a bakinsu bare manya, na fita da tunani samo musu duk abinda ya sawaqa , amma amma ina babu abinda na samo sai dawowa nayi, a ranar kuma akayi sa'a ana bikin wata yarinya anan, babbar sa'a da mukayi shine kasancewar Khairat a cikin qawayen amaryar, koda na dawo kasa shiga cikin gidan nayi saboda ba zan juri kallon yaran ba a wannan halin, hakan yasa na zauna a qofar gida na zabga tagumi, a lokacin Khairat ta fito daga gidan dake kallon nan gidan ta ganni a wannan hali, saboda kyakyawar zuciya yasa tazo inda nake ta tambayeni me yake faruwa, nan na fad'a mata halin da nake ciki, gani nayi ta zubar da hawaye da bansan kona miye ba,tambayarta nayi me yasa take kuka sai tace karna damu , komawa tayi gidan data fito ta jima kafin ta fito, abin mamaki da al'ajabi sai Hajia Khairat ta cire hauran makka dake haqoranta da k'arfi har suna mata jini ta bani tace naje na siyar, kuma ta bani hak'uri tace babu kud'i ne a jikinta kuma gashi wayarta ta d'auke bare ta kira, amma ta gargad'eni na gaggauta siyar da hauran guda biyu na siyawa yara abinci, duk da naso mata godiya bata bani damar hakan ba saboda tafiyarta da tayi, nan na tafi na siyar da hauran biyu kuma sunyi daraja sosai sannan na siyowa yara kayan abinci na kawo gida, kasan meya faru Umar Faruk?"
Kai kawai Umar Faruk ya girgiza yana kallonshi, d'orawa yayi da "wallahi yara na cikin cin abincin Hajia Khairat ta shigo gidan tare da wasu matasa da wasu kayan abincin, bata bar gidan ba saida ta tambayi duk yaran matsalolinsu na makaranta ta biya musu, wani babban alherin data sake yi mana da yasa na kusa mutuwa saboda farin ciki shine, kyautar *million d'aya* data bani tace naja jari, tofa tun daga wannan rana na d'auki girma da matsayi na bata kamar na mahaifiyata saboda mahaifiyata bata raye, kuma wallahi wallahi Umar Faruk, zan iya fansan ran Hajia Khairat da rayuwar d'an daya fito daga cikina, domin kuwa da gaba d'aya rayuwarmu tata ce, ina fatan Allah ubangiji ya dauke duk wani ciwo da radadi dake jikin Hajia Khairat ya dawo dashi kaina koda zai zama ajalina ne, wallahi a shirye nake dana bada rayuwata dominta."
Kallon Zuby yayi yace "shine yasa a lokacin data nemi taimakona ban kasa yi mata ba saboda ta wuce hakan a gurina, kuma banji dad'i ba sam dana samu labarin rashin kunyar da kike mata, kinga mijinki gashi nan?" ya fad'a yana nuna Umar Faruk.
Da qyar Zuby ta d'aga kai dan ita kanta jikinta yayi sanyi saboda girman al'amarin Khairat, ci gaba yayi da "to wallahi zan iya sashi ya sakeki inhar zaki din cin zarafin yarinyar nan, idan ma bai sakeki ta dad'i ba zan iya yin shari'a dashi danya sakeki, dan haka ki kiyaye in kina son zaman lafiya da albarka, kuma bawai na fad'a miki haka bane dan bana sonki ko kuma ina son aurenki ya mutu, a'a ina sone na nuna miki girmanta a gareni, ina fatan kin fahimta? Allah ya muku albarka ya baku zaman lafiya da hak'uri da juna."
Umar Faruk kad'ai ya amsa da "ameen Baba."
Haka suka dawo gida Zuby na sake jin kunyar Khairat da kanta, Umar Faruk kuma na sake jinjina al'amarin Khairat, dan inbai manta ba ta fad'a mishi ta manta sunan wanda tabawa hauran makkanta, ashe bata manta ba kawai dai bata son fad'a ne saboda kawai tayi dan Allah, a lokacin daya shiga wanka doushe ya lumshe ido ya furta a hankali cewa " *Allah ka azurtani da zuciya irinta bauwarkan nan, Allah ka cire min son abin duniya, Allah ka bani ikon yin komai dan kai, matata kuma Allah ka dubi kyakyawar zuciyarta ta son taimako ka cireta a halin da take ciki.*"
Nidai nace "Ameen."
_Haka ma team d'in Khairat da *"ameeeen."* suka amsa._
*Bayan sati d'aya*, ranar litinin su Zuby suku fara shiga jarabawa, Umar Faruk ya kaita dan zana jarabawa, sunyi sai dai Zuby saida tayi qwalla saboda sarewa da tayi, a lokacin da suka tashi Umar Faruk ya zo d'aukarta tare da Khairat daya d'aukota daga wajen awo, suna jirar fitowarta wata mota ta fito daga cikin makarantar, babban mutum ne amma yana ganin Khairat zaune a motar ya fito daga tashi yazo inda take, tana ganinshi ta sauke glass d'in motar suka gaisa, mutumin ne yace "Hajia Khairat na ganki anan, lafiya daiko?"
"Lafiya lau wallahi, munzo d'aukar qanwata ne."
"Allah sarki, anan take jarabawar itama?"
