ta ji sauki?”

Hurriya ta yi shiru idonta da kanta a kasa kana ganinta ka ga natsantsiyar yarinya.

“Tana iya tashi zaune da kanta?”

Huriyya ta yi shiru na dakiku kamin ta girgiza kai.

“Ashha dai, Allah yasa jinya ta zama kaffara, ni fa ina son naje na dubata amman ina gudun ka ce na ce, idan kin je dai ki gaisheta”

“Toh Hajiya”

Hajiya Kaltume ta dauko wayarta ta bude Gallary ta kama hoton wani farin lace ta mikawa Hurriya wayar.

“Duba ki gani, daman wani Lace ne nake son na siya muku”

Bata yarda ta karbi wayar ba, a madadin haka ma sai ta bi Hajiya da wani kalami.

“Aa Hajiya na gode”

“Toh har da kyautar Iyami ta hanaki karba?”

“Aa Hajiya ai Amma bata iya magana, bata ce min kar na ki karbar kyautar kowa ba, ni ce dai ban karba a karan kaina”

“Toh tashi ki kara gaba, daman duk yadda aka muku mutuncin sai kun ce ba ayi ba, an riga an gado bakin hali, daman ni ai ba so na zaku yi har abada”

Hajiya Kaltume kamar wanda ta zare haka ta rika fadawa Hurriya kalamai marar dadi, Hurriya dai bata dauki ko daya a nan gurin da ta fada mata su a nan ta bar su, ta fice daga dakin. Fitar Hurriya da kamar minti goma Kulu ta shigo dakin ta zube kasa tana dagawa Hajiya hannu kamar wata sarauniya ko matar sarki.

“Ranki ya dade gani, Khairiya ta fada mjn ina nema ma na fito har na kusa sai na hango ta doso nan tare da Hurriya shiyasa na koma”

Hajiya Kaltume ta yi kamar bata ji ba ta shiga wani bangaren na wayarta, kamin ta kara wayar a kunnenta.

“Yasir kana kusa?”

Yasir ya amsa a dayan bangaren.

“Eh ina nan waje, muna tare da Kamal ne”

“Asibiti nake son mu tafi idan ka gama”

“Waye ba lafiya”

“Ni ce, amman dai da sauki, ka bari sai ka gama ni ma akwai abun da zan yi yanzu”

“Toh”

Ta sauke wayar ta kalli Kulu, sai a lokacin take amsa mata maganar da ta yi.

“Ai kara da kika yi haka, saboda kaucewa ido”

“Duk wani abun da zai saka Momy ta ji ko ta gane akwai alaka a tsakaninmu ina kokarin ganin na gujewa haka”

“Kin kyauta, dabam na ce a kira min ke ne, saboda mu yi wata magana da ke, kamin nan tashi ki tura kofar dakin”

Kulu ta kike tsaye ta nufi kofa da ta bari a bude ta rufe, sannan ta dawo ta zauna ta natsu sosai tana sauraren matar da ta fi tsoronta a yanzu fiye da uwar dakinta.

“Aminci ne ya saka na nake tambayarki abu ko na saka ki yi, na san ba dan kin dauki sarka da kudi ba, wata kila ba zamu san juna ba, amman bana son kina kallon wannan a yanzu, ni daman tuni na tattara wannan abun na aje a gefe daya”

“Hajiya ai ba dan karki ce na yi karya ba, nikam da nace satar nan ta zame min alheri domin sanadinta na hadu dake”

Hajiya Kaltume ta sauke ajiyar zuciya ta marairaice fuska.

“Kulu ke da yar'uwata duk daya a yanzu, shiyasa har na kira ki nake son na fada miki damuwata, kuma neman samun mafita a gareki”

“Hajiya tafi kanki tsaye, duk wani abun da kike so zan miki shi, yadda kika rufa min ba ni da kamar ke a duniyar nan”

Dogon numfashi Hajiya Kaltume taja ta sauke sannan ta furta.

“Kulu ina cikin damuwa da matsala kala kala, amman wanda ta fi min yawa, ita ce ciwon kafar nan dake damuna, yanzu haka kiran da kika ga nayi ma Yasir ita zan kai asibiti, na dade ina ciwon nan amman har yanzu babu sauki babu alamarsa, tun ina barin ciwon a cikina abun ya fara min yawa, to yanzu kuma sai abin da biyo har da mafarkai da ba su dace ba, kuma ciwon nan sai cigaba yake, abun ya ba ni tsoro, ga maganin asibitin nan yi ake amman a banza”

Kulu ta dukufa a tunani har wani kada ido take tana jinjina kai.

“Hajiya ba zaki gwada na hausa ba? Ko Allah zai saka a dace?”

Kamar an yi ma Hajiya Kaltume albishir haka ta ji, saboda Kulu ta sosa mata gurin dake mata kaikaiyi.

