aljannu zasu ce sai sun shiga a jikin wani za su kwanta da ita, har ta fara lalaben number Hajiya Kaltume sai kuma ta tuna ya ce mata aljannun sun ce basa son magana.
“Kai.... Kai.... Kai... Wannan bala'i da me yayi kama? Wannan tashin hankali duk na minene? Abun da ban yi kurciya ba zan yi yanzu? Haka ina ji ina gani yara kanana suka keya min rigar mutunci, yanzu kuma ga wata sabuwar matsalar ta fuskanto ni, karshenta kuma idan ban amince ba zai ce cikin nan bayyana zai yi idan kuma haka ta faru ya zan yi da duniya”
Ta fashe da kuka sosai ta sauko kasa ta zauna tana kuka har wani gurnanin ke fita.
“Wanna yarinya Afrah kin cuceni ba dan ke ba da ban san kofar gidan ko wane malami ba, da yanzu duk wannan bala'in be same ni, saboda ke dan abun da Alhaji ya bar min duk ya kare, kuma ban samu biyan bukata ba, ko da Matsalar ba taki ce ke kadai ba, tun da zuwan na Kaltume ne, kuma ita ba a mata komai ba, gashi ta samu biyan bukata ni kuma ina cikin bala'i”
Kuka take sosai tana kara jin tsanar surukarta a cikin ranta, kuka ta yi sosai har sai da idonta ya kumbura bakinciki ya hade mata, idan cikin bayyana babu wanda zai yarda a daji ta samo shi, domin shekara uku yanzu da faruwar abun, sannan kuma bata san abun da zata fadawa danta da yan'uwanta ba, gashi kuma ba zata iya amincewa da bukatar Aljannu Malam ba, idan ta tuna da fason dake kafarsa ma sai ta ji kamar zata yi amai balle kuma ace ta kwanta gado daya da shi, bakauyen da gora ya gama yi ma fenti a hakora, mutumen da be wuce zama mai gadin gidanta ba. Har aka kira Isha'i kuka take ko da ta hakura idan ta tuna sai ta ji kukan ya dawo mata, ita ba da samun nasara ba ita da kwasar ciki ga kuma bukatar Malam a yanzu, da zuciyarta take shawara ko dai ta kyaleshi ta nemi wani Malamin ne, ta wani bangaren kuma tana ganin kamar kamin ta samu Malamin da zai iya kwantar mata da cikin kamar yadda wannan yayi abu ne mai wahala kuma bata san sherin da zai iya binta da shi ba, ta kuma san cikin ba zai cire a yanzu ba a lokacin da yake wata uku ma aka fada mata akwai matsala a zubarwa bayan kuma ta sha magani be zube ba balle kuma yanzu da ciki ya sha kwanci shekara uku. Carbin dake hannunta kawai take ja ta rasa ma ta ina zata fara, salati zata yi ko tasbihi ko istigifara gaba daya ta rasa abun kamawa sai kuka kawai take tana juya carbin.
“Sallamu Alaikum”
Ta yi gaggawar kawar da fuskarta ba tare da ta amsa sallamar ba, sai dai haka be hana danta Fadeel fahimtar kuka take ba, ya fahimci fushi take dashi domin dazun da ya shigo gaisheta da safe bata amsa masa ba.
“Subhanallahi Hajiya Lafiya”
Ya fada bayan ya zauna a gefenta yana kallonta damuwar dake tattare da shi ta gagara boyuwa. Kamar mai nema sai kawai ta fashe da kuka, abun yana cinta a rai kuma bata isa ta yi labarin da kowa ba, domin babu wanda ya san komai sai aminiyarta Kaltume, ko da zata fadawa kowa a duniya ba zata yi gangancin fadawa Fadeel ba, tana jin kamar ace abun da zata iya fitarwa ne ta tattauna amman babu hali.
“Allah yasa ba ni ne silar zubar hawayen nan ba Hajiya”
Ta kara kawar da kai ta tsakaiga kukan ta share hawayenta, sai dai bata yarda ta kalli gefen da yake ba ma, hakan kuma sai ya kara daga masa hankali.
“Hajiya... Ki yi hakuri dan Allah idan ni na bata miki”
“Fadi ba shi da amfani domin na sha fada babu abun da ya canja, amman dai zan baka zabi uku a yanzu, Fadeel ko dai ka saki Afrah, ko ka kara aure, ko kuma na yafeka yafewa ta har abada...!”
Be san lokacin da jikinsa ya saki ba yayi nauyi a gurin.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Hajiya ta tabbata dai saboda da ni kike zubar da hawayen nan. Hajiya ina son matata sosai domin ina jindadin zama da ita, amman Wallahi zan iya rabuwa da Afrah matukar hakan ne burinki, kuma zan kara aure idan har hakan zai saka ki farinciki, amman ba zan iya hakura da ke ba, ba zan yarda ki yafe ni ba, ba nida wani abu da ya fi ki muhimmanci a duniyar nan, gaisuwar da na yi miki dazun ma na tafi baki amsa min ba, ban wuni cikin farinciki ba”
Ya sauke ajiyar zuciya ya sauke kansa kasa.
