yasa ya d'an shafi kanta yace "Allah miki albarka."
Tashi tayi zata koma wajenta ta zauna Umar Faruk da Abbakar sukayi sallama tare da Ishaq, gaishe da Bala sukayi harda Umar Faruk dake mamakin ganinshi, danya tuna shine suka had'u a shago ranar, Bala ne ya kalli Umar Faruk yace "wannan ne surukin nawa ko? masha Allah Allah yayi albarka."
Da mamaki Umar Faruk ya kalleshi yace " suruki kuma,amma bakai muka had'u da kai a....."
Khairat ce tayi saurin cewa "baby surukinka ne baka gane ba, baban Zuby ne fa?"
Maida kallonsu sukayi gareta har saida Bala ya fahimci hakan sannan yayi gyaran murya yace "bai sani bane ai shi yasa, amma yanzu kowa zaisan komai."
"Kai, wai baka da hankali ne, tashi ka fita daga gidan nan?" cewar Mama.
Zuby ce ta mik'e tsaye tace "a'a Mama barshi, nasan turoshi akayi, kuma ba kowa bace sai wannan shegiyar matar marar mutunci."
"Ke." Bala ne ya daka mata tsawa tare da tashi tsaye shima, a hassale yake kallonta idonshi har sunyi ja, ganin abin fa ba qarami bane yasa Mama tattara yaran dake wajen tace suje d'aki, Bala ne ya kalli Ma'u cikin b'acin rai yace "Asma'u, kina jin irin furucin dake fita daga bakin wannan yarinyar amma baki tab'a taka mata birki ba, yanzu wannan maganar ta dace aji ta fito daga bakinta? to kinga ni ba b'ata lokaci nazo yi ba, ki fad'a mata ko wanene ni a wajenta kawai."
Hannu biyu Ma'u tasa ta dafe ciki saboda murd'awar da yake mata, kowa kuma qura mata ido yayi yana kallo, Mama ce cike da nutsuwa tace " yar uwata, kinsan mutumin nan ne, meya kawoshi me kuma yake fad'a ne haka?"
Wasu yawu ta had'e masu nauyi da d'aci tana kallon Mama, Umar Faruk ne ya kalli Khairat yace "meye haka, waya gayyatoshi gidan nan?"
Da mamaki tace "ni kuma taya za ayi na sani, gashi a gabanka mana ka tambayeshi."
Tsaki yayi sannan ya kalli Bala yace "dan Allah malam inba wani abu mai mahammanci bane ya kawoka zaka iya tafiya."
Saida Bala ya kalli Ma'u ya kalli Zuby da Umar Faruk yace "wannan yar tawa nazo karb'a, karb'a kuma ba ina nufin zan rabaka da matarka bane, ina so ne ka ara min ita muje tare taga yan uwanta kawai."
Salati kowa ya fara dake wajen ana kallon kallo, Khairat ma bud'e baki tayi cike da irin tana mamakin nan, Zuby da gabanta ke dukan uku uku ne ta qurawa Mama ido ta kasa d'aukewa, da qyar ta d'aga qafafunta ta matso kusan Mama tana ci gaba da kallonta.
Cikin wani irin gunjin murya tace "Mama, kina jin abinda mutumin nan ke fad'a, shin da gaske ne?"
Kasa jurewa Mama tayi sai hawaye da suka taho mata, sake maimaitawa tayi tace "Mama tambayarki nake, da gaske ne abinda yake fad'a cewar ni 'yarsa ce?"
Da k'arfi ta fashe da kuka ta durk'ushe gaban Zuby tayi zaune tana rera kuka, hakan kuma ya bawa kowa tabbacin abinda Bala yake fad'a gaskiya ne, duk'awa Zuby tayi ta dafa Mama tace "Mama ki fad'a min gaskiya dan Allah, zuciyata bugawa take karta fashe."
Kai Mama ta girgiza mata cikin matsanancin kuka tace "kiyi hak'uri Zuby, wallahi ban tab'a tunanin wannan ranar zata zo ba shi yasa ban shirya mata ba, kiyi hak'uri dan Allah ki yafe min, haqiqa wannan shine mahaifinki, kuma hakan ya faru ne lokacin da nake kallon mahaifinsu Uwani ba'a bakin komai ba, amma wallahi nayi nadama Zuby na tuba."
Hawaye ne ke fitowa daga idonta amma ta kasa ko qyabta ido, lokacin da kanta yayi wata sarawa ne yasa ta kwamtsa qara mai k'arfin gaske ta qarasa zubewa wajen somammiya, ganin haka yasa hankalin kowa ya sake tashi, da gudu Khairat ta qarasa wajenta dan gaba d'aya ta manta da abinda ke tsakaninta da Zuby, zubewa tayi ta fara girgiza Zuby cike da tsoro da tunanin halin da take ciki take fad'in,
"Zubeida, Zubeida ki tashi dan Allah, ki tashi Zubeida karki mutu, dan Allah ki tashi Zubeida karki dora min laifin mutuwarki , wallahi ba nayi haka bane danna saki wani hali, kawai nayi tunanin zan kub'uta ne daga yawan aibata iyayena da kike, dan Allah Zubeida ki bud'a idonki wal....."
