naki a ciki? Ki yi hakuri a matsayinki na uwa ki danne duk abun da kike ji dan Allah”

“Ba zan iya ba Alhaji Sadiq, Engr ya nuna min ba ni da muhimmanci a rayuwarsa da ta dansa, shiyasa be duba shawarata ko ra'ayina ba ya aikata abub da ya aikata”

Ta fice daga falon tana kuka, Hajiyar Maru wacce ta kasance abokiyar zaman Nene ta bi bayanta tare da Momy Ikilima, Alhaji Sadiq da Alhaji ya dafa kafadar Captain yace

“Ka dauko wani aiki mai nauyi Jamal, idan baka yi hakuri ka kai zuciya nesa ba ba zaka iya karasa ba, ka bawa kowa hakkinsa matarka da mahaifiyarka, Allah ya bada zaman lafiya ya hada kanku”

Ficewa suka yi daga falon sai ya rage daga Captain sai Nene a falon har jikokin Nene yan matan da kanana duk babu ko daya.

“Ka yi hakuri Jamal kowa ya ce zai iya sai an gwada aka ko zai iya dauka saboda haka ka saka kana'a a zuciyar.... ”

Sakin baki ta yi tana kallon ikon Allah ba tare da ta karasa maganar ba. Gira Captain yake daga masa ya sumbanci goro da dabino da Daddy ya ba shi, sannan ya zuba shi a alijihu ya bude babban rigarsa yana nufar ina da take da rawa. Nene ta rike baki.

“Ah...ah... Ah... Ja'irin yaro? Wato ni ka raina ko? Kake min rawa me yasa baka yi ba a gaban iyayenka”

“Su ai iyayena ne, ke kuma kakata ce my first wife my kalbi”

“Tsohon makiri, amman tsaye ka yi a gabansu ba wani murna ba komai kamar wanda aka yi ma auren dole, ashe kana so....”

Ya kyalkyale da dariya ya sumbanci kumatunta.

“Nene na godiya da kika haifo min gwarzon namiji kamar Daddy, ba dan shi ba da yanzu na rasa yarinyar nan”

Nene ta kai masa duka a fuska.

“ja'irin yaro, amman kai da gaske baka ganin illar abun da yarinyar nan ta yi?”

“Bata aikata ba sheri aka yi mata, kuma asiri zai tonu nan ba da jimawa ba, kowa be wuce kaddara ba hakan zai iya faruwa da ni, ko da wani a cikin jikokinki sheri ne aka yi mata saboda a lalata sunanta”

“Haka ne, abun kam babu dadin ji babu dadin fadi, amman na tausaya mata matuka”

Captain ya daga hannayensa sama fafaren hakoransa na bayyana yayi ma Allah godiya.

“Allah ka ba ni ikon kyautata ma yarinyar da daukar nauyinta yadda ya dace, ka ba ni ikon faranta mata, ka taimaka min gurin tarbiyarta da na yaran da zamu haifa Allah, ya Allah ka karkato da zuciyar mahaifiyata da hankalinta ta fahimce kuma ta so abun da nake so, Allah ya ba mu zaman lafiya ka kawar da shaidan da mahassada a wannan aure”

“Ameen”

Nene ta amsa masa tana kallonsa cike da burgewa.

“Kana da hankali matuka Jamal, ba dan kana jikana ba hakika wannan yarinyar ta yi dacen miji, matukar ba zata fusata ka ba to zaku zauna lafiya da ita”

“In shaa Allah Nene”

Ya kara taka mata rawar sai a lokacin yake jin wani kalar farin ciki da be san a muhalin da zai aje shi ba, a lokacin ne wani shaukin auren da annashuwa da zumudi suka same shi. Hanyar da dakinsa yake ya nufa yana tafe yana gyara babbar rigar abun ka da wanda be saba saka manya kaya irin wannan ba. Agaban madubi ya zauna yana shafa fuskarsa ya dauki ragowar tutaren ya feshe a jikinsa, wani irin yanayi yake jin kansa da be taba samun kansa a ciki ba, yanayi ne dabam da yake zuwa sau daya a rayuwar ko wane saurayi fa budurwa, yanayin da kan canja yanayin ango da Amarya tun daga yanayin gari har zuwa na hallita da mu'amala da kuma na iskar da aka shaka. Hoton da ya dauka na Hurriya ya kama a wayarsa yana kallo yana shafa screen din da hannunsa.

“You're the only thing i want touch.... Kin kawo ni a wata duniya da ban yi mafarkin zuwanta a kusa ba, kin haska min abubuwa da yawa da duhun watan soyayyarki bata bari na gani ba, zan baki kyauta duniyar dake cike da haske da farinciki sai na dawo miki da abubuwan da kika rasa, bakinciki da kike ciki zan maye miki gurbinsa da farinciki, zan canja shafin rayuwarki har ki bata damuwa baya, zaki gode Allah ki yi alfahari da ya baki ni a matsayin miji.... QURRATUL AYN (meaning
Delights Of The Eye, Darling, sanyin idaniya...)”