“Na ji dadin da kika saukaka min kika ba ni zabi har uku, kuma na zabi na uku zan kara aure kuma na miki alkawari matar da kike so ita zan aura, Allah ya huci zuciyarki”
Ya mike tsaye yana fadin.
“Zan tafi Allah ya tashe mu lafiya”
Har ya fice bata juya ta kalli inda yake ba, bata jin tana da wata makiyiya a yanzu fiye da Afrah, saboda tana ganin saboda ita danta baya mata biyayya kuma ya canja mata. Ada can baya kamin Fadeel yayi aure shi din Mommy's Boy ne kullum yana gida ba shi da abokin hira sai ita, komai zai yi sai ya fada mata tufafi ma ita take bashi shawarar wadanda zai saka, a gidanta yake zaune. Sai dai yana haduwa ya Afrah sai ya fara canja mata, bayan kuma ya guji matar da ta so ya aura da farko, har ta kai ya kasa zama a gidan kamar yadda ta bukata saboda Afrah ta nuna masa ta fi sha'awar zama a gidanta ita kadai ba dole sai a gidan mahaifinsa ba kamar yadda Hajiya Fatee take so, shi ma kuma da yayi tunani sai ya yarda da shawararta, yana yin auren sai rayuwarsa ta koma gaba daya a gidan matarsa, zabin tufafinbda zai saka wasa da dariya ko wani abun na rayuwa da matarsa yake ba da ita ba, idan ma zai nemi shawararta sai idan wani abun ne da ya shafeta ko kuma yake da muhimmanci sosai, idan zai siya mata tufafi zai dauki Afrah su tafi tare Afrah ta zaba mata tufafi mai kyau mai tsada su kawo mata, sai dai hakan baya kara komai sai wutar kiyayyar Afrah a zuciyarta, duk kuwa da kasancewar tana kyautata mata. Wannan ya saka ta fara zagon kasa tana son ya saki matarsa shi kuma ya nuna mata yana sonta sosai, kuma idan ya rabu da ita ba shi da mai rike masa yaransa.
Cikin matukar damuwa Fadeel ya isa gidansa, ya samu kansa da zama a cikin motar ya kasa budewa ya fita, shi dai a ra'ayin kansa ba shi da burin aure mace fiye da daya saboda baya son tashin hankali kuma yana son matarsa tana sonsa, ya yanzu ma yana cikin tashin hankalin rashin jituwar da suke samu da Hajiyarsa ina ga ya kara aure, and all this love da biyayya da Afrah take masa ya rasa da me zai saka mata sai kishiya. Jin yayi ana kwankwasa kofar motar yana daga kai sai yayi arba da annurin zuciyarsa tana aiko masa da murmushi. Ta tsaba ado kamar Sequence Wax din da ya siya mata a gurin Khadeeja Candy ta karbi jikinta sai kyali take kamar an wantsa mata gold. Ya sauke gilashin motar
“Madam”
“Yallabai yau lafiya kake kuwa”
Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya bude motar ya fito ya rufe.
“Habibina fada min me yake damunka daman tun jiya na lura da haka, me ke damunka?”
Sai da ya kasa bakinsa sau biyu sannan ya iya aje numfashi a muhallinsa.
“Afrah yau na ga Hajiya a cikin wani hali da ban taba ganinta ba, ban san wata rana da Hajiya ta zubar da hawaye saboda da ni ba, sai na ranar da aka daura aurena shi amman na farinciki ne yau kuma akasinsa ne”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, me ka aikata haka wanda ya bata mata rai Abban Aiman?”
Yayi shiru yana kallonta ba tare da ya amsa mata ba, tana ganin haka ta san inda matsalar take kuma bata bukatar karin bayani, a take zuciyarta ta fara bugawa.
“Cewa ta yi ka rabu da ni? Hajiya ta ce ka sake ni ne? Dan Allah karka kara minti daya a gidan nan baka aikata abun da mahaifiyarka ta bukata ba, akwai pen da takarda a cikin motar nan dan girman Allah ka dauko ka rubuta min matukar haka ne silar zubar hawayenta”
“Ba saboda haka ba ne”
Ya amsata still yana kallonta.
“To minene?”
“Aure take son na kara....”
Bugun zuciyar da ta ji a yanzu da ya fada mata bukatar Hajiya ya dara wanda ta ji a lokacin da take zargin sakinta Hajiya ta ce yayi. Sai dai ko kadan bata yarda ta nuna masa ba, sai ma dariya data fara yi dariya sosai har sai da mai gadinsu ya juyo ya kalli gurin da suke tsaye.