Bata qarasa ba Umar Faruk ya suri Zuby ya rumgume ya fita da ita yasa mota, kai tsaye asibiti ya nufa da ita inda ta kwanta kwanan baya, Khairat bata tashi daga wajen ba hankalin kowa baya jikinshi Ma'u ta d'auko tab'arya, a lokacin da Mama Maimuna ta kula lokacin tana daf da kaiwa ga Khairat, ai kuwa saita sauke wa Khairat ita akai, qarar da tayi tare da zubewa wajen yasa kowa ya kallesu, da sauri kowa yayi kansu dan kai mata d'auki, ganin ko motsi ba tayi itama yasa matan suka kamata suka sa a motar Bala aka nufi asibiti da ita, Mama ce ta fad'a mishi asibitin da zai kaisu, acan suka samu Umar Faruk da aka shiga da Zuby urgency, ganin halin da suka shigo da Khairat sai hankalinshi ya kuma tashi, ana shiga da ita itama ya fad'i zaune a qasa ba tare daya ma san ya zauna ba, cire hular kanshi yayi ya dafe kai hawaye na zuraro mishi, a hankali yake furta "inna lillahi wa inna ilaihi raju'un."
Haka yake maimatawa tsawon lokaci har aka d'auki minti talatin, babu wanda ya zauna sai Umar Faruk da baya hayyacinshi, tunaninshi matanshi da baisan halin da suke ciki, kuma babu wanda ke cikin nutsuwarshi daya damu ya rarrasheshi ma, ana haka kuma wata likita ta fito daga d'akin da Zuby take, zunbur ya mik'e yana fad'in "ya ake ciki dan Allah, tana raye?"
Kallon mutanen da suka kewayeta tayi kafin ta kalli Umar Faruk daya kawota tace "tana nan lafiya, jininta ya hau sosai, kuma ba'a son haka na faruwa dan zai iya janyo mata matsala, musamman qaramin cikin dake jikinta, dan Allah a dinga kiyayewa."
Da sauri yasa hannu ya rufe ido yana sauke numfashi, a hankali ya furta "alhamdulillah."
Jin qarar bud'a d'akin da Khairat ce ciki yasa suka sake d'unguma suna tambayar Jamila data fito daga ciki, qura mata ido kawai sukayi babu mai magana saboda murmushin dake kan fuskarta, kallon Umar Faruk tayi tace "yallab'ai zan maka albishir amma saika ban goron tukuici na."
Da mamaki yake kallonta cikin dakusashiyar muryarshi yace "matata kwance a asibiti kuma kina maganar na baki goron albishir?"
"Eh mana, saboda na gano maka tana d'auke da d'an qaramin cikinka."
Wani irin bayyanannen farin ciki ne ya bayyana a fuskarshi tare da cakumo hannun Jamila ya rik'e jim yana fad'in "ki fad'i abinda kike so zan bakishi , tabbas kin kawo min albishir mai dad'i, kuma dole na muku babbar kyauta, dan wannan daidai yake da albishir d'in haihuwar yan biyu."
Kowa na wajen dariya yake da farin ciki fal a fuska, saida ya basu tukuici duka likitocin kafin suka d'aukosu suka tafi gida, suna shiga Mama ta taso ta tarbi Zuby, hannu ta d'aga mata tace "dan Allah ki tafi bana son ganinki yanzu.", zatayi magana Mama ta dafata tace "ki barta kawai, yanzu ranta a b'ace yake, muje d'akina.", wucewa sukayi itama ta shiga nata d'akin, sai lokacin Umar Faruk ya kirasu Mamie ya fad'a musu halin da ake ciki, amma babban abin birgewa shine yanda mahaifiyar Khairat ta nuna kamar ba komai a zahiri, koda dai bata ji dad'i ba amma dai bata nuna mishi ba, fad'a mishi tayi zasu zo anjima su ganta, saida akayi sallah magrib Baba ya buqaci ganin kowa a d'akinshi, a lokacin Zuby na kwance a d'aki ta dunqule tana hawaye Umar Faruk ya shigo, saida ya tayar da ita zaune ya rumguma a jikinshi yace,
"Meye kuma na kuka yanzu, shin baki san abinda kike dauke dashi bane? yanzu fa damuwa da tunani ba naki bane, ina so ki d'auki hakan a matsayin qaddarar rayuwarki, tunda dai ya tabbata wannan ne mahaifinki to kiyi hak'uri ki d'aukeshi a matsayin mahaifinki, damuwarki kawai nake buqatar ki kawar da ita ki tayani rainon d'an gatan nan, kinji ko."
Ya qarashe yana kallon fuskarta, wasu hawaye ne suka sake gangaro mata kanta qasa ta kasa kallonshi, share mata yayi yace "haba dai, ba nace bana so ba, kina so nima na shiga damuwa ne, ko kuma kina so ki b'ata min rai ne?"
Kai ta girgiza cike da nadama da qunci tace "yah Umar taya zan daina damuwa, ai dole na damu kuma nayi kuka, wanda nake tunanin shine mahaifina yau ance bashi bane, wanda nake kallon yan uwana nasu uwa d'aya uba d'aya yau an raba alaqar zama uba d'aya dasu, yah Umar yau naji kunyar kaina dana mutane, abin baqin ciki bata hanyar aure aka sameni ba, da aure akayi zina aka samu cikina, yah Umar me mahaifiyata ta zama haka, me yasa zata lalata min rayuwa, me yasa zata cutar dani haka? yanzu shikenan ta rabani da kai."