"Eh, anan take."
"Masha Allah, to Hajia meye sunanta?"
"Me yasa kake tambaya?" cewar Khairat.
"Hajia aimu qasa muke dake, bamu cika samun irin wannan damar ba, ba kuma zanyi wasa da ita wajen kyautata miki kema."
"Zubeida..." kallon Umar Faruk tayi tace "sunan babanta?"
"Hamza, amma ai kinsan ba shine originale d'in ba." cewar Umar Faruk.
Murmushi tayi ta kalli dattijon tace "Zubeida Hamza."
"Shikenan Hajia, ki d'auka qanwarki taci."
Cewar Khairat "amma dai a dinga duba cancanta , idan za'a dinga bawa mutane irinmu saboda wani abu, to wanda basu da alfarma fa?"
"Hajia aike ba kamar kowa bace, amma insha Allah za'a kiyaye."
Lokacin Zuby ta fito, gaishe da dattijon tayi sai taga yana washe mata baki ba kamar idan suna cikin makaranta ba, baya ta shiga tana fad'in "sannu."
Khairat ce ta fara amsawa da "sannu."
Saida ya aje Khairat gida sannan ya wuce da Zuby gida....
*Bayan gama jarabawa*, da daddare Umar Faruk ya dubowa Zuby sakamakonta, tun a hanya ya kira ya fad'a mata taci écris, zo kaga murna da farin ciki, cikin qanqanin lokaci fad'awa kowa, Umar Faruk dai kallonta yake yana ganin kawai ta samune a sanadiyar Khairat.
*A gurguje*
Umar Faruk dai ya zage damtse sosai wajen yiwa Khairat magani da addu'a, kuma cikin ikon ubangiji komai yayi sauqi yanzu, sai ciwon qafafu da yan abinda ba'a rasa ba, sai dai bai d'auki kowane mataki ba ga tanti ko Zuby, idan har lokacin arziqinka yayi to ba fashi , duk da hankalinshi ba'a kwance yake ba amma ubangiji na bud'a mishi tako wace hanya, yanzu haka da taimakon Allah har an fara aiki a compganinshi daya siya, ga kuma shaguna da yanzun suma suke shigo mishi da kud'i, yanzu haka baya qarqashin kowa zaman kanshi yake shima yana cin gumin kanshi, yanzu haka yana nan ya siyi wani babban fili daf da gidansu har an fara gini dansu koma gaba d'aya ahalinshi, kuma duka 'yan uwanshi maza suna tare dashi suma suna cin arzik'i, sai dai kawai ace alhamdulillah, a wajen Zuby kuma baqin cikine ya isheta saboda rashin nasara akan maganin data saka mishi, shi kuma dama ya dogara ga Allah ne yasan babu abinda zai faru dashi dama, kuma har yau bai nuna mata komai ba, idan ka ganta kace cikin yan uku ne da ita, shi yasa ma uwarta ke kiranta da uwar uku wani lokacin.
Duk da lokacin da Khairat ta d'auka a gida bata son komawa gidanta, kuma kullum Umar Faruk sintirin zuwa gidan yake, yanzu haka *cikinta na wata na biyar*, amma idan ka ganshi za kace cikin wata hud'u ne, sai dai yanzu da dama ciwo yayi sauqi, musamman amai da rashin son cin abinci, yanzu duka tana ci kuma tana sha, sai dai matsalar Salim a yawon sakata damuwa, dan yaron yazo da raini sosai da rashin kunya, Mamie kullum cikin baqin ciki take akan yaron, sai tsirfa iri iri kamar mai ciki, zuciya kuma bata da qashi sai Allah yasawa Papa son yaron saboda yana ganinshi namiji ne, da wannan taskun kullum basa farin ciki, ga kuma karb'ar kud'i da yaron ke yawan yi, amma duk abinda ya nema Papa yi mishi yake.
Wani bala'i daya taso musu shine yad'uwar maganar Salim a kafafen sada zumunta da gidajen tv da redio, wannan abu sosai ya tab'a mutuncin Papa har saida ya kai ya daina fita waje, ga kuma kira daya sameshi daga jam'iyarsu wai an cireshi daga partie d'insu, bai damu da wannan ba ko kad'an tunda dama tunaninshi barin siyasa, maganganu marasa dad'i kawai ake a social media da gidajen radio, sai dai masoyanshi na alaqanta hakan da yarfe na siyasa, hakan ya sake tadowa Khairat tsohon ciwonta na qirji da ciwon kai, hakan kuma ya d'aga hankalin iyayen nata da mijinta, hakan yasa Umar Faruk d'amarar binciko gaskiyar alamarin, dan yanzu suma iyayenshi ne ba ita kad'ai ba.
*Yau* ma kamar kullum zaune suke a falon ana hira sama sama, hankalinsu ne ya koma kan tv saboda wani shiri da ake tattaunawa akan manyan mutane har aka d'auko misali da Papa, mai gabatar da shirinne yakewa d'aya tambaya da "to yallab'ai me zaka iya cewa akan wannan magana, ace shuwagabanni daya kamata ace muna koyi dasu kuma sune suke aikata bad'ala a doron qasa?"