“Shi ne kawai? Oh Ya Rabbi ai Hajiya ta yi min da sauki, ni a yanzu ba ni da tashin hankali kamar na rabuwa da kai, ko da raina Hajiya zata ce ka cire ka kawo mata duk mai sauki ne matukar bata ce na rayu babu kai ba”
Ta mamaki yake kallonta babu alamar tashin hankali a tare da ita sai ma farinciki.
“Afrah you're joking?”
Ta ware hannayenta ta rika hannunsa suka nufi cikin gidan, sai da ta raka shi har dakinsa ta taimaka masa ya fara cire tufafinsa sannan ta ce.
“Yallabai ko da ka auro ni fa, mahaifina mace uku yake aure, na bude ido a gidan mu na ga mahaifiyata da abokan zama ba ita kadai ba”
“I know amman na san kina hakan ne just to support me amman ku mata baku son kishiya ai”
“Abban Aiman idan ban taimaka maka ka yi ma Hajiya biyayya ba ni da kai duk a wuta zamu tashi, karka manta ni fa yar gidan Malamai ce, an karantar da ni ni ma na karantar, na san hakki uwa akan yaya ta ina zan yarda Hajiya ta sake zubar da hawaye saboda mu? Dan Allah karka fara tunanin wani abu ko ka damu, kuma wanda Hajiya take so zaka aura”
Ta fada tana lakatar hancinsa tana dariya as normal yadda ta saba kamar be fada mata komai ba.
“Shiga ka yi wanka ka fito bari na shirya abinci, kuma sauran idan ka fito ka manta baka yaba kwalliyar da na yi maka ba”
Ta bukata sannan ta fice tana dariya, shi dai mamakin karfin halinta ya hana shi motsawa daga inda yake ma. Tana fita dakin ta nufi kitchen dinta kofar kitchen din ta fara rikewa ta kai hannu ta dafa zuciyarta dayan hannun kuma ta rike kofar kitchen din kamin ta saki ta nufi sink ta dora hannayenta hawaye suka fara floating.
HURRIYA POV.
Sai da aka fara kiran Magariba sannan ta fito daga Garden din ta dawo cikin falon, dakinta ta shiga ta yi alwala ta yi sallah sannan ta sauko Namra na yi mata magana.
“Na tura miki kudin”
Ta dauri ta nufi gurin da take zaune ta rumgume ta.
“Na gode sosai Yaya Namra”
“Never mind yar kanwata”
Namra ta amsa mata tana dariya, Hurriya ta zauna kusa da ita tana matsar yatsun hannunta.
“Yaya Namra”
Ta dago ta dubeta.
“Ina son na tafi gidansu Husna dan Allah”
“Yanzu?”
“Eh ba zan dade ba”
“Okay sai kin dawo”
“Amman Momy bata sani ba, kar ta zo duba ni, kuma kin san bata son a shiga dakinta balle na fada mata”
“tafi zan fada mata”
Ta tashi cikin jindadi da murmushi a fuskarta ta sake haurawa sama ta shiga dakinta, jakarta ta bude ta dauko ATM dinta ta boye a cikin rigarta sannan ta dauko hijab ta saka ta sake saukowa ta fice. Tafiya take kamar ana dagata sama saboda sauri tsoronta kar wani ya fito daga yaran Hajiya Kaltume su hanata fita ko kuma Appa ya dawo a daidai lokacin ta san shi ma ba zai barta ta fita ba. Kamar an korota haka ta rika knocking gate din gidansu kawarta kuma Neighbor dinsu a house four ne tsakaninsu. Mai gadin na bude gate din ta fada da sauri.
“Ina wuni Baba”
“Lafiya Kalau Hurriya ce”
“Ni ce Baba sannu da aiki”
“Yauwa”
Ta nufi main door din tana tafiya a hankali saboda ta shigo cikin gidan. A falo ta samu kawarta da sisters dinta suna hira, Husna na ganinta ta tashi da sauri ta rumgume ta
“Oyoyo Hurry”
Hurriya ta yi dariya, sai da ta gaishesu gaba daya sannan suka shiga dakin Husna. ATM dinta ne first abun da ta fara danka mata.
“Me zan yi da Atm”
“Ba ke na bawa ba, dan Allah taimako na ke son ki yi min Husna kin ga ke ana barinki fita, dan Allah ki kaiwa Amma akwai kudi a ciki 20k dazun Yaya Namra ta saka min, kin ga ni ba school nake zuwa ba yanzu balle na biya, kuma idan na ce zan je Hajiya ba zata bari ba, Appa ma fada yake yi”
“In Shaa Allah zan kai mata, Hurriya wai ya zancen makarantar ki, an kusa rufe siyar da form fa, kin ga da kina zuwa makaranta irin wannan duk ba zai gagara ba sai ki yi satar hanyar kawai ki tafi”
“Ban sani ba Husna, ba ni zan saka kaina makaranta ba Appa kuma be yi wani motsi ba, sun kyale ni haka nan zama kawai nake, gidan ma babu dadi”
Ta sauke kanta kasa hawaye suka fara sauko mata.
