder da aka d'auki muryar Salim, murmushi ya masa yace "yana da daraja, dan haka zaka biya farashinshi."

"Meye wannan d'in?"

"Duk wasu hujjoji da zasu ruguza rayuwar siyasarka, dan da zaran wannan sunje gaban alqali, to babu tamtama cewar za'a yanke maka hukunci ba tare da ansha wahala ba, ni kuma bana son haka ta faru, shi yasa na kawo makasu danka biyani."

Fizge takardun yayi yana fad'in "ka fad'i farashinka ni kuma zan biya."

Yana fad'a mishi kud'in yace ya amince, kallonshi yayi yace "taya ka samu wannan hujjojin?"

Nunfasawa yayi yace "surukinshi mana."

"Wa kenan?"

"Umar Faruk, wanda ke auren Khairat."

Musa ne yace "zaka iya nuna mana shi?"

"Eh to, yanzu bansan ina zan sameshi ba, amma ai gobe zaku had'u dashi a kotu, dan dole zaije duk da ya buqaci karna fad'i shiya samo hujjojin nan."

"Allah ya kaimu goben." cewar Musa yana wata zazzafar qwafa.

**************

Umar Faruk ne ya shigo gidan da sallama, Mama dake bakin panpo ta amsa mishi da fad'in "sannu da zuwa."

"Sannu Mama, ya gida?" ya fad'a yana kallon d'akin Zuby, kallon Mama yayi yace "wai Mama badai yarinyar nan tafiya tayi ba?"

"Um, ta tafi."

Tsaki yayi ya wuce d'akin Khairat ya shirya sannan ya fito, kai tsaye gidansu Khairat d'in ya nufa, falo ya sameta zaune da doguwar riga mai siraran hannaye ta girke plate d'in wainar qwai gabanta da fritte sai yaji da take dangwalawa tana ci, da sauri ya zauna gabanta tare da d'auke robar yajin yana fad'in "kaji min yarinyar nan, yaji ne kike hambad'a haka? gaskiya bana so."

Marairaicewa tayi tace "dan Allah baby ka bani, yafi dad'i da yajin mana."

"Ki shiga hankalinki fa." ya fad'a yana rufe robar yajin.

Turo baki tayi gaba taci gaba da ci tana kallonshi, shima kallonta yake yanda take cin abincin da matuqar birgewa, ganin yana kallonta yasa ta fara saka mishi a baki shima, Mammie ce ta fito cikin shiri zata fita, gaisawa sukayi Mammie tace "ni zan wuce saina dawo."

"Sai kin dawo." cewar Umar Faruk.

Khairat ce ta qara da "qawata ki siyo min abu mai dad'i dan Allah."

"Kamar me?" cewar Mammie.

"Abu mai dad'i fa nace."

"To angama."

Tana fita Khairat ta kalli Umar Faruk tace "baby, docteur fa yace da zaran na fara naquda muje asibiti."

Sanin waye docteur d'in yasa yace "kinga ki rabu da wannan likitan, insha Allah da kanki zaki haihu, karma ki d'aga hankalinki kinji."

"Amma fa baby...."

"Amma me?" ya katseta.

"Na fad'a miki karki damu, da kanki zaki haihu."

Kallonshi tayi tace "a gaskiya ba zan bari nasha wahala ba, tunda yace ga yanda za ayi to kawai ayi yanda yace."

A zafafe ya daka mata tsawa yace "na fad'a miki zaki haihu da kanki, karki qara min maganar banzan likitan nan."

Kallonshi take kamar zata fashe da kuka, d'aga muryar da yayi ne yasa Mamie fitowa daga d'aki, Khairat na ganin Mamie ta tashi da qyar ta juya ta nufi d'akinta yana binta da kallo ganin yanda cikin ya fito sosai har yana mamakin girmanshi, zaune Mamie tayi saman kujera tana kallonshi tace "Umar Faruk, lafiya nake jiyo muryarka haka?"

D'an sosa kai yayi yace "Mama akan maganar da likitan nan ne yayi duk tabi tasa a ranta ta yarda da abinda ya fad'a."

D'an murmushi tayi itama tace "ayya, Umar Faruk ai dole ta yarda, gaskiya fa Shehu ya fad'a maka, dole a gaggauta kaita asibiti data fara naquda."

A sauqaqe yace "Mama, karmu cire rai da rahamar ubangiji, idan muka kai kukanmu ga Allah zata haihu da kanta kuma lafiya qalau."

