mutumen kwarai ne zai so ganinki haka? Dan Allah ku rika kiyayewa mana muna fa cikin makiya da basa son cigaban mu, abu kadan dariya za'ayi mana a ji dadi”

“Wallahi Hajiya ba ni kadai nake jan abun magana ba, Hurriya ma baki ga mutanen da suke mata magana ba a gurin, babu wanda be san Adam ba dan gidan Alhaji Buba Sarauta yaron da yayi kaurin suna gurin iskanci amman haka ta zauna yana ta zuba mata dollars har daukarta yayi suka fita ya dawo da ita, amman da yake makira ce shi ne ta kira Yaya ta fada masa ya zo ya tarwatsa min taro”

Ta karasa tana jin wani irin bakinciki ko cake din birthday da ta kashewa kudi mai yawa bata ci ba. Gashi kuma Yayanta ya ci mutuncinta a gaban friends dinta on a special day like this one zai zame mata abun magana.

“To an yi mugun gado, indai shigewa maza ne Hurriya ta fara yi to gurin uwarta ta gado, ba yau aka fara ba a nono ta sha, ba haka ta yi har ta aure min miji ba, ai barewa ba zata yi gudu danta yayi rarrafe ba, kamar kumbo kamar kurensa. Tashi ki saka rufafin kwarai mu tafi asibiti a duba fuskar nan taki kar ta kwana tana miki zogi”

Ta tashi daker tana kuka sosai ta nufi stairs sai a lokacin suka lura da Ruma dake tsaye a stairs din tana kallonsu ita bata sauko ba kuma ita bata koma ba.

“Toh lafiya? Kin san yanzu kin zama aljanna ni tsoronki ma nake, kin zama wata halittar ta dabam a cikinmu”

Hajiya ta fada tana nuna Ruma da har lokacin bata ce komai ba, sai ma juyawa da ta yi ta koma sama, gaba daya ta canja tun bayan da ta dawo daga hannun masu garkuwa da mutane ta tsani gidan da mutanen cikinsa, ba kasafai zaka ganta a wani abu da kowa yake tarayya ba, wannan dalilin ya hanata zuwa birthday din Khairi kuwa da kusanci na kasancewarta yar'uwarta. Hajiya kamar wata gurguwa haka ta hau sama daker ta shiga nata dakin ta dauko mayafinta da jakarta sannan ta kira direba ta fasa masa ya kunna mota za su fita. Sai da ya shiga dakin Khairi sai ta same ta har lokacin kuka take tana zaune a kasa.

“Ba zaki je ba na tafi? Ba saboda zuwanki ne kadai ba ina son na kai kafar nan a duba min”

Cikin kuka Khairi ta kalleta ta ce

“Hajiya ba ki ga wulakanci da Hurriya taja aka yi min ba Wallahi, Yaya ya wulakanta ni gaban friends dina”

“Toh ya zaki yi sai ki yi hakuri munafurci daman ai ya cikawa Hurriya ciki, ganewa ne ba a yi sai yanzu amman na san maganinta ai, ke ma kuma fa baki kyauta ba ni Allah yasa dai Fadeel be ganki da wannan shigar ba, abu kamar karuwar Lagos haba Khairi”

Ta tashi tana kuka ta nufi gurin da tufafinta suke ta bude, cikin kuka ta canja tufafin sannan ta biyo bayan Hajiya Kaltume da tuni ta sauka kasa.



HURRIYA POV.

Tana tsaye a waje har Yasir ya fito ransa a bace ya sake shiga motarsa da kallo ta bishi har ya fice sannan ta dan leka bangaren Hajiya Kaltume kamar zata shiga wai dan ta wanke kanta ta fadawa Khairi da Hajiya Kaltume ba ita ta zugo shi ya shigo gurin ba, sanin ba za su kwashe da dadi ba ya saka ta juya ta fice daga bangaren ta nufi bangaren Momy. A hankali ta tura kofar falon ta shiga tsoron dake cikin cikinta ya hanata sallama har ta isa tsakiyar falon.

“Salon labe ne ko kuma rainin wayo? Zaki shigo min falo babu sallama?”

“Yi hakuri Momy mantawa na yi”

Ta fada da muryarta da bata gama fita ba.

“Daga ina kika?”

“Gurin Birthday din Yaya Khairi”

Momy ta dauke kai ta cigaba da latsa wayarta, Hurriya na ganin haka ta raba ta haye sama ta shiga dakinta. Sai kusan magariba Namra ta dawo gidan, tufafinta kawai ta cire ta shiga dakin Momy tana bata labarin abun da ya faru ita kanta ta cika da mamaki irin shigar da Khairi ta yi ga kuma wasu watsassun kawayenta da bata san a ina ta samo su ba.

“To ke me kike baki dawo gida da tun dazun ba?”