“Husna I'm lonely, komai baya min dadi yanzu i miss those old days da zan zauna na yi hira da Appana yana dariya, na yi marmari jin muryar Amma, na yi marmarin ganinmu a inuwa daya, na yi marmarin Hamad fadan da muke ma na yi marmarinsa, Husna kowa yana da uwa a gidan yana da abokin hira ni kuma ba ni da shi, idan suna bukatar abu kowa zai je gurin mahaifiyarsa ta yi masa ko Appa ni kuma ba ni da uwa a gidan, idan kuma na kusanci gurin da Appa yake sai ya rufe ni da fada, baya ma son ganina”
Husna ta dafa kafarta tana jin tausayinta.
“Ki yi hakuri Hurriya, wata rana komai zai wuce ya zama tarihi”
Hurriya ta kalleta hawaye na mata sallama.
“Hakan na nufin Appa ba zai sake so na kamar da ba kenan? Hamad ba zai dawo ba?”
“Ba haka nake nufi ba, ina nufin wata rana rayuwar farinciki zata dawo komai zai wuce, dazun ma sai da muka yi hirarki da Umma ita ma take tambayata maganar karatunki, tace kina bata tausayi sosai saboda halin da kike ciki”
“Husna ina cikin kunci ina jin rashin sakewa sai na ji kamar a wani guri nake rabe ba a gidan mahaifina ba”
“Komai zai wuce Hurriya, ki yi hakuri, me Amma zata yi da wannan kudin?”
Ta share hawayenta.
“Gwaggo ta fada min an kai Amma gurin magani kuma mutumen yace sai an bashi 150k shi ne dazun da Yaya Namra zata siya min abu na ce bana so ta ba ni kudin kawai zan bawa Amma, saboda Gwaggo ta ce basu da kudi yanzu duk sun kashe kudin da ya rage musu gidan da suke ciki za a siyar ni kuma bana son a siyar da gidan, kuma ban isa na tunkari Appa na ce ina son kudi ba, sai ya fara min fada ni tsoron ganinsa ma nake yanzu”
“Innalillahi Abun har ya kai haka? Wallahi duk wanda ya raba ki da mahaifinki ya ci amanarki Hurriya, da a baya ne ko miliyan kika ce kina so Appa zai baki. Ya Allah ka dubi Amma ka bata lafiya, zan fadawa Umma in Shaa Allah zata cika kudin”
Hurriya ta rumgume ta da sauri.
“Na gode Husna, na gode Allah ya saka miki da alheri”
“Ba komai, Allah ya kawo miki sauki”
“Ameen, zan tafi kar a fara nema bana kusa”
“Okay muje ki gaishe da Umma sai na raka ki”
Sun tashi a tare Husna ta saka Hijab dinta suka fito daga dakin, Husna ce ta yi mata jagora zuwa dakin Ummanta not because of gidan yana bakonta sai dan zata fi sakewa idan Husna ta shiga gaba. Mahaifiyar Husna ta amsa da far'a tana sakawa Hurriya Albarka sannan ta kara ja mata kunne akan addu'a da kuma hakuri.
“Karki yi wasa da addu'a kina ganin yadda aka maida mahaifiyarki bayan an cireta a gidan ubanki, ke ma kuma an shata muku layi, ki yi ta fadawa Allah matsalarki, sannan ki kara hakuri ki yi da hakuri Hurriya komai zai wuce”
“In Shaa Allahu Umma na gode”
Ta tashi ta fito, suka jero da Husna a harabar gidan suna tafi suna hira, sam bata lura da Yayan Husna dake tsaye can gefe dare da Abokinsa yana hira ba har sai da abokin ya kirata.
“Hey Young Lady...”
A tare suka juya suna hada ido sai ya sakar mata mata murmushi ita ma ta dan yi masa murmushinta mai tsada kadan ta gaishe su.
“Ina wuninku”
Mutumen ya tako ta karaso gurin da suke tsaye tare da Yayan Husna, still tufafin da ta fara ganinshi da su ne sanye a jikinsa wato wando sojoji da bakar rigarsu T-shirt.
“Kin gane ni”
Ta daga kai kadan sai yayi murmushi.
“Ina kawarki?”
“Yayata ce”
“Amma fa ta iya driving, kun ba ni wahala dazun fa, but still i enjoyed it, it was fantastic”
Bata ce masa komai ba har ya sake wata tambayar.
“Nan unguwar kuke”
Nan ma bata amsa masa ba, Yayan Husna ya tambaye shi.
“Ka santa ne Ethiopian?”
“Yeah i meet them today at Sarauta's Mall”
Ta juya zata fara tafiya.
“Please ki kirata mu gaisa idan kusa ne, or invite me na je na gaishe da Yayarmu”
“Zan fada mata”
Ta fada ba tare da ta juyo ba.
“Okay ina nan ina jira”
As always bata ce masa uffan ba, sai kallon juna da suka yi da Husna, sannan ta shiga fadawa Husna yadda suka hadu...