Mutumin da aka tambaya ne ya gyara zama zai bada amsa Mamie ta kashe tv, Papa kuma qasa yayi da kanshi cike da takaici da kunyar iyalinshi, shiru da falon ya d'auka yasa Papa cewa cikin muryar nadama yace " kuyi hak'uri ku yafeni, ni naja muku wannan abun kunyar, haqiqa na bar muku abinda har jikokinku zasu ji kunya, yanzu ne nake qara tir da rayuwata, ku yafe min dan Allah, nasan na cutar daku."
Babu wanda yayi magana sai Umar Faruk yace "kuyi hak'uri Papa, wannan itace jarabawarku, kuyi qoqari ku cinyeta, insha Allah Allah ba zai kunyatar daku ba kuma zaku samu sakamako koda ranar gobe ce."
Salim ne ya shigo yana wasa da makullin tsandareriyar motar da zab'inshi ce wato *Prado*, kai tsaye dinning ya nufa yana bud'a kwanukan abinci, tsaki yaja ya juyo yana kallon Mamie yace "wai me yasa ne ni ake nuna min wariyar launin fata a gidan nan ne? nasha fad'a bana cin macca amma dole sai an dafa, to yanzu me zanci kenan?"
Yunqurawa tayi ta tashi tsaye da nufin
taje wajenshi, da k'arfi ta koma ta zauna kamar an jefata saboda ciwon da qafafunta keyi, rik'e hannunta Umar Faruk yayi yana kallon fuskarta yayi ganin yanda take hararan Salim yasa ya kamata suka tashi ya kaita d'akinta, duk da abinda Salim ke fad'a tana so ta tsaya Umar Faruk ya hanata, saida suka shiga ya kwantar da ita ya rufeta sannan ya kalli fuskarta yace "qaninki ne fa, ki kama girmanki mana karya rainaki."
"Wallahi ba d'an uwana bane waccen banzan yaron, rainin wayonshi yayi yawa, kullum da kalar iskancin da yake zuwa."
Wani mayan kallo ya mata ya kwantar da kanshi a qirjinta yana sauke numfashi, shafa kanshi tayi tace "ya dai baby?"
D'ago kai yayi yana kallonta a marairaice yace "Khairat nayi kewarki sosai wallahi, dan Allah ki daure mu koma gida Khairat kona d'an rage zafi, wallahi na kusa kaiwa matakin qarshe."
"Karka damu zan koma." ta fad'a a tak'aice.
"Yaushe?" ya tambaya.
Kallonshi tayi tace "nan da sati d'aya, lokacin na qara warwarewa."
Rumgumeta yayi yace "Allah ya yarda baby, zanyi farin ciki da wannan ranar fiye da farin cikin da nayi a lokacin da aka kawo minke gidana."
Ya jima suna hira saida yaga bacci ya fara dibarta sannan ya shafeta da addu'a ya rufe mata d'akin ya fita, Salim ya samu gaban Papa yana fad'in "Allah idan ba tayi hankali ba zanyi maganinta a gidan nan, yanzu kawai ka bani wani abu nan zanje na samu wani abu naci, tunda a gabanka ake nuna min bana da mahimmanci kuma ka kasa d'aukar mataki, dan anga uwata bata cikin gidan."
Kallonshi kawai Papa yayi yace "yanzu kace baka da kud'in cin abinci a wajenka?"
"Eh, bana da." ya fad'a yana hararan Mamie.
D'auke idonshi yayi daga kan Mamie cikin akasi suka had'a ido da Umar Faruk, wata arniyar harara daya gabza masa yasa yaji gabanshi ya fad'i, kallonsu Papa yayi yace "saida safenku."
Tunda Umar Faruk ya sanar a gida da Khairat zata dawo hankalin Zuby ya tashi, dan gani take yanzu zai rage nuna mata kulawa, duk yanda zaiyi dare a gidansu Khairat baya wuce k'arfe 10:00, kuma bata gansu ba bare taga me sukayi, dan haka hankalinta ke kwance, nan ta fad'awa Mama abinda ke faruwa, ita kuma fad'a ta mata tace da tayi aiki da maganin data bata da ba za taji sha'awar dawowa ba.
**************
Tunda sukayi maganar dawowarta sai kuma ciwo suka dawo, ya kuma fahimci gidan ne bata san zama yanzu, dan haka yayi shirin d'aukar mataki akan hakan.
Da sallama ya shigo gidan ya samesu falo tare da likitan Papa dake dubata, ko gaisawa basuyi ba ya zuba ido yana kallonsu shima, likitan ne ya d'ago ya kalli Papa yace "a gaskiya bansan dalilin da yasa cikin ke haka ba, amma dai abinda zan iya fad'a muku anan shine, da zaran ta fara naquda ku gaggauta kaita asibiti dan a mata tiyata."
A duburburce Umar Faruk yace "me, tiyata, akan me?"
Kallonshi likitan yayi yace "eh tiyata, saboda ba zata iya haihuwa da kanta ba."
"Akan me, kaine keda iko akan haka da zaka fad'i haka? babu wanda ya isa ya fasa min mata wallahi, zata haihu da kanta."
Likitan Papa ya kalla yace "kafi kowa sanin wacece 'yarka, dan haka nidai na fad'a muku abinda ya dace, idan baku ji ba zaku wahalar da itane da d'an cikinta a banza."
