mu, Hamad ma ya ji muryarki shiyasa kika ce a kashe shi”
Hajiya Kaltume ta yi saurin rufewa Ruma baki tana juyata ta kalli kofar dakin, sannan ta juyo ta kalli Ruma tana kuka.
“Wallahi ban ce a kashe shi ba, Yaushe zan ce a kashe shi? Wallahi ban ce a kashe shi ba, kuma Wallahi idan wani ya ji maganar nan Ummu Rumana sai kin yi bakincikin zuwa duniya”
Hajiya Kaltume ta sake ta fice daga dakin da sauri tana share hawayenta, da hakki ta isa nata dakin ta zauna bakin gado kamar wadda ta yi gasar tsere hakki ne na mai jin tsoro da fargaba faruwa wani ba, ba na wanda yayi wani aiki ba. Da sauri ta lalabi wayarta ta kira macen da ke share mata kukanta...
“Hajiya Fatee ke kadai kike?”
“Ni kadai nake Hajiya Kaltume Lafiya?”
Hajiya Kaltume ta fashe da kuka tana fada mata abun da Ruma ta yi mata.
“Ah toh ita kuma duk saboda wa kike abun?”
“Ita wannan bata gani ai, da ma Khairi ce ita ce mai irin zuciyata, kuma ni Wallahi ban dauki yaron nan dan a kashe shi ba, kaddara ce kawai ni ba ma shi na so a dauka ba, yar makauniyar na so a dauka, amman abu ya zo a haka”
“To yanzu me ye abun yi?”
“Abun yi kawai a rufe mata baki, domin na lura tona min asiri zata yi, tun da ta dawo gaba daya ta bi ta canja, sai zancen barin gidan take nan gaba kadan zata iya cewa zata fadawa wani idan abu ya cika”
“Lallai da maganarki, haka ya kamata, daman ita bata san kan duniya ba shekara goma sha bakwai miye ta sani, ai da gaskiyarki da baki saka ta a lamurranki duk da shige miki da take da sabon da kuka yi, wannan ai sai ta fadawa duniya mun je gurin kaza da kaza”
“Ina zan yarda? Ai duk yarana bana zuwa da ko daya, sai dai na fada musu”
“Haka ya kamata gaskiya ki kirashi ki fada masa komai idan akwai yadda za ayi a danne bakinta nan dan kar ta fada”
“Zan kira shi, daman ban gama fita bakincikin Iyami ba yanzu kuma ita zata tsirar min wani sabon shafi”
“Wallahi kuwa shegiyar dagar ta sake jefo masa yan biyu haihu kamar karya kuma duk maza, ta dai rantsa sai ta ci gadon Alhaji daman shi ne take ta yi ma wannan haife haifen, ai Wallahi an rage mugun iri ma, yaron nan ba fadar kike yana damunku”
“Wallahi ya addabi kowa, kuma ni ba shi na ce a dauka ba, iya yar macijiyar na ce a dauka, su kuma sai suka bata aikin suka kira wayata a gabansu yaro ya ji muryata, shi ne duk sila ni kaina kullum tunanin yaron nan nake nake Wallahi abun ya hana ni sukuni sam”
“Allah dai ya rufe asiri kar wannan yar autar taki ta janyo mana jagwal”
“Ameen, ai maganinta zan yi”
Daga haka suka yi sallama, babu bata lokaci Hajiya Kaltume ta lalabo number Malaminta a wayar ta kira shi domin kai masa kukanta, daman kiran Hajiya Fatee da ta yi na neman jin shawarar abun da zata ce ne domin bata yanke hukunci sai ta shawarci aminiyarta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻*HURIYYA*
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 6️⃣
The following week Appa ya aika mota dauko Hurriya, a lokacin ne hankalin Amma ya tashi sosai daman babu irin magiyar da bata yi ma Hajiya Binta ba a lokacin da ta zo mata da sakon cewar Appa zai aiko da mota a dauki Hurriya next week, Hajiya Binta ma ta yi iya kokarinta amman be saurareta ba, saboda ba zai iya tsabawa abun da Hajiya Kaltume take so a yanzu ba, ita kadai zata ba shi shawara ya dauka bayan ita baya sauraren kowa ciki har da mahaifiyarsa da kuma Momy da bata ma gane kansa yanzu, sai dai bata cika damuwa da al'amurransa ba domin ta bussinees dinta take da harka da manyan mutane. Son ta mallaki gida ko ta mallake Alhaji Haruna baya gabanta domin jin take kamar ma ta kusa gogawa da shi a arziki. Hurriya kamar zata shide haka aka fito da ita daga gidan ita kuka Amma kuka Gwaggo kuka Rukayya kuka tana rikon Amma amma na rike ta kamar wadanda za a raba rabuwa ta har abada. Ita dai bata son komawa gidan saboda babu dan'uwanta mai tare mata fada a cikin haka kuma babu mahaifiyarta, kuma a yadda ta fahimta ba zata sha da dadi kamar da ba a hannun Appa yanzu. Amma kuma tana jin kamar za a kara mata kewa ne domin babu Hamad a kusa da ita a yanzu Hurriyar take gani tana jin sanyi yanzu kuma za a dauke ta. Har aka iso gida da ita kuka take sosai kamar na mutuwa, gaba daya ta bi ta rike ce da direban yayi parking ta rasa ina zata shiga bangaren Hajiya Kaltume ko Momy gurin da dakinta yake a yanzu, ko kuma bangaren mahaifiyarta da babu kowa a cikin, kamar wata bakuwa haka ta rika kallon gidan.