[11/10, 5:55 AM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘 08036126660
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to
Showing 39001 words to 42000 words out of 215510 words
“Kai.... Kai.... Kai... Wannan bala'i da me yayi kama? Wannan tashin hankali duk na minene? Abun da ban yi kurciya ba zan yi yanzu? Haka ina ji ina gani yara kanana suka keya min rigar mutunci, yanzu kuma ga wata sabuwar matsalar ta fuskanto ni, karshenta kuma idan ban amince ba zai ce cikin nan bayyana zai yi idan kuma haka ta faru ya zan yi da duniya”
Ta fashe da kuka sosai ta sauko kasa ta zauna tana kuka har wani gurnanin ke fita.
“Wanna yarinya Afrah kin cuceni ba dan ke ba da ban san kofar gidan ko wane malami ba, da yanzu duk wannan bala'in be same ni, saboda ke dan abun da Alhaji ya bar min duk ya kare, kuma ban samu biyan bukata ba, ko da Matsalar ba taki ce ke kadai ba, tun da zuwan na Kaltume ne, kuma ita ba a mata komai ba, gashi ta samu biyan bukata ni kuma ina cikin bala'i”
Kuka take sosai tana kara jin tsanar surukarta a cikin ranta, kuka ta yi sosai har sai da idonta ya kumbura bakinciki ya hade mata, idan cikin bayyana babu wanda zai yarda a daji ta samo shi, domin shekara uku yanzu da faruwar abun, sannan kuma bata san abun da zata fadawa danta da yan'uwanta ba, gashi kuma ba zata iya amincewa da bukatar Aljannu Malam ba, idan ta tuna da fason dake kafarsa ma sai ta ji kamar zata yi amai balle kuma ace ta kwanta gado daya da shi, bakauyen da gora ya gama yi ma fenti a hakora, mutumen da be wuce zama mai gadin gidanta ba. Har aka kira Isha'i kuka take ko da ta hakura idan ta tuna sai ta ji kukan ya dawo mata, ita ba da samun nasara ba ita da kwasar ciki ga kuma bukatar Malam a yanzu, da zuciyarta take shawara ko dai ta kyaleshi ta nemi wani Malamin ne, ta wani bangaren kuma tana ganin kamar kamin ta samu Malamin da zai iya kwantar mata da cikin kamar yadda wannan yayi abu ne mai wahala kuma bata san sherin da zai iya binta da shi ba, ta kuma san cikin ba zai cire a yanzu ba a lokacin da yake wata uku ma aka fada mata akwai matsala a zubarwa bayan kuma ta sha magani be zube ba balle kuma yanzu da ciki ya sha kwanci shekara uku. Carbin dake hannunta kawai take ja ta rasa ma ta ina zata fara, salati zata yi ko tasbihi ko istigifara gaba daya ta rasa abun kamawa sai kuka kawai take tana juya carbin.
“Sallamu Alaikum”
Ta yi gaggawar kawar da fuskarta ba tare da ta amsa sallamar ba, sai dai haka be hana danta Fadeel fahimtar kuka take ba, ya fahimci fushi take dashi domin dazun da ya shigo gaisheta da safe bata amsa masa ba.
“Subhanallahi Hajiya Lafiya”
Ya fada bayan ya zauna a gefenta yana kallonta damuwar dake tattare da shi ta gagara boyuwa. Kamar mai nema sai kawai ta fashe da kuka, abun yana cinta a rai kuma bata isa ta yi labarin da kowa ba, domin babu wanda ya san komai sai aminiyarta Kaltume, ko da zata fadawa kowa a duniya ba zata yi gangancin fadawa Fadeel ba, tana jin kamar ace abun da zata iya fitarwa ne ta tattauna amman babu hali.
“Allah yasa ba ni ne silar zubar hawayen nan ba Hajiya”
Ta kara kawar da kai ta tsakaiga kukan ta share hawayenta, sai dai bata yarda ta kalli gefen da yake ba ma, hakan kuma sai ya kara daga masa hankali.
“Hajiya... Ki yi hakuri dan Allah idan ni na bata miki”
“Fadi ba shi da amfani domin na sha fada babu abun da ya canja, amman dai zan baka zabi uku a yanzu, Fadeel ko dai ka saki Afrah, ko ka kara aure, ko kuma na yafeka yafewa ta har abada...!”
Be san lokacin da jikinsa ya saki ba yayi nauyi a gurin.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Hajiya ta tabbata dai saboda da ni kike zubar da hawayen nan. Hajiya ina son matata sosai domin ina jindadin zama da ita, amman Wallahi zan iya rabuwa da Afrah matukar hakan ne burinki, kuma zan kara aure idan har hakan zai saka ki farinciki, amman ba zan iya hakura da ke ba, ba zan yarda ki yafe ni ba, ba nida wani abu da ya fi ki muhimmanci a duniyar nan, gaisuwar da na yi miki dazun ma na tafi baki amsa min ba, ban wuni cikin farinciki ba”
Ya sauke ajiyar zuciya ya sauke kansa kasa.
