ubanci bana miki kallon haka, ina kallonki ne kamar uwa daya uba daya muke, tashi ki ci abinci”

Ta tashi ta gyara zamanta sai dai kamin ta kai hannunta cikin abinci Khairy ta shigo sanye da karamin mayafinta wayarta a hannunta, is like kamar an mata dole haka ta tsaya bakin kofar falon babu ko sallama.

“Hurriya taso muje”

Hurriya ta kalleta.

“Ina?”

“Ki taso idan zaki taso Malama”

Namra ta daga kai ta kalli Khairy da duba na wulakancin.

“Ba zata tashi ba abinci zata ci”

“Okay sannu uwarta, bari naje na fadawa Yaya uwarta ta hanata zuwa, ita ma kuma ta ce ba zata je ba”

Hurriya na jin kiran na Yayanta ta tashi tsaye da sauri zata nufi kofar.

“Dauko mayafinki Hajiya”

Ta juya ta dauko mayafin kamar yadda Khairy ta bukata, sannan ta bi bayanta suka fice, at first ta yi zaton bangaren Hajiya Kaltume za su nufa sai kuma ta ga ta nufi gate.

“Ba yaya kika ce yana kirana ba?”

“Yana waje”

Huriyya ta bi bayanta suka fita gate, close to gate din wata mota ce fake da ba ta gidan ba. Gurin motar suka nufa ta bude ma Hurriya baya.

“Shiga”

“Amman wannan ba motar Yayana ba ce... ”

“Zaki shiga ko sai ya fito ya mareki? Ba shi ya ce mu jira shi a mota ba”

Hurriya ta shiga da sauri, Khairy ta rufe bayan sannan ta bude front seat ta shiga ta zauna tana taba wayarta. After like five minutes aka bude motar ta Driver seat aka shigo, tana leken fuskarsa yana juyo ya kalleta wa zata gani ba Adam ba.

“Thank you Khary”

“This should be the last time sa zaka cilasta min fitowa da yarinyar nan”

Ta fada a kufule. Hurriya ta kalleta fuska kamar zata fashe da kuka, murya kamar a shagwabe ta ce.

“Amman yaya Khairy kin san me Appa yace ko kuma kin san Yayana zai yi fada idan ya sani”

Adam yayi saurin tarar numfashinta.

“Ba dadewa zamu yi ba Hurriya, kawai ina son na ganki ne kuma na baki hakuri abun da ya faru, and na aiko da box an baki?”

Khairy ta watsa masa wani kallo.

“Okay ni zan hana mata box din kenan?”

“Waya sani, tun da har kika iya bata ni a gurinta ai zaki iya hana ta ganin box din”

“Ni ban bata ka ba”

“And why take min kallon mutumen banza? Ni ba iskanci ne ya kawo ni gurinta ba, ki daina fada mata bad things about me, na ga ai natsantsiya ce not like you that's why i like her”

With shock Khairy take kallonsa.

“Adam what's the meaning of all this?”

“Sonta nake yi, and I'm ready to prove it, i want to talk to her parents da duk wani mai son hana alakata da ita tafiya I'm serious”

Khairy ta tsaya kallonsa for some seconds kamin ta dauke kai ta bude motar, Hurriya ma ta bude motar zata fita.

“Fita zata yi idan kika fita, ki zauna sai na gama magana da ita”

Ya fada da kamar fada yana kallon Khairy da bata fita motar ba, jin haka ya saka ta fasa fitar ta rufe motar, Hurriya kam bata tsaya ba ta fice ta tana ganin Adam ya bude motar ta ranta a na kare ta shige gida da sauri, a fusace ya dawo motar ya rufe Khairy da fada

“Kin ga abun da kike ja ko? Kin dauki tsanata kin sakawa yarinyar har guduna take”

“Toh wai kai Adam duk yan matan duniya ka rasa wa zaka so sai Hurriya? Yarinyar da ko jami'a bata fara ba”

“Ba ruwanki”

Ya bude gurin da yake ajiyar kudi ya dauko rafar dubu daya ya mika mata

“Je ki gyara abun da kika bata ina son yarinyar nan ta so ni”

Khairy ta kalli kudin ta kalleshi, kamar ta yi magana sai kuma ta saka hannu ta karba ta bude motar ta fita.

“Why Adam why...”