Ya sumbanci hoton sannan ya dorashi a kirjinsa ya rumgume ya lumshe ido yana murmushi, a zuciyarsa yake ayyana Hurriya tsaye a gabansa tana kallonsa da murmushi a fuskarsa fararen tufafi sanye a jikinta.

“Ya... Ya... Ya... Na.. ”

Ya ji yana fitowa between her soft lips tana motsa halshenta a hankali.

“Uhmmm..... ”

Ya bude ido yana amsawa, a nan ya gane imagination ne yake ba gaskiya ba, murmushi yayi mai sauti ya cige bakinsa ya maida idonsa ya rufe yana jin kamar ace yana da damar ganin Hurriya a yanzu.


HAJIYA KALTUME POV.

“Hurriya fa ka ce Yasir ko dai zolayata kake?”

“Taya zan zolaye ki Hajiya? Ga abun da yake zahiri, goro da dabino suna waje, idan baki yarda ba ki tambayi Appa ki ji”

Hajiya Kaltume ta juyo ta kalli Khairy da ke kallon sarkar kamar wanda ta yi arba da wani abun tashin hankali.

“Da wannan sarkar aka biya sadakin Hurriya? Wanene? Be san abun da yake yawo a gari ba ne Yaya?”

“Ba za su rasa sani ba, wata kila ma shi ne dalilin da yasa suka zo neman auren a yanzu, kuma zai iya yiyu ba su sani ba din ko ma dai minene an riga da an daura fatan mu Allah ya bada zama lafiya”

Ya karasa yama dauko wayarsa daya dake aljihu ya amsa kiran Appa.

“Hello Appa... Eh tana hannuna okay gani nan zuwa”

Ya mike tsaye ya rufe sarkar.

“Appa yake kirana, yace ma kawo masa sarkar”

Ya nufi kofa, Hajiya da Khairy suka bi shi da kallo kamar wasu kauyawa. Hajiya Kaltume ta kalli Khairy

“Anya Nafisa ta sani kuwa? Sadaki da sarkar zinari?”

“Abun kamar hankali ba zai dauka ba Hajiya, duk wannan cecekucen da ake akan Hurriya ace wani ya zo ya aureta a rana daya kuma ya biya sadaki mai yawa haka?”

“To ni ma mamakin abun nake, abun dai kamar a mafarki”

“Kuma Wallahi idan wanda nake zargi ne dan Alhaji Turaki Hurriya ta warke Hajiya, kin san yan'uwan Momy babu talaka balle kuma AA Turaki”

“Shin waye be san ubansa a kasar nan ba? Wai ko mafarki na ke dai”

Ta mari kanta baren dama ta koma hagu ta mari kanta ya mursa idonta ta hade yawu.

“Kuma fa ta makance kuma ya yarda zai aureta ko dai asiri aka masa?”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye ta dauki dankwalinta a hannu, ta nufi sama. A gurin da wayarta take aje ta dauka ta kira number Hajiya Fatee.

“Sallamu Alaikum”

“Ba sai na amsa sallamarki ba balle gaisuwa, Hajiya Fatee duniyar nan fa tana shirin rikice min, wai ashe motocin da kika gani dazun sun shiga bangaren Nafisa neman auren Hurriya aka zo?”

“Hurriya? Ko dai Namra?”

“Hurriya dai da kika sani yar wajen Iyami... Kuma Alhaji ya ba su ba su bar gidan ba sai da aka daura auren”

“Ina na taba jin abu haka? A bada aure kuma a daura a take? Anya mutanen kwarai ne kuwa ko da yake Mahaifinta yana neman a raba shi da abun kunya ba dole ya amince ba”

“Ba auren ne abun mamaki ba, wanda ta aura ne da kuma wanda ya zo nemam auren ne abun mamaki”

“Toh... Wata kila dan fashi ne ko ko kuma masu yankan kai, domin su ne kadai za su iya runtse ido su auri Hurriya a yanzu, ganin manyan motoci ba shi ke nuna mai daraja zata aura ba wata kila ma ba zai wuce mai sharar gidan masu arziki, ya walkilta mai gidansa nema masa aurenta”

“Alhaji Aliyu Turaki ne fa Hajiya Fatee, Yayan Nafisa, ya zo neman aurenta.”

“Oh... To... Wata kila yaron gidansa ya yi ma kara ko kuma ubanta ya nemo mai raba shi da abun kunya ayi hadaka, ke waya sani ma ko tsoho ne za a hada ta saboda su basa kunyar auren ko wace mace Sugar daddys din nan da kike ji da gani”

“Wannan saurayi ne sabo dal a cikin kwali, ďan Alhaji Aliyu Turaki ne wanda yake zuwa gurin Nafisa, ina kare miki zance da zinari aka yi sadakinta na naira na gugar naira har naira miliyan hansi....”