“Na ji dadin da kika saukaka min kika ba ni zabi har uku, kuma na zabi na uku zan kara aure kuma na miki alkawari matar da kike so ita zan aura, Allah ya huci zuciyarki”
Ya mike tsaye yana fadin.
“Zan tafi Allah ya tashe mu lafiya”
Har ya fice bata juya ta kalli inda yake ba, bata jin tana da wata makiyiya a yanzu fiye da Afrah, saboda tana ganin saboda ita danta baya mata biyayya kuma ya canja mata. Ada can baya kamin Fadeel yayi aure shi din Mommy's Boy ne kullum yana gida ba shi da abokin hira sai ita, komai zai yi sai ya fada mata tufafi ma ita take bashi shawarar wadanda zai saka, a gidanta yake zaune. Sai dai yana haduwa ya Afrah sai ya fara canja mata, bayan kuma ya guji matar da ta so ya aura da farko, har ta kai ya kasa zama a gidan kamar yadda ta bukata saboda Afrah ta nuna masa ta fi sha'awar zama a gidanta ita kadai ba dole sai a gidan mahaifinsa ba kamar yadda Hajiya Fatee take so, shi ma kuma da yayi tunani sai ya yarda da shawararta, yana yin auren sai rayuwarsa ta koma gaba daya a gidan matarsa, zabin tufafinbda zai saka wasa da dariya ko wani abun na rayuwa da matarsa yake ba da ita ba, idan ma zai nemi shawararta sai idan wani abun ne da ya shafeta ko kuma yake da muhimmanci sosai, idan zai siya mata tufafi zai dauki Afrah su tafi tare Afrah ta zaba mata tufafi mai kyau mai tsada su kawo mata, sai dai hakan baya kara komai sai wutar kiyayyar Afrah a zuciyarta, duk kuwa da kasancewar tana kyautata mata. Wannan ya saka ta fara zagon kasa tana son ya saki matarsa shi kuma ya nuna mata yana sonta sosai, kuma idan ya rabu da ita ba shi da mai rike masa yaransa.
Cikin matukar damuwa Fadeel ya isa gidansa, ya samu kansa da zama a cikin motar ya kasa budewa ya fita, shi dai a ra'ayin kansa ba shi da burin aure mace fiye da daya saboda baya son tashin hankali kuma yana son matarsa tana sonsa, ya yanzu ma yana cikin tashin hankalin rashin jituwar da suke samu da Hajiyarsa ina ga ya kara aure, and all this love da biyayya da Afrah take masa ya rasa da me zai saka mata sai kishiya. Jin yayi ana kwankwasa kofar motar yana daga kai sai yayi arba da annurin zuciyarsa tana aiko masa da murmushi. Ta tsaba ado kamar Sequence Wax din da ya siya mata a gurin Khadeeja Candy ta karbi jikinta sai kyali take kamar an wantsa mata gold. Ya sauke gilashin motar
“Madam”
“Yallabai yau lafiya kake kuwa”
Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya bude motar ya fito ya rufe.
“Habibina fada min me yake damunka daman tun jiya na lura da haka, me ke damunka?”
Sai da ya kasa bakinsa sau biyu sannan ya iya aje numfashi a muhallinsa.
“Afrah yau na ga Hajiya a cikin wani hali da ban taba ganinta ba, ban san wata rana da Hajiya ta zubar da hawaye saboda da ni ba, sai na ranar da aka daura aurena shi amman na farinciki ne yau kuma akasinsa ne”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, me ka aikata haka wanda ya bata mata rai Abban Aiman?”
Yayi shiru yana kallonta ba tare da ya amsa mata ba, tana ganin haka ta san inda matsalar take kuma bata bukatar karin bayani, a take zuciyarta ta fara bugawa.
“Cewa ta yi ka rabu da ni? Hajiya ta ce ka sake ni ne? Dan Allah karka kara minti daya a gidan nan baka aikata abun da mahaifiyarka ta bukata ba, akwai pen da takarda a cikin motar nan dan girman Allah ka dauko ka rubuta min matukar haka ne silar zubar hawayenta”
“Ba saboda haka ba ne”
Ya amsata still yana kallonta.
“To minene?”
“Aure take son na kara....”
Bugun zuciyar da ta ji a yanzu da ya fada mata bukatar Hajiya ya dara wanda ta ji a lokacin da take zargin sakinta Hajiya ta ce yayi. Sai dai ko kadan bata yarda ta nuna masa ba, sai ma dariya data fara yi dariya sosai har sai da mai gadinsu ya juyo ya kalli gurin da suke tsaye.
“Shi ne kawai? Oh Ya Rabbi ai Hajiya ta yi min da sauki, ni a yanzu ba ni da tashin hankali kamar na rabuwa da kai, ko da raina Hajiya zata ce ka cire ka kawo mata duk mai sauki ne matukar bata ce na rayu babu kai ba”
Ta mamaki yake kallonta babu alamar tashin hankali a tare da ita sai ma farinciki.