Ajiyar zuciya Mamie ta sauke tace "abinda baka fahimta ba shine, Khairat na d'aya daga cikin irin matan nan masu matsatsen gaba, kuma nasan kasan haka a matsayinka na mijinta, ba zata iya ba da kanta wahala kawai zata sha in ba'a kaita da wuri ba."

Shiru yayi yana tunani, ashe dama wannan ne dalilin da yasa take matse, ashe halitattar tace haka shi yasa kullum take shan wahala idan zan shigeta, lallai in haka ne kam ba lallai ta iya haihuwa da kanta ba, take ya fahimta ya kuma shiga d'akinta ya bata hak'uri akan tsawar daya mata.

*Washe gari* an shiga kotu, a zaman farko lawyern Papa ya bada wannan qaramin recorder a matsayin hujjar data rage musu ita kad'ai yana fad'in "ya mai girma mai shara wannan itace hujjarmu ta farko kuma ta qarshe da muke da a hannu, da wannan d'aukar ne mai girma mai shari'a zamu samu adalci."

Mik'awa magatakarda yayi, abin mamaki koda aka danna d'aukar sai akaji babu komai a ciki, dan haka lawyern SS ya mik'e ya fad'i ra'ayinshi akan ana so a b'ata sunan SS ne kawai, saida suka gama jawabansu tsaf alqali ya fara magana Umar Faruk ya d'aga hannu ya nemi izinin magana, umarni alqali ya bashi dan haka ya mik'e tsaye ya kalli tanti Odette dasu Musa sannan yace,

"Ya mai girma mai shari'a, ina neman alfarmar kotu data sake bamu wata damar danmu sake kawo wasu hujjojin?"

Saida alqalin yayi yan rubuce rubuce sannan ya kalli Umar Faruk ya kalli lawyensu yace "lawyen mai qara, mai zaka ce akan wannan qorafin?"

Tsaye lawyer ya mik'e yana zufa da in ina yace "muna neman alfarma ya mai girma mai shari'a."

Nanma saida yayi rubutu kafin yace "bayan neman alfarmar kotu da lawyen mai qara yayi, kotu ta karb'i qorafinsu ta basu nan da gobe su kawo hujojjinsu, idan ba haka ba za ayi watsi da wannan qarar, dan ba za'a b'ata lokacin kotu ba, zama ya qare."

Juyawa yayi ya kalli lawyen yana mishi wani banzan kallo, maida kallonshi yayi ga tanti Ma'u, a haka zama ya qare abu ba dad'i.

**************

Da kanshi yaje gidan tanti Ma'u neman Zuby dan yaga lafiyarta data abinda ke cikinta, habaice da zagi da baqar magana ya jisu, amma haka ya toshe kunnenshi har saida ta gama sannan ta fad'a mishi Zuby bata nan, tambaya yayi tana ina amma taqi fad'a dan itama bata san ina take ba, haka ya baro gidan yana kiran wayar Zuby, k'in d'auka tayi dan rayuwarta harta canza cikin qanqanin lokaci.

**************

Bayan yaje gida Khairat ta tambayeshi ina zai samu wasu hujjojin? amma yace ta kwantar da hankalinta ba komai, a raunane ta kalleshi tace "baby, ina jin tsoro fa, dan Allah karka saka mana kanka a matsala, idan wani abu ya ta faru da kai wallahi nima zan shiga wani hali, dan Allah ka fitar da kanka a maganar nan."

Shafa kumatunta yayi yace "karki damu kanki, insha Allah za muyi nasara, kuma mun riga mun fara, kinga bai kamata na cire hannuna ba."

A shagwab'e tace " kenan ba zaka cire hannunka ba?"

Da kai ya ta mata alamar eh, tureshi tayi daga kan gadon ta fashe da kuka tace "shikenan kaje, tunda kana sha'awar ganina ina takaba, mutanen nan ba imani ne dasu ba, kaje kayi abinda kake so."

Juya masa baya tayi yayi rarrashi harya gaji, sai lokacin zai tafi ya ya fad'a mata fa sun rabu da Zuby, ta girgiza sosai ta kuma tambayi laifin me ta mishi, 'kin fad'a mata yayi dan haka ta sake yin wani hushi tace ya tafi itama babu ruwanta dashi, haka ya baro gidan sai dai yasan dole zasu shirya, amma girmanta ya qaru a idonshi.

A hanyarshi ta zuwa gida su Musa suka tareshi, yana ganinsu ya fito yana murmushi yana kallonsu, gaban motar yaja ya tsaya ya rumgume hannaye yana kallonsu suna takowa wajenshi, suna zuwa gabanshi suka tsaya kafin suyi magana yace "Ya dai matasa, kunzo ku gaisheni ne?"