"Ke ke." yayi saurin katseta, d'orawa yayi da "waya fad'a miki zamu rabu, ina tare dake har abada Zubeida, wannan abun ba zai zama silar dagulewar alaqarmu ba, ke baki ga yanzu ma muka sake gyara sabon zama ba, domin kuwa akwai ajiyata anan." ya qarasa da zolaya.
Murmushi tayi tace "ka tabbata ba zaka rabu dani ba?"
Kai ya girgiza mata yace "hanyar da aka sameki Zubeida ba zai shafi aurena dake ba, kuma koda baki mazaunin matata haka ta faru ai akwai aure tsakaninmu kuma zan iya aurenki, bare kuma kina matsayin matata, dan haka dan Allah kar kisa damuwar da har zata haifar miki da wata matsalar, ba zanso hakan ba kuma zan iya yin hushi dake idan kika ja mana matsala."
Murmushi ta sake yi tace "shikenan yah Umar, na daina insha Allah ba zan sake ba."
"Yawwa yarinyar kirki, tashi muje to Baba nasan ganinmu."
Hijabi tasa suka fito, a qofar d'akin yace "kije zan kira 'yar uwarki."
Da kai ta masa alamar to ta wuce d'akin Baba, da sallama ya shiga d'akin Khairat dake kwance akan qafar Mammie da basu jima da zuwa ba tare da Mamie, kallonta yake harya zauna yana kallon bandejin dake kanta, gaishe dasu Mammie yayi ya d'ora da "ya mai jikin?"
"Ah jiki da sauk'i." cewar Mamie.
"Allah ya qara sauk'i, ya kiyaye gaba."
Da "ameen." suka amsa.
Kallonta yayi yace "Khairat, Baba kesan ganinmu a d'akinshi yanzu, zaki iya tafiya?"
Ta d'an dafe kai ta tashi zaune tana kallonshi, saida ta daidaita zamanta tace "zan iya mana, muje kawai."
Tsaye ya mik'e tare da mik'o mata hijabinta tasa, hannunta ya kama suka fara takawa a hankali, suna daf da fita daga d'akin ta kalleshi tace " kuyi hak'uri Faruk dan Allah karku d'ora min laifi, nima ba'a son raina bane."
Murmushi ya mata yace "karki damu, muje."
Yana rik'e da ita har sukayi sallama d'akin suka shiga, kusa dashi ya zaunar da ita kafin suka maida hankalinsu ga Baba, kallonshi Baba yayi yace "amma ba naga mahaifiyarta sunzo ba?"
"Eh Baba suna ciki."
"To ka musu magana mana." cewar malam.
Tashi yayi ya koma d'akin ya kirasu suma dan ayi gabansu, zaune sukayi suma ana kallon kallo, Baba ne yace "to alhamdulillah kowa ya hallara, kuma ba komai yasa na taramu ba sai dan kawo qarshen matsalar data kunno mana kai, da farko ina so nasan musabbabin matsalar danta hakane zamu yaki matsalar dan gudun sake faruwar haka anan gaba."
Khairat ya kalla yace "Khairat, kinyi wata magana a lokacin da Zuby ta some wacce nake tunanin kinsan komai, shin zaki iya fad'a mana meya faru?"
Kallon Zuby tayi ta kalli Mama ta kuma kalli Umar Faruk kafin ta kalli malam ta fara magana cikin taushin murya da rawar murya tace "sanin kanku ne inhar cacar baki zai had'ani da Zubeida, to sai tasa iyayena musamman mahaifina, jiya ma hakane ya faru lokacin da Papa ya aiko mana da kud'i nida ita, bayan bata karba ba saida ta fad'a min baqar magana da banji dad'inta ba, kuma Ruk'ayya da aunty Saratu shaida ne dan suna wajen, shi yasa ni kuma naci alwashin kawo qarshen matsalar ta hanyar bayyana mata mahaifinta na gaskiya, dama kuma nasan Bala tunda jimawa, kuma shine ya fad'a min ita 'yarsa ce da suka haifa bata hanyar aure ba, shi yasa nace yazo ya karb'eta koba komai zata san mahaifinta na gaskiya."
Ajiyar zuciya malam ya sauke yace "to Zubeida kinji dalilin da yasa tayi haka, kuma inhar za abi ta gaskiya to kece kika tunzurata har tayi haka, a zahirin gaskiya ba zamu ce tayi kuskure ba, koba kamai ta taimakeki wajen sanin mahaifinki na gaskiya wanda mahaifiyarki ke b'oye miki, laifinta kawai data tona abinda bai kamata ace ta tona ba, da tayi hak'uri wataqila lokaci ne zai bayyana hakan, dan haka ina rokonku da ku gafarci junanku ku kuma yafewa juna, rashin had'a kanku da ku kaki yine ya janyo hakan, yana da kyau kusan shifa aure ibada ne, kuma qarin aure ma Allah ne ya hallata mana shi, fad'a da kuke da junanku sam bai dace ba, idan kuka had'a kanku kuka zauna lafiya, shi kanshi mijinku zaifi samun nutsuwa da kwanciyar hankali, haka kuma Allah zai qara yalwata mishi arziqinshi, dan haka ina sake baku hak'uri tare da shawartarku daku yafewa junanku dan Allah dan soyayyarku da Allah."
Kallon da yake musu yasa Khairat sauke ajiyar zuciya ta kalli Zuby tace "kiyi hak'uri Zubeida, ki yafe min? nima kuma na yafe miki abisa komai."