Hajiya Fatee ta amsa da karfi.

“Ke.... Hajiya Kaltume... Hurriyar? Har kin sa cikina ya murda”

“Ai ni fitsari kubce min suka yi, yar Iyami? Sauran yaran gida ba a musu ba sai ita da duniya ta gama wulakantawa? Zama be gan ni ba Hajiya Fatee wannan yakin ba na uwar Hurriya kadai ba ne har da Hurriya, Wallahi ba zan yarda ta fi yayana more rayuwa ba, bayan duk abun da uwarta ta yi min? Ta aure min miji ta zo ta yi miki a gidana yanzu kuma ta tafi yarta zata taka nairar da ta fi ta ubanta, yar mai aiki? Uwarta ta mallake min miji ta yi yadda take so ita kuma yanzu ta take mu koma karkashin inuwar ta muna daga kai mu nunata?”

“Ke ni fa wani abun ma mamaki yake ba ni, anya zuri'arsu suna barin namiji a banza kuwa? Idan yaron be da hankali kuma iyayensa sai suka yarda? Ko da ba yaron kwarai ba ne?”

“Captain ne fa na Soja, Nafisa ma jinsa take ballw iyayensa, kuma ko bayan haka idan ta aure shi ai ta take, nan gaba sai a fara lissafi da ita a cikin yara kanana masu arziki, Hajiya Fatee bana son Iyami bana son zuri'arta dan haka bana fatan wani abun farinciki ya same su”

“To yanzu me ye abun yi?”

“Abun yi ki shirya gobe a gidanki zan yi karin kumallo, mu kama hanyar kauyen nan muje mu samu malamin nan da kanmu, idan be fara aiki ba ya tada idan kuma ya riga da ya fara a kara fetur hayaki ya baibaiye ko'ina a rikita Iyami da iyalinta a karkato da hankalin mijina gareni”

“Amman fa ina tsoron kauyen nan Hajiya Kaltume kin san fa irin wahalar da muka sha wacan karon, mussamman ma ni da kanana yara suka haikewa har da guziri na yo, ko dai aika zamu yi?”

“Wannan zuwa da kai ne ya fi aike, yadda hankalina yake a tashe idan ban je garin nan na yi magana da Malam ba na hura masa wuta ba zan samu salama ba, duk wani tsoro ya kau min a yanzu, ai sawun giwa ya zarce na rakumi, idan ma ba zaki je ba, ni zan shirya ma tafi”

“Aa ba zan bari ki tafe ke kadai ba, idan kin zo zamu tafi tare”

“Sai na shigo”

Ya katse wayar tana daga zanenta ta duba fitsarin da ke bin kafarta har lokacin mararta ta kasa rike su.

“Dole, wannan tashin hankali da me yayi kama? Ina ga Iyami ta dawo gidan nan kuma yarta ta auri mai kudi? Goma ta hadu da ashiri, rayuwa ta samu kenan”

Ta jefar da wayar akan gado.

“Ba zan taba bari ba, ba za a mareni a tsinka min jaka ba... ”




Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[12/19/2023, 12:58 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURRIYA*

4️⃣5️⃣





“Ni kaina ban yi farinciki da wannan auren ba, sai dai ba zaka iya nunawa Yaya ba ya fada maka ba daidai ba ko ma yace ba ka yi tunani ba, amman yarinyar sam bata dace da matar Jamal ba sam, sam sam”

Cewar Momy Ikilima a madadin ta kwantar da hankalin Ammy sai zugata take, Hajiyar Maru ce ta kawar da maganar Momy Ikilima ta hanyar nunawa Ammy ta karbi wannan kaddara ta so abun da danta yake so.

“Ba zan iya kallon yarinyar a matsayin surukata ba Hajiyar Maru, shi kansa zafin soyayya ne da rashin tunani yake dawainiya da shi, amman da zarar ya dawo hayyacin zai gane kuskure suka aikata shi da mahaifinsa”

“Kamin su gane hakan, sai ki zuba musu ido ki ga yadda abubuwan za su yi, kin san dai ba zaki iya ja da mijinki ba ko?”

“Ba zan iya ja da shi ba Hajiya amman ba zan karbi yarinyar nan a matsayin sukura ba”

Hajiyar Maru ta mike tsaye ganin ta yi iya nata ta fice ta bar ma Ammy dakin. Hajiya Turai ta dafe kanta tana kiran kukan da baya kusa da idonta.

“Sallamu Alaikum, daman ni na san ba da saninki Yaya ya aikata wannan abun ba, abun bakinciki abub takaici abun Allah wadai”

Momy ce take fadar hakan daga shigowarta dakin, Hajiya Turai ta dago ta dube.

