shigo”

Ita dai tun da take bata taba ganin tukunyar shisha a fili ba sai yau, tana dai ganinta a fina fina kuma ta san abun da ake yi da ita domin wadanda ake nunawa rike da ita sha suke suna fitar da hayaki.

“I'm Adam by name, please ki shigo mana Hurriya”

“Na gode zan kira yayana ya zo ya kai ni gida”

“So you get phone please saka min number ki a nan”

Yayi picking latest IPhone dinsa dake cikin motar ya cire key ya mika mata. Ta kalli wayar ta sake kallo sannan ta kai hannu ta karba without saying anything ta saka number yayanta daman daga numbersa sai ta Appa da Ammanta ta haddace a kai. Kara wayar ta yi a kunne

“Hello Yayana.. Ka zo ka dauke ni please ina jin tsoro kuma ina bakin titin gurin Event din ba kowa”

“Me ya fito dake to?”

“Ni na gaji ne bana son zama ciki gida nake so, kuma su ba su gama bikin ba babu wanda zai kawo ni”

“Okay ki koma ciki gani nan zuwa”

“Toh Yayana ka yi sauri ance I'm not safe here”

“Waya ce haka?”

Ta kalli mutumen dake jiran ta ba shi wayarta.

“Adam”

“Wane Adam”

“Ni ma ban san shi ba, yanzu na hadu da shi”

“Okay ina kusa da gurin koma ciki zan zo na dauke ki”

“Toh”

Ya kashe ya mika masa wayarsa.

“Thank You”

Ta juya ta cigaba da tafiyarta har ta koma ciki, wannan karon masu gadin ba su hanata ba domin sun gane ita ce ta dazun. Ciki ta koma ta samu gurin inda ba za a ganta ba ta zauna ta zubawa kofar shigowa ido Yayanta kawai take son gani. Tana hango Adam ya shigo ta kara boya kamar ta san ita zai fara nema, sai ko ya hau rabon ido yana neman inda zai ganta, gaba daya ta tafi da shi, a gurinsa duk abun da take tana masa yanga ne saboda ta ga tana da kyau. Ta yi rabin awa a gurin sannan ta tashi ta nufi kofa kamar mai shirin sata ta fice tana duddubawa ko Yayanta ya zo, aikuwa ta yi sa'a tana fitowa motarsa na shigowa harabar da sauri ta nufi shi yana fakawa ta bude front seat ta shiga.

“A tsorace kike Hurriya me ya faru?”

Ya tambaya yana kokarin kashe motar.

“Ba komai ni gida nake so”

“Ina Khairi ita da waye a gurin cikin yan gida?”

“Yaya Namra kawai na gani, sauran duk kawayenta ne ban sansu ba”

Ya duba agogo hannunsa.

“Su ma ai ya kamata ace kowa ya tafi gida yanzu, Je ki kirata”

“Yaya ba zata fito ba, kuma zata ce na bata mata birthday fa”

Ta saka mishi kuka domin ta san halin Khairy ko a banza ta dora mata laifi balle kuma da dalili.

“Karki ce ni nake kiranta, ki ce wani ne yake kiranta, idan ba haka ke ma sai na bata miki rai”

Ta fita motar ba dan ta so ba sai dan Yasir yayi mata dole, ciki ta koma ta isa har gurin da Khairi take tana rawa ana zuba mata kudi ta rikota ta kai bakinta kunneta.

“Wani yana kiranki a waje”

“Waye?”

“Ban san shi ba”

“Je ki ce masa ya shigo ciki”

Hurriya ta juyo, ita dai bata san yadda aka yi masu gadin suka bar Yasir ya shigo ba, sai hangon shi ta yi ya kankance ido yana kallon mutanen dake ta kai da kawo a gurin. Ta nufi shi ma ya nufo gurin Khairy da bata san me ke faruwa ba sai rawarta take ana zuba mata kudi. Galala Hurriya ta yi tana kallonsa ganin ya wuce ta ya nufi gurin Yayarta, yana isa be tsaya komai ba ya dauke Khairy da mari ya fara dukanta kamar an zugoshi.

“Wannan iskacin ne birthday? Kin mai da kanki kamar yar kafirai? Babu mutum daya mai mutumci a nan kim hada maza da mata ana shashanci ki cw birthday? Daman sai na hana Hajiya ta ce sai an yi saboda kawai ku ja mana zagi”

Dukanta yake ta ko'ina wadanda suka san yayanta suka fara ficewa da sauri, wasu suka suka fara kai mata dauki ciki har da ma'aikatan gurin.





HAJIYA KALTUME.

“Hello”

Hajiya Fatee ta amsa daga dayan bangaren.

