ciki”

Sai Hajiya Fatee ta daga hannu tana fadin.

“Wata kila abun yar'uwar ne ya shafeta kin san abun da ya taba gira shi ya kai ga ido har ya taba hanci, idan abun da ta yi karki saka kanki a damuwa kwana nawa ya rage miki ki har gidan ma, kuma wannan ai abun farinciki a gurinku, kowa be lalace ba sai Hurriya na tabbatar da Iyami tana lafiya ace wani ne a cikin yaran Hajiya Kaltume yayi haka farinciki zata yi ”

“Kwarai kuwa shiyasa ni ma bana fatan alheri ya same ta sai sheri”

Hajiya Fatee ta wuce gaba suka jera da Kaltume har wajen gidan, kamin Fadeel ya juya motarsa suka nufi karamin gate din gidan na bangaren Hajiya Kaltume. Daga inda suke tsaye suka hango shigowar manyan motocin na alfarma har hudu cikin gidan, duka motocin aka nufi bangaren Momy da su.

“To baki kuka yi kuma?”

“Ta yi dai ita yar karyar arziki, ita din ma ba barinta zan yi ba Wallahi”

“Aifa ki bari aikin Malam ya fara kawai sai wanda kika so zai zauna a gidan nan, ni na manta ban fada miki ba Afrah fa tana gidansu yaran suna gidana shi kanshi jiya gida ya kwana”

Hajiya Kaltume ta rike baki.

“Ki ce Allah”

“Ba kina wasa da lamarin Malam ba? Hmmmm”

Hajiya Kaltume ta jinjina kai tana kara ganin girman Malamin da kwarewar aikinsa, Afrah da ta gagari Hajiya Fatee yau ace Fadeel ya kora Afrah gida. Babu halin yin wata doguwar magana saboda Fadeel ya faka mota a gabansu ya budewa mahaifiyarsa.

“Hajiya Fatee zamu yi waya”

Hajiya Fatee bata sake furta wani abu ba saboda Fadeel yana gurin sai dai ta yi murmushi mai sauti ta shiga motar, Fadeel ya ja bayan yayi ma surukarsa to be sallama.




Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[12/15/2023, 4:15 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURRIYA*

4️⃣2️⃣




Da tunani kala kala Momy ta sauko falon Namra na bayanta.

“Yaya yau kai ne a cikin gidana?”

Daddy dake zaune akan kujera tare da sauran yan'uwansa yayye da kanne yayi murmushi.

“Nafisa mamakin zuwana kike ne?”

“Kwarai kuwa, Yaya tun da aka kawo ni gidan nan sau daya ka taba zuwa gidan nan fa, da Hajiya Turai ce ba zan yi mamaki ba, amman ganinka ya saka ni a fargaba Allah yasa ba Captain ya ce na yi masa wani abu ba?”

Alhaji Munzali yayi dariya, Daddy ma dariyar yayi ya ce.

“Saboda ba ni da kunya zai na taso na kawo miki takakka har gida?”

Ta yi dariya.

“Namra duk a firgicce take ita ma ta dauka Captain ya turoka, saboda jiya ya zo nan yana neman a kai shi gidansu Hurriya na hana Namra, wata kila hakan ya fusata shi ya kai karata a gurinka”

“Hakan da kika yi ai kin yi daidai, Ammy sa ma ta yi masa magana be so ma amman daga karshe dai ya fahimta kuma yace ya hakura”

Momy ta zaro ido tana dukan kirjinta.

“Ya hakura yaya? Amman ya kyautawa kansa daman can yarinyar bata dace da shi ba Wallahi, ni daman na san Hajiya Turai ba zata yarda danta ya auri yarinyar nan ba”

Daddy ya gyara babbar rigarsa yana kallon Namra dake jera musu abun karyawa.