“Afrah you're joking?”
Ta ware hannayenta ta rika hannunsa suka nufi cikin gidan, sai da ta raka shi har dakinsa ta taimaka masa ya fara cire tufafinsa sannan ta ce.
“Yallabai ko da ka auro ni fa, mahaifina mace uku yake aure, na bude ido a gidan mu na ga mahaifiyata da abokan zama ba ita kadai ba”
“I know amman na san kina hakan ne just to support me amman ku mata baku son kishiya ai”
“Abban Aiman idan ban taimaka maka ka yi ma Hajiya biyayya ba ni da kai duk a wuta zamu tashi, karka manta ni fa yar gidan Malamai ce, an karantar da ni ni ma na karantar, na san hakki uwa akan yaya ta ina zan yarda Hajiya ta sake zubar da hawaye saboda mu? Dan Allah karka fara tunanin wani abu ko ka damu, kuma wanda Hajiya take so zaka aura”
Ta fada tana lakatar hancinsa tana dariya as normal yadda ta saba kamar be fada mata komai ba.
“Shiga ka yi wanka ka fito bari na shirya abinci, kuma sauran idan ka fito ka manta baka yaba kwalliyar da na yi maka ba”
Ta bukata sannan ta fice tana dariya, shi dai mamakin karfin halinta ya hana shi motsawa daga inda yake ma. Tana fita dakin ta nufi kitchen dinta kofar kitchen din ta fara rikewa ta kai hannu ta dafa zuciyarta dayan hannun kuma ta rike kofar kitchen din kamin ta saki ta nufi sink ta dora hannayenta hawaye suka fara floating.
HURRIYA POV.
Sai da aka fara kiran Magariba sannan ta fito daga Garden din ta dawo cikin falon, dakinta ta shiga ta yi alwala ta yi sallah sannan ta sauko Namra na yi mata magana.
“Na tura miki kudin”
Ta dauri ta nufi gurin da take zaune ta rumgume ta.
“Na gode sosai Yaya Namra”
“Never mind yar kanwata”
Namra ta amsa mata tana dariya, Hurriya ta zauna kusa da ita tana matsar yatsun hannunta.
“Yaya Namra”
Ta dago ta dubeta.
“Ina son na tafi gidansu Husna dan Allah”
“Yanzu?”
“Eh ba zan dade ba”
“Okay sai kin dawo”
“Amman Momy bata sani ba, kar ta zo duba ni, kuma kin san bata son a shiga dakinta balle na fada mata”
“tafi zan fada mata”
Ta tashi cikin jindadi da murmushi a fuskarta ta sake haurawa sama ta shiga dakinta, jakarta ta bude ta dauko ATM dinta ta boye a cikin rigarta sannan ta dauko hijab ta saka ta sake saukowa ta fice. Tafiya take kamar ana dagata sama saboda sauri tsoronta kar wani ya fito daga yaran Hajiya Kaltume su hanata fita ko kuma Appa ya dawo a daidai lokacin ta san shi ma ba zai barta ta fita ba. Kamar an korota haka ta rika knocking gate din gidansu kawarta kuma Neighbor dinsu a house four ne tsakaninsu. Mai gadin na bude gate din ta fada da sauri.
“Ina wuni Baba”
“Lafiya Kalau Hurriya ce”
“Ni ce Baba sannu da aiki”
“Yauwa”
Ta nufi main door din tana tafiya a hankali saboda ta shigo cikin gidan. A falo ta samu kawarta da sisters dinta suna hira, Husna na ganinta ta tashi da sauri ta rumgume ta
“Oyoyo Hurry”
Hurriya ta yi dariya, sai da ta gaishesu gaba daya sannan suka shiga dakin Husna. ATM dinta ne first abun da ta fara danka mata.
“Me zan yi da Atm”
“Ba ke na bawa ba, dan Allah taimako na ke son ki yi min Husna kin ga ke ana barinki fita, dan Allah ki kaiwa Amma akwai kudi a ciki 20k dazun Yaya Namra ta saka min, kin ga ni ba school nake zuwa ba yanzu balle na biya, kuma idan na ce zan je Hajiya ba zata bari ba, Appa ma fada yake yi”
“In Shaa Allah zan kai mata, Hurriya wai ya zancen makarantar ki, an kusa rufe siyar da form fa, kin ga da kina zuwa makaranta irin wannan duk ba zai gagara ba sai ki yi satar hanyar kawai ki tafi”
“Ban sani ba Husna, ba ni zan saka kaina makaranta ba Appa kuma be yi wani motsi ba, sun kyale ni haka nan zama kawai nake, gidan ma babu dadi”
Ta sauke kanta kasa hawaye suka fara sauko mata.