Ta fada cikin yanayin damuwa da gajiyawa tana tafiya ba tare da ta juyo ba. _____________________

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/14, 6:50 AM] AMINA KABIR CAPS: 𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘


Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲


𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣6⃣

Sai da Hurriya ta shigo gidan sannan ta daina gudu, sai dai hango Hajiya Kaltume tsaye a karamin gate din part dinta ya kara daga mata hankali sosai domin irin tsayin da Hajiya ta yi ya nuna kamar ita take jira. Rage tafiyar da take ta yi gabanta na faduwa tana ta sake sake domin ta san halin Hajiya Kaltume da ma Khairy din za su iya wanke kansu ita su jefata a ruwa. Tana daf da shigewa bangaren Momy Hajiya Kaltume ta yi kiranta da hannu, a lokacin ne tsoro ya kara cika zuciyar Hurriya, haka dai ta daure ta karasa gurin da take tsaye.

“Hajiya gani”

“Ina kika fito?”

“Yaya Khairy na raka waje gurin Saurayinta”

Hajiya Kaltume ta yi fuskar mamaki.

“Saurayinta kuma? Waye?”

“Ban san shi ba ni ma”

“Okay. Je ki BQ din Nafisa ki kira min Kulu, kuma ban ce ki fadawa Nafisa ba, sannan ki fada mata ta same ni bangarena magana ce mai muhimmanci ki kirata dabam ki fada mata ba a cikin mutane ba”

“To Hajiya”

Ta mike tsaye tana jin sanyi a ranta, na rashin zafafa bincike ko binta da zagi da Hajiya Kaltume bata yi a yau. Tana shiga gate din da nufi BQ din Momy har karamar kofar bangaren masu aikin ta fara budewa ta shiga ciki, dukansu suna waje suna hira har da dare dare.

“Mama Kulu ina wuninku”

Ta gaishesu, duk suka amsa mata har Kulu, sannan Hurriya ta ce.

“Mama Kulu wai ki zo”

“Ni”

Ta nuna kanta.

“Eh”

“In ji wa?”

Dayar dake zaune kusa da ita ta saka dariya.

“Ke ma dai da neman tsawaita zance kike, waye zai kiraki duk gidan nan ban da Momy? Kuma tun da kika ga Hurriya a kin san ita take nemanki”

Hurriya dai bata ce komai ba ta juyo ta fara tafiya, a bakin kofar ta tsaya har sai da Kulu ta fito sannan ta tare tace.

“Ba Momy ke nemanki ba, Hajiya”

“Hajiya kuma?”

She asked with shock.

“Eh nima na dawo daga waje na ganta tsaye tace na kiraki kuma kar na bari kowa ya ji, ta ce ki same ta bangarenta magana ce mai muhimmanci”

“Toh... Allah yasa dai lafiya”

Hurriya dai ban da kallonta babu abun da ta yi, domin ita ma bata san dalilin kiran ba balle ta fada mata ita kuma bata daina faduwar gaba ba har ta isa bangaren na Hajiya Kaltume. Daman Hurriya tana isar mata da sako ta shiga bangaren Momy ta bar a guri..

Cikin tsoro ta shiga falon da Momy tana sallama. Ruma ce kadai zaune a falon tana cin abinci, hannu ta sauke ta aje plate a kasa bayan ta amsa sallamar Kulu, ita kanta mamakin ganinta a bangaren take.

“Hajiya na ciki ta ce tana son ganin”

“Eh tana ciki bari na kirata”

Ta mike tsaye tana tsude hannu ta nufi stairs, slowly ta tura kofar dakin Hajiya ta lake.

“Hajiya ga Kulu mai aikin Momy a kasa tana nemanki”

“Je ki ce mata ta shigo”

“Nan eh?”

“Eh”

Ta juya ta koma, tun kamin ta karasa saukowa ta fadawa Kulu sakon Hajiya Kaltume.

“Ta ce ki shigo”

“Na shigo kuma?”

Ruma ta daga mata kai, Kulu ta daga kai ta kalli stairs din da bata taba hawa ba, tun zuwanta gidan, shigarta bangaren Hajiya Kaltume ma za a iya kidayashi domin bata zuwa sai idan Momy ta aikota, kuma ba kasafai Momy take haka ba. Da tsoro Kulu ta taka ta hau stairs sai ta rasa wane daki zata shiga domin duka dakunan a rufe suke kuma bata taba kaiwa gun ba balle ta gane wanene dakin Hajiya Kaltume. Kwatantawa ta yi da dakin Momy sai ta isa bakin kofar dakin ta yi sallama ta kwankwasa.

“Shigo”

Ta murda kofar ta shiga idonta na bayyana tsoronta a fili domin bata san dalilin kiran ba, gashi ance mata magana ce mao muhimmanci kuma har ba a son kowa ya ji. Kusa da kofar ta tsaya ta rigina tana zuba gaisuwa.