A cije Zuby tace "na yafe miki, nima ki yafe min."
"Ba komai 'yar uwa." cewar Khairat.
"To masha Allah, sai kuma ke Zubeida, ina so kisan abinda ya faru qaddara ce kuma jarabawa, kiyi iya qoqarinki wajen cinye wannan jarabawar, hakan zai qara hauda imaninki a wani mizani da zai qara miki qarfin imani, kuma karki saki ki kalli mahaifiyarki da wani ido dama idon rahama ba, haka shima mahaifin naki ki girmamashi dan saikin kyautata musu ne duniya da lahirarki zasuyi kyau, kiyi koyi da sahhabai da tabi'ai wajen hak'uri nuna soyayya da kuma cinye jarabawa ko wace iri ce, ki zama jarumar gaske wajen shanye abinda ke zuciyarki, kuma karki tab'a kallon Khairat da abun, hakan zaisa shaid'an ya sake galaba a kanki, kuma ki sani iyaye nada girma da darajar da babu mai ita a duniya idan kika cire Allah da manzonsa Annabi Muhammad (S.A.W)."
Sosai malam ya mata nasiha daga bisani kuma sauran iyayen suma suka tofa albarkacin bakinsu, a haka suka tashi daga zaman cike da fatan alkairi, amma fa duk abinda aka tattauna ta bayan kunnan Mama yabi ya wuce, dan tayi niyyar saita d'auki fansa akan Khairat dama shi kanshi Bala...
*Wasa farin girki*
_Ku biyoni dan jin me kuma zaici gaba da faruwa yanzun._
_Wannan sadaukarwa ne ga *Ummu Fawzan,* sama da tsawon lokaci har yau tana tambayata lafiyar mahaifiyata, wanda zaiso mahaifiyarka babban masoyine wallahi, ina sonki sister_
29/08/2019 Γ 14:33 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*MUJI TSORON ALLAH AKAN DUK ABINDA ZAMUYI*
_Bismmilahir-rahman-rahim_
5β£6β£
Kwance take akan qafafunshi suna hira yana shafar kanta, bacci ne ya fara d'ibarta yanata surutu amma yaji shiru, leqa fuskarta yayi yace "wai bacci ki kayi?"
D'an bud'a ido tayi ta kalleshi lokaci d'aya kuma ta maidasu ta rufe, dariya yayi yace "lallai aiki fa ya samu."
"To shikenan tunda dai bacci kike, kinga gobe kenan ba zuwa gida gaskiya, dan ba zan kaiki ba kije kina musu bacci ba a gida."
Tunda yaji shiru ya tabbatar bacci take bilhaqqi, dan da idonta biyu da zata tashi ta fara mishi rigima, gyara mata kwanciyar yayi yana kallon fuskarta yana yawo da yatsunshi a tsakanin fuskarta da qirjinta, saida yaji bacci na shirin d'aukarshi shima sannan ya tofa musu addu'a ya kwanta yana qara matseta jikinshi kamar za'a rabashi da ita.
*************
Da safe kuma fitowa sukayi cikin shiri ita da Zuby saboda zai kaisu gidajensu ne duka su wuni, tare suka fita bayan sunyi sallama da mutanen gidan, gidan baya Zuby ta bud'a ta shiga Khairat kuma gaba, saida ya fara aje Zuby a gida ya shiga tare da Khairat dansu gaisa, duk sallamar da sukayi Mama bata amsa ba, gaisheta sukayi shima shiru ko kallo, tausayinta ne ya kama Khairat dan haka ta d'an matsa da nufin ta mata magana, da hannu ta nunata tace "karki kuskura wallahi, kinga raunin kanki yanzu zan miki wanda ya fishi, wallahi na tsaneki bani bake har abada, kuma zaki gani a cikin qwaryar cin tuwanki , bake kad'ai ba harda shi banzan Balan daya taimaka miki, wallahi saikun gane kurenku, saina nuna muku nayi nisan da bana jin kira, kuma kamar yanda banji tsoron bakin iyayena ba wallahi ba zanji tsoron bakin wasu ba, dan saina nuna muku bakin mahaifiyata na yawo dani har yanzu, zan ajiye sauran imanin daya rage mini domin na tarwatsa ratuwarki, kuma abin kunya ba gareni farau ba bare ya qare kaina, dan haka ba zan sake jin kunyar wani ko wata ba akan abinda nayi, tunda wasu sunyi fiye da abinda na aikata, kuma ki zuba ido kiga abinda zai faru, ba dai kin tona min asiri ba, to kema zan tona miki naki asirin, wallahi sai kinji abinda nida 'yata mukaji, ku b'ace min daga gida, har kai bana son sake ganinka."
Da qyar Khairat ta iya tashi ta kama hanya, Umar Faruk na bayanta shima yana tunanin abinda Mama ta fad'a, tunda suka shiga mota babu mai magana harya ajeta gida suka shiga, ba wani kuzari haka suka gaisa sannan ya barta, yana fita Khairat ba tayi nauyin baki ba wajen fad'awa su Mamie abinda Ma'u tace, Mammie ce tace ta Allah ba tata ba kuma babu abinda zata gani sai alkairi, haka dai tayi wurin ranar ba walwala ba kuzari, sai bayan sallah isha'i yazo ya d'auketa daga nan suka wuce suka d'auko Zuby, wacce itama tayi wunin ba dad'i ba
Showing 150001 words to 153000 words out of 186119 words
Tashi tayi zata koma wajenta ta zauna Umar Faruk da Abbakar sukayi sallama tare da Ishaq, gaishe da Bala sukayi harda Umar Faruk dake mamakin ganinshi, danya tuna shine suka had'u a shago ranar, Bala ne ya kalli Umar Faruk yace "wannan ne surukin nawa ko? masha Allah Allah yayi albarka."
