nayiwa kaina ba."

"Babu wanda zai wulak'antaki Khairat, ina tare dake, wallahi wallahi Khairat ni _Umar Faruk, nayi alk'awarin ba zan tab'a bari wani ko wata ya sake cin zarafinki ba, ke matata ce kuma uwar 'ya'yana, zan iya b'atawa da kowa a kanki Khairat inhar kika cire iyayena, Khairat ki yarda dani kema ki bani kanki danni na mallaka miki kaina, kiyi yanda kike so dani Khairat, wallahi sai yanda ki kaso za kiyi dani bana da bakin magana."_

A take maganar Mamie ta fad'o mata a rai cewar tana so a daren farkonta ta samu kyauta zuviyar mijinta dashi kanshi, share hawayenta tayi danta hango tsantsar gaskiya a tare dashi, hannunshi ta kama tana d'an murmushi tace "Faruk ka yafe min, nayi maka laifi a baya , amma yanzu zan gyara kuskure na."

Fuskarta ya shafa yace "wane irin laifi kuma? a iya sanina nidai babu."

"Akwai Faruk."

"To ina jinki."

Qasa tayi da kanta cike da kunya tace "ranar dana fad'a maka kalmar so, wallahi a ranar ba daga zuciyata ta fito ba, amma yanzu na fahimci kaine wanda ya dace naso kuma kafi cancanta dani, Umar Faruk ka yafe min dan Allah, wallahi yanzu ina sonka so na gaskiya nima."

Murmushi yayi tare da janyota jikinshi, "washhhh." ta fad'a saboda zafin da taji daga qasanta.

Da sauri ya kalleta yace " ayya sannu, bara na d'ora miki ruwan zafi kinji."

Yana fad'a ya sauka daga kan gado ya d'auko doguwar riga yana zura, wani kallo ta dinga masa hakan yasa yace "kodai na dawo ne?"

"Ayi me?" ta fad'a tana kallonshi.

" *Jihadi* mana."

Da sauri ta juya baya tana fad'in "a'a ba dani ba, kaje kai kad'ai."

Fita yayi ya d'ora mata ruwan, kafin suyi zafi kuma ya shiga wanka, sai lokacin ne ya fara jin wata irin matsannanciyar qaunar Khairat na sake ratsa kowace gab'a ta jikinshi, sonta kuma ya gauraya da numfashinshi ta yanda baya jin zai iya rayuwa babu ita, rufe ido yayi yana tunano abinda ya faru awa biyu data wuce, tabbas Khairat ta cancanci ya mallaka mata komai daya mallaka a fad'in duniya, ta cancanci ya sota fiye da yanda yake son kansa, tabbas Khairat ta bashi farin cikin da tunda yake a rayuwa bai tab'a shiga kwatankwacinshi ba, hak'ik'a in dai har haka Khairat take to zai dage da addu'a Allah ya bashi ikon yin adalci a tsakaninta da Zuby, dan Khairat da Zuby tamkar moto ne da jirgin sama, murmushi ne mai tsadar gaske a fuskarshi harya fito ya juye mata ruwan.

Tuna irin wahalar da yasha yayi kafin ya samu k'ofar shiga, hakan ma yasa yayi wani tunani, anya kuwa an yiwa Khairat fyad'e, anya maza hud'u sun santa a matsayin 'ya mace, taya wacce maza hud'u suka yiwa fyad'e da k'arfi kuma take tsuke haka, me yasa, me yasa to???

D'aga kafad'a yayi yace " Umar Faruk dai a budurwa ya samu Khairat, dan haka daga yau babu wanda zai sake aibata min matata."

"Gaskiya ne an mata fyad'e." cewar wani b'angare na zuciyarshi.

Da sauri ya tusa hannunshi cikin kanshi saboda bala'in kishin da yaji ya taso mishi, kenan in dai har wasu sun rigashi saninta, kenan duk abinda yaji suma sunji, watak'ila ma fiye da wanda yaji tunda su sune farko, rintse ido yayi sosai zuciyarshi na tafarfasa kamar zata fito ga wani irin haushin su Musa ya kamashi.