Ficewa yayi su kuma suka zauna Mammie ce ta kalli Umar Faruk tace "duba kaga abinda cikinta keyi fa."
Da sauri ya sunkuya gaban Khairat ya janye rigarta yana kallon cikinta, waro ido yayi cike da tsoro saboda ganin yanda dan cikinta ke motsi, bawai motsi bane kamar kowane, wannan kamar yana neman hanyar fitowa ne ta hanyar parka cikin nata ya fito, yawo kawai yake mata ko ina, ita kuma harta darrahe ta barwa Allah sai ruwa kawai dake fita a idonta, kallonta yayi yace "kiyi hak'uri Khairat, nasan zaki sha wahala, amma dole ayita ta qare."
Wasu hawayen ne suka sake bulbulo mata ta qara qamqame hannunshi, girgiza mata kai yayi alamar ta daina kuka, cikin muryar kuka cike da tausayin kanta tace " *Umar Faruk*."
Kallonta yayi sosai dan shine na farko tunda sukayi aure da yaji sunan Umar Faruk a bakinta, ci gaba tayi da cewa "ni kad'ai nasan me nake ji a jikina, na wahala iya wahala, nasan jarabawa ce daga Allah, wataqila had'e da hukuntani akan kurakuraina na baya, Umar Faruk bana jin zan rayu saboda azabar nake sha, amma ina so kamin alk'awarin zaka kula min da abinda zan haifa idan Allah yasa ya fito duniya, ina so ka bawa abinda zan haifa tarbiyar da ban samu ba, ka yafe min Faruk akan komai dana maka."
Hannayenta tasa ta janyo kanshi ta had'a goshinsu waje d'aya tana kallonshi tace "ina sonka Umar Faruk, ina qaunarka fiye da abinda yake cikin nan nawa."
Rintse ido Umar Faruk yayi hawaye suka zubo mishi ya d'an kawar da kanshi gefe kafin ya kalleta cikin kukan da bai tab'a irinshi ba yace "me yasa Khairat, me yasa zaki soni fiye da yanda kike son abinda yake cikinki? me yasa ba zaki kalleni a matsayin wanda yayi sanadiyar shigarki wannan halin, Khairat ban cancanci wannan soyayyar ba, ko kad'an ban cancanci wannan soyayyar ba Khairat."
Ya qarashe da sake fashewa da kuka, Mamie Mammie Papa duka babu wanda bai zubar musu da hawaye ba, saida suka ci kukansu babu mai rarrashi kafin Umar Faruk ya goge nashi hawayen ya tashi tsaye, kamata yayi suka nufi d'akinta ya kalli Mamie yace "dan Allah kuzo."
Bayanshi Mamie tabi saisu Mammie da yace ma "ku tayamu da addu'a."
Suna shiga d'akin ya zaunar da ita qasa ya sata tsakiyar qafafunshi, janyota yayi jikinshi sosai yasa bakinshi a kunnanta ya fara sambad'a mata karatu, tun yana karatun tana d'an motsi a hankali harta fara turmushe turmushe, Mamie ya kalla yace "ku kawo ruwan nan dana kawo tana sha."
D'aukowa Mamie tayi ta bashi ta koma gefe sai addu'a take duk wacce tazo bakinta, koda ya watsa mata ta kwamtsa qara tare da qoqarin fincikewa daga jikinshi, wani d'an banzan rik'o da yayi mata saida ya rufe idonshi saboda yasan zata wahala haka ma d'an cikinta, ko kad'an bai saurara mata ba haka ya dinga karatu da watsa mata ruwan nan, kuka take cikin gumjin murya ana fad'in yayi hak'uri zamu fita amma bai saurara ba, saima cewa da yayi "aina fad'a muku ku fita a jikinta lafiya kafin aji kanmu amma baku ji ba."
Turmuje turmuje take sosai tana kokawa dashi amma ina, har saida takai kayan jikinta sun fita saboda bala'i shima kuma ta yaga mishi riga, idonta ne sukayi jawur dasu kamar wuta, cikin muryar shan wahala akace "zamu fita, wallahi zamu fita har abada, ka fad'a mana ta ina kake so mu fita?"
Cikin d'aga murya yace "ta hancinta, kuma bana so ku cutar da ita, sannan kumin alk'awarin ba zaku sake dawowa gareta ba."
"Munyi, munyi wallahi, amma fa zamu...."
Shurin da sukayi yasa yace "amma me, me zakuyi?"
"Gaskiya zamu koma kan masu hannu a turo mu, saboda munsha wahala."
"Karku fara wallahi, ku barni dasu kosu waye ni zanyi maganinsu, in kuma baku ji ba to zaku mutu wallahi, kunji na rantse."
Wata irin bille bille Khairat ta fara ga wata irin majina dake fita ta hancinta kamar an kunna panpo, a cikin haka kuma take had'awa da atshawa kuma idonta rufe, saida tayi atshawa ba adadi kafin ta fad'i kwance amma kuma majinar nan naci gaba da fita daga hancinta ba qaqqautawa, gyara mata kwanciya yayi ya kalli Mamie yace "Alhamdulillah, yanzu sun fita, kuma insha Allah ba zasu sake dawowa ba da yardar Allah, yanzu ku canza mata kaya saiku barta ta samu bacci."