“Momy ina can ina jiran wanda zai dauko ni fa, gaba daya a hargitse aka watse taron saboda Yaya Yasir ni ma ba dan na boya ba Allah kadai ya san kalar dukan da zai min”

“Ya dokeki saboda shi ya haifa ki? Ai ba zan dauki wannan ba, ya taba dinka kala daya ya kawo miki? Sai yanzu da girmanki zai ce ya saka miki hannu ya dakeki saboda bikin da kanwarsa ta shirya?”

“Momy dan baki ga bikin ba ne, bari na nuna miki dress din Khairi kamar ba yar gidan nan ba”

Ta shiga gallery wayarta ta kama hotunan da ta yi ma Khairi tana nunawa Momy.

“Momy kalli fa, ni ma raina ya bace da abun da ta yi Wallahi, ai na jidadi da Hurriya ta fadawa Yaya Yasir ya zo ya watse taron nan”

“Au Hurriyar ce ma ta fada masa abun da ake yi? Ina ta ganshi to?”

“Oho mu ma kamar daga sama muka ganshi ina ganin ya fada jibgar Khairi na boya ban bari na gan ni ba”
[11/3, 4:06 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 10*


“Ikon Allah yaushe kuma Hurriya ta fara zama munafuka? Hada yaya da kanwa? Wannan kam ba shi da kyau ai, ko bata fada masa ba ai ya san kanwarsa zata aikata yadda take jin ita sa'ar kowa ce kawaye babu na albarka ai dole ma ta aikata, kuma Alhaji ba zai ce komai ba duk abun da Kaltume ta yi ai shi ne daidai a gidan nan ita da yaranta yanzu basa laifi”

“Gaskiya Momy kawayenta gaba daya babu na gari, wani dayan frind dinta ya zo yana yi ma Hurriya liki da dollars”

“Rawa ta yi”

“Aa Momy kin san ai ba zata yi rawa ba, Momy kin san shi ma Adam ne fa, dan gidan Sarauta”

“Ba dai dan Hajiya Nana ba?”

“Shi fa, yaron nan yana wasa da kudi”

“A ina ta san shi?”

“Ni ma ban sani ba, bari ma na tafi na tambayeta”

Ta tashi da saurinta ta bar wayar a gurin ta fice daga dakin Momy bata zame ko'ina ba sai dakin Hurriya. Cikin natsuwa irin na masu son gulma ta tura kofar dakin ta shiga, Hurriya na tsaye jikin windows, dan kwalin abayarta ya sauko saman wuyanta hannunta kuma yana wuyanta tana shafawa zuciyarta kuma ta tafi wata duniyar karatu.

“Hurriya...”

Ta juyo ta kalli yayarta, Namra ta maida kofar ta rufe ta nufi gurin da Hurriya take tsaye.

“Me kike yi”

“Ba komai kawai ina tunanin Hamad ne”

Ta fada tana sauke idonta kasa.

“Ke dai kin saka Hamad a ranki Hurriya, idan yana raye Allah ya bayyana shi idan kuma ya mutu Allah ya jikansa da Rahma”

“Amin”

Hawaye ya sauko mata.

“Da ace yana nan kusa da mu, wata kila da yanzu muna son junanmu ba kamar baya ba, wani lokacin ina jin bukatar abokin tattaunawa, har yanzu na kasa sabawa da rashinsa ina jin kadaici sosai”

“Ki yi ta addu'a abun zai cire miki In Shaa Allah, amman shiga damuwar da kike ina tunanin shi ne silar daya kara jefa Amma cikin damuwa”

“Ina kokari Yaya Namra bana bari ta gane ina cikin damuwa”

“Haka na da kyau, yauwa Hurriya kin san wannan wanda yayi miki karin kudi dazu?”

Ta share hawayenta da gefen hannun rigar abayar.

“Aa ban san shi ba, dazun ne ma na fara ganinsa”

“Toh amman kuma yake miki karin kudin haka nan kawai?”

“Ni ma abun ya ba ni mamaki sunana ma ban san inda ya ji ba”

“Maybe ko ya sanki wani gurin ke ce baki san shi ba”

“Ni da ba fita nake ba, amman ni ma mamaki nake”

“Toh ki yi hankali da shi yaron nan dan shaye shaye ne”

Ta amsa mata kai kamin ta ce.

“Yaya Namra dan Allah zaki taimaka min na fadawa Hajiya ba ni na kira Ya Yasir ya shiga ciki ba?”

“To waya kira shi?”