Haka kuma ya fito sam ba walwala a tare dashi, duk da ya taimaka mata ta samu ta gasa jikinta tare da tsarkake kanta, amma ta lura da sabon canji daga gareshi, daurewa kawai tayi dan tasan dole zata fuskanci wannan matsin dama, doguwar rigar bacci tasa ta kwanta zuciyarta na rawa tana ji kamar ta sake fashewa da wani kukan, juya mishi baya tayi dan tasan ko ba tayi ba shi zaiyi, bacci harya fara d'ibarta saboda wahalar da tasha kawai taji Umar Faruk ya mirgino da ita ya d'orata akan qirjinshi yana shafata tare da daddab'ata, wani farin ciki ya lullubeta hakan yasa ta qamqameshi ta fara sauke numfashi sai bacci.

Ci gaba yayi da shafarta yana sumbatarta yana sake matsata a jikinshi shima har baccin ya d'aukeshi......

_Me kuka ce masoya?_

πŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ
06/08/2019 Γ  00:06 - Meerahgee❀: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*JIHADI*
_Umar faruk_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•
_My *Heenat*, my *Meelat*, my *BK*, haqiqa kun taka rawar gani a cikin rayuwar Sameera ta yanda harta kawo yanzu data zama wata tsiya, ku na dabanne a gareni kuma na musamman, ina alfahari daku mutanena._
πŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’ž


_Bismmilahir-rahman-rahim_


3⃣8⃣

Ganin yanda take baccin tana sauke numfashi yasa kawai ya gyara mata kwanciyarta ya tashi ya tafi masallaci, bai jima yau dan ana sallamewa ta dawo gida, yanda ya barta haka ya sameta saida ya sake kura mata ido ya kalleta yana ji komai nata na birgeshi kuma yana da kyau kafin ya tangale kanshi da hannu ya sumbaci bakinta, a hankali Khairat ta fara bud'a ido harta sauke akan Umar Faruk, murmushi ya sakar mata tare da fad'in "barka da asuba *madame Faruk*."

Itama murmushin ta sakar masa ta shafi fuskarshi tace "barka da asuba malam Faruk."

Saida ya d'ora bakinshi a kumatunta yace "ya jikinki?"

Zanin rufar dake jikinta taja ta rufe fuska tana murmushi, kallonta yake yace "wai kunya, to bara ki gani."

Yana fad'a ya zame zanin rufar yayi sama da ita bai tsaya ko ina ba saida ya direta douche, bud'a ido tayi ta kalleshi yace mata "akwai ruwan d'umi a butar nan, nasan zasu miki anfani."

Cikin shagwab'a tace "uhum uhum, nifa zafi nake ji."

Sumbatar bakinta yayi yace "hak'uri za kiyi, dole kiyi anfani dasu, inba haka ba kuma."

"Inba haka me?"

"Kedai ki gama kawai ki fito." yana fad'a ya fita ya barta.

Kafin ta dawo harya canza zanin gadon tare dana rufa, cire rigarshi yayi ya kwanta dan wani sanyin baccin ne yake jin yana ratsashi, shigowarta ce yasa ya bud'a ido, yana kallonta harta canza kaya ta fara sallah, tana gamawa kuma ta d'auko kayan karatu tazo ta hau gadon itama, a pillow d'aya kansu yake ta bud'a littafin amma fa yau an samu matsala, saboda rashin bitar karatun da ba tayi ba yasa sam ta kasa kawoshi yau, kallon da Umar Faruk ya mata yasa ta lab'e baki, fuskar nan a had'e yace "kika min kukan nan karyaki zanyi, mena miki to, tun ban dakekin ba?"

Zaune ta tashi tace "yanzu saika dakeni?"

"Me zai hana? ai karma kiyi tunanin zan d'aga miki qafa, dan yanzu muna matsayin malami da d'aliba ne."

Za tayi magana yace "sauka qasa."

Baki ta bud'e tana kallonshi, "dake fa nake magana."

Bata daina kallonshi ba harta sauka tayi tsaye tana kallonshi, qare had'e rai yayi yace "aro min cazar wayarki."

Juyawa tayi ta d'auko cazar ta kawo mishi, "gwiwanki qasa." ya fad'a.

Da mamaki take kallonshi sai kuma ta tuna ranar data sakashi zube gwiwoyinshi qasa a office d'inta, a hankali ta sulale qasa tana ci gaba da kallonshi, sai lokacin ya kalleta ya tashi zaune, kallonta yake sosai yace "meya hana ki kawo karatunki yau?"

Had'e baki tayi tana rarraba ido ta kasa magana, muryarshi taji yace "wasa kika tsaya ko?"