Da mamaki Umar Faruk ya kalleshi yace " suruki kuma,amma bakai muka had'u da kai a....."
Khairat ce tayi saurin cewa "baby surukinka ne baka gane ba, baban Zuby ne fa?"
Maida kallonsu sukayi gareta har saida Bala ya fahimci hakan sannan yayi gyaran murya yace "bai sani bane ai shi yasa, amma yanzu kowa zaisan komai."
"Kai, wai baka da hankali ne, tashi ka fita daga gidan nan?" cewar Mama.
Zuby ce ta mik'e tsaye tace "a'a Mama barshi, nasan turoshi akayi, kuma ba kowa bace sai wannan shegiyar matar marar mutunci."
"Ke." Bala ne ya daka mata tsawa tare da tashi tsaye shima, a hassale yake kallonta idonshi har sunyi ja, ganin abin fa ba qarami bane yasa Mama tattara yaran dake wajen tace suje d'aki, Bala ne ya kalli Ma'u cikin b'acin rai yace "Asma'u, kina jin irin furucin dake fita daga bakin wannan yarinyar amma baki tab'a taka mata birki ba, yanzu wannan maganar ta dace aji ta fito daga bakinta? to kinga ni ba b'ata lokaci nazo yi ba, ki fad'a mata ko wanene ni a wajenta kawai."
Hannu biyu Ma'u tasa ta dafe ciki saboda murd'awar da yake mata, kowa kuma qura mata ido yayi yana kallo, Mama ce cike da nutsuwa tace " yar uwata, kinsan mutumin nan ne, meya kawoshi me kuma yake fad'a ne haka?"
Wasu yawu ta had'e masu nauyi da d'aci tana kallon Mama, Umar Faruk ne ya kalli Khairat yace "meye haka, waya gayyatoshi gidan nan?"
Da mamaki tace "ni kuma taya za ayi na sani, gashi a gabanka mana ka tambayeshi."
Tsaki yayi sannan ya kalli Bala yace "dan Allah malam inba wani abu mai mahammanci bane ya kawoka zaka iya tafiya."
Saida Bala ya kalli Ma'u ya kalli Zuby da Umar Faruk yace "wannan yar tawa nazo karb'a, karb'a kuma ba ina nufin zan rabaka da matarka bane, ina so ne ka ara min ita muje tare taga yan uwanta kawai."
Salati kowa ya fara dake wajen ana kallon kallo, Khairat ma bud'e baki tayi cike da irin tana mamakin nan, Zuby da gabanta ke dukan uku uku ne ta qurawa Mama ido ta kasa d'aukewa, da qyar ta d'aga qafafunta ta matso kusan Mama tana ci gaba da kallonta.
Cikin wani irin gunjin murya tace "Mama, kina jin abinda mutumin nan ke fad'a, shin da gaske ne?"
Kasa jurewa Mama tayi sai hawaye da suka taho mata, sake maimaitawa tayi tace "Mama tambayarki nake, da gaske ne abinda yake fad'a cewar ni 'yarsa ce?"
Da k'arfi ta fashe da kuka ta durk'ushe gaban Zuby tayi zaune tana rera kuka, hakan kuma ya bawa kowa tabbacin abinda Bala yake fad'a gaskiya ne, duk'awa Zuby tayi ta dafa Mama tace "Mama ki fad'a min gaskiya dan Allah, zuciyata bugawa take karta fashe."
Kai Mama ta girgiza mata cikin matsanancin kuka tace "kiyi hak'uri Zuby, wallahi ban tab'a tunanin wannan ranar zata zo ba shi yasa ban shirya mata ba, kiyi hak'uri dan Allah ki yafe min, haqiqa wannan shine mahaifinki, kuma hakan ya faru ne lokacin da nake kallon mahaifinsu Uwani ba'a bakin komai ba, amma wallahi nayi nadama Zuby na tuba."
Hawaye ne ke fitowa daga idonta amma ta kasa ko qyabta ido, lokacin da kanta yayi wata sarawa ne yasa ta kwamtsa qara mai k'arfin gaske ta qarasa zubewa wajen somammiya, ganin haka yasa hankalin kowa ya sake tashi, da gudu Khairat ta qarasa wajenta dan gaba d'aya ta manta da abinda ke tsakaninta da Zuby, zubewa tayi ta fara girgiza Zuby cike da tsoro da tunanin halin da take ciki take fad'in,
"Zubeida, Zubeida ki tashi dan Allah, ki tashi Zubeida karki mutu, dan Allah ki tashi Zubeida karki dora min laifin mutuwarki , wallahi ba nayi haka bane danna saki wani hali, kawai nayi tunanin zan kub'uta ne daga yawan aibata iyayena da kike, dan Allah Zubeida ki bud'a idonki wal....."