Cikin takaici Bello yace "kai, mune zamu zo gaisheka d'in, kama rainamu wallahi."

Cike da dariyar mugunta da raini Umar Faruk yace "to kenan meya kawoku nan, ko kunzo karbar hujjoji ne?"

"Yawwa d'an gari, abinda ya kawomu kenan, idan ka bamu saimu tafiyarmu salin alin, amma idan ka k'i kuma sai kaji a jikinka." cewar Musa.

Murmushin gefen labb'a yayi yace "da ganina nasan kunsan ni ba matsoraci bane, kamar yanda ni ba ragon namiji bane, dan haka kuyi duk abinda kuke ganin zakuyi, amma fa ba zan baku ba."

"Haka kace?" cewar Musa.

Gira kawai ya d'aga mishi alamar eh, ganin suna tunkarowa wajenshi yasa ya gyara tsayuwarshi yana tattare hannayen rigarshi, Musa ne yasa hannu aljihu ya ciro wata qaramar wuqa yana fad'in "da alama kai jarumi ne, amma fa karka manta mu sojoji ne, kaga kuwa dole ka shafa mana lafiya."

Dariya Umar Faruk yayi yana fad'in "kaji sakarai, jarumi kake so a kiraka kenan? ai jarumta irin taka ba'a fatanta, ka rasa inda zaka nuna jarumtarka sai akan mata wajen yi musu fyad'e, ai jarumta yana nufin shanye duk wani d'aci da qunci harka riski farin ciki."

Dariya Musa yayi yace "to ai ba ragwayen maza ke iya yiwa mace fyad'e ba, musamman ma masu taurin kai da tirjiya irin matarka Khairat."

Yana fad'a suka bushe da dariya dukansu har suna tab'a hannu, lumshe ido yayi dan zafin da zuviyarshi keyi, ji yake kamar ya ciccira namansu a wajen, muryar Bello ce ta dawo dashi yana fad'in "a kan matarka na fara sanin 'ya mace, amma har yanzu ban had'u da wacce ta kaita ba, gaskiya da naji ance tayi aure saida naji ina kishi da wanda ta aura, kullum kowane dare kasa bacci nake saboda tunanin yanzu yana can yana shan romon da muka sha."

Aminou ne ya bashi hannu suka tapa yana fad'in "wallahi kuwa, nima fa har mafarkin wannan ranar nake, gaskiya yarinyar ta had'u."

Cewar Musa "ai zazzafa ce ta qarshe, waiku dan ma baku ne farko ba, aini zan fad'a muku gaskiyar magana nida na fara, a lokacin dana shiga wannan duniyar kai kace a aljanna aka tsundu....."

Bugun daya sauka akan bakinshi ne yasa ya fad'i qasa kwance yana dafe da wuri, kallon Umar Faruk suke da idonshi suka canza kamar ba mutum ba, kafin su ankara ya sake shaqo wuyan rigar Musa ya d'agoshi tsaye yana fad'in " kamar me kake so kace, kamar an tsundumaka a aljanna? banza mahaukaci, kai kana tunanin zaka shiga aljanna bayan ketawa mata haddinsu da kake, aiko a wuta ma zaiyi wuya ka samu mazauni."

Yana fad'a ya sake kai mishi bugu, da azama sukayo kansu suka fara qoqarin rabasu, sosai ya shaqi Musa yake dukanshi, suma dai ganin ya kasa sakinshi yasa suka rufeshi da duka toko ina, amma duk da haka baya jin dukansu dan hango Musa yake akan gado yana kokawa da Khairat har yayi nasarar shiga gonarshi, dan haka yake jin kamar ya cinyeshi d'anye, suna ta dakuwa da bawa hammata iska kawai Umar Faruk yaji wani abu ya sokeshi a ciki, kallon wajen yayi yaga ashe Musa ne yayi nasarar soka mishi wannan qaramar wuqar da wahala ta kai mishi.

A hankali ya fara sakinshi harya sulale qasa, basu barshi haka ba saida suka sake binshi da duka hakan yasa suka canza mishi kamaninshi, duk jini ne ta ko ina, saida suka ga baya motsi sannan suka nufi motarshi suka bincike, ganin basu samu komai ba yasa suka lalaba har jikinshi, nan ma babu komai haka suka tafi babu nasara.