Baki bud'e take kallonshi hakan yasa yace "rufe bakin, sannan ki bani hannunki."

Mik'a masa hannu tayi tunaninta zai taimaka mata ne ta tashi zaune, harara ya wurga mata yace "tafin hannunki."

Da sauri ta juya tafin hannun tana kallonshi kamar sakarya, ganin ya d'aga cazar wayarta zai tsula mata a hannu yasa tayi saurin janye hannun tayi baya da k'arfi, da azama shima ya rik'o hannunta ta dawo gabanshi, tana ganin haka tasa kuka tana fad'in "wayyo Mamie na dan Allah ki taimakeni, kayi hak'uri malam wallahi gobe zan kawoshi, dan Allah karka dakeni, banda lafiya fa."

"Meya sameki?" ya fad'a fuska a had'e.

Cikin turo baki tace "to ba kaine ba jiya da daddare ka...."

Hannu yasa ta rufe mata baki ya zaro mata ido yace "idan har akace muna cikin ajin karatu, to zaifi miki kyau ki manta da abinda ke tsakanina dake, na fad'a miki haka tun farkon fara karatunmu, ki d'auka abinda ya faru jiya da mijinki ne, yanzu kuma kina ajine gaban malaminki."

"Kin fahimta?" ya fad'a da sake zaro mata ido.

"Eh, eh na fahimta."

"Bani hannunki." yayi maganar yana sakin hannunta yana gyara cazar hannunshi.

Yawu ta had'iye sosai ta fure ido ta bashi hannun, "ahhhhhh."

Ta fashe da qara saboda cazar data ratsa hannunta, sake rintse idonta tayi sosai hawaye na zubowa taji yace "bani hannun."

Gani nayi shima ya rufe ido tare da kau da kanshi sannan ya sake tsala mata a hannu, da sauri ta janye hannun tana matsashi da d'aya hannun tana kuka, jin shiru yasa ta ta bud'e ido a hankali hawaye suka sake zubowa, yana ganin ta bud'e ido ya basar ya daidaita kansa kamar baiji komai ba, alhalin ita taji zafin ne a hannu shi kuma zafin yana ratsa zuciyarshi ne, da hannu ya nuna mata gefenshi ta zauna sannan ya sake maimaita mata karutun jiya tare da qara mata kad'an.

Suna gamawa ta haye gadon taja zanin rufa ta kalleshi a lokacin daya tashi yana zura rigarsa tace "in dai sunana Khairat, wallahi daga yau ba zaka sake dukana ba akan rashin kawo karatu."

Dariya yayi lokacin daya saka rigar ya matso kusanta tare da manna mata sumba a goshi yace "haka ake son d'alibi ya zama, fatan alkairi madame Faruk."

Tana kallonshi ya fita daga d'akin tasan wajensu Mama zaije ya gaishesu da kuma Zuby, tashi tayi itama ta canza kayan jikinta tasa hijab sannan tabi bayanshi, d'akin Mama ta fara shiga ita shi kuma d'akin Mama Sa'a, a haka suka dinga sab'ani shi zai shiga can ita ta fito, saida ta gama ta fito zata koma d'aki ta ganshi ya nufi d'akin Zuby, da sauri ta qarasa d'aki ta haye gado tayi shiru, duk qoqarinta saida taji hawaye na neman zubo mata, basarwa tayi kawai ta d'auki wayarta da abin sauraro ta danna wani indian film tana kallo.

Yau ma haka ya fito daga d'akin Zuby duk da qoqarin da yayi ya rumgumeta amma ita sai tayi ta tureshi tana bata so, yana zuwa ya sake cire rigarshi ya kwanta kusan Khairat dan bacci yake so yayi sosai tunda yau lahadi ba aiki, ganin abinda take kallo yasa yace "kina jin me suke fad'a kenan? tunda naga kema 'yar garinsu ce."

Murmushi kawai ta saki ba tace komai ba, zare d'aya abin sauraron yayi yasa a kunnenshi yaji indianci ne, kallonta yayi yace "ki dinga fassara min to."

"To." ta fad'a tare da jinjina kai, suna rumgume da juna suna kallo tana fassara masa wani, wani kuma tayi shiru har bacci ya d'aukesu.