Yana fad'a ya d'auketa ya mayar kan gado sannan ya fita, su Papa ya samu har yanzu suna tsaye cirko cirko, kallonsu yayi yace "karku damu, ta samu lafiya da izinin Allah."
Yana fad'a ya fita su kuma suka shiga d'akin Khairat dan ganin halin da take ciki, saida ya shiga mota ya kula da rigarshi, a haka yaje gida yana fita ya fad'a cikin gidan yana d'an kare rigarshi, kai tsaye d'akin Zuby ya shiga bai kula kowa dake zaune ba, zaune ya sameta tana shan exotic d'in daya wadatata dashi, rigarshi ya cire yana shirin cire wandon Zuby tace.....
_To Hajia
Showing 162001 words to 165000 words out of 186119 words
Kai kawai Umar Faruk ya girgiza yana kallonshi, d'orawa yayi da "wallahi yara na cikin cin abincin Hajia Khairat ta shigo gidan tare da wasu matasa da wasu kayan abincin, bata bar gidan ba saida ta tambayi duk yaran matsalolinsu na makaranta ta biya musu, wani babban alherin data sake yi mana da yasa na kusa mutuwa saboda farin ciki shine, kyautar *million d'aya* data bani tace naja jari, tofa tun daga wannan rana na d'auki girma da matsayi na bata kamar na mahaifiyata saboda mahaifiyata bata raye, kuma wallahi wallahi Umar Faruk, zan iya fansan ran Hajia Khairat da rayuwar d'an daya fito daga cikina, domin kuwa da gaba d'aya rayuwarmu tata ce, ina fatan Allah ubangiji ya dauke duk wani ciwo da radadi dake jikin Hajia Khairat ya dawo dashi kaina koda zai zama ajalina ne, wallahi a shirye nake dana bada rayuwata dominta."
Kallon Zuby yayi yace "shine yasa a lokacin data nemi taimakona ban kasa yi mata ba saboda ta wuce hakan a gurina, kuma banji dad'i ba sam dana samu labarin rashin kunyar da kike mata, kinga mijinki gashi nan?" ya fad'a yana nuna Umar Faruk.
Da qyar Zuby ta d'aga kai dan ita kanta jikinta yayi sanyi saboda girman al'amarin Khairat, ci gaba yayi da "to wallahi zan iya sashi ya sakeki inhar zaki din cin zarafin yarinyar nan, idan ma bai sakeki ta dad'i ba zan iya yin shari'a dashi danya sakeki, dan haka ki kiyaye in kina son zaman lafiya da albarka, kuma bawai na fad'a miki haka bane dan bana sonki ko kuma ina son aurenki ya mutu, a'a ina sone na nuna miki girmanta a gareni, ina fatan kin fahimta? Allah ya muku albarka ya baku zaman lafiya da hak'uri da juna."
Umar Faruk kad'ai ya amsa da "ameen Baba."
Haka suka dawo gida Zuby na sake jin kunyar Khairat da kanta, Umar Faruk kuma na sake jinjina al'amarin Khairat, dan inbai manta ba ta fad'a mishi ta manta sunan wanda tabawa hauran makkanta, ashe bata manta ba kawai dai bata son fad'a ne saboda kawai tayi dan Allah, a lokacin daya shiga wanka doushe ya lumshe ido ya furta a hankali cewa " *Allah ka azurtani da zuciya irinta bauwarkan nan, Allah ka cire min son abin duniya, Allah ka bani ikon yin komai dan kai, matata kuma Allah ka dubi kyakyawar zuciyarta ta son taimako ka cireta a halin da take ciki.*"
Nidai nace "Ameen."
_Haka ma team d'in Khairat da *"ameeeen."* suka amsa._
*Bayan sati d'aya*, ranar litinin su Zuby suku fara shiga jarabawa, Umar Faruk ya kaita dan zana jarabawa, sunyi sai dai Zuby saida tayi qwalla saboda sarewa da tayi, a lokacin da suka tashi Umar Faruk ya zo d'aukarta tare da Khairat daya d'aukota daga wajen awo, suna jirar fitowarta wata mota ta fito daga cikin makarantar, babban mutum ne amma yana ganin Khairat zaune a motar ya fito daga tashi yazo inda take, tana ganinshi ta sauke glass d'in motar suka gaisa, mutumin ne yace "Hajia Khairat na ganki anan, lafiya daiko?"
"Lafiya lau wallahi, munzo d'aukar qanwata ne."
"Allah sarki, anan take jarabawar itama?"
"Eh, anan take."
"Masha Allah, to Hajia meye sunanta?"
"Me yasa kake tambaya?" cewar Khairat.
"Hajia aimu qasa muke dake, bamu cika samun irin wannan damar ba, ba kuma zanyi wasa da ita wajen kyautata miki kema."
"Zubeida..." kallon Umar Faruk tayi tace "sunan babanta?"
"Hamza, amma ai kinsan ba shine originale d'in ba." cewar Umar Faruk.
Murmushi tayi ta kalli dattijon tace "Zubeida Hamza."
"Shikenan Hajia, ki d'auka qanwarki taci."
Cewar Khairat "amma dai a dinga duba cancanta , idan za'a dinga bawa mutane irinmu saboda wani abu, to wanda basu da alfarma fa?"