“Husna I'm lonely, komai baya min dadi yanzu i miss those old days da zan zauna na yi hira da Appana yana dariya, na yi marmari jin muryar Amma, na yi marmarin ganinmu a inuwa daya, na yi marmarin Hamad fadan da muke ma na yi marmarinsa, Husna kowa yana da uwa a gidan yana da abokin hira ni kuma ba ni da shi, idan suna bukatar abu kowa zai je gurin mahaifiyarsa ta yi masa ko Appa ni kuma ba ni da uwa a gidan, idan kuma na kusanci gurin da Appa yake sai ya rufe ni da fada, baya ma son ganina”
Husna ta dafa kafarta tana jin tausayinta.
“Ki yi hakuri Hurriya, wata rana komai zai wuce ya zama tarihi”
Hurriya ta kalleta hawaye na mata sallama.
“Hakan na nufin Appa ba zai sake so na kamar da ba kenan? Hamad ba zai dawo ba?”
“Ba haka nake nufi ba, ina nufin wata rana rayuwar farinciki zata dawo komai zai wuce, dazun ma sai da muka yi hirarki da Umma ita ma take tambayata maganar karatunki, tace kina bata tausayi sosai saboda halin da kike ciki”
“Husna ina cikin kunci ina jin rashin sakewa sai na ji kamar a wani guri nake rabe ba a gidan mahaifina ba”
“Komai zai wuce Hurriya, ki yi hakuri, me Amma zata yi da wannan kudin?”
Ta share hawayenta.
“Gwaggo ta fada min an kai Amma gurin magani kuma mutumen yace sai an bashi 150k shi ne dazun da Yaya Namra zata siya min abu na ce bana so ta ba ni kudin kawai zan bawa Amma, saboda Gwaggo ta ce basu da kudi yanzu duk sun kashe kudin da ya rage musu gidan da suke ciki za a siyar ni kuma bana son a siyar da gidan, kuma ban isa na tunkari Appa na ce ina son kudi ba, sai ya fara min fada ni tsoron ganinsa ma nake yanzu”
“Innalillahi Abun har ya kai haka? Wallahi duk wanda ya raba ki da mahaifinki ya ci amanarki Hurriya, da a baya ne ko miliyan kika ce kina so Appa zai baki. Ya Allah ka dubi Amma ka bata lafiya, zan fadawa Umma in Shaa Allah zata cika kudin”
Hurriya ta rumgume ta da sauri.
“Na gode Husna, na gode Allah ya saka miki da alheri”
“Ba komai, Allah ya kawo miki sauki”
“Ameen, zan tafi kar a fara nema bana kusa”
“Okay muje ki gaishe da Umma sai na raka ki”
Sun tashi a tare Husna ta saka Hijab dinta suka fito daga dakin, Husna ce ta yi mata jagora zuwa dakin Ummanta not because of gidan yana bakonta sai dan zata fi sakewa idan Husna ta shiga gaba. Mahaifiyar Husna ta amsa da far'a tana sakawa Hurriya Albarka sannan ta kara ja mata kunne akan addu'a da kuma hakuri.
“Karki yi wasa da addu'a kina ganin yadda aka maida mahaifiyarki bayan an cireta a gidan ubanki, ke ma kuma an shata muku layi, ki yi ta fadawa Allah matsalarki, sannan ki kara hakuri ki yi da hakuri Hurriya komai zai wuce”
“In Shaa Allahu Umma na gode”
Ta tashi ta fito, suka jero da Husna a harabar gidan suna tafi suna hira, sam bata lura da Yayan Husna dake tsaye can gefe dare da Abokinsa yana hira ba har sai da abokin ya kirata.
“Hey Young Lady...”
A tare suka juya suna hada ido sai ya sakar mata mata murmushi ita ma ta dan yi masa murmushinta mai tsada kadan ta gaishe su.
“Ina wuninku”
Mutumen ya tako ta karaso gurin da suke tsaye tare da Yayan Husna, still tufafin da ta fara ganinshi da su ne sanye a jikinsa wato wando sojoji da bakar rigarsu T-shirt.
“Kin gane ni”
Ta daga kai kadan sai yayi murmushi.
“Ina kawarki?”
“Yayata ce”
“Amma fa ta iya driving, kun ba ni wahala dazun fa, but still i enjoyed it, it was fantastic”
Bata ce masa komai ba har ya sake wata tambayar.
“Nan unguwar kuke”
Nan ma bata amsa masa ba, Yayan Husna ya tambaye shi.
“Ka santa ne Ethiopian?”
“Yeah i meet them today at Sarauta's Mall”
Ta juya zata fara tafiya.
“Please ki kirata mu gaisa idan kusa ne, or invite me na je na gaishe da Yayarmu”
“Zan fada mata”
Ta fada ba tare da ta juyo ba.
“Okay ina nan ina jira”
As always bata ce masa uffan ba, sai kallon juna da suka yi da Husna, sannan ta shiga fadawa Husna yadda suka hadu...
[11/10, 5:55 AM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘 08036126660
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14 Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72