“Hajiya ina wuni”

“Rufe kofar ki matso nan”

Ta juya ta kalli kofar sannan ta saka hannu biyu ta rufe ta, ta matsa kusa da Hajiya ta zauna a kasa.

“In ce dai ba wani laifin na yi ba”

Hajiya Kaltume ta kalleta tana murmushi.

“Aa ba ki yi laifi ba for now, na ma kiraki ne na yaba miki, sai dai nan gaba ban sani ba ko zaki yi laifin idan kika biyewa sherin zuciya”

“Hajiya kin saka ni a hudu me ya faru?”

Hajiya Kaltume ta gyara ta kalleta da kyau irin duban nan dake nuna babu alamar wasa a zancenta.

“Ke kika dauki kudin da yake uwar dakinki Nafisa, da sarkokinta da kuma sarkar Namra ko ba haka ba?”

Hausawa suka ce marar gaskiya ko a ruwa gumi yake. A take gumi ya karyowa Kulu ta fara hadeye yawu tare da dora hannu akai tana zaro ido.

“Ni Kuma? Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un Allah Wallahi Hajiya... ”

Hajiya ta daga mata hannu.

“Ban ce ki rantse min ba, abun da na sani ne nake fada miki, kuma bana bukatar ki jadadamin, idan kuma kin yi musu zan mu iya zuwa ni da ke da Nafisa da kowa ma na gidan na nuna gurin da kika boye kudin, bayan dakunanku cikin itacen fulawa”

Jikin Kulu ya fara rawa irin rawar nan dake kara bayyana rashin gasjiyarta.

“Kin ga daga nan sai Alhaji ya koreki, daman kuma ita Nafisa na san ba zata kyaleki ba sai ta hadaki da Police, baki ga aikinki ba ki ga kudin da kika sata, kuma ga zubewar mutumci da zuwa gurin yan sanda”

“Hajiya ki rufa min asiri dan girman Allah ki yafe min, ki dubi girman Allah ki rufa min asiri, Wallahi zan maida duk abun da na dauka, dole ce ta saka na sata, shekarata nawa a gidan nan amman ban tana daukar ko akaifa ba balle kudi”

Ta karasa da kuka sosai ko'ina na jikinta yana rawa, ta dayan bangaren kuma tana mamakin ta ina Hajiya ta san da wannan bayan bata fadawa kowa ba, kuma babu wanda ya san gurin da ta binne kudin.

“Ban ce ki maida kudi ba, da ki maida kudi da karki maida kudi duk daya ne a gurina, ni ina ma jinjina miki da kika aikata hakan, domin Nafisa ban da bakar rowa da wulakanci bata aje komai ba, na kira ki a nan saboda na fada miki cewar na sani, kuma na jidadi da baki wahalar da kanki gurin bayyana gaskiya ba, ni nan da kika ganina har duniya ta nade ba zan taba fadawa kowa cewar ke kika saci kudin Nafisa ba ko sarkarta”

“Hajiya ina kika ji wannan magana?”

“Da wa kika yi maganar?”

Ta daga hannayenta sama.

“Wallahi ban yi da kowa ba.. ”

“Karki damu da inda naji, ba wani ya fada min ba, abun da nake son ki damu da shi ne, abun da zan fada miki yanzu”

Ta kara gyara zama tana hade yawu da karfi.

“Toh Hajiya”

“Daga yanzu ina son ki zama karkashin ikona ba ikon Nafisa ba, ita kike yi ma aiki amman ni nake da iko dake, ina son ki saka min ido sosai akan uwar dakinki, kuma nan gaba duk abun da na ce ki aikata zaki aikata shi”

“An gama Hajiya Wallahi an gama.. Komai kike so shi za'ayi”

“Yayi kyau, ke kuma asirinki zai yi ta rufuwa har ki mutu, kuma zan cigaba da biyanki bayan biyan da Nafisa take miki”

“Hajiya ni ba sai kin ba ni komai ba, kawai dai ki rufa min asiri idan kika min haka kin biya ni”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi ta dauke fuskarta ta dauki wayarta tana latsawa, haka ta kyale Kulu a gurin tana ta share gumi har na kusan minti biyar sannan ta kalleta ta ce.

“Wake share dakin Hurriya?”