Bata qarasa ba Umar Faruk ya suri Zuby ya rumgume ya fita da ita yasa mota, kai tsaye asibiti ya nufa da ita inda ta kwanta kwanan baya, Khairat bata tashi daga wajen ba hankalin kowa baya jikinshi Ma'u ta d'auko tab'arya, a lokacin da Mama Maimuna ta kula lokacin tana daf da kaiwa ga Khairat, ai kuwa saita sauke wa Khairat ita akai, qarar da tayi tare da zubewa wajen yasa kowa ya kallesu, da sauri kowa yayi kansu dan kai mata d'auki, ganin ko motsi ba tayi itama yasa matan suka kamata suka sa a motar Bala aka nufi asibiti da ita, Mama ce ta fad'a mishi asibitin da zai kaisu, acan suka samu Umar Faruk da aka shiga da Zuby urgency, ganin halin da suka shigo da Khairat sai hankalinshi ya kuma tashi, ana shiga da ita itama ya fad'i zaune a qasa ba tare daya ma san ya zauna ba, cire hular kanshi yayi ya dafe kai hawaye na zuraro mishi, a hankali yake furta "inna lillahi wa inna ilaihi raju'un."
Haka yake maimatawa tsawon lokaci har aka d'auki minti talatin, babu wanda ya zauna sai Umar Faruk da baya hayyacinshi, tunaninshi matanshi da baisan halin da suke ciki, kuma babu wanda ke cikin nutsuwarshi daya damu ya rarrasheshi ma, ana haka kuma wata likita ta fito daga d'akin da Zuby take, zunbur ya mik'e yana fad'in "ya ake ciki dan Allah, tana raye?"
Kallon mutanen da suka kewayeta tayi kafin ta kalli Umar Faruk daya kawota tace "tana nan lafiya, jininta ya hau sosai, kuma ba'a son haka na faruwa dan zai iya janyo mata matsala, musamman qaramin cikin dake jikinta, dan Allah a dinga kiyayewa."
Da sauri yasa hannu ya rufe ido yana sauke numfashi, a hankali ya furta "alhamdulillah."
Jin qarar bud'a d'akin da Khairat ce ciki yasa suka sake d'unguma suna tambayar Jamila data fito daga ciki, qura mata ido kawai sukayi babu mai magana saboda murmushin dake kan fuskarta, kallon Umar Faruk tayi tace "yallab'ai zan maka albishir amma saika ban goron tukuici na."
Da mamaki yake kallonta cikin dakusashiyar muryarshi yace "matata kwance a asibiti kuma kina maganar na baki goron albishir?"
"Eh mana, saboda na gano maka tana d'auke da d'an qaramin cikinka."
Wani irin bayyanannen farin ciki ne ya bayyana a fuskarshi tare da cakumo hannun Jamila ya rik'e jim yana fad'in "ki fad'i abinda kike so zan bakishi , tabbas kin kawo min albishir mai dad'i, kuma dole na muku babbar kyauta, dan wannan daidai yake da albishir d'in haihuwar yan biyu."
Kowa na wajen dariya yake da farin ciki fal a fuska, saida ya basu tukuici duka likitocin kafin suka d'aukosu suka tafi gida, suna shiga Mama ta taso ta tarbi Zuby, hannu ta d'aga mata tace "dan Allah ki tafi bana son ganinki yanzu.", zatayi magana Mama ta dafata tace "ki barta kawai, yanzu ranta a b'ace yake, muje d'akina.", wucewa sukayi itama ta shiga nata d'akin, sai lokacin Umar Faruk ya kirasu Mamie ya fad'a musu halin da ake ciki, amma babban abin birgewa shine yanda mahaifiyar Khairat ta nuna kamar ba komai a zahiri, koda dai bata ji dad'i ba amma dai bata nuna mishi ba, fad'a mishi tayi zasu zo anjima su ganta, saida akayi sallah magrib Baba ya buqaci ganin kowa a d'akinshi, a lokacin Zuby na kwance a d'aki ta dunqule tana hawaye Umar Faruk ya shigo, saida ya tayar da ita zaune ya rumguma a jikinshi yace,
"Meye kuma na kuka yanzu, shin baki san abinda kike dauke dashi bane? yanzu fa damuwa da tunani ba naki bane, ina so ki d'auki hakan a matsayin qaddarar rayuwarki, tunda dai ya tabbata wannan ne mahaifinki to kiyi hak'uri ki d'aukeshi a matsayin mahaifinki, damuwarki kawai nake buqatar ki kawar da ita ki tayani rainon d'an gatan nan, kinji ko."
Ya qarashe yana kallon fuskarta, wasu hawaye ne suka sake gangaro mata kanta qasa ta kasa kallonshi, share mata yayi yace "haba dai, ba nace bana so ba, kina so nima na shiga damuwa ne, ko kuma kina so ki b'ata min rai ne?"
Kai ta girgiza cike da nadama da qunci tace "yah Umar taya zan daina damuwa, ai dole na damu kuma nayi kuka, wanda nake tunanin shine mahaifina yau ance bashi bane, wanda nake kallon yan uwana nasu uwa d'aya uba d'aya yau an raba alaqar zama uba d'aya dasu, yah Umar yau naji kunyar kaina dana mutane, abin baqin ciki bata hanyar aure aka sameni ba, da aure akayi zina aka samu cikina, yah Umar me mahaifiyata ta zama haka, me yasa zata lalata min rayuwa, me yasa zata cutar dani haka? yanzu shikenan ta rabani da kai."