“Shiyasa na kiraki ai, kin san ku ne mutanen kauye, kun fi sanin irin abubuwan nan, wata kila ba zaki rasa sanin masu irin aikin ba”

“Akwai su Hajiya kala kala, akwai wata mai aljannu tana bada taimako sosai, kuma akwai namiji ma yana yi”

“Yauwa namijin dai zai fi, ni ban cika son mata masu aljanu ba, na fi son inda zan tafi a fada min ko minene, jifa ce ko kuma ciwo ne ko iska ne”

“Aiko kina tafi gurin Malam na gangare zai fada miki ko menene, domin shi baya son ma ka fada masa abin da ya kawo ka shi zai baki labarin komai, har abun da baki sani ba, da madubi yake aikinsa yana kallo madubi ya fadi magana ta tabbata, kuma ko minene a take zai rabaki da shi, idan jifa aka yi miki ko turbuda a take ma zai ciro shi”

Hajiya Kaltume ta dauki filo ta dora a cinyarta ta kwantar da hannayenta akai tana gyada kai.

“Yauwa irin su nake so masu aiki kamar yankan wuka masu zafi”

“To idan kika kai gareshi magana ta kare, domin shi ko mutum kika ce ya kashe miki zai kashe”

“Irinsa ya dace, kin ga ko minene a take zai fada maka kuma ya karya shi, a ina hake Kulu?”

“A kauye uku yake, dake nan cikin bunguɗu”

“Babu nisa sai dai ban san yanayin hanyar ba?”

“Hanya lafiya kalau take, ai garin mu babu irin bata gari, su kansu suna tsoron mutanen yankin”

“Maa Sha Allahu, sai dai kuma tafiyarmu kamar ba zata yi a tare ba, saboda uwar dakinki Nafisa ba zata bari ba nake gani”

“Wannan ba matsala ba ne Hajiya, kina shiga garin Bunguďu ki dauke hanyar kauye uku, da kin isa ki ce gidan Malam Ashiru mai Yasin da Allon karfe kike nema, ko karamin yaron zai kai ki, idan kuma kina jin ba zaki iya haka ba ke nemi gidan su Kulu taroro kina shiga gidan ki ce ni na aiko ki gurin Malam Ashiru za a kai ki, zaki iya ma kira na yi magana da su”

“Allah dai ya saka miki da alheri Kulu, ina ganin ma ba zan tafi asibitin nan ba, gobe ina gama karyawa zan kama hanyar garin, zan iya tafiya da direba na ma ya kai ni garin”

“Daman Hajiya tafiya da daren ba ai ya fi sirrin da sauki”

“Haka zan yi, zan fara zuwa gidan na ku sai na kira na ba su ku gaisa idan ya so sai kun iso gurin Malamin zai fi sauki”

“Toh Hajiya, Allah ya bada lafiya”

“Amin”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye daker tana cige baki kafar kuma kamar zata yi gurmanta da ita haka ta taka ta isa gurin kayanta ta bude wardrobe ta dauko wani lace da ba a dinka ba ta jefawa Kulu.

“Ahhhhh Kai Hajiya duk ni kadai? Alhamdulillah Hajiya na gode na gode, Allah ya kara rufa asiri ya biya bukata, Allah ya kara lafiya ya tsare ki daga duk wani sheri”

“Amin, wani abun kulu ai sai na samu lafiya ma, da yardar Allah idan bukata ta biya zan kyautata miki, ta shi ki tafi kamin Yasir ya shigo”

“Toh Hajiya, amman zan bar leshin a nan saboda idon mutane, sai idan na ga sarari zan zo na karba”

“Dadina da ke wayo Kulu kin iya sirri”

“Gidan na mu ne Hajiya sai da haka, kamin a fara fadar ana ganina bangarenki ”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi. Ita kuma ta mike tsaye ta yi mata sallama.

“Mu kwana lafiya”

Kamin ta isa kofar dakin ta bude Yasir ya bude sai dai be shigo ba ya bata hanya ta fita yana amsa gaisuwar da take masa.

“Me ta zo yi nan?”

Hajiya ta nuna masa lace din dake kasa

“Nafisa ta aiko min da lace?”

“Ke kuma?”

Ya tambaya kamar mai shakku, Hajiya dai bata sake ce masa komai ba ta nufi gurin da ta tashi ta zauna da tafiyar nan nata kamar zata yi dingishi.

“A kafa kike jin ciwon ne?”

“Eh gurin da na taba jin ciwo kwanan baya, a nan na sake jin ciwo haka nan kawai sai na ji kamar an tureni na fadi kasa”

“Ko santsin gurinki ne ke janki”

Ya soma duba kafar da ta dan dago masa tana jin kamar ana yanka gurin sai sululi yake mata kamar an watsa ruwan zafi.