“So jiya mun yi magana da Captain saboda ya shigar da kara DSS yanzu kuma yana son ya janye karar ne a hannata komai a gurin mahaifinta, ni kuma yau zan koma Kaduna, shiyasa na zo yanzu na san be isa fita ba ina son na yi magana da shi mu kai karshe”

“Hakan yayi, ban da Abin Captain na son wahalar da kai miye na wani shigar da kara, yarinyar nan fa makauniya ce ma idon za su bude ba za su bude ba Allah masani amman ya tsoma kansa a damuwarta har da ikirarin aurenta kamar wanda baya cikin hayyacinsa”

“Wannan maganar kuma ina tunanin ta wuce Nafisa, ki sallamawa mai gidanki zan yi magana da shi”

“Toh Yaya”

Ta tashi jikina na rawa ta nufi bangaren Appa, a nan Daddy ya samu gaisawa da Namra yana tambayarta ya karatu.

“Ai na kare, next week zan tafi service Kaduna In Sha Allah”

“Abu yayi kyau, muna da bakuwa kenan”

Daddy ya fada sai ta yi murmushi tana jin farinciki jin cewar Captain ya hakura da auren Hurriya. Kamar yayan mahaifiyarta Alhaji Munzali ya san dalilin farincikinta sai ya bijiro mata da makamanciyar maganar.

“Aure fa Namra?”

Ta yi shiru ta noce kai kasa, Daddy yayi murmushi ya amsawa Alhaji Munzali yana kare yarsa.

“Za'ayi a daga mana kafa mana Alhaji, komai ai lokaci ne za ayi babu jimawa In Shaa Allah”

Yanayin yadda Daddy ya bada amsar sai ta ji kamar yana mata inkiya da auren Captain ne, hakan ya kara fadada farincikinta.

“Alhaji Rufa'i ku taba wani abu mana, kamin nan da wasu shekaru Nafisa ta mana gorin mun shago gidanta ba mu ci komai ba, kasan Nafisa akwai rike abu ga iya gori”

Sai duk suka saka dariya har Daddy da yayi maganar. Daddy ya dauki ruwa ya sha ya ci yankan cake daya sauran kuma kowa ya ci abun da yake sha'awa even though ba san da zuwansu ba abun da yake gidan na tabawa ne Namra ta kawo. Appa ne ya shigo dakin yana sanye da Babbar riga irin ta Malam Bahaushe sky blue shaddar dake jikinsa har wani kara take tsabar sabun taka, be zauna ba sai da ya mikawa Alhaji Aliyu Turaki hannu biyu suka gaisa yana masa maraba da zuwa.

“Yau Yaya da kansa a gidanmu”

“To kai ma gorin zaka min kenan, daman ance idan zama yayi dadi miji yana daukar dabi'un mata, mata ma tana daukar dabi'un miji”

Momy ta yi dariya tana zaunawa, Appa ma dariyar yayi ya mikawa sauran hannu suka gaisa, sannan ya zauna.

“Toh Allah yasa ba laifi muka yi ba”

Appa ya fada, sai Daddy ya kalli Alhaji Sadiq ya ce.

“Ka gani ko? Ita ma haka ta ce mana”

Sai duk suka saka dariya har Namra, sai suka natsu sannan Daddy ya kalli Namra da Momy ya ce.

“To Nafisa ke da Namra ku ba mu guri zamu yi magana”

Momy ta tashi ta wuce sama ranta fes, Namra ma ba laifi ta ji farincikin fasa auren da Captain yayi a yanzu kuma ba zata iya fadar dalili ba. Sai da suka haye sama gaba daya sannan Daddy ya kalli Appa ya ce.

“A cikin mu nan babu mai bukatar gabatar da kansa, musamman ma ni na san ni na baka auren Nafisa da hannuna, domin ni mahaifinmu ya wakilta na bada aurenta a madadinsa”

“Haka ne ranka ya dade”

Appa ya fada cikin girmama, domin bayan alakar auratayya Appa ya san waye Engr A A Turaki a fannin naira da kasuwanci.