"Ke ke." yayi saurin katseta, d'orawa yayi da "waya fad'a miki zamu rabu, ina tare dake har abada Zubeida, wannan abun ba zai zama silar dagulewar alaqarmu ba, ke baki ga yanzu ma muka sake gyara sabon zama ba, domin kuwa akwai ajiyata anan." ya qarasa da zolaya.
Murmushi tayi tace "ka tabbata ba zaka rabu dani ba?"
Kai ya girgiza mata yace "hanyar da aka sameki Zubeida ba zai shafi aurena dake ba, kuma koda baki mazaunin matata haka ta faru ai akwai aure tsakaninmu kuma zan iya aurenki, bare kuma kina matsayin matata, dan haka dan Allah kar kisa damuwar da har zata haifar miki da wata matsalar, ba zanso hakan ba kuma zan iya yin hushi dake idan kika ja mana matsala."
Murmushi ta sake yi tace "shikenan yah Umar, na daina insha Allah ba zan sake ba."
"Yawwa yarinyar kirki, tashi muje to Baba nasan ganinmu."
Hijabi tasa suka fito, a qofar d'akin yace "kije zan kira 'yar uwarki."
Da kai ta masa alamar to ta wuce d'akin Baba, da sallama ya shiga d'akin Khairat dake kwance akan qafar Mammie da basu jima da zuwa ba tare da Mamie, kallonta yake harya zauna yana kallon bandejin dake kanta, gaishe dasu Mammie yayi ya d'ora da "ya mai jikin?"
"Ah jiki da sauk'i." cewar Mamie.
"Allah ya qara sauk'i, ya kiyaye gaba."
Da "ameen." suka amsa.
Kallonta yayi yace "Khairat, Baba kesan ganinmu a d'akinshi yanzu, zaki iya tafiya?"
Ta d'an dafe kai ta tashi zaune tana kallonshi, saida ta daidaita zamanta tace "zan iya mana, muje kawai."
Tsaye ya mik'e tare da mik'o mata hijabinta tasa, hannunta ya kama suka fara takawa a hankali, suna daf da fita daga d'akin ta kalleshi tace " kuyi hak'uri Faruk dan Allah karku d'ora min laifi, nima ba'a son raina bane."
Murmushi ya mata yace "karki damu, muje."
Yana rik'e da ita har sukayi sallama d'akin suka shiga, kusa dashi ya zaunar da ita kafin suka maida hankalinsu ga Baba, kallonshi Baba yayi yace "amma ba naga mahaifiyarta sunzo ba?"
"Eh Baba suna ciki."
"To ka musu magana mana." cewar malam.
Tashi yayi ya koma d'akin ya kirasu suma dan ayi gabansu, zaune sukayi suma ana kallon kallo, Baba ne yace "to alhamdulillah kowa ya hallara, kuma ba komai yasa na taramu ba sai dan kawo qarshen matsalar data kunno mana kai, da farko ina so nasan musabbabin matsalar danta hakane zamu yaki matsalar dan gudun sake faruwar haka anan gaba."
Khairat ya kalla yace "Khairat, kinyi wata magana a lokacin da Zuby ta some wacce nake tunanin kinsan komai, shin zaki iya fad'a mana meya faru?"
Kallon Zuby tayi ta kalli Mama ta kuma kalli Umar Faruk kafin ta kalli malam ta fara magana cikin taushin murya da rawar murya tace "sanin kanku ne inhar cacar baki zai had'ani da Zubeida, to sai tasa iyayena musamman mahaifina, jiya ma hakane ya faru lokacin da Papa ya aiko mana da kud'i nida ita, bayan bata karba ba saida ta fad'a min baqar magana da banji dad'inta ba, kuma Ruk'ayya da aunty Saratu shaida ne dan suna wajen, shi yasa ni kuma naci alwashin kawo qarshen matsalar ta hanyar bayyana mata mahaifinta na gaskiya, dama kuma nasan Bala tunda jimawa, kuma shine ya fad'a min ita 'yarsa ce da suka haifa bata hanyar aure ba, shi yasa nace yazo ya karb'eta koba komai zata san mahaifinta na gaskiya."
Ajiyar zuciya malam ya sauke yace "to Zubeida kinji dalilin da yasa tayi haka, kuma inhar za abi ta gaskiya to kece kika tunzurata har tayi haka, a zahirin gaskiya ba zamu ce tayi kuskure ba, koba kamai ta taimakeki wajen sanin mahaifinki na gaskiya wanda mahaifiyarki ke b'oye miki, laifinta kawai data tona abinda bai kamata ace ta tona ba, da tayi hak'uri wataqila lokaci ne zai bayyana hakan, dan haka ina rokonku da ku gafarci junanku ku kuma yafewa juna, rashin had'a kanku da ku kaki yine ya janyo hakan, yana da kyau kusan shifa aure ibada ne, kuma qarin aure ma Allah ne ya hallata mana shi, fad'a da kuke da junanku sam bai dace ba, idan kuka had'a kanku kuka zauna lafiya, shi kanshi mijinku zaifi samun nutsuwa da kwanciyar hankali, haka kuma Allah zai qara yalwata mishi arziqinshi, dan haka ina sake baku hak'uri tare da shawartarku daku yafewa junanku dan Allah dan soyayyarku da Allah."
Kallon da yake musu yasa Khairat sauke ajiyar zuciya ta kalli Zuby tace "kiyi hak'uri Zubeida, ki yafe min? nima kuma na yafe miki abisa komai."