“Hajiya ina ta kira baki daga ba”

“Yanzu na shigo dakin, kin gan ni garin sauri har faduwa na yi kamar an turo ni”

“Subhanallahi, sannu daman ina ta kira na ce miki Fadeel zai zo”

“Ya ma zo har ya tafi, ya ce wai kin ce ya zo ya kai Khairi bata samu mota ba”

“Eh haka na ce masa saboda na samu ya zo, wato Hajiya akwai abun da nake tunani sai dai gan gama yanke shawara ba sai kin zo, shiyasa da kika fada min zata birthday na fara da wannan”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi tana murza kafarta dake zogi.

“Toh Hajiya Fatee kenan wato idan hagu ta ki a koma dama”

“Kwarai kuwa, idan ba zai iya rabuwa da wacan bakar karyar ba da ta dafa ta ba shi ya shanye, to ya karo wata idan ya auro wanda nake so ko da bakinciki ai sai ta bar gidan”

“Wato Hajiya Fatee magana nan ba ta waya ba ce, bari dai sai na zo kawai ko kuma idan kin shigo”

“Toh shikenan Hajiya sai mun hadu”

Ta sauke wayar tana murmushin jindadi, domin an yi tsara akan gaba Khairy ta kamalla karatu daman kuma can tana sha'awar hada jini da aminiyarta ko dan karfafa zumuncinsu.


**** **** ****

Hajiya Fatee ma da murmushi ta sauke wayar, sannan ta fito falo ta zauna tana ta sake saken yadda zata kara bullowa lamarin. Domin ta san ba karamar wahala zata sha ba kamin ta samu kan danta Fadeel ya yarda zai aure, a ganinta mallakar da Afrah ta yi masa ba karama ba ce ta yadda ta hana idonaa ganin ko wace mace sai ita kadai.

“Sallamu Alaikum”

Ta dago tana amsa masa.

“Wa'alaikassalam har ka dawo?”

“Eh ko da na je Already ta wuce ma”

Ta yi tusar baki tana jin rashin dadin bw tarardar Khairy ba.

“Aikin banza, zuwan kawai ka yi kenan”

Ya yi dariya yana saka keys din hannunsa ya taba kunnensa.

“No na sauke kanwarta yar farar nan ita ce bata samu mota ba, sai na kaita”

“Oh yar makauniya? Ko yar wajen Hajiya Nafisa?”

“Tana gani Hajiya fa”

“Amman sai da gilashi ai, ita da makafi duk daya, Allah yasa dai ka shiga ciki”

Ya yi fuskar mamaki.

“No why would i?”

“To wish her happy birthday mana, kuma Allah yasa dai baka je mata hannu sake ba”

Ya zauna yana dariya.

“Hajiya Khairi kanwata ce fa, kuma ban ma san tana birthday ba, sai da kika kira ni kika fada min naje na daukota, ban shirya komai ba”

“Toh sai ka shirya wani abun ka kai nata daga baya, ko tana kanwarka ai tana sin kyautatawa”

“Yanzu kuma ai ya wuce, sai da mu hari gaba kuma”

Ya mike tsaye yana cigaba da wasa da keys din hannunsa.

“Bari na tafi na bar aiki a office”

“Wane irin aiki yanzu da yamma, wai shike nan ba dama na zauna na yi hira da kai sai ka ji kamar kama kan kaya, yar hirar ma sai a hana ka?”

“Waye zai hana ni hira dake duk duniyar nan Hajiya?”

Ta tabe baki ta dauke kai.

“Dan Allah karki ce Afrah bata ma san na zo nan ba, ki daina dora mata laifi kina daukar alhakinta ne kawai”

“Kullum ai ni mai daukar alhakinta ce, daman ta ina Afrah zata yi laifi a gurinka? Yar zinari, ina dai son ka sani ni uwarka ce ko kana so ko baka so, matarka bata fi ni matsayi ba”

“Ai ba za a ma hada ba, babu mai matsayin uwa a duk duniyar nan Hajiya, amman duk da haka tana da nata iyaka mata ma tana da muhallinta, ban san miyasa kika tsani mutanen Afrah ba, yarinyar nan tana mutuntatako daidai gwargwado tana miki biyayya”

“Na ji dan Allah kama hanya ka tafi Allah ya bada sa'ar aiki”

Rokonsa take har da hade hannaye. Ya sauke ajiyar zuciya cikin yanayi na damuwa ya koma ya zauna domin ba zai iya barin gidan ran mahaifiyarsa a bace ba.


Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/3, 4:06 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 9*


“Ka tashi ka yi tafiyarka bana bukatar zaman ka daman ai bana da muhimmanci a gurinka, da ina da muhimmanci ba zaka wulakanta ni ba”

Maganarta ta sake sukarsa gaba daya sai mood dinsa ya sake sauyawa. Sometime baya ganewa rikicin Hajiya Fatee gashi bata yi tsufan da zai ce ya kai ace bata gane wasu abubuwan amman sau ta rika furta kalama anyhow.