“Ni amman na ce masa ya zo ya dauke ni ne kawai saboda wannan saurayin ya takura min kuma ba ni da wanda zai kai ni gida, amman WallahI ban ce ya shiga ciki ba”

“To ai ke kika yi kuskuren Hurriya kema kin san dole zai shiga ai, kuma yanzu babu mai wanke ki a gurin Hajiya”

“Ba Hajiya kadai nake tsoro ba, har da Yaya Khairi na san ni zata dorawa laifin”

“To kije ki ba su hakuri mana”

“Zan yi haka”

Ta fada cikin yanayin damuwa wasu hawayen na kara cika idonta. Namra ta fice tare da ja mata kofa. Hurriya ta kai hannu ta taba hancinta kamin ta dago ta sake juyawa top side view ta rumgume hannayenta.



Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/3, 4:06 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 11*



Misalin tara da rabi Hurriya na zaune dakinta ta ji an kwankwasa kofa, tana jin haka ta san wanda be saba shigowa dakin ba ne domin Momy ko Namra basa kwankwasa mata kofa balle kuma Miwan da Musib da basa gidan ma. Ta tashi da saurinta ta nufi kofar ta bude sai ta yi arba da Ruma.

“Appa na kiranki”

“Ni”

Ta nuna kanta, Ruma ta daga mata kai.

“Eh”

Ta juya ta bar kofar ta fara sauka kasa, Hurriya bata tsaya komai ba ta bi bayanta tana sanye da kayan bachi kanta sanye da hular saka. Ruma na gaba Hurriya na bayanta tana jin kamar ta tambaye ta me ya faru kuma dai bata tambaya ba. Cikin tsoro da fargaba ta shiga falon na Hajiya Kaltume gabanta na faduwa. Hankalinta be kara tashi ba sai da ta yi arba da fuskar mahaifinta dake hade babu annuri a tare da shi, bata yarda ta karasa cikin falon ba ta tsaya daga jikin kofa cike da ladabi ta ce

“Appa ga ni”

“Okay tasowa zan yi na iskoki can kenan? Ni zan same ki a inda kike na yi magana da ke ko?”

“Aa Appa ka yi hakuri dan Allah”

Ta taso ta karaso kusa da shi, ba duka take tsoro ba domin be taba dukanta ba, fadansa take tsoro tun daga lokacin da ya canja mata sai ya zame mata abun tsoro bata ma son zuwa kusa da shi sai da dalili domin ta lura baya bukatar ganinta.

“Appa gani”

Ta durkusa gabansa tana kallonsa ta cikin gilashin idonta, Yasir na tsaye gefen Hajiya Kaltume dake zaune kusa da Appa, Khairi kuma na zaune a dayar kujerar tana shafa man zafi.

“Miye wannan?”

Appa ya nuna mata video karin kudin da aka yi mata. Sai ta saka hannu biyu ta karba tana kallo jikinta na rawa kamar yadda bakinta ma yake rawa domin bata san me zata ce ba.

“Wace ce a nan?”

“Ni ce Appa”

Ta amsa da sauri.

“Waye wannan da yake miki liki”

“Ban san shi ba Appa Wallahi”

Tana rufe baki Hajiya Kaltume ta kai mata duka a bakin da mugun karfi.

“Baki san shi ba zai zo yana zuba miki dollars haka?”

Apoa ya kalli Hajiya cikin yanayi na rashin jindadin kai hannu da ta yi ta daki Hurriya.

“Ba sai kin dake ta ba, magana ma ta isa a yanzu shata nata line zan yi”

“Ai idan ba a dake ta ba, ba zata san Annabi ya faku ba, karya da munafurci babu kalar wanda bata iya ba, ka duba yadda ta zuga Yasir ya fasawa Khairi jiki”

Appa ya daka mata tsawa da ta saka ta fashe da kuka ta ja baya tana girgiza kai.

“Waye wannan mutumen na ce?”

“Ban san shi ba Appa Wallahi ni ma yau na fara ganinsa?”

“Karya take yi Wallahi Alhaji bata san shi ba”

Hajiya ta kai kafa ta halba mata wani shuri, kamin ta janye da sauri saboda ciwon da kafar take mata har yanzu.

“Karya take munafuka baki san shi ba zai zuba miki kudi haka kuma kina zaune gashi har sunanki ake fada”

Yasir dai yana tsaye sai kallo yake baya son yayi magana Hajiya Kaltume ta rufe shi da fada, bayan kuma ga wanda ya kamata a rufe da fada nan wato Khairi.

“Ku dai duk abun da zai zubar min da mutunci ko kima a idon duniya shi kuke kokarin aikatawa? Ko soyayya zaki yi me zaki yi da mashayi? Kaltume ta fada min yaron nan yayi kaurin suna gurin iskanci da shaye shaye”

Hurriya ta saka hannu ta rufe bakinta, ta san duk wani abu da zata fada ba zai wanke ta ba, ita kan da ta sani ma ba zata tafi bikin ba.