Tun Zuby na had'a abin kari take leken kofar tana ganin takalman Umar Faruk amma shiru ba motsinsu, harta gama taci tayi wanka ta shirya, mutanen gidan suka fara kujuba kujubarsu amma su shiru kake ji, zuciyarta ce ta fara tafasa ji take kamar ta dinga aika ashar ta yanda kowa na gidan hankalinshi zai tashi.

Ruk'ayya ma haka tazo ta tattara kwanukan wajen tayi wanke wanke tayi shara amma koda wasa ko lek'awa ba tayi ba bare taga meke faruwa, *10:25* Umar Faruk ya farka, saida ya fito daga wanka harya shirya kafin ya dawo wajen Khairat ya kalli fuskarta ya shafa, sumbatarta yayi a kumatu sannan ya daddab'ata.

Itama wanka ta shiga ta fito tana cikin shiri kuma Umar Faruk ya shigo da leda a hannunshi, plate ya d'auka ya juye musu abincin a lokacin ta gama shiryawa sannan suka ci, suna idawa ya kalleta yace "zan fita gari, ki kula min da kanki kinji, ina sonki *alkairina*."

Rumgumeshi tayi tace "nima ina sonka jarumina."

"Yaushe na cancanci wannan sunan?" ya fad'a da zolaya.

Cikin kunya tace " *daren jiya*."

Sake qamqameta yayi sosai yace "ashe jarumtata har takai haka? ai kuwa zan qara himma."

"Lahhh, idan ka qara himma zan iya mutuwa fa, wallahi ba qaramar wahala nayi ba jiyan nan."

D'ago fuskarta yayi yace "ki fad'a min sirrin abinda naji jiya, danni na kasa yarda cewa wasu sun fara..." sai kuma yayi shiru.

"Sun fara kafin kai?" ta qarasa masa.

Kai ya d'aga mata alamar Eh, cike da tabbatarwa tace "tabbas wasu sun rugaka, amma ni bansan komai ba."

Shafar jikinta ya fara tare da mata wani salo yana sumbatar wuyanta dan yaji zafin maganarta, kawai baya so ta fahimta ne, cikin rad'a yace "amma fa ni ban tabbatar ba, kawai dai nasan nasha wahala kafin na samu hanyar wucewa izuwa duniyar Khairat mai wuyar mantawa."

Idonta ne suka kawo qwalla ta kalleshi a marairaice duk tayi kalar tausayi tace "dan Allah ka fad'a min gaskiya Umar Faruk, shin nima zaka iya kallona da darajar da zaka iya kallon wacce ka samu a matsayin budurwa? Umar Faruk zan shiga tashin hankali da damuwa idan ka juya min baya, ba zan iya jura rasaka ba domin kuwa haka na taso tun farko, ina samun duk abinda nake so, bana so na rasaka Umar Faruk zan iya mutuwa, wallahi mutuwa zanyi idan ka wulak'antani ko ka rabu dani, Umar Faruk mutuwa zanyi ba zan iya rayuwa ba."

Ta qarashe da sulalewa qasa tana fashewa da matsanancin kuka, ita kanta bata san lokacin da take fad'an maganganun ba ta daisan kawai daga zuciyarta suke, shi kanshi ji yayi kamar zaiyi kuka amma dakkakiyar zuciyarshi ba zata bari ba , sunkuyawa yayi ya d'agota ya fara share mata hawayen kafin yace "Khairat, ki kwantar da hankalinki dan Allah ki sawa zuciyarki nutsuwa da salama, in dai har kin yarda da cewar kina samun duk abinda kike so, to ki yarda kin samu Umar Faruk, Khairat ki d'auka Umar Faruk ya zama naki, kuma ba zan tab'a juya miki baya ba saboda kin zama rayuwata nima."

Cikin kuka ta kalleshi tace "ka tabbatar?"

"Na tabbata Khairat, babu abinda zaisa na gujeki, muna tare har qarshen ratuwarmu."

Dariya tayi tare da kamo kanshi tasa bakinta a nashi, saida taji ya fara birkicewa kafin ta barshi, cikin muryar galabaita yace "ni na wuce."

Hannunshi data rik'e yasa ya juyo yana kallonta da idonshi da har sun canza, "ya dai?" ya tambaya.

Langab'e kai tayi tace "ina so ne na maka kallon qarshe, dan daga yau zamu nesanta na d'an wani lokaci."

Shi kam harga Allah harya manta da yau ne, marairaicewa yayi ba tare daya nuna mata rashin jin dad'in hakan ba a fili yace "da nasan haka zan samu Khairat, da banyi qasa a gwiwa ba wajen wuce wannan wurin."

Cikin dariyar mugunta tace "nima da nasan haka zan sameka da jarumta, da ban yarda na baka ba ko jiya."

"Ashe dai na bada tsoro." ya fad'a yana shirin ficewa daga d'akin.

"Kawai ma, ba wani tsoro, kara nake maka dan kar kaji ba dad'i idan nace maka *ragon namiji*, amma ba komai da naji."

Juyowa yayi yana mata wani mugun kallo, k'ofar d'akin ya tsaya ya mik'o mata hannunshi yana murmushin mugunta yace "zo baby."

Ita kam da bata fahimci komai ba takawa tayi a hankali ba kamar yanda take tafiyarta ba tana d'an cije lips saboda ciwon da take ji a qafarta da qasanta, saida ta kusa kaiwa gareshi ya kauce da sauri ya shigo d'akin ya sake mik'a mata hannu yana fad'in " so nake naga kin taho kamar yanda kika saba da k'arfi."

Kai kawai ta girgiza masa ta sake tahowa a hankali, bata tantance ba taji ya fizgo hannunta ta fad'a qirjinshi, wata qara ta saki da k'arfi dan ji tayi kamar qafarta ta cire hakama k'ugunta, rufe mata baki yayi yace "me kika ji?"

D'agawa tayi daga jikinshi ta koma kan kujera ta zaune tana hararanshi, dariya kawai yake mata harya zo kusanta ya danna mata sumba a goshi ya tallabo fuskarta yace "ina sonki Khairat, ki kular min da kanki, saina dawo."

Janyo fuskarshi tayi ta sumbaci bakinshi itama tace "ina sonka baby, ka kula min da kanka, kuma karka bari wata ta qwace mana kai."

Dariya yayi yaja dogon hancinta yace "kishi ko? toni me zanyi da wata bayan Allah ya bani ku."

Bye bye ya mata ya fita, gyara zama tayi ta rumgume hannayenta ta shiga duniyar tunani, da farko kishi ne ke ciciyarta na abinda ya fad'a, amma sai tayiwa kanta karatun tanutsu ta shiga tunanin sabbin hanyoyin da zata samu zuciyar Umar Faruk, dan yanzu itama sonshi take so na gaskiya, sai inda k'arfinta ya qare a kanshi.

****************

Mamie ce zaune tayi tagumi Mammie ta sameta a wurin, harta zauna bata sani ba saida ta d'aga murya wajen magana, "ke, waime kike tunani?"

"Na'am Mama, ba komai."

"Ya za kice ba komai bayan ga komai na gani, fad'a min meke faruwa?"

Ajiyar zuciya ta sauke tace "Mama, sai jiya na tuna da wani *kuskure* da nayi mai girma a rayuwa wanda ba lallai yanzu ya gyaru ba."

"Wane irin kuskure ne wannan da ba zai gyaru ba?"

"Mama, jiya Khairat ta kirani take fad'a min da kanta tayi girki, Mama abin takaici shine dad'i take ji saboda tayi girki d'aya tak a gidan miji, tun farko dana koya mata da duk haka bata faru ba, yanzu bansan ya za tayi ba gashi tana da kishiya, Mama nayi kuskure sosai a game da rayuwar Khairat, tabbas bamu rik'eta ba kamar yanda ubangiji yace mu kula da 'ya'yanmu ba, rashin iya girki ba qaramar matsala bace a gurin 'ya mace, shi yasa nake tunanin abinyi."

Saida Mammie ta jinjina al'amarin kafin tace "akwai mafita har yanzu, duk da tayi aure ba zai hana ki jata a jikinki ba sannan ki koya mata girki."

"Nima haka nace mata jiya Mama, amma kinsan halin Khairat."

"Karki damu, ni zan mata magana saita fara zuwa nan kina koya mata in mijinta ya amince."

"Yawwa Mama na gode."

"Karki damu."


***************

*16:30* Khairat na zaune tana waya da Papa, tambayarta Papa yayi ita kuma ta fara kora mishi bayani kamar haka "wallahi Papa ba komai, Faruk yana sona kuma nima ina sonshi, kuma kaga zamu zo tare dashi Germany, ina farin ciki da kasancewarmu tare, kuma kunga yana koya min karatu kullum, yanzu haka na
Showing 105001 words to 108000 words out of 186119 words