“Ni ce Hajiya ni nake sharewa na yi mopping ko'ina na saka turare”

“Yayi kyau da ba ke ba ce zan ce ki karba ki share saboda, aikin da nake son ki fara min a yanzu shi ne, ki shiga dakin Hurriya ki bincike min komai na dakinki idan kika ga wata laya ko wani kullin magani ko wani abun na dabam ki dauko min shi”

“Toh Hajiya amman sai gobe, saboda dare ne yanzu, kuma Momy bata son kowa ya shiga bangarenta idan tana nan”

“Ni ma ban ce ki yi yanzu ba, amman dai ki tabbatar kin samo wani abu karki zo min hannu sake, domin ni na san akwai abu a dakin shiyasa na ce miki ki dauko, kamar yadda na san ke kika yi sata kuma na san gurin da kika boye kudin”

“Toh Hajiya, Wallahi zan yi”

“Shi ke nan tashi ki tafi”

“To na gode Hajiya na gode Allah ya saka da alheri Allah ya rufa mana asiri, Allah ya kareki daga duk shari”

Hajiya Kaltume bata ji zata iya amsa addu'ar ba dan haka bata amsa ba, sai kawai ta daga mata hannu. Kulu ta tashi ta fice rike da zanen da ya kwance kuma ta kasa daurawa sai rike shi da ta yi a jikinta ta sauka haka. Hajiya Kaltume bata sake fitowa dakin ba sai da ta auna lokacin da ya kamata ace Khairy ta dawo cikin gidan sannan ta fito dakinta ta nufi dakin Khairy, sai ta same ta kwance ruf da ciki bandir din 1k a gafenta wayarta ma a gafenta aje. Sai da Hajiya ta gama kallon komai sannan ta zauna kusa da ita ta kai hannu ta taba ta

“Ke Lafiya kike?”

Khairy ta bude ido.

“Lafiya kalau”

“Waye ya zo gurinki?”

“Waya fada miki wani ya zo gurina?”

“Na ga Hurriya na tambaye ta ina ta fito tace min ke ta raka gurin saurayinki, waye wannan?”

Khairy bata son jin magana dan haka ta ce.

“Baki san shi ba”

“Hakan yayi, danan bana son saninsa, domin bana son ganin kowa a tare da ke sai Fadeel”

Da far'a Hajiya Kaltume ta fadi haka tana kai hannu ta shafa bayan yarta irin na uwa mai alfahari. Sai a lokacin Khairy ta zabura ta tashi zaune ta kalli Hajiya Kaltume.

“Wane Fadeel kuma Hajiya?”

“Fadeel dai, dan wajen Hahiya Fatee yayanki”

Khairy ta lumshe ido ta bude alamar gajiyawa.

“Hajiya ina tunanin na nuna miki tun ranar da kika min maganar nan cewar Fadeel baya a cikin tsarina, namiji mai mata da yara uku me zan yi da shi?”
*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah...!*
Hajiya Kaltume ta juyo da kyau ta fuskance ta tana kokarin lurar da ita duniya.

“Irinsu ai sun fi rikon aure, balle kuma shi da muka san halinsa ciki da waje? Baki ga yadda yake zaune da matarsa ba? Sannan yayansa ai ba ke zaki rika su ba ko da ya rabu da matar, sannan yaron nan yana da kyau ga kudi, irin sa mata suke rubibi fa amman ke Allah ya kawo miki shi a arha”

“Ko duniya yake da ita, ni baya cikin tsarina bana sonsa, ina da wanda nake so... Saurayi matashi be taba aure ba kuma shi ma mai kudi ne dan masu kudi da baya jin zafin kashe naira”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi.

“Yaro yaro ne, ke Khairy ban da yarinta irin naki, har akwai saurayin da zai fi Fadeel a garin nan? Ke dai ki bude idonki kuma ki ba zuciyarki hadin kai nan da nan zaki ji kina sonsa, kuma ki duba ko amincin dake tsakanina da mahaifiyarsa”

A karo na biyu Khairy ta runtse ido ta bude da karfi, cikin ihu ta ce.

“Hajiya bana son Fadeel kuma ba zan so shi ba, baya cikin mazanjen da nake so, ni ina da wanda nake so”

“Khairy lafiyarki kuwa? Ni kike yi ma magana da daga murya haka?”

“Toh Hajiya kina son cilasta ni auren wanda bana so, na fada miki bana ra'ayin Fadeel, ba a auren dole yanzu”

Rai a bace Hajiya Kaltume ta mike tsaye tana nuna Khairy da wayarta a hannu

“Baki isa ba, shi da yake namiji be bijirewa mahaifiyarsa ba balle ke da kike mace, kuma duk samarinki nan naki na banza ba, domin babu wanda ya nuna alamar da gaske yake har kika gama karatunki, kowa na ganki da shi sai ki ce abokinki ne, sai yanzu da na gabatar miki da wanda nake son ki aura mutumen kwarai wanda zai rike ki da gaske sai ki gabatar min da wata maganar banza, to baki isa ba dole ne ki bi zabina, ni na haife ki
Showing 48001 words to 51000 words out of 215510 words