“Toh da farko dai na zo nan ne saboda na jajanta maka abun da ya faru da yarka, ba abu mai dadi ba muna jajanta maka”

Appa ya sauke ajiyar zuciya ransa yayi masa babu dadi.

“Wani ne yake kokarin ganin ya mutuncina, domin wannan abun ni aka taba ba wai Hurriya ba, kuma yarinyar nan ta da kur'ane a gaban yan'uwanta a gabana ta ce bata aikata ba, sheri ne kawai na makiya, ba kuma zan bar maganar ba yanzu haka mun yi da Lawyer na zai zo ya same ni yau mu tatauna matakin da ya kamata mu dauka”

Daddy yayi murmushi

“Wani suruki da baka san da zamansa ba har ya dauki matakin kai yaron DSS, ya riga ka daukar mataki ina zaton be san ma Hurriya ta yi rantsuwa ba amman yana gaba gaba gurin yarda da cewar bata aikata ba, kusan shi ne silar zuwana nan hankalinsa ya tashi har yana zaton ko ka kore Hurriya ne?”

Appa yayi ma Daddy kallon rashin fahimta

“Aa ban koreta ba, Gwaggonta ta tafi da ita zata fi samun kulawa a can saboda bakinciki abun da aka yi mata, ya taba ta sosai har ya zama jijiyar dake aika sako a idonta zuwa kwakwalwarta ta tabu, idon ya rufe gaba daya”

“Duka sukurinka ya fada mana haka, babu kalar haukar da be mana ba akan Hurriya”

Wannan karon Alhaji Munzali ne yayi magabar. Appa ya kalli Daddy ya ce.

“Ranka ya dade ban gane inda ka dosa ba, Wallahi”

Daddy yayi murmushi ya sake yin murmushi sannan ya dora.

“Mun zo jaje ne da rokon iri, na baka auren kanwata yau kuma ina zaune a gidanka ina nemawa ďana Captain Jamal auren yarka Hurriya.... ”

“Ranka ya dade Hurriya?.... Dan ka ranka ya dade..... Danka....”

Appa ya saka kalmar shahada yana jin abun wani iri a lokacin da be saka ran faruwar hakan ba.

“Ranka ya dade Huriyya dai ko wata dabam a cikin yayana”

“Hurriya dai Alhaji Haruna...”

Daddy ya nanata masa, a gudun kuskure ko samun akasi Appa ya sake share gafe ya shimfida musu abun da ya faru.

“Ita ce yarinyar na da kake maganar an yada hotunan ta fa”

“Za mu hukunta wandanda suka yi haka fiye da yadda kai zaka yi, kuma ina tabbatar maka zamu rike da mutunci da girmamawa”

“Ranka ya dade Hurriya bata gani sam a halin yanzu da nake maka magana”

“Za mu nema mata lafiya kuma za a dace da yardar Allah”

“Allahu Akbar....”

Idon Appa ya cika da kwalla, ba dan baya iya yin abun da Daddy yace za su yi na Hurriya ba, sai dan gata da ya zo mata daga Allah na mallaka mata AA Turaki a matsayin suruki, a lokacin da duniya take zaginta kuma ta rasa idonta, aka nemawa yaron da ake ji da shi a Family su aurenta.

“Ranka ya dade na baka, na mallakawa Captain Hurriya Halak Malak”

Daddy yayi murmushi na musamman yana farinciki da farincikin ďansa.

“Alhamdulillah... Amman Alhaji Haruna baka yi gaggawa ba? Ya kamata mu ji ta bakin yarinyar ko tana son ďana”

Appa ya saka hannu ya tsargar da hawayen da suka so zubo masa.

“Hurriya yarinya ce mai tsananin Biyayya ranka ya dade, tana da gudun bacin rai ba zata ki zabin mahaifinta ba, kuma na san ban zaba mata mugun abu ba, na san waye kai kuma na san waye Jamal, babu uban da ba zai so Jamal ya zo masa a matsayin suruki ba”

“Maa Shaa Allah na yi farinciki da jin haka, daman kuma na yi tsammanin samun haka a gurinka, halinka na kirki shiyasa mahaifinmu ya baka auren Nafisa kuma Alhamdulillah aure yayi albarka”

Appa yayi murmushi jindadi marar misaltuwa.

“Ranka ya dade idan ba zaka damu ba, zan yi ma ďana Yasir magana sai a daura auren yanzu a nan”

Appa yayi hakan ne saboda yana ganin kamar labari zai iha canja ko kuma shedan ya shiga ciki daga baya..

“Toh ka yi mana irin abun nan na iyayen zamani, hakan zai saka ďana a farinciki sosai gashi kuma ba mu zo da sadaki ba, kuma ba a yanka mana”

“A biya sadakin daga baya”

Alhaji Sadiq ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin 100k ya aje.

“Wannan yayi?”

“Aa Jamal yace min yarinyar mai tsada ce, ya kamata mu siye ta da Ƙima, je ka yi magana da ďanka, ni ma zan yi magana da Nafisa”

Appa ya tashi yana sauri ya fice daga falon cikin zumudi da murna. Daddy ya kalli kanensa

“Alhaji Munzali a fita a samo mana goro da Dabino ko?”

“Toh Alhaji”

Alhaji Munzali ya tashi ya fice, Daddy ya daga wayarsa ya kira Momy, sai gata ta sauko da far'arta domin zuwansa ya faranta ranta.

“Yaya har kun kare”

“Aa tukuna dai, Nafisa a cikin sarkokinki an zinarina wacece ta fi tsada?”

“Wanda na siye 50 million, ban taba saka ya na siye na aje ne dai kawai a matsayin kaddara”

“Dauko min ita yanzu nan?”

Har ta yi kamar ta tambaya dalili sai kuma wata zuciyar ta nuna mata idan ta yi haka bata kyauta ko ma minene ai zata ji daga baya. Sama ta koma ta shiga dakinta ta bude akwaitin sirrinta da take aje yi kudi ta dauko sarkar dake cikin wani box da shi kanshi abun kallo ne, tare da receipt dinta ta sauko ta aje ma Yayanta.

“Gata yaya”

“Shiga ciki zan kira ki idan na gama”

“Toh”

Ta juya cikin rashin natsuwa da tunani ta koma dakinta. Daddy na zaune a gurin Appa ya shigo falon da saurinsa.

“Ranka ya dade Bismillah ga shimfida na yi a waje”

Daddy da kansa dauki sarkar ya miki tsaye tare da yan'uwansa suka fice daga falon, babbar harabar gidan Appa ya shimfida Carpet, sai da Daddy ya fara zaunawa sannan sauran suka zauna. Yasir ya ba su hannu suka gaisa daya bayan dayan sannan shi ma ya samu guri ya zauna, Appa ya gayyato har da masu aikin gidan domin shaidar daurin auren Hurriya a gurin aka daura auren, Daddy ya wakilta Alhaji Sadiq a matsayin wanda zai karbawa Captain aure, Appa kuma da kansa ya bada auren Hurriya, bayan ya karbi zinarin a matsayin sadakin Hurriya. Bayan an daura auren ne Alhaji Munzali ya dawo gidan, ya fito mota ya bude bayan motarsa Appa ya saka masu aikin suka kwaso goro da dabino, Daddy ya sa an fasa goro da dabino ya cire dabino uku da goro daya ya saka aljihunsa, sannan yayi musahaba da Appa yan'uwansa ma suka yi.

“Ba sai mun koma ciki ba, rigimar Nafisa ba zan iya da ita ba a yanzu, zata ce an yi komai ba tare da ta sani ba, ka sanar mata a madadina”

“Ranka ya dade na gode, Allah ya baka danka ikon riketa amana”

Appa yana rike da hannun Daddy yake fadar hakan.

“Ameen, babu kai babu mugun suruki da yardar Allah Jamal zai rike yarinyar nan fiye da yadda kake fata”

Daddy ya kara tabbatar masa da yarsa bata shiga mugun hannu ba. Appa ya takasu tare da Yasir har gurin motarsu suka shiga sannan ya koma ya cire dabino da goro ya nufi bangaren Momy yana murmushi kana ganinsa ka san yana cikin farincikin da ya dade be yi ba. Yasir ne ya rabawa mutanen da suka shaidin daurin auren a gurin sannan ya dauki sarkar Zinarin da Appa ya ba shi riko ya shiga bangaren mahaifinyarsa yana murna. A falo ya tararda Hajiya Kaltume da Khairy zaune a kujera daya.

“Hajiya kina nan har yanzu”

“Wallahi kuwa, ka ga tun da na raka Hajiya Fatee nake zaune a nan muna hira da Khairy, wai kiran me mahaifinka ya shigo yana maka a gaggauce?”

Ya zauna saman kujera yana rike da kwatin na zinari.

“Auren Hurriya aka daura...”

Khairy da Hajiya Kaltume suka kalleshi jin abin banbaragwai.

“Baka da hankali wane irin aure kuma?”

Yasir yayi murmushi daman ya san ba lallai kowa ya ji ya yarda ba.

“Aure dai Hajiya, Wallahi aure aka daura mata yanzu nan, wasu ne suka zo tambayar aurenta Appa ya ce ba za su tafi ba sai an daura auren”

“Allah sarki to su ba su da labarin abun da ta yi ne? Ko kuma yan'uwan Adam din ne suke neman a rufawa juna asiri?”

“Ba su ba ne, yarinyar nan fa ta rantse Hajiya bata aikata ba, be kamata ki fadi haka ba”

“To ko da bata aikata ba ai dai mutuncin ta ya zube, duk wanda ya aureta kila ba zata wuce gobe ba zai sake ta, da alama ba su da labari ne, shiyasa suka zo shi kuma Appanku yana neman a raba shi da abun kunya a dole ya rike su a daura auren a gurin, ko dai shi yayi sadaka da ita? Wa ta aura dan baro ko dan shara? Ko cikin masu ban ruwan fulawoyin gidan nan”

Yasir girgiza kai yana murmushi, ya bude akwatin zinari dake hannunsa.

“Wani ne mai daraja Hajiya, dan'uwan Momy ne da Zinari mahaifinshi yayi sadakinta, na naira miliyan hansi...”

A take fitsari ďan tsirin ya kubucewa Hajiya Kaltume ta cire dankwalin kanta ta aje a cinyar Khairy tana kallon zinarin kamar zata yaga ido....



**** **** **** ****

Bayan Daddy ya rufe motarsa, suka jero tare da yan'uwansa suna tafiya ya ce.

“Mahaifinta yayi dabara ni ma na jidadin haka, ka ga mun tsallake ma duk wani tarko a yanzu, shi kan shi Jamal sau biyu ana saka ranar aurensa ana fasawa saboda fushi da wasu hujjoji da ba su kai ba, mu kuma muna biye masa ne saboda farincikinsa muke nema, amman yanzu ka ga wannan duk ya kau a yanzu”

“Gaskiya haka ya fi, ka ga an huta da fitinar Hajiya Turai”

“Daman fitinarta ai zan iya da ita, matata ce fa abun da dai nake tsoro ta canjawa Jamal din ra'ayi gaba daya”

“Wannan gaskiya ne”

Cewar Alhaji Sadiq. A falon Nene suka zauna gaba dayansu, sai Daddy ya sa a kira masa Captain dake dakin sama tun safe be fito ba, kamin ya fito Daddy ya kalli Momy Ikilima ya ce.

“Ikilima ki shiga gurin Turai a cikin kayana akwai wata shadda irin wannan ta jiki sabuwa ce a cikin leda, a dauko ta ta hado miki da sabuwar hula, da turaren da ba a fasa ba”

“Toh Yaya”

Ta tashi ta fice, domin bangaren
Showing 147001 words to 150000 words out of 215510 words