“Sannan kuma ka ja mata kunne akan munafurci abun da take ba shi da kyau, kina hada yan'uwa fada kina sa a ciya daya mutumci a cikin mutane”

Sai a lokacin Yasir ya saka baki.

“Ni ba ita ta fada min Khairi tana wani abu a gurin ba, daukarwa kawai naje yi sai kuma na yi decide na shiga ciki, kuma idan ma Hurriya tana da laifi to laifin Khairi ne, domin ita ta shirya biki kuma Appa da ka ga irin shigar da ta yi da irin mutanen da ta tara a gurin sai ranka ya bace”

Hajiya Kaltume ta watsa masa harara.

“Ita Khairi da ka raina ba, ita meye laifinta? Birthday kawai ta yi fa, kuma ina ce Hurriya ce silar kowa ya fara yin birthday a gidan nan amman ba ayi mata fada ba sai Khairi”

Appa ya mike tsaye.

“Ban shigo nan dan ku rufe ni da ka ce na ce ba, and Hurriya ina jan kunnenki idan wani abu makamancin wannan ya sake faruwa sai na baki mamaki”

Yana kaiwa nan ya fisge wayarsa da Hajiya Kaltume ta tura masa video ya fice daga falon. Hurriya ban da aikin kuka babu abun da take yi, ta rasa ta ina zata fara wanke kanta.

“Munafuka sahibar kuka, ki yi ta rerawa mutane kuka saboda a tausaya miki a kyale ki ko? To yanzu dai kin ji abun da Alhaji ya fada idan zaki kama kanki gurin yan iskan samarin nan ki kama, idan kuma ba zaki yi ba yi, ga ki ga guri duniya ce”

“Wallahi Hajiya ban san shi ba, ni ban taba ganinsa ba”

Ba dan Yasir na tsaye gurin ba da babu abun da zai hana Khairi saka baki, sai dai tana tsoron ta yi magana ya sake rufeta da duka. Dan haka ta ja bakinta ta yi shiru sai kallonsu take, Hajiya Kaltume kuma ta rufe Hurriya da fata ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, sai balbale Hurriya take da bala'i ta ko'ina kamar ita ce ta aikata abun da Khairi ta aikata. Sallama aka yi sai suka dago baga dayansu suka kalli kofar amman aka rasa wanda zai amsawa Rukayya sai Yasir dake kokarin sakin fuska.

“Rukayya”

“Na'am Yasir ya gd”

“Lafiya kalau”

Hurriyya ta tashi da sauri ta nufi kanwar mahaifiyarta ta rumgume ta da sauri tana kuka.

“Mama Rukayya kara da kika zo”

“Idan ta zo magani zata miki? Idan dai zaki canja hali ki canja domin hanyar da kika daukarwa kanki yanzu ba mai daurewa ba ce”

Hajiya Kaltume tana fada tana tabe baki, Rukayya da ke rumgume da Hurriya ta kalli Hajiya ta ce.

“Ba zan mata magani ba, amman Allah zai mata”

Yasir yayi sauri cire hannayensa aljihu.

“Rukky Please aa karki fara abun da ba halin ba”

Ta kalli Yasir sai kuma ta dauke kai ta rika hannun Hurriya suka fice daga falon, Hajiya ta bita da harara da maganganun kala kala.

“A dare kamar wannan yarinya budurwa ace bata gidansu, kuma ta shigo nan tana neman fada min magana ita marar tarbiya”

“Haba Hajiya Rukayya tana da tarbiya Wallahi dan Allah ki daina fadar haka, kuma baki san abun da ya kawota ba, be kamata ku samu tsabani da ita ba, ni zaku haifar da matsala”

Yana magana fuskarsa a raunace kamar zai yi kuka. Sannan ya bi bayansu yana jin Hajiya na jan tsaki.

A waje Hurriya sai rantsuwa take yi ma Rukayya na cewar bata san yaron ba, amman saboda shi Appa ya rufeta da fada.

“To miyasa ba zaki bude baki yi magana ba, idan kina irin wannan zaman sai kin cutar da kanki, ba zaki bude baki ki yi magana ba sai ki zauna kina kuka, ko da kina da gaskiya a rashin gaskiyar za a baki”

“Basa bari na yi magana kuma idan na fada basa yarda”

“Amman duk abun da ba halinki ba ai an san ba halinki ba ne”

“Toh sarkin masifa me kike karanta mata?”

Rukayya ta juyo ta kalli Yasir da isowarsa kenan gurin, shi ma kansa yau sai ya bata haushi saboda abun da mahaifiyarsa ta yi. Bata ce masa komai ba ta kalli Hurriya

“Daman na fito daga gidan Anty Hauwa ne na ce mai napep ya biyo ta nan zan duba ki”

Hurriya ta rike hannunta tana jin kamar ta bita
Showing 27001 words to 30000 words out of 215510 words