Umar Faruk na kwance baisan inda kanshi yake ba, ya jima a wajen kwance yana zubar da jini, wata mota ce ta nufo wajen da yake, mutanen dake motar ne suka ganshi kwance suka fito, da ikon Allah suka taimaka mishi suka d'aukeshi sukayi asibiti dashi, ta hanyar wayarshi suka kira lambar daya kira qarshe lambar Abbakar, cikin tashin hankali Abbakar ya sanar a gida suka nufi asibiti, ganin halin da yake ciki ga jini ana qara mishi yasa basu kira d'aya daga cikin matanshi ba.


Saida safe ya farfad'o, lokacin Khairat na kiranshi dan tuni sun hallara a kotu rashin ganinshi yasa take kiranshi, Abbakar ne ya d'auki kiran saida suka gaisa take tambayar "yah Abbakar ina Umariri ya shiga ne?"

Sunan data kira saida yasa ya d'an murmusa, dakewa yayi yace "baya kusa, ina asibiti ne."

"Asibiti kuma, meya faru, waye bashi da lafiya?"

Ajiyar zuciya ya sauke yace "ki kwantar da hankalinki Khairat, idan zaki iya zaki iya samunmu a babban asibiti."

Rintse ido tayi saboda fad'uwar da gabanta yayi, a kaurare tace "inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un."

Shiru ne ya ratsa kafin ta sake cewa "yah Abbakar sun mishi wani abu ko? ni nasan dama yasa kanshi a had'ari."

"Karki damu Khairat, jikinshi da sauqi sosai."

"Shikenan yah Abbakar, gani nan zuwa."

Papa ta fad'a ma suka nufi asibitin su Mamie suka jirasu.

**************

Koda ya farka ya tashi zaune ya Fara qoqarin cire qarin ruwan da aka maka mishi, Abbakar ne ya aje wayar ya fara rik'eshi, tureshi yayi da qarfi ya fizge sirinjin hakan yayi sanadiyar fitowar jini daga hannunshi, a tsawace Abbakar yace "wai meye haka, me kake yi ne haka?"

Kallon Abbakar yayi yace "tafiya zanyi, ba zan zauna ba, dole saina qarasa abinda na fara."

Qafafunshi ya zuro da niyyar saukowa, da sauri ya dafe cikinshi inda aka soka mishi wuqar tare da cije lips ya rufe ido, Abbakar ne yace "uhum, ga irinta ai, ina zaka je a wannan halin?"

Bud'e ido yayi ya sauko daga kan gado cike da jarumta da dauriya, rigarshi ya kalla da duk taji jiki itama, Abbakar ya kalla yace "taimakon da zaka min shine, ka kaini gida."

"Umar, baka da lafiya fa, yanzu haka Khairat nakan hanyar zuwanta nan."

Cikin fitar hayyaci ya shaqo wuyan rigar Abbakar cikin d'aga murya yace "me, kana nufin ka fad'a mata, me yasa to zaka fad'a mata? Khairat nada rauni sosai, komai zai iya faruwa da ita idan taga halin da nake ciki."

Shigowar Baba dasu Mama ne yasa saki wuyan rigarshi yana kallon Baba, "lafiya, meya faru?" cewar Baba.

"Ba komai Baba, wai gida yake so ya tafi a wannan halin da yake ciki."

"Gida kuma, me zakayi a gidan?"

A marariraice yace "dan Allah Baba ku barni na tafi, wallahi akwai mahimmanci zuwana yanzun."

Kallonshi Baba yayi sosai kafin yace "shikenan, bara muga ko mun samo maka takardar sallama."

"A'a Baba, ku barsu kawai, ba lallai bane su sallameni."

Haka dai shida Abbakar suka sulale suka bar asibitin, kai tsaye gida suka nufa yana shiga ya canza riga sannan ya had'a sauran hujjojin da suka rage mishi sannan suka tafi kotu.

***************

Koda su Khairat suka zo asibiti su Baba ma na shirin tafiya kotu, da qyar suka fad'a mata jikinshi da sauqi suka lallab'ata suka bar wajen, kai tsaye kotu suka hallara suma, tana ganinshi ta ruga a guje ta rumgumeshi tana kuka, sosai ya rintse ido saboda wani bala'in zafi dake ratsashi saboda dafe wani ciwo da tayi amma ya kasa fad'a mata, yanda take qara cukwikwiyeshi yasa ya saki qara bai shirya ba, da sauri ta d'ago tana kallonshi da mamaki, turo baki yayi gaba tare da dafe wajen data rik'e yana fad'in "kin min famin ciwona."

B'ata rai tayi ta kai
Showing 171001 words to 174000 words out of 186119 words