“Aa ba wani tsantsi shekara nawa ina gidan nan da can tsantsin be ja ni ba sai yanzu? Turo ni ake yi fa”

“To wa yake turoki Hajiya”

“Yo ina zan sani tun da abu ne na aljanu, amman tabbas ba faduwa ce zallar faduwa ba, turo ni aka yi”

Yasir yayi murmushi tare da kai hannu ya latsa gurin.

“Ban san me yasa ku mata kuke yarda da irin abubuwan nan ba, haka Last week Rukayya take ce min wai ance aljannu ne a jikin Amma, ku dai komai kun fi son ace aljannu ne, wani abun fa daga Allah yake kai tsaye idan ana na asibiti zaki ga an dace, ita kanta Amma da za a fitar da ita waje a dubata duba mai kyau za a gane Matsalarta”

Hajiya ta janye kafarta da sauri saboda lasa gurin da Yasir yake yi.

“Ku kuma ba ku yarda da aljannu ba ko?”

“Mun yarda da su mana, amman ba lallai komai ace su ba, kin ga kafar nan take da zaki iya daurewa mu bari sai da safe mu tafi asibitin, hoto za su miki su duba matsalar”

“Eh haka zan yi, mu hakura da tafiya asibitin nan sai gobe da safe”

“Ba sosai kafar take damunki ba”

“Yanzu dai ta min sauki ba kamaf dazun ba, kai Allah sarki na tausaya wa Iyami gaskiya, a kafa kawai ina jin ciwon nan kamar zan mutu balle ita da ta ke kwance bata iya komai shekara da shekaru, wai har yanzu bata iya tashi da kanta?”

“Rukayya ta ce min tana tashi da kanta yanzu, kuma da kanta take cin abinci, rayuwar Amma akwai ban tausayi sosai, gashi ba wani karfi yanzu sosai ”

‘Munafuka Hurriya wato kin iya kini bibi ko? Ni zaki yi ma karya?’

Ta fada a ranta tana wani kashe ido, a zahiri kuma sai ta ce.

“Allah ka raba mu da wahalar duniya, wato Yasir yanzu ka zama dan gidan ka san ciki da waje”

Murmushi yayi ya mike tsaye.

“Daman can ai dan gida ne ni, ba wai sai saboda Rukayya ba”

“Haka ne, Allah ya zaba abun da ya fi zama alheri amman dai ina son ka sani ba zan taba yarda ka dauko yar'uwar makiyiyata uwa daya uba daya ka kawo a gidanka ba da sunan mata”

“Hajiya Amma ce makiyiyar? Idan ma kuna kallon junanku da wannan ne ban isa na canja ba, amman matsalarku dabam be kamata ta shafe mu ba, musamman ma ita Rukayya meye nata a ciki?”

“Wai dan Allah duk matan garin Gusau ka rasa wanda zaka so sai ita? Me ta fi mata da shi ne?”

“Hajiya ni dai ita nake so kuma ita zan aura da yardar Allah”

Hajiya ta daure fuska sosai tana watsa masa danta da be kishinta harara.

“Ina fada maka bana bukatarta a matsayin suruka kana karanta min ita zaka aura, saboda kai ne uba ni ce ya ko? To mu zuba ni da kai shege ka fasa, ko saboda ka ga wacan karon ka min magana na maka sanyi? Ina duba gudun ruwanka ne? Amman Wallahi ko Rukayya ita kadai ta rage a duniya ba zaka aureta ba”

Gudun sa'insa da ita ya saka shi ficewa daga dakin ba tare da ya ce mata komai ba, sai dai kana kallon fuskarsa zaka san kalaman na Hajiya Kaltume ba su masa dadi ba.

“Wallahi ba zaka aureta ba, ni gaba daya ma kamar an canja min kai, kai kenan namiji Allah ya ba ni amman baka min biyaya, idan ina kiyayya da mutum kai sai ka dauke shi masoyi, haka kake rawar jiki akan Hurriya sai ka ce ni na haifi yarinyar nan”

Ta yi ƙwafa, kamin ta juyar da fadan gurin Hurriya da bata san tana yi ba.

“Ita kuma tsohuwar makira wai ita nan har ta iya canja labari ta fada min Iyami bata ji sauki ba, wannan yarinyar da wata babbar mace ce da ni zata yi kishi nan gaba, amman zan maganinku duka”

Ta mike tsaye tana daga kafar ta nufi bandakinta.



Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/28, 5:22 AM] AMINA KABIR CAPS: *KHADIJA CANDY*

*PAGE 2️⃣7️⃣*



“Ruwa duk ya jika ka fa”

Ya kalli jikinsa ya daga fadunsa.