"Hajia aike ba kamar kowa bace, amma insha Allah za'a kiyaye."
Lokacin Zuby ta fito, gaishe da dattijon tayi sai taga yana washe mata baki ba kamar idan suna cikin makaranta ba, baya ta shiga tana fad'in "sannu."
Khairat ce ta fara amsawa da "sannu."
Saida ya aje Khairat gida sannan ya wuce da Zuby gida....
*Bayan gama jarabawa*, da daddare Umar Faruk ya dubowa Zuby sakamakonta, tun a hanya ya kira ya fad'a mata taci écris, zo kaga murna da farin ciki, cikin qanqanin lokaci fad'awa kowa, Umar Faruk dai kallonta yake yana ganin kawai ta samune a sanadiyar Khairat.
*A gurguje*
Umar Faruk dai ya zage damtse sosai wajen yiwa Khairat magani da addu'a, kuma cikin ikon ubangiji komai yayi sauqi yanzu, sai ciwon qafafu da yan abinda ba'a rasa ba, sai dai bai d'auki kowane mataki ba ga tanti ko Zuby, idan har lokacin arziqinka yayi to ba fashi , duk da hankalinshi ba'a kwance yake ba amma ubangiji na bud'a mishi tako wace hanya, yanzu haka da taimakon Allah har an fara aiki a compganinshi daya siya, ga kuma shaguna da yanzun suma suke shigo mishi da kud'i, yanzu haka baya qarqashin kowa zaman kanshi yake shima yana cin gumin kanshi, yanzu haka yana nan ya siyi wani babban fili daf da gidansu har an fara gini dansu koma gaba d'aya ahalinshi, kuma duka 'yan uwanshi maza suna tare dashi suma suna cin arzik'i, sai dai kawai ace alhamdulillah, a wajen Zuby kuma baqin cikine ya isheta saboda rashin nasara akan maganin data saka mishi, shi kuma dama ya dogara ga Allah ne yasan babu abinda zai faru dashi dama, kuma har yau bai nuna mata komai ba, idan ka ganta kace cikin yan uku ne da ita, shi yasa ma uwarta ke kiranta da uwar uku wani lokacin.
Duk da lokacin da Khairat ta d'auka a gida bata son komawa gidanta, kuma kullum Umar Faruk sintirin zuwa gidan yake, yanzu haka *cikinta na wata na biyar*, amma idan ka ganshi za kace cikin wata hud'u ne, sai dai yanzu da dama ciwo yayi sauqi, musamman amai da rashin son cin abinci, yanzu duka tana ci kuma tana sha, sai dai matsalar Salim a yawon sakata damuwa, dan yaron yazo da raini sosai da rashin kunya, Mamie kullum cikin baqin ciki take akan yaron, sai tsirfa iri iri kamar mai ciki, zuciya kuma bata da qashi sai Allah yasawa Papa son yaron saboda yana ganinshi namiji ne, da wannan taskun kullum basa farin ciki, ga kuma karb'ar kud'i da yaron ke yawan yi, amma duk abinda ya nema Papa yi mishi yake.
Wani bala'i daya taso musu shine yad'uwar maganar Salim a kafafen sada zumunta da gidajen tv da redio, wannan abu sosai ya tab'a mutuncin Papa har saida ya kai ya daina fita waje, ga kuma kira daya sameshi daga jam'iyarsu wai an cireshi daga partie d'insu, bai damu da wannan ba ko kad'an tunda dama tunaninshi barin siyasa, maganganu marasa dad'i kawai ake a social media da gidajen radio, sai dai masoyanshi na alaqanta hakan da yarfe na siyasa, hakan ya sake tadowa Khairat tsohon ciwonta na qirji da ciwon kai, hakan kuma ya d'aga hankalin iyayen nata da mijinta, hakan yasa Umar Faruk d'amarar binciko gaskiyar alamarin, dan yanzu suma iyayenshi ne ba ita kad'ai ba.
*Yau* ma kamar kullum zaune suke a falon ana hira sama sama, hankalinsu ne ya koma kan tv saboda wani shiri da ake tattaunawa akan manyan mutane har aka d'auko misali da Papa, mai gabatar da shirinne yakewa d'aya tambaya da "to yallab'ai me zaka iya cewa akan wannan magana, ace shuwagabanni daya kamata ace muna koyi dasu kuma sune suke aikata bad'ala a doron qasa?"
Mutumin da aka tambaya ne ya gyara zama zai bada amsa Mamie ta kashe tv, Papa kuma qasa yayi da kanshi cike da takaici da kunyar iyalinshi, shiru da falon ya d'auka yasa Papa cewa cikin muryar nadama yace " kuyi hak'uri ku yafeni, ni naja muku wannan abun kunyar, haqiqa na bar muku abinda har jikokinku zasu ji kunya, yanzu ne nake qara tir da rayuwata, ku yafe min dan Allah, nasan na cutar daku."
Babu wanda yayi magana sai Umar Faruk yace "kuyi hak'uri Papa, wannan itace jarabawarku, kuyi qoqari ku cinyeta, insha Allah Allah ba zai kunyatar daku ba kuma zaku samu sakamako koda ranar gobe ce."
Salim ne ya shigo yana wasa da makullin tsandareriyar motar da zab'inshi ce wato *Prado*, kai tsaye dinning ya nufa yana bud'a kwanukan abinci, tsaki yaja ya juyo yana kallon Mamie yace "wai me yasa ne ni ake nuna min wariyar launin fata a gidan nan ne? nasha fad'a bana cin macca amma dole sai an dafa, to yanzu me zanci kenan?"
"Uwarka, nace uwarka kaji, marar kunya d'an rainin hankali." cewar Khairat dake b'antarar d'anyan mangaro.
Yunqurawa tayi ta tashi tsaye da nufin
taje wajenshi, da k'arfi ta koma ta zauna kamar an jefata saboda ciwon da qafafunta keyi, rik'e hannunta Umar Faruk yayi yana kallon fuskarta yayi ganin yanda take hararan Salim yasa ya kamata suka tashi ya kaita d'akinta, duk da abinda Salim ke fad'a tana so ta tsaya Umar Faruk ya hanata, saida suka shiga ya kwantar da ita ya rufeta sannan ya kalli fuskarta yace "qaninki ne fa, ki kama girmanki mana karya rainaki."
"Wallahi ba d'an uwana bane waccen banzan yaron, rainin wayonshi yayi yawa, kullum da kalar iskancin da yake zuwa."
Wani mayan kallo ya mata ya kwantar da kanshi a qirjinta yana sauke numfashi, shafa kanshi tayi tace "ya dai baby?"
D'ago kai yayi yana kallonta a marairaice yace "Khairat nayi kewarki sosai wallahi, dan Allah ki daure mu koma gida Khairat kona d'an rage zafi, wallahi na kusa kaiwa matakin qarshe."
"Karka damu zan koma." ta fad'a a tak'aice.
"Yaushe?" ya tambaya.
Kallonshi tayi tace "nan da sati d'aya, lokacin na qara warwarewa."
Rumgumeta yayi yace "Allah ya yarda baby, zanyi farin ciki da wannan ranar fiye da farin cikin da nayi a lokacin da aka kawo minke gidana."
Ya jima suna hira saida yaga bacci ya fara dibarta sannan ya shafeta da addu'a ya rufe mata d'akin ya fita, Salim ya samu gaban Papa yana fad'in "Allah idan ba tayi hankali ba zanyi maganinta a gidan nan, yanzu kawai ka bani wani abu nan zanje na samu wani abu naci, tunda a gabanka ake nuna min bana da mahimmanci kuma ka kasa d'aukar mataki, dan anga uwata bata cikin gidan."
Kallonshi kawai Papa yayi yace "yanzu kace baka da kud'in cin abinci a wajenka?"
"Eh, bana da." ya fad'a yana hararan Mamie.
D'auke idonshi yayi daga kan Mamie cikin akasi suka had'a ido da Umar Faruk, wata arniyar harara daya gabza masa yasa yaji gabanshi ya fad'i, kallonsu Papa yayi yace "saida safenku."
Tunda Umar Faruk ya sanar a gida da Khairat zata dawo hankalin Zuby ya tashi, dan gani take yanzu zai rage nuna mata kulawa, duk yanda zaiyi dare a gidansu Khairat baya wuce k'arfe 10:00, kuma bata gansu ba bare taga me sukayi, dan haka hankalinta ke kwance, nan ta fad'awa Mama abinda ke faruwa, ita kuma fad'a ta mata tace da tayi aiki da maganin data bata da ba za taji sha'awar dawowa ba.
**************
Tunda sukayi maganar dawowarta sai kuma ciwo suka dawo, ya kuma fahimci gidan ne bata san zama yanzu, dan haka yayi shirin d'aukar mataki akan hakan.
Da sallama ya shigo gidan ya samesu falo tare da likitan Papa dake dubata, ko gaisawa basuyi ba ya zuba ido yana kallonsu shima, likitan ne ya d'ago ya kalli Papa yace "a gaskiya bansan dalilin da yasa cikin ke haka ba, amma dai abinda zan iya fad'a muku anan shine, da zaran ta fara naquda ku gaggauta kaita asibiti dan a mata tiyata."
A duburburce Umar Faruk yace "me, tiyata, akan me?"
Kallonshi likitan yayi yace "eh tiyata, saboda ba zata iya haihuwa da kanta ba."
"Akan me, kaine keda iko akan haka da zaka fad'i haka? babu wanda ya isa ya fasa min mata wallahi, zata haihu da kanta."
Likitan Papa ya kalla yace "kafi kowa sanin wacece 'yarka, dan haka nidai na fad'a muku abinda ya dace, idan baku ji ba zaku wahalar da itane da d'an cikinta a banza."
Ficewa yayi su kuma suka zauna Mammie ce ta kalli Umar Faruk tace "duba kaga abinda cikinta keyi fa."
Da sauri ya sunkuya gaban Khairat ya janye rigarta yana kallon cikinta, waro ido yayi cike da tsoro saboda ganin yanda dan cikinta ke motsi, bawai motsi bane kamar kowane, wannan kamar yana neman hanyar fitowa ne ta hanyar parka cikin nata ya fito, yawo kawai yake mata ko ina, ita kuma harta darrahe ta barwa Allah sai ruwa kawai dake fita a idonta, kallonta yayi yace "kiyi hak'uri Khairat, nasan zaki sha wahala, amma dole ayita ta qare."