“Hajiya yanzu laifina na rashin bawa Khairi kyauta ne? Zan je na siye na kai mata shi ke nan”

Ta yi kamar bata ji ba har ya mike tsaye ya fara tafiya sai kuma ya juyo yana kallonta domin a lokacin ne wani tunani ya zo masa.

“Hajiya me yasa kika damu da zancen siyawa Khairi gift?”

Ya tambaya with little confused domin shi be ma tana jin ta yi maganar birthday Khairi ba sai yau kuma ta nuna damuwarta akai sosai.

“Dalili ba na birthday ne ba kawai, ina ta karkata ha hankalinka ka gagara fahimta, saboda hankalin gaba daya yana can gurin matarka”

Ya koma ya zauna yana cigaba da kallonta irin kallon nan dake nuna karin bayani yake nema.

“To me nene dalilin Hajiya?”

Ta juyo ta fuskance shi.

“Magana muka yi da Hajiya Kaltume ganin Khairi ta gama makaranta yanzu, kuma ba wani tsayaye take da shi ba zamu hadaku domin aminci na da Hajiya Kaltume ya kamata ace akwai auratayya a tsakaninmu ya kamata ace tarayyar ta wuce abokanta”

Wani kalar faduwar gaba ne ya same shi, jin yadda Hajiya Fatee ta gabato masa da maganar aure kai tsaye abun da be yi tsammani ba, domin ba shi da ra'ayin aure mace fiye da daya.

“Amma....Hajiya....”

Kamin ya furta ta tari numfashinsa.

“Aha... Ai sai ni ita da yake tana da yar albarka tana mata magana ta amince ita da take mace balle kuma ni da nake da ďan namiji, amman gashi nan zaka fara musamin gashi nan tun ba aje ko'ina ba zaka fara cewa ba haka ba”

Ya saka hannu daya ya shafa kansa gaba daya sai ta ruda masa tunani ya rasa ta ina ma zai bullowa lamarin.

“Ai na sani yanzu zaka fara lissafa min cewar baka da ra'ayin aure mace fiye da daya ko?”

Ya dago ya kalleta yana shafa fuskarsa sai dai be ce mata komai ba ya mike tsaye.

“Hajiya zan tafi gida”

“Toh a gaishe da sarauniya daman ai karshe na san haka za a rabu”

Ya sake kallonta cikin yanayi na damuwa sannan ya fice daga falon. Kamar marar lafiya haka ya isa gurin motarsa ya bude ya shiga, yayi zaman minti goma a ciki sannan ya murza key ya juya motar ya fice daga gidan. Kamar baya son driving haka yake tuka motar a madadin ya karasa gurin aiki sai ya koma gida, domin gaba daya jin yake jikinsa ma babu dadi. Tun daga kofar falon ya jiyo sautin muryar Afrah tana rera karatun qur'ane, a fakin ta zauna kan cushion ya dafa kansa gaba daya Hajiya Fatee ta gama ruda masa tunani, shi ko aure zai kara Khairi bata cikin irin matan da yake so, balle ma ba shi da burin na auren mace fiye da daya. Matarsa tana da duk wasu qualities da yake so a jikin mace, kuma suna zamansu lafiya tana masa biyayya daidai gwargwado gata da addini, why Hajiya zata rikita masa lissafi yanzu da wani zancen aure, sanannen abu ne Hajiya bata son matarsa kuma babu wani abu da zai iya yi akan haka sai hakuri.

“Rabin raina?”

Ya dago ya kalleta murmushin da yayi arba da shi a fuskarta ya saka shi jin sanyi, daman a duk lokacin da zuciya ta yi arba da wanda take so, idan ta kalleshi farinciki take ji. Kusa da shi ta zauna ta kai hannu ta shafa kansa zuwa bayansa.

“Yau kuma ta ina aka taba angona? Gurin aikin ne ko friends ko kuma a hanya”

“Ba ko daya kawai dai bana jindadi ne”

A take hankalinta ya tashi ta saka hannunta cikin rigarsa tana taba jikinsa.

“Me ya same ka? Fever ko headache?”

“Ba rashin lafiya ta jiki ba, rai na ne babu dadi”

Ta mike tsaye ta cire hijabin dake jikinta ta aje ta nufi kitchen sai ya bi kyakkyawar surarta da kallo, skirt din da ta saka irin wannan ne mai bin jiki gashi Allah ya hore mata baya. Tashi yayi ya bi bayanta tana kokarin dauko ruwa a fridge ta ji ya shafa gurin da ya fi ko'ina daukar hankalinsa.

“Wannan kwalliya haka ai sai ki mantar da ni damuwata ma, ni yanzu kin kwashe min tunani gaba daya kin bar kwakwalwar fanko”

Ta saka dariya tare da rufe fridge din.

“Kai da ba wani nan wayo ne dan kar na tambaye damuwar kuma sai na tambaya”

Ya juyo da ita ya rika bayanta yana kankance idonsa.

“To ai na manta, kin taba ganin an bada abun da babu?”

Da sauri ta ja baya shi kuma ya cire hannunsa a jikinsa sakamakon jin motsin yaransu da suka yi, ta nufi gurin cups shi kuma ya juya ya tarbeshi yana murmushi.

“Daddy...”

Ya daga ta farin din sannan ya daga mai binta ya aje ya sake daga na ukun da yake namiji ya aje.

“Daddy sannu da zuwa”

“Yauwa ashe kuna cikin gidan ko? Da na shigo ban ji motsin yarana ba”

“Daddy baka duba dakin mu ba da zaka gan mu ai, Aiman ne ya leka windows ya ce Daddy sai muka gano ka dawo”

Babbar data fi su wayo ta fada, ya rage tsawo ya shafa kansu yana murmushi.

“Na manta ai ban duba dakin ba, laifin Momy ne ita ce ta dauke min hankali”

Ya dago ya kalleta yayinda take mika masa kofin ruwa sai ya kashe mata ido yayi mata alama da bayanta ba tare da yaran sun gani ba. Dariya ta yi

“Allah ya shirya min mijina”

Daga yaran har shi suka amsa da Ameen ya ba su hannu suka tana sannan ya sanye ruwan ya rika hannunsu suka fice daga kitchen din.



KHAIRI POV.


Hajiya Kaltume ta sauko da saurinta cike da karfin hali domin har yanzu kafarta ciwo take. Cikin tashin hankali ta kalli Khairi da Yasir ya gama kumbura mata fuska.

“Lafiya wannan kuka kamar an yi mutuwa?”

“Da mutuwa da abun da Khairi ta yi yau duk daya Hajiya. Akan wane dalili zata saka tufafi jiki duk a waje da sunan birthday, daman sai da na ce kar ta yi party nan a waje amman kika goya mata baya, gashi nan na je na ga babu kowa a gurin sai tarin yan iska marasa sanin darajar kai, ita kuma ta saka tufafi kamar wata karuwa”

“Haba Yasir haba Yasir saboda wannan sai ka nemi raunata nata mata jiki? Idan ma bata yi daidai ba ne kamata ka mata duka har haka ba”

Da mugun mamaki Yasir yake kallon Hajiya Kaltume, ganin tana kokarin kare Khairi instead of ta yi mata fada.

“Hajiya kin san abun da wannan abun zai janyo? Idan hotunan birthday nan suka yi yawo mutumcin Appa da naki duk zai zube a idon mutane, wannan abubuwa da Khairi take yi kina kyaleta ba tarbiya ba ne, tun abun nan yana ga kawayen banza har ta kai ita da kanta yanzu ta fara kwaikwayon rayuwarsu”

Hajiya Kaltume ta nufi Khairi dake ta kuka ta dagota tana duba fuskarta.

“To sai ka zo ka nuna min yadda zan yi tarbiyar, idan tarbiya ce ban iya ba, kai ya taka take? An fada maka doka na gyara tarbiya ne? Fisabilillahi ko da Khairi ta yi ba daidai ba fada ba zai isa ba sai ka sauya mata fuska haka ko'ina jini kamar mai fada da sa'ansa? Bana goyon bayan ta aikata abun da zai zubar mana da mutumci amman wannan hukuncin naka ba zan lamunta da shi ba, wata kila ma cikin mutane ka rufe ta da dukan”

Dubanta yayi irin duban da magana ta makale masa a makoshi yake ganin kamar furta ma ba shi da amfani, ya kalli Khairi da har lokacin take zaune a inda ya wurgar da ita tana kuka ya dauke kai ya fice daga falon.

“Oh ni wannan Yasir sai zuciya ta yi ta dibansa yana kai miki hannu kamar wanda ta kashe masa wani”

Cikin kuka Khairi ta ce.

“Hajiya ba laifinsa ba ne, Hurriya ce ta fada masa yana shigowa dakin taron ya hau ni da duka a gaban mutane sannan ya fito da ni ya saka ni a mota yana ta zagina”

Hajiya ta zauna a kujera tana hade fuska.

“Ja'irar yarinya wato ita nan har ta iya munafurci, to yayi kyau zata ko ci ubanta a gidan nan, ke ma kuma da laifinki miye na zuwa ki yi wannan shigar rabin jikinki duk a waje, Fisabilillahi Khairi wani
Showing 24001 words to 27000 words out of 215510 words