“Na tuna baya ne”

Ya fita daga cikin ruwan ya karaso bakin kofar ruwan na siyaya a jikinsa. T-shirt din dake jikinsa na bayyana yadda Allah ya zuba hallita a jikinsa saboda jikewar da rigar ta yi da ruwan sama.

“Rayuwar baya kuma Captain? Ko dai akwai abun da yake damunka? Baka saba irin haka? Zuwa ka yi aiki a gidan nan, ga kuma tsaya a ruwan sama kamar wani karamin yaro kalli fa har wristwatch dinka ya jike”

Ya kalli agogon.

“Kudi ne nan ba zallar agogo ba, ruwa baya masa illa, lemme go and change set the table please ban ci abincin rana ba”

Yana fadar hakan ya nufo gurin da take tsaye sai ta masa ta ba shi hanya tana binsa da kallo gabanta na bugawa da mugun karfi, har sai da ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi sannan ta samu sa'ida. Hakika Jameel ya kai namiji ya cika ta ko'ina irin cikar da ake so a jikin kowane jarumin namiji, Allah ya hada masa abubuwa da yawa ya bashi kyauta ba tare da ya roka ba. Da kallo ta bishi har ya haye sama sannan ta dauke idonta ta nufi dinning domin duba abun da babu. Abu na farko da ya fara yi bayan shiga dakin shi ne canja tufafinsa ya saka wadanda ke karamar jakarsa. Ya saka kai wadanda ya cire a toilet sannan ya bude kofar na saka kafarsa waje Hurriya ta juyo da sauri tare da ihu domin bata san da mutum a dakin na Miwan ba, ya janyo kofar a hankali ya rufe yana kallonta ko'ina na jikinta siyayarda ruwa yake.

“Aljani kika gani?”

Ta girgiza kai.

“Karki sake min ihu”

Ta daga mishi kai tana kallonsa ido kamar za su fado.

“Daina kallona”

Ta yi saurin sauke idonta kasa, ta juya ta bude kofar dakinta da sauri ta shige ciki ta rufe. Murmushinsa mai tsada yayi sannan ya taka ya fara sauka stairs din da sassarfa.

“Tafiya zan dafa maka, saboda na san baka cin tuwo, ni san na manta ma tuwo aka yi yau Wallahi”

Namra ta fada tun kamin ya karaso dinning din. And she's right baya son tuwo baya cin tuwo ko da yunwa zata kashe shi ba ya iya cin tuwo. Ya dafa kujerar yana kallonta

“Ina yarinyar nan kanwarki?”

Ta dan motsa ido gafe da gafe.

“Hurriya?”

“Yea kira ta ta girka min”

“I can cook for you”

“You don't have to stress yourself Pretty, kira ta girka”

The way he said kar ta yi stressed kanta ya saka ta ji she's special kuma hakan ya nuna har a gurinsa tana da muhimmanci.

“Okay”

Ta amsa da murmushi sannan ta nufi hanyar stairs, shi kuma ya nufi gurin da ya zauna dazun ya zauna. Ya cigaba da aikin da yake, Namra bata dauki lokaci ba ta sauko.

“Sallah take amman na fada mata zata sauko idam ta gama”

Ya amsa mata da kai hankalinsa da natsuwarsa gaba daya yana gurin aikin da yake a yanzu. Momy ce ta sauko tana sanye da bakar abaya tana murmushi.

“Captain aiki ake take yi”

“Aiki nake Momy akwai abun da ya kamata na yi typing na aika Abuja kamin gobe”

Ita ma dai ya amsa mata ba tare da dago kai ba.

“Amman ka ci abinci?”

“Za a dafa min yanzu”

Momy ta kalli Namra dake tsaye.

“Namra tafi ki sama masa wani abun yanzu mana, kin san fa baya son tuwo”

“Na ce zan yi yace kar na yi stressing kaina Hurriya zata dafa?”

“Hurriya kuma? Bata gidan ma fa”

“Ta dawo tana ciki, dazun ai Inna Shatu ta gama gage gurin data bata da ruwa saboda ta jika tufafinta”

“Okay to kin fada mata”

“Eh”

“Bari na shiga ciki har ka gama aikin Captain”

“Okay Momy”

Still be dago ba, Momy ta juya ta koma ciki, Namra kuma ta zauna kusa da shi tana duba wasu daga cikin takardun da yake aikin. Captain be dago ba har sai da ya ji karar talkamin Hurriya tana saukowa daga stairs din, yadda sautin takun tafiyar ke fita ya fahimci ita ce, kamar an saka hannu biyu an rika fuskarsa da karfi an juyar da ita zuwa stairs din haka ya ji. Ba kwalliya ta yi ba amman green atamfar dake jikinta ta karbe ta sosai ta yi mata kyau, Brown hullar dake kanta
Showing 87001 words to 90000 words out of 215510 words