Wasu hawayen ne suka sake bulbulo mata ta qara qamqame hannunshi, girgiza mata kai yayi alamar ta daina kuka, cikin muryar kuka cike da tausayin kanta tace " *Umar Faruk*."
Kallonta yayi sosai dan shine na farko tunda sukayi aure da yaji sunan Umar Faruk a bakinta, ci gaba tayi da cewa "ni kad'ai nasan me nake ji a jikina, na wahala iya wahala, nasan jarabawa ce daga Allah, wataqila had'e da hukuntani akan kurakuraina na baya, Umar Faruk bana jin zan rayu saboda azabar nake sha, amma ina so kamin alk'awarin zaka kula min da abinda zan haifa idan Allah yasa ya fito duniya, ina so ka bawa abinda zan haifa tarbiyar da ban samu ba, ka yafe min Faruk akan komai dana maka."
Hannayenta tasa ta janyo kanshi ta had'a goshinsu waje d'aya tana kallonshi tace "ina sonka Umar Faruk, ina qaunarka fiye da abinda yake cikin nan nawa."
Rintse ido Umar Faruk yayi hawaye suka zubo mishi ya d'an kawar da kanshi gefe kafin ya kalleta cikin kukan da bai tab'a irinshi ba yace "me yasa Khairat, me yasa zaki soni fiye da yanda kike son abinda yake cikinki? me yasa ba zaki kalleni a matsayin wanda yayi sanadiyar shigarki wannan halin, Khairat ban cancanci wannan soyayyar ba, ko kad'an ban cancanci wannan soyayyar ba Khairat."
Ya qarashe da sake fashewa da kuka, Mamie Mammie Papa duka babu wanda bai zubar musu da hawaye ba, saida suka ci kukansu babu mai rarrashi kafin Umar Faruk ya goge nashi hawayen ya tashi tsaye, kamata yayi suka nufi d'akinta ya kalli Mamie yace "dan Allah kuzo."
Bayanshi Mamie tabi saisu Mammie da yace ma "ku tayamu da addu'a."
Suna shiga d'akin ya zaunar da ita qasa ya sata tsakiyar qafafunshi, janyota yayi jikinshi sosai yasa bakinshi a kunnanta ya fara sambad'a mata karatu, tun yana karatun tana d'an motsi a hankali harta fara turmushe turmushe, Mamie ya kalla yace "ku kawo ruwan nan dana kawo tana sha."
D'aukowa Mamie tayi ta bashi ta koma gefe sai addu'a take duk wacce tazo bakinta, koda ya watsa mata ta kwamtsa qara tare da qoqarin fincikewa daga jikinshi, wani d'an banzan rik'o da yayi mata saida ya rufe idonshi saboda yasan zata wahala haka ma d'an cikinta, ko kad'an bai saurara mata ba haka ya dinga karatu da watsa mata ruwan nan, kuka take cikin gumjin murya ana fad'in yayi hak'uri zamu fita amma bai saurara ba, saima cewa da yayi "aina fad'a muku ku fita a jikinta lafiya kafin aji kanmu amma baku ji ba."
Turmuje turmuje take sosai tana kokawa dashi amma ina, har saida takai kayan jikinta sun fita saboda bala'i shima kuma ta yaga mishi riga, idonta ne sukayi jawur dasu kamar wuta, cikin muryar shan wahala akace "zamu fita, wallahi zamu fita har abada, ka fad'a mana ta ina kake so mu fita?"
Cikin d'aga murya yace "ta hancinta, kuma bana so ku cutar da ita, sannan kumin alk'awarin ba zaku sake dawowa gareta ba."
"Munyi, munyi wallahi, amma fa zamu...."
Shurin da sukayi yasa yace "amma me, me zakuyi?"
"Gaskiya zamu koma kan masu hannu a turo mu, saboda munsha wahala."
"Karku fara wallahi, ku barni dasu kosu waye ni zanyi maganinsu, in kuma baku ji ba to zaku mutu wallahi, kunji na rantse."
Wata irin bille bille Khairat ta fara ga wata irin majina dake fita ta hancinta kamar an kunna panpo, a cikin haka kuma take had'awa da atshawa kuma idonta rufe, saida tayi atshawa ba adadi kafin ta fad'i kwance amma kuma majinar nan naci gaba da fita daga hancinta ba qaqqautawa, gyara mata kwanciya yayi ya kalli Mamie yace "Alhamdulillah, yanzu sun fita, kuma insha Allah ba zasu sake dawowa ba da yardar Allah, yanzu ku canza mata kaya saiku barta ta samu bacci."
Yana fad'a ya d'auketa ya mayar kan gado sannan ya fita, su Papa ya samu har yanzu suna tsaye cirko cirko, kallonsu yayi yace "karku damu, ta samu lafiya da izinin Allah."
Yana fad'a ya fita su kuma suka shiga d'akin Khairat dan ganin halin da take ciki, saida ya shiga mota ya kula da rigarshi, a haka yaje gida yana fita ya fad'a cikin gidan yana d'an kare rigarshi, kai tsaye d'akin Zuby ya shiga bai kula kowa dake zaune ba, zaune ya sameta tana shan exotic d'in daya wadatata dashi, rigarshi ya cire yana shirin cire wandon Zuby tace.....
_To Hajia
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55 Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63