“Hurriya”
Ta dago da sauri ta kalli Dattijon direban da ya kawo ta, jikinta na rawa.
“Ki yi hakuri ki yi da addu'a babu abun da yake daurewa”
Tana kokarin amsa masa da kai sai ta kasa, daman shi kam baki ba zata iya furta komai ba.
“Ina zaki je? Gurin Momy ko gurin Hajiya Kaltume?”
Sai kawai ta fashe masa da kuka.
“Ko kuma gurin Alhaji zaki je? Yana nan ciki daman yace ba zai fita ba sai kin dawo”
Ta daga kai da sauri, sai ya kama hannunta suka isa bangaren mahaifinta sai da suka isa daf da kofar falonsa sannan ya saki hannunta.
“Ki shiga ciki”
Ta daga masa kai, sai da ya wuce sannan ta kwankwasa kofar part din kamar wata bakuwa bayan ba haka ta saba ba, idan zata shiga bangaren Appanta sai dai ta tura ta shiga da murnarta tana rangada sallama. Sai da ta yi knocked sau uku sannan ta tura kofar falon ta shiga, sanyin ac ya fara yi mata maraba da zuwa, kaminnta juyo muryar mahaifinta a dayan falon da alama waya yake, babu komai a hannunta sai carbin Amma da ta dauko, tufafinta ma sai daga baya za a dauko mata ko kuma ta yi using wadanda suke gidan na bangaren Momy. Hawaye na sauko mata kamar ba gobe haka ta shiga karamin falon tana ta son ta bude baki ta yi sallama amman ta kasa. Appa na ganinta a take annurin dake fuskarsa ya gushe kamar wanda yayi arba da bakin maciji, a take ya yanke wayar da yake ya mike tsaye ya nufota yana fada.
“Ya aka yi? Kin dawo kina ta yi ma mutane kuka mutuwa aka yi? Ni ba dan Kaltume ta matsa ba ai sai ki zauna can a gurin uwar taki”
“Appa”
Ta furta tana kallonsa gilashin dake mata garkuwa na daf da faduwa. A madadin ya amsa sai yace waye bana son jin muryarsa ba ke ba, a take korata ya saka ta gaba.
“Muje can bangaren Nafisa tafi tafi”
Ta tsaya a gurin tana kallonsa kamar hoto har ya iso, ganin ba tafiya zata yi ba ya saka shi fisgar hannunta ya wuce gaba ya hanyota sai kallonsa take har suka isa cikin falon Momy ya sannan ya saki hannunta. Kamin ya ce komai Momy ta aje plate din doyar dake hannunta ta rafka salati.
“Haba Alhaji, ina laifi ka barwa Iyami yarinyar tana ganinta tana jin sanyi? Ni dai tsakani da Allah hankali ya fi kwanciya yarinyar ta zauna a gurin uwarta”
Ita ma kamar Appa na jiranta sai ya rufeta da fada.
“A nan nake son ta zauna, a nan zata zauna ke kanki gurin da na ga dama zaki zaun balle kuma ita da take yata, karki sake fada min abun da ya kamata na yi, ba shawararki nake nema ma”
Tabe baki ta yi bata sake cewa komai ba har ya fice, sannan ta ce
“Ni ma dan an rasa ya za'ayi da ni ne, na cika na make gurin kuma sai hakuri Wallahi, ni da zai maida Iyami ki koma can gurinta ya fi min kwanciyar hankali, ina zan iya da rikon yayan wasu yayan da idan suka girma suka samu arikin uwarsu za su nema”
Hurriya dai tana tsaye a gurin da Appa ya barta ta kasa matsawa ko'ina sai hawaye take. Mahaifinta ya canja mata, ta rasa dan'uwanta kuma ta rasa mahaifiyarta a kusa da ita.
“Lafiya kika tsaya nan kika zuba min ido? Mahaifinki ma baki da amfani a gurinsa yanzu balle kuma ni, wuce ki tafi dakinki tun da an kawo min kaya ya zan yi, Iyami ta haifa mana ta tafi ta bari”
Huriyya ta dauke kai da sauri ta fara tafiya, sai kuma Momy ta kirata.
“Hurriya”
Ta juyo a hankali ta kalleta ta kasa amsawa har lokacin hawaye take.
“Zo ki zauna yi hakuri kinji”
Hurriya ta dawo ta zauna saman kujerar dake dama da Momy.
“Gaskiya dai Alhaji ya ci amanarki Wallahi, ni ai ko da bala'i sai na karbi yayana, ko da yake Iyami ba zata iya ja da Alhaji ba, ta ina talauci zai ja da arziki, amman dai gaskiya be dace ya rabaki da Iyami yanzu ba, ai sai tunanin ya hade miki ga na dan'uwa ki kamu da hawan jini da kurciyarki, kai Kaltume bata da imani, haka fa ta raba Sapna da ubanta, Sapna bata isa ta tako garin nan ta ce zata zo gurin ubanta ba, tana can kauye cikin talauci shi kuma ya kyaleta... Hmmmm”
Ta mike tsaye tana kwalawa mai aