account ne, ya fara gani, dayan kuma a bauchi yake shi kuma yace min turo masa hotunan aka yi, na bukaci ya fada min account din da na bincika sai na samu an goge account din”
“Kana aje wayar nan, ka duba list din mutanen da suka dora hotunan karka damu da yawansu ka turo min su, tare da sunanyen gidanjen jaridun, ka hado min da account number dinka”
“Okay Sir”
Ya sauke wayar.
“Za su san sun taba mai gata, na miki alkawarin farinciki Hurriya zan cika miki shi... ”
Ya fada sannan ya nufi madubin dake bandaki ya dora wayar ya cire tufafinsa ya sakarwa kansa shower. Ya bata minti arba'in a bandakin sannan ya fito yana rike da wayarsa jikinsa kuma na daure da tawul.
“Good Nafi'u”
Yayi forwarding sakon zuwa mabanbanta gurare sannan yayi waya da mutane daban daban. At the end ya kira Namra.
“Hello Captain”
“Wace asibiti aka kai Adam? Kanen Salim”
“Ban sani ba, ya jikanka?”
“Bincika min yanzu”
“Toh”
Ya aje wayar ya dauki wani tawul din ya goge jikinsa, sannan ya zauna gaban madubi yana hararo abubuwa da yawa. After like one hour yana zaune kan carpet bayan ya sallame sallah wani kiran ya shigo a wayarsa bayan na calls din dake ta shigo masa na yan'uwa da abokan aiki masu son tambayar jikinsa. Amman be amsa kiran kowa ba sai na Namra.
“Yana yana asibitin Yariman Bakura, layin ya hadurra”
“Good”
Ya yanke kiranta tun kamin ta kara cewa komai, ya shiga whatsapp dinsa ya sake sauke hotunan da Salim ya turo masa, ya yanke iya gurin da fuskar Adam take ya turawa wata number tare da address, sannan ya fito whatsapp din ya shiga contact dinsa ya nemo number the same person da ya turawa sakon ta whatsapp.
“Hello Sir”
“Uzairu na turo maka hoto da addreshin wani dan'iskan yaro yanzu a whatsapp, ni ya taba so the fight is between me and him.. Ka duba address din ka dauki mutanenka ki shiga cikin asibiti ku dauko shi ku aje min shi wani gurin da babu haske kuma babu rahma, ku masa doka irin dukan da idan na masa tambaya zai ba ni amsa a take amman ban ce ku kashe shi ba, ku aje shi a gurin for 10 hours”
“Yes Sir... ”
Ya sauke wayar, sannan ya amsa dayan kiran daya fito daga bachi.
“Yeah good so nake ku kama mai gidan jaridar ku bincike shi a ina ya samu hotunan, at the end ku sa ya rubuta cewar sheri aka yi mata kuma yana neman yafiyar Hurriya, ku saka yayi hakan tun a cikin office din ku idan be yi haka ba ku karya kafarsa”
“Amman Captain me yayi maka?”
“Yarinyar da suka batawa suna yarinya ce mai tsada she is innocent, please karku ragawa kowa a gurin”
“Subhanallahi, aiko za su ga aikin DSS”
“Thank You My friend”
Ya sauke wayar ya amsa wata wayar, haka yayi ta bata umarni a inda umarninsa suke jira a inda alfarma yake nema sai ya roki ayi masa haka.
HURRIYA POV.
“Daure ki sha tea ne kuma ba mai yawa ba”
Hajiya Binta na lalabata tana hada mata tea. Gwaggo ta ce.
“Babu yadda ban yi da ita ba amman ta ki cin komai tun safe har yanzu”
“Bana iya cin komai ne, ko na ci bana iya hadewa”
“Hurriya wannan abun duk zai wuce, wata kila an buga an buga an ga babu sa'a ne shi ne aka bullo ta nan, amman duk wanda ya sanki ya san ba zaki aikata ba, babu wanda zai yarda kawai ana son a jefaki a damuwa ne, dan haka karki bari damuwar da suke son jefaki ta tasirantu akanki karbi ki sha”
Ta mika hannu tana lalaben kofin ta karba ta kai bakinta ta kurba kadan sai ta gagara hadewa.
“Hajiya bana iya hadewa”
Hajiya ta karbi kofin ta rike tana kallon jikarta cike da damuwa sosai a fuskarta.
“Jibi zan wuce Ummara zan miki addu'a mai karfi a can, da yardar Allah wanda ya aikata miki haka ba zai sake sanin rahma a rayuwarsa ba”
“Amin Hajiya”
Gwaggo ta amsa, sannan suka daga kai gaban dayansu suka kalli kofar dakin da aka turo. Cikin wani irin yanayi kamar na kunya kamar tsoro Yasir ya shigo dakin fuskarsa a raunane.
“Yasir”
“Na'am Hajiya”
Hurriya ta sauke kanta kasa duk da kasancewar bata ganin kowa tana jin kunyar aga fuskarta saboda an yada tsiraicinta. Yasir ya tsaya daga tsaye suka gaisa da Hajiya da Gwaggo be ce da Hurriya komai ba ita ma bata iya dagowa ba balle tace masa wani ba sai hawaye take.
“Appa ya ce na zo da Hurriya”
“Ka zo da ita kuma? Be san tana asibiti ba?”
“Ya sani, yace na yi magana da likitan ya bata sallama”
“Saboda me? Be san idonta ya samu matsala ba?”
“Ya sani Namra ta fada mana komai, Hajiya idan za ayi mata aikin idon a ba nan za'ayi ba kuma abu ne da yake bukatar shiri da tantance inda ya kamata da kuma likitan da ya dace”
Hajiya zata sake magana Gwaggo ta dakatar da ita
“Je ka karbo sallamar, zamu tafi da ita mu ga iya gudun ruwansa amman ba zan bar Hurriya ta zauna a gidan nan ba har bada...!”
Yasir ya juya ya fita daga dakin ba tare da yace komai ba, Hajiya Binta kuma ta hau masifa ta daga wayarta ta kira shi kiran be shiga ba. Misalin karfe biyar da mintuna Yasir ya faka a harabar Appa, Gwaggo ta fara fita sannan ta fito da Hurriya Hajiya Binta ma ta fito tana kara shiryawa duk wani abu da ďanta zai yi. Hurriya ta kama hannun Gwaggo ta rike da karfi.
“Gwaggo tsoro yake kar Appa yace be yafe min ba”
“Ko da ya fada ba zai kama ki ba, domin ba ki aikata ba kuma Allah mai adalci ne”
Cikin karayar zuciya da duhun idanuwa Hurriya ya shiga bangaren na Appa Gwaggo tana mata jagora komai bata iya banbance komai a yanzu. Yanayin yadda ta ji numfashi na tashi ya karantar da ita falon cike da mutane da bata san su waye ba, yan gidansu ne kadai ko kuma dai duka familynsu da suke garin. Me Appa zai fada akanta shi ne abun da ya fi tsorata ta, da lalabe ta zauna a falon kusa da Gwaggo, hawaye na mata zuba, ta wani bangaren tana gode Allah da bata iya ganin komai, a yanzu da bata san da wane ido zata kalli Appanta ba.
“Hurriya...!!!”
Gabanta ta kasa amsa kiran da Appa yayi mata gabanta sai bugawa yake da karfi.
“Kina da wata hujja ta kare kanki akan abun da muka gani tsakanin jiya zuwa yau?”
Ta yi shiru, Gwaggo ta ce.
“Ka san dai ba zata aikata ba...”
“Gwaggo dan Allah ki yi hakuri ki bari ta amsa min”
Appa ya bukata cikin yanayi da ke nuna shi ma yana cikin damuwa kwatankwacin wanda Hurriya take ciki.
“Appa akai ni na yi alwala”
Tana fada ta mike tsaye tana kuka.
“Ba sai kin rantse ba abun da duk ba halinki ba ba zaki aikata shi ba”
Hurriya ta girgiza ma Hajiya Binta kai ba dan tana ganinta ba.
“Idan ban rantse ba babu wanda zai yarda da ni, ni ma kuma ba zan samu sukuni ba, dan Allah ku kai ni bandaki”
Yasir ya kalli Ruma.
“Tashi ki kaita”
Ruma ta tashi ta rika hannunta suka shiga bandakin dake cikin falon, Hurriya ta yi alwala ta fito ta bukaci a bata kur'ane.
“Bari zaka yi ta yi rantsuwar nan Tsoho?”
Appa ya kasa amsawa mahaifiyarsa, shi ma ji yake kamar Hurriya ba zai aikata hakan ba sai dai zuciyarsa ta kasa natsuwa. Yasir ya tashi da shiga bandakin da Hurriya ta fito yayi alwala ya shiga bedroom din Appa ya dauko mata alkur'ane ya kama hannu ya mika mata, shi kansa idan ta rantse zai fi jin natsuwa, domin ya shirya ui mata mummunan hukuncin idan har ta tabbata ta aikata. Hurriya ta rike qur'anen da dayan hannunta sai ta dora hannunta na dama a saman kur'ane ta dafa.
“Na rantse da littafin nan, abun da yake cikinsa da wanda ya aiko da shi ban aikata ba Appa”
Ta karasa cikin kuka... Gwaggo ta saka kalma shahada.
“La'ilaha Illaha Muhammad Rasulullah”
Sai gaba daya falon ya amsa suka karasa a tare.
“Sallalahu Alaihi Wassalam...”
Appa ma ya sauke kansa kasa ya fashe da kuka, babu wanda be yi hawaye ba a falon kuma babu wanda be tausaya mata ba ciki har da Momy. Yasir ya sa hannu ya karba yana hawaye da murmushi a fuskarsa, yar'uwarsa ta tsarkake kanta a gaban kowa hakan ya kwantar masa da hankali yanzu kam ya yarda hundred percent bata aikata ba.. Appa ya dago hawaye na zubowa daga idonsa ya mika mata kamar ance masa tana ganinsa.
“Zo nan gareni yata, fada min wa kika tarewa farinciki ya aikata miki haka?”
Hurriya ta fara takawa ta inda take jiyo sautin muryarsa tana kuka tana lalaben hanya, Yasir ya rika hannunta ya karasa ta ita gurin Appa, hannayensa ta fara kamawa sannan ta zube kasa a gabansa ta kwantar da kanta a kafarsa.
“Allah ya tsinewa wanda ya aikata miki wannan abun Hurriya, ba zai gama lafiya ba, bakinciki da ya saka mana da neman bata miki da sunan gidan nan Allah ya ninka masa shi...”
Kowa ya amsa da Ameen ban da Khairy da Namra dake ta kuka kai ka rantse da Allah su aka aikatawa haka ba Hurriya ba.
“Ba zan bar maganar nan ba, sai na yi shari'a da yaron nan, ya ci mutuncina ya ci mutuncin ƴata ba zan kyale shi ba”
“Ni ma na yi wannan tunanin Appa, na kudirta a raina idan har ta tabbata Hurriya bata aikata abun nan ba, ba zan kyale maganar nan ba”
Yasir na aje aya Hajiya Binta ta ce.
“Da kun kyauta daman be kamata a kyale ba”
Momy ta tashi ta fice ba tare da tace komai ba, Ruma ta bi bayanta. Gwaggo ma ta mike tsaye fuska a daure ta ce.
“Zan tafi gida, kuma zan tafi tare da Hurriya saboda a can zata samu kulawa”
Appa be ce komai ba bayan shafa kan Hurriya da yake, har Gwaggo ta iso gurin ta kama hannunta suka fice. Sai da suka kusa isa gate sannan Yasir ya cin musu da mota ya bukaci su shigo ciki ya sauke su gida, Gwaggo kamar bata shiga ba saboda yana dan Hajiya Kaltume sai kuma ya daure ta shiga saboda saukaka Hurriya wahalar fita titi zuwa neman abun hawa. Back seat suka shiga ita da Hurriya har suka isa Yasir be yi wata magana ba, balle kuma Gwaggo da ta matsu su sauka a motarsa. Har cikin gidan ya faka ya fito ya budewa Gwaggo ta fito ita kuma ta riko Hurriya ta fito suka shiga cikin gidan. Yasir ya bisu da kallo gaba daya Hurriya ta zama abun tausayi a yanzu.
“Kina ganin jarabawa Hurriya”
Ya furta sannan ya sauke ajiyar zuciya ya bude motarsa ya shiga. Rukayya na ganin Hurriya ta shigo falon tana lalabe sai ta fashe da kuka ta saki kofin kurar da zata bawa Amma ta nufi Hurriya ta rumgume ta suna kuka. Gwaggo ta girgiza mata kai domin bata son Amma ta sani, sai dai abin da bata sani ba Rukkaya ta fada ma Amma komai bayan tafiyarta.
Jin kukan Hurriya sai ya saka Amma ma ta fashe da kuka, kukan da ta shekara hudu bata yi irinsa ba, kukan da tun da ciwon ya kamata bata taba kuka anji muryarta ba sai yau. Hurriya na jin sautin kukan Amma ta saki Rukkayya ta fara lalaben gurin da Amma take, Amma ta rika fuskarta ta saka hannunta ta bude cikin idonta tana kuka.
“Bana gani Amma bana ina ganin komai....”
Amman ta girgiza kai ta fashe da wani idin kuka mai taba zuciya.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un...”
Amma ta furta da wani irin karfi irin an mai kwancen murya. Rukkayya ta kalleta da sauri ta rufe baki tana kuka, Gwaggo kuma ta zauna kusa da ita ta fadata.
“Iyami... Allahu Akbar....”
“Na jefaki a halaka Hurriya na je kaina, sun kashe min Hamad ke ma kuma so suke su ga bayanki, da na san haka GOBENA zata kasance da ban auri Alhaji Haruna ba, na yi nadamar wannan aure na kaddara.... ”
Da in'in'ina take maganar muryarta na rawa as well as bakinta saboda dadewar da ta yi ba ta yi maganar ba, Twins dinta suka zo a guje suka tsaya suna kallonta, abu ne da ba su tana gani ba, tun da aka haife su suka yi wayo Amma bata tana magana ba, ba su taba jin sautin muryar uwarsu ba, bata taba kiran sunansu sun ji da kunnensu ba.
“Amma... Amma... Ammma. Muryarki ya bude Alhamdulillah Ala kulli halin, Alhamdulillahi hamdam kasiram”
Hurriya ta fada tana kuka tana dariya a lokaci daya sai kuma ta rumgume Amma. Gaba daya sai falon ya karade da sautin kuka, Amma kuka, Gwaggo kuka, Rukayya kuka. Su ma Twins sai suka fashe da kuka ganin Amman da Hurriya na kuka.
HAJIYA KALTUME POV.
“Kuma be ce zai dauki wani mataki ba?”
Khairy ta girgiza kai.
“Yace zai dauki mataki na wanda ya aikata mata haka, Ya Yasir ma yace zai dauki mataki akai”
“Dan'iya daman idan be dauka ba ai be cika Yasir ba, amman na yi mamakin ace Alhaji be mata komai ba, da ada ne Wallahi korarta zai yi”
“Kuka ma yayi sosai, Appa ya zubar da hawaye Hajiya kuma yayi tsinuwa akan duk wanda ya aikatawa Hurriya wannan abun...”
Khairy ta fada cikin kuka.
“To ke miye naki a ciki? Har da wani kuka ni kowaye ya aikata haka ya biyani Wallahi, dan Allah ni tashi ki ba ni guri zan yi waya”
Khairy ta mike tsaye ta fice daga dakin, Hajiya Kaltume kuma ta daga wayarta ta kira Hajiya Fatee. Khairy ta shigo dakinta tana share hawaye ta nufi wayarta dake aje ta dauka ta kira Adam.. Sai da kiran ya kusa yankewa sannan Adam ya daga.
“Adam ka ga abun da ka janyo ko?”
“Sai na kasheki Khairy sai na kasheki, ni zaki zaki yi betrayed? Sai na koya miki hankali Khairy”
“Ban aikata komai ba, laifin ba nawa ba ne kana ne, kai ka lalata komai Adam... Na yi nadamar saninka a rayuwata”
Ta dauke wayar a kunnenta tana kuka.......
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[12/15/2023, 4:14 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURRIYA*
4️⃣0️⃣
A hankali ya maida fork a plate din kankanar dake gabansa ya kalli mahaifiyarsa wacce ta tsare shi fa ido.
“Na koshi”
“Baka wani ci da yawa ba, kuma ka saka na yi cancelled tickets din da na siya, idan na yi magana ka ce ka ji sauki”
“Na ji sauki mana Ammy baki gani ba?”
“Me kake son ci yanzu? Watermelon din nan kawai ka ci zuwanka gidan nan”
Ammy ta fada cikin yanayin damuwa. Ya duba wayarsa da sako ya shigo.
“Good... Ku turo location din gurin da kuka aje shi yanzu”
Ya masa reply sannan ya kalli mahaifiyarsa.
“Taliya nake son ci mai zafi sosai, and ke nake son ki girka min”
Ta kai hannu ta shafa fuska cikin tsananin so da kauna da kuma tausayinsa.
“Ko wani kake son na girkawa zan girka masa Captain balle kuma kai, zan girka maka yanzu”
“Thank You”
Ta mike tsaye ta dauke plate din ta fice, binta yayi da kallo sai da ta rufo kofar dakin sannan yayi rejecting kiran Salim dake shigowa wayarsa. Ya mike tsaye ya nufi kofar ya bude ya sauko a hankali ya shiga falon Kakarsa domin ita a kasa aka yi mata nata bangaren saboda kafafuwa da take fama da su, karamin falon ya fara shiga sannan ya karasa bakin kofar dakinta. Daga bakin kofar dakin ya tsaya yana kallonta.
“Nene.. ”
Tsohuwar dake rike da carbi ta dube shi da murmushin a fuskarta ta ce.
“Ango ya karfin jiki?”
“Alhamdulillah, Nene key motarki zaki ara min”
“Ina zaka je? Kai da baka da lafiya?”
Yayi mata alama da ta yi shiru.
“Ba sai kin fada kowa ya ji ba, Ammy zata iya hanani fita kuma abu mai muhimmanci daga office ne”
“Ba a aiki da dare ai”
“Aikin mu ba shi da hutu, zaki ba ni key din ko na je gurin Hajiyar Maru na karba?”
Ta dan yi shiru kamin ta amsa masa.
“Yana nan cikin drawer, amman dai idan turaki ya san ka fita zai yi fada”
“Ba za su sani ba”
Ya nufi gurin da keys din suke ya dauka ya fice daga dakin, sai da ya fara bude falon ya leka ya ga babu kowa a babban falon sannan ya fito ya rufe kofar ba tare da ya bari ta yi motsi ba, ya fice salin alim, hankalinsa be kwanta ba har sai da ya fice daga gidan. Har ya isa asibitin FMC Salim be daina kiran wayarsa ba, shi kuma be amsa ba kuma ba zai amsa ba domin ya san tatsuniyar gizo bata wuce ta koki. Kai tsaye ya nufi ward din da Hurriya take, sai fa ga fara
Showing 138001 words to 141000 words out of 215510 words
“Kana aje wayar nan, ka duba list din mutanen da suka dora hotunan karka damu da yawansu ka turo min su, tare da sunanyen gidanjen jaridun, ka hado min da account number dinka”
“Okay Sir”
Ya sauke wayar.
“Za su san sun taba mai gata, na miki alkawarin farinciki Hurriya zan cika miki shi... ”
Ya fada sannan ya nufi madubin dake bandaki ya dora wayar ya cire tufafinsa ya sakarwa kansa shower. Ya bata minti arba'in a bandakin sannan ya fito yana rike da wayarsa jikinsa kuma na daure da tawul.
“Good Nafi'u”
Yayi forwarding sakon zuwa mabanbanta gurare sannan yayi waya da mutane daban daban. At the end ya kira Namra.
“Hello Captain”
“Wace asibiti aka kai Adam? Kanen Salim”
“Ban sani ba, ya jikanka?”
“Bincika min yanzu”
“Toh”
Ya aje wayar ya dauki wani tawul din ya goge jikinsa, sannan ya zauna gaban madubi yana hararo abubuwa da yawa. After like one hour yana zaune kan carpet bayan ya sallame sallah wani kiran ya shigo a wayarsa bayan na calls din dake ta shigo masa na yan'uwa da abokan aiki masu son tambayar jikinsa. Amman be amsa kiran kowa ba sai na Namra.
“Yana yana asibitin Yariman Bakura, layin ya hadurra”
“Good”
Ya yanke kiranta tun kamin ta kara cewa komai, ya shiga whatsapp dinsa ya sake sauke hotunan da Salim ya turo masa, ya yanke iya gurin da fuskar Adam take ya turawa wata number tare da address, sannan ya fito whatsapp din ya shiga contact dinsa ya nemo number the same person da ya turawa sakon ta whatsapp.
“Hello Sir”
“Uzairu na turo maka hoto da addreshin wani dan'iskan yaro yanzu a whatsapp, ni ya taba so the fight is between me and him.. Ka duba address din ka dauki mutanenka ki shiga cikin asibiti ku dauko shi ku aje min shi wani gurin da babu haske kuma babu rahma, ku masa doka irin dukan da idan na masa tambaya zai ba ni amsa a take amman ban ce ku kashe shi ba, ku aje shi a gurin for 10 hours”
“Yes Sir... ”
Ya sauke wayar, sannan ya amsa dayan kiran daya fito daga bachi.
“Yeah good so nake ku kama mai gidan jaridar ku bincike shi a ina ya samu hotunan, at the end ku sa ya rubuta cewar sheri aka yi mata kuma yana neman yafiyar Hurriya, ku saka yayi hakan tun a cikin office din ku idan be yi haka ba ku karya kafarsa”
“Amman Captain me yayi maka?”
“Yarinyar da suka batawa suna yarinya ce mai tsada she is innocent, please karku ragawa kowa a gurin”
“Subhanallahi, aiko za su ga aikin DSS”
“Thank You My friend”
Ya sauke wayar ya amsa wata wayar, haka yayi ta bata umarni a inda umarninsa suke jira a inda alfarma yake nema sai ya roki ayi masa haka.
HURRIYA POV.
“Daure ki sha tea ne kuma ba mai yawa ba”
Hajiya Binta na lalabata tana hada mata tea. Gwaggo ta ce.
“Babu yadda ban yi da ita ba amman ta ki cin komai tun safe har yanzu”
“Bana iya cin komai ne, ko na ci bana iya hadewa”
“Hurriya wannan abun duk zai wuce, wata kila an buga an buga an ga babu sa'a ne shi ne aka bullo ta nan, amman duk wanda ya sanki ya san ba zaki aikata ba, babu wanda zai yarda kawai ana son a jefaki a damuwa ne, dan haka karki bari damuwar da suke son jefaki ta tasirantu akanki karbi ki sha”
Ta mika hannu tana lalaben kofin ta karba ta kai bakinta ta kurba kadan sai ta gagara hadewa.
“Hajiya bana iya hadewa”
Hajiya ta karbi kofin ta rike tana kallon jikarta cike da damuwa sosai a fuskarta.
“Jibi zan wuce Ummara zan miki addu'a mai karfi a can, da yardar Allah wanda ya aikata miki haka ba zai sake sanin rahma a rayuwarsa ba”
“Amin Hajiya”
Gwaggo ta amsa, sannan suka daga kai gaban dayansu suka kalli kofar dakin da aka turo. Cikin wani irin yanayi kamar na kunya kamar tsoro Yasir ya shigo dakin fuskarsa a raunane.
“Yasir”
“Na'am Hajiya”
Hurriya ta sauke kanta kasa duk da kasancewar bata ganin kowa tana jin kunyar aga fuskarta saboda an yada tsiraicinta. Yasir ya tsaya daga tsaye suka gaisa da Hajiya da Gwaggo be ce da Hurriya komai ba ita ma bata iya dagowa ba balle tace masa wani ba sai hawaye take.
“Appa ya ce na zo da Hurriya”
“Ka zo da ita kuma? Be san tana asibiti ba?”
“Ya sani, yace na yi magana da likitan ya bata sallama”
“Saboda me? Be san idonta ya samu matsala ba?”
“Ya sani Namra ta fada mana komai, Hajiya idan za ayi mata aikin idon a ba nan za'ayi ba kuma abu ne da yake bukatar shiri da tantance inda ya kamata da kuma likitan da ya dace”
Hajiya zata sake magana Gwaggo ta dakatar da ita
“Je ka karbo sallamar, zamu tafi da ita mu ga iya gudun ruwansa amman ba zan bar Hurriya ta zauna a gidan nan ba har bada...!”
Yasir ya juya ya fita daga dakin ba tare da yace komai ba, Hajiya Binta kuma ta hau masifa ta daga wayarta ta kira shi kiran be shiga ba. Misalin karfe biyar da mintuna Yasir ya faka a harabar Appa, Gwaggo ta fara fita sannan ta fito da Hurriya Hajiya Binta ma ta fito tana kara shiryawa duk wani abu da ďanta zai yi. Hurriya ta kama hannun Gwaggo ta rike da karfi.
“Gwaggo tsoro yake kar Appa yace be yafe min ba”
“Ko da ya fada ba zai kama ki ba, domin ba ki aikata ba kuma Allah mai adalci ne”
Cikin karayar zuciya da duhun idanuwa Hurriya ya shiga bangaren na Appa Gwaggo tana mata jagora komai bata iya banbance komai a yanzu. Yanayin yadda ta ji numfashi na tashi ya karantar da ita falon cike da mutane da bata san su waye ba, yan gidansu ne kadai ko kuma dai duka familynsu da suke garin. Me Appa zai fada akanta shi ne abun da ya fi tsorata ta, da lalabe ta zauna a falon kusa da Gwaggo, hawaye na mata zuba, ta wani bangaren tana gode Allah da bata iya ganin komai, a yanzu da bata san da wane ido zata kalli Appanta ba.
“Hurriya...!!!”
Gabanta ta kasa amsa kiran da Appa yayi mata gabanta sai bugawa yake da karfi.
“Kina da wata hujja ta kare kanki akan abun da muka gani tsakanin jiya zuwa yau?”
Ta yi shiru, Gwaggo ta ce.
“Ka san dai ba zata aikata ba...”
“Gwaggo dan Allah ki yi hakuri ki bari ta amsa min”
Appa ya bukata cikin yanayi da ke nuna shi ma yana cikin damuwa kwatankwacin wanda Hurriya take ciki.
“Appa akai ni na yi alwala”
Tana fada ta mike tsaye tana kuka.
“Ba sai kin rantse ba abun da duk ba halinki ba ba zaki aikata shi ba”
Hurriya ta girgiza ma Hajiya Binta kai ba dan tana ganinta ba.
“Idan ban rantse ba babu wanda zai yarda da ni, ni ma kuma ba zan samu sukuni ba, dan Allah ku kai ni bandaki”
Yasir ya kalli Ruma.
“Tashi ki kaita”
Ruma ta tashi ta rika hannunta suka shiga bandakin dake cikin falon, Hurriya ta yi alwala ta fito ta bukaci a bata kur'ane.
“Bari zaka yi ta yi rantsuwar nan Tsoho?”
Appa ya kasa amsawa mahaifiyarsa, shi ma ji yake kamar Hurriya ba zai aikata hakan ba sai dai zuciyarsa ta kasa natsuwa. Yasir ya tashi da shiga bandakin da Hurriya ta fito yayi alwala ya shiga bedroom din Appa ya dauko mata alkur'ane ya kama hannu ya mika mata, shi kansa idan ta rantse zai fi jin natsuwa, domin ya shirya ui mata mummunan hukuncin idan har ta tabbata ta aikata. Hurriya ta rike qur'anen da dayan hannunta sai ta dora hannunta na dama a saman kur'ane ta dafa.
“Na rantse da littafin nan, abun da yake cikinsa da wanda ya aiko da shi ban aikata ba Appa”
Ta karasa cikin kuka... Gwaggo ta saka kalma shahada.
“La'ilaha Illaha Muhammad Rasulullah”
Sai gaba daya falon ya amsa suka karasa a tare.
“Sallalahu Alaihi Wassalam...”
Appa ma ya sauke kansa kasa ya fashe da kuka, babu wanda be yi hawaye ba a falon kuma babu wanda be tausaya mata ba ciki har da Momy. Yasir ya sa hannu ya karba yana hawaye da murmushi a fuskarsa, yar'uwarsa ta tsarkake kanta a gaban kowa hakan ya kwantar masa da hankali yanzu kam ya yarda hundred percent bata aikata ba.. Appa ya dago hawaye na zubowa daga idonsa ya mika mata kamar ance masa tana ganinsa.
“Zo nan gareni yata, fada min wa kika tarewa farinciki ya aikata miki haka?”
Hurriya ta fara takawa ta inda take jiyo sautin muryarsa tana kuka tana lalaben hanya, Yasir ya rika hannunta ya karasa ta ita gurin Appa, hannayensa ta fara kamawa sannan ta zube kasa a gabansa ta kwantar da kanta a kafarsa.
“Allah ya tsinewa wanda ya aikata miki wannan abun Hurriya, ba zai gama lafiya ba, bakinciki da ya saka mana da neman bata miki da sunan gidan nan Allah ya ninka masa shi...”
Kowa ya amsa da Ameen ban da Khairy da Namra dake ta kuka kai ka rantse da Allah su aka aikatawa haka ba Hurriya ba.
“Ba zan bar maganar nan ba, sai na yi shari'a da yaron nan, ya ci mutuncina ya ci mutuncin ƴata ba zan kyale shi ba”
“Ni ma na yi wannan tunanin Appa, na kudirta a raina idan har ta tabbata Hurriya bata aikata abun nan ba, ba zan kyale maganar nan ba”
Yasir na aje aya Hajiya Binta ta ce.
“Da kun kyauta daman be kamata a kyale ba”
Momy ta tashi ta fice ba tare da tace komai ba, Ruma ta bi bayanta. Gwaggo ma ta mike tsaye fuska a daure ta ce.
“Zan tafi gida, kuma zan tafi tare da Hurriya saboda a can zata samu kulawa”
Appa be ce komai ba bayan shafa kan Hurriya da yake, har Gwaggo ta iso gurin ta kama hannunta suka fice. Sai da suka kusa isa gate sannan Yasir ya cin musu da mota ya bukaci su shigo ciki ya sauke su gida, Gwaggo kamar bata shiga ba saboda yana dan Hajiya Kaltume sai kuma ya daure ta shiga saboda saukaka Hurriya wahalar fita titi zuwa neman abun hawa. Back seat suka shiga ita da Hurriya har suka isa Yasir be yi wata magana ba, balle kuma Gwaggo da ta matsu su sauka a motarsa. Har cikin gidan ya faka ya fito ya budewa Gwaggo ta fito ita kuma ta riko Hurriya ta fito suka shiga cikin gidan. Yasir ya bisu da kallo gaba daya Hurriya ta zama abun tausayi a yanzu.
“Kina ganin jarabawa Hurriya”
Ya furta sannan ya sauke ajiyar zuciya ya bude motarsa ya shiga. Rukayya na ganin Hurriya ta shigo falon tana lalabe sai ta fashe da kuka ta saki kofin kurar da zata bawa Amma ta nufi Hurriya ta rumgume ta suna kuka. Gwaggo ta girgiza mata kai domin bata son Amma ta sani, sai dai abin da bata sani ba Rukkaya ta fada ma Amma komai bayan tafiyarta.
Jin kukan Hurriya sai ya saka Amma ma ta fashe da kuka, kukan da ta shekara hudu bata yi irinsa ba, kukan da tun da ciwon ya kamata bata taba kuka anji muryarta ba sai yau. Hurriya na jin sautin kukan Amma ta saki Rukkayya ta fara lalaben gurin da Amma take, Amma ta rika fuskarta ta saka hannunta ta bude cikin idonta tana kuka.
“Bana gani Amma bana ina ganin komai....”
Amman ta girgiza kai ta fashe da wani idin kuka mai taba zuciya.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un...”
Amma ta furta da wani irin karfi irin an mai kwancen murya. Rukkayya ta kalleta da sauri ta rufe baki tana kuka, Gwaggo kuma ta zauna kusa da ita ta fadata.
“Iyami... Allahu Akbar....”
“Na jefaki a halaka Hurriya na je kaina, sun kashe min Hamad ke ma kuma so suke su ga bayanki, da na san haka GOBENA zata kasance da ban auri Alhaji Haruna ba, na yi nadamar wannan aure na kaddara.... ”
Da in'in'ina take maganar muryarta na rawa as well as bakinta saboda dadewar da ta yi ba ta yi maganar ba, Twins dinta suka zo a guje suka tsaya suna kallonta, abu ne da ba su tana gani ba, tun da aka haife su suka yi wayo Amma bata tana magana ba, ba su taba jin sautin muryar uwarsu ba, bata taba kiran sunansu sun ji da kunnensu ba.
“Amma... Amma... Ammma. Muryarki ya bude Alhamdulillah Ala kulli halin, Alhamdulillahi hamdam kasiram”
Hurriya ta fada tana kuka tana dariya a lokaci daya sai kuma ta rumgume Amma. Gaba daya sai falon ya karade da sautin kuka, Amma kuka, Gwaggo kuka, Rukayya kuka. Su ma Twins sai suka fashe da kuka ganin Amman da Hurriya na kuka.
HAJIYA KALTUME POV.
“Kuma be ce zai dauki wani mataki ba?”
Khairy ta girgiza kai.
“Yace zai dauki mataki na wanda ya aikata mata haka, Ya Yasir ma yace zai dauki mataki akai”
“Dan'iya daman idan be dauka ba ai be cika Yasir ba, amman na yi mamakin ace Alhaji be mata komai ba, da ada ne Wallahi korarta zai yi”
“Kuka ma yayi sosai, Appa ya zubar da hawaye Hajiya kuma yayi tsinuwa akan duk wanda ya aikatawa Hurriya wannan abun...”
Khairy ta fada cikin kuka.
“To ke miye naki a ciki? Har da wani kuka ni kowaye ya aikata haka ya biyani Wallahi, dan Allah ni tashi ki ba ni guri zan yi waya”
Khairy ta mike tsaye ta fice daga dakin, Hajiya Kaltume kuma ta daga wayarta ta kira Hajiya Fatee. Khairy ta shigo dakinta tana share hawaye ta nufi wayarta dake aje ta dauka ta kira Adam.. Sai da kiran ya kusa yankewa sannan Adam ya daga.
“Adam ka ga abun da ka janyo ko?”
“Sai na kasheki Khairy sai na kasheki, ni zaki zaki yi betrayed? Sai na koya miki hankali Khairy”
“Ban aikata komai ba, laifin ba nawa ba ne kana ne, kai ka lalata komai Adam... Na yi nadamar saninka a rayuwata”
Ta dauke wayar a kunnenta tana kuka.......
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[12/15/2023, 4:14 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURRIYA*
4️⃣0️⃣
A hankali ya maida fork a plate din kankanar dake gabansa ya kalli mahaifiyarsa wacce ta tsare shi fa ido.
“Na koshi”
“Baka wani ci da yawa ba, kuma ka saka na yi cancelled tickets din da na siya, idan na yi magana ka ce ka ji sauki”
“Na ji sauki mana Ammy baki gani ba?”
“Me kake son ci yanzu? Watermelon din nan kawai ka ci zuwanka gidan nan”
Ammy ta fada cikin yanayin damuwa. Ya duba wayarsa da sako ya shigo.
“Good... Ku turo location din gurin da kuka aje shi yanzu”
Ya masa reply sannan ya kalli mahaifiyarsa.
“Taliya nake son ci mai zafi sosai, and ke nake son ki girka min”
Ta kai hannu ta shafa fuska cikin tsananin so da kauna da kuma tausayinsa.
“Ko wani kake son na girkawa zan girka masa Captain balle kuma kai, zan girka maka yanzu”
“Thank You”
Ta mike tsaye ta dauke plate din ta fice, binta yayi da kallo sai da ta rufo kofar dakin sannan yayi rejecting kiran Salim dake shigowa wayarsa. Ya mike tsaye ya nufi kofar ya bude ya sauko a hankali ya shiga falon Kakarsa domin ita a kasa aka yi mata nata bangaren saboda kafafuwa da take fama da su, karamin falon ya fara shiga sannan ya karasa bakin kofar dakinta. Daga bakin kofar dakin ya tsaya yana kallonta.
“Nene.. ”
Tsohuwar dake rike da carbi ta dube shi da murmushin a fuskarta ta ce.
“Ango ya karfin jiki?”
“Alhamdulillah, Nene key motarki zaki ara min”
“Ina zaka je? Kai da baka da lafiya?”
Yayi mata alama da ta yi shiru.
“Ba sai kin fada kowa ya ji ba, Ammy zata iya hanani fita kuma abu mai muhimmanci daga office ne”
“Ba a aiki da dare ai”
“Aikin mu ba shi da hutu, zaki ba ni key din ko na je gurin Hajiyar Maru na karba?”
Ta dan yi shiru kamin ta amsa masa.
“Yana nan cikin drawer, amman dai idan turaki ya san ka fita zai yi fada”
“Ba za su sani ba”
Ya nufi gurin da keys din suke ya dauka ya fice daga dakin, sai da ya fara bude falon ya leka ya ga babu kowa a babban falon sannan ya fito ya rufe kofar ba tare da ya bari ta yi motsi ba, ya fice salin alim, hankalinsa be kwanta ba har sai da ya fice daga gidan. Har ya isa asibitin FMC Salim be daina kiran wayarsa ba, shi kuma be amsa ba kuma ba zai amsa ba domin ya san tatsuniyar gizo bata wuce ta koki. Kai tsaye ya nufi ward din da Hurriya take, sai fa ga fara
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47 Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72