A cije Zuby tace "na yafe miki, nima ki yafe min."
"Ba komai 'yar uwa." cewar Khairat.
"To masha Allah, sai kuma ke Zubeida, ina so kisan abinda ya faru qaddara ce kuma jarabawa, kiyi iya qoqarinki wajen cinye wannan jarabawar, hakan zai qara hauda imaninki a wani mizani da zai qara miki qarfin imani, kuma karki saki ki kalli mahaifiyarki da wani ido dama idon rahama ba, haka shima mahaifin naki ki girmamashi dan saikin kyautata musu ne duniya da lahirarki zasuyi kyau, kiyi koyi da sahhabai da tabi'ai wajen hak'uri nuna soyayya da kuma cinye jarabawa ko wace iri ce, ki zama jarumar gaske wajen shanye abinda ke zuciyarki, kuma karki tab'a kallon Khairat da abun, hakan zaisa shaid'an ya sake galaba a kanki, kuma ki sani iyaye nada girma da darajar da babu mai ita a duniya idan kika cire Allah da manzonsa Annabi Muhammad (S.A.W)."
Sosai malam ya mata nasiha daga bisani kuma sauran iyayen suma suka tofa albarkacin bakinsu, a haka suka tashi daga zaman cike da fatan alkairi, amma fa duk abinda aka tattauna ta bayan kunnan Mama yabi ya wuce, dan tayi niyyar saita d'auki fansa akan Khairat dama shi kanshi Bala...
*Wasa farin girki*
_Ku biyoni dan jin me kuma zaici gaba da faruwa yanzun._
_Wannan sadaukarwa ne ga *Ummu Fawzan,* sama da tsawon lokaci har yau tana tambayata lafiyar mahaifiyata, wanda zaiso mahaifiyarka babban masoyine wallahi, ina sonki sister_
29/08/2019 Γ 14:33 - Meerahgeeβ€: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*MUJI TSORON ALLAH AKAN DUK ABINDA ZAMUYI*
_Bismmilahir-rahman-rahim_
5β£6β£
Kwance take akan qafafunshi suna hira yana shafar kanta, bacci ne ya fara d'ibarta yanata surutu amma yaji shiru, leqa fuskarta yayi yace "wai bacci ki kayi?"
D'an bud'a ido tayi ta kalleshi lokaci d'aya kuma ta maidasu ta rufe, dariya yayi yace "lallai aiki fa ya samu."
"To shikenan tunda dai bacci kike, kinga gobe kenan ba zuwa gida gaskiya, dan ba zan kaiki ba kije kina musu bacci ba a gida."
Tunda yaji shiru ya tabbatar bacci take bilhaqqi, dan da idonta biyu da zata tashi ta fara mishi rigima, gyara mata kwanciyar yayi yana kallon fuskarta yana yawo da yatsunshi a tsakanin fuskarta da qirjinta, saida yaji bacci na shirin d'aukarshi shima sannan ya tofa musu addu'a ya kwanta yana qara matseta jikinshi kamar za'a rabashi da ita.
*************
Da safe kuma fitowa sukayi cikin shiri ita da Zuby saboda zai kaisu gidajensu ne duka su wuni, tare suka fita bayan sunyi sallama da mutanen gidan, gidan baya Zuby ta bud'a ta shiga Khairat kuma gaba, saida ya fara aje Zuby a gida ya shiga tare da Khairat dansu gaisa, duk sallamar da sukayi Mama bata amsa ba, gaisheta sukayi shima shiru ko kallo, tausayinta ne ya kama Khairat dan haka ta d'an matsa da nufin ta mata magana, da hannu ta nunata tace "karki kuskura wallahi, kinga raunin kanki yanzu zan miki wanda ya fishi, wallahi na tsaneki bani bake har abada, kuma zaki gani a cikin qwaryar cin tuwanki , bake kad'ai ba harda shi banzan Balan daya taimaka miki, wallahi saikun gane kurenku, saina nuna muku nayi nisan da bana jin kira, kuma kamar yanda banji tsoron bakin iyayena ba wallahi ba zanji tsoron bakin wasu ba, dan saina nuna muku bakin mahaifiyata na yawo dani har yanzu, zan ajiye sauran imanin daya rage mini domin na tarwatsa ratuwarki, kuma abin kunya ba gareni farau ba bare ya qare kaina, dan haka ba zan sake jin kunyar wani ko wata ba akan abinda nayi, tunda wasu sunyi fiye da abinda na aikata, kuma ki zuba ido kiga abinda zai faru, ba dai kin tona min asiri ba, to kema zan tona miki naki asirin, wallahi sai kinji abinda nida 'yata mukaji, ku b'ace min daga gida, har kai bana son sake ganinka."
Da qyar Khairat ta iya tashi ta kama hanya, Umar Faruk na bayanta shima yana tunanin abinda Mama ta fad'a, tunda suka shiga mota babu mai magana harya ajeta gida suka shiga, ba wani kuzari haka suka gaisa sannan ya barta, yana fita Khairat ba tayi nauyin baki ba wajen fad'awa su Mamie abinda Ma'u tace, Mammie ce tace ta Allah ba tata ba kuma babu abinda zata gani sai alkairi, haka dai tayi wurin ranar ba walwala ba kuzari, sai bayan sallah isha'i yazo ya d'auketa daga nan suka wuce suka d'auko Zuby, wacce itama tayi wunin ba dad'i ba
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51 Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63