“Ta ina zan yarda Captain ya auro yarinyar nan, Engr be yi shawara da ni ba, be fada min ba kawai yaje ya aiwatar da abun da zuciyarsa take so”

“To wai haka kika hade hannaye suka zuba ido ba tare da daukar mataki ba?”

“Matakin me zan dauka Hajiya Nafisa? An riga an daura aure me zan yi? Kin san dai Engr ba zai bari na cilastawa Captain sakin yarinyar a yanzu ba”

Momy ta zauna tana karkasa yadda bakincikin ya rabu mata gida gida. Har La'asar Hajiya Turai da Momy suna cikin dakin suna ta juya zancen, bayan saukowa daga sallah La'asar ne Daddy ya shigo dakin, Hajiya Turai ta dauke kai ta juya fuska sai dai hakan be hana shi zama kusa da ita ba, sai ma dariya da yayi yana tsokanarta a gaban Momy.

“Haba Turaita yar Baturiya yau kuma da Engr ake fushi?”

Momy ta kalli dan'uwanta cikin bacin rai ta ce.

“Dole Hajiya Turai ta yi fushi, abin nan ya wuce duk inda kake tunani Yaya, kuma ba a kyauta mata ba, ni ma kuma ba a kyauta min ba, na aikata abu ba tare da tunanin halin da zamu shiga ba, yanzu haka ko da na fito na bar Namra tana kuka saboda bakin auren nan da aka daura a yau da bakar yarinyar can, Namra da Captain suna kaunar junansu amman yanzu wannan auren da daura masa a yau ya lalata komai”

Da kamar mamaki Daddy yake kallon fitinanniyar kanwar tasa.

“Amman Jamal be taba gabatar min da wata magana makamancin haka ba a game da Namra, kuma ni na aikata abun da na aikata ne a yau saboda na gama karantar abun da Jamal yake so ne, sannan abun da kuke ta kushe yarinyar nan da shi koraren ne a gurin wanda ya san gaskiya, ni dai na ga video kuma yanzu haka shigowar da na yi a nan na zo ne da maganar Bashir Sarauta yana falo yana jirana yanzu haka”

“Ai dansa ne ma ya dace ya auri yarinyar tun da yar'uwar badalarce, amman be nema nemawa dansa ba sai mu, kamar dai masu bakin uwa”

Daddy yayi murmushi yana kallon fuskar kyakkyawar matarsa take magana cikin kuka da fushi.

“Sheri ne aka yi mata Turai bata aikata ba, kuma ko da ta aikata tun da har danki yaji zai iya zama da ita a haka mu miye na mu a ciki?”

“Ni dai ba zan karbeta a matsayin suruka ba, kuma ba zan bari ayi bikin komai ba domin ba za a yada hotunanta a matsayin matar Captain ba”

“Daman daura aure dai shi ne wajib, kuma an yi, wadanna abubuwa ne da al'ada ta tana da, shi ma kuma idan bangaren yarinyar suka nuna sha'awar yin haka ba zamu hana su ba, ke dai a bangarenki ne ba zaki yi haka ba, ni ba tsegumi ya kawo ni nan ba, Bashir Sarauta ne ya zo tare da yan'uwansa da iyalinsa akan maganar yarinyar, da yi tunanin ko zaki so saurare a matsayinki na mahaifiyar Captain ko ba komai haka zai share zargi da rashin ganin kimar yarinyar nan da kike yi, amman yanzu na fahimci baki bukatar hakan”

Ya kalli agogon dake daure a wuyan hannunsa.

“Ki shirya na fada miki jirgina zai tashi 5pm na yamma”

“Babu inda zan tafi na tafi na bar yarona a nan da wannan yarinyar nan, idan na bar garin nan sai idan tare da amaryar ne”

Daddy yayi murmushi.

“Amaryar da kika ce baki so? Ayi haka?”

“An dai riga an daura aure yanzu a ba mu amaryarmu mu tafi da ita Kaduna?”

“Ina aka taba haka? Daga daura aure yau babu kintsawa babu komai sai mu tafi karbar Amarya kuma mu wuce da ita Kaduna? A kaduna ina zata zauna ma? Ai dole  mu ma muna bukatar lokaci ba yanzu yanzu ba”

“Duk gidanjen da suke garin Kaduna ace ba a san wanda zata zauna ba? Kai kace wata yar zinari?”

“Tarin gidaje ba shi ne mafitar ba, sai wanda mijinta yake sha'awar su zauna tukuna, wannan ma na aikin mu ba ne, ta ina ma za a dauki amarya akai a Kd bayan mijinta yana nan garin Gusau yana aiki, tare da mu zata zauna ni ba zan iya
Showing 156001 words to 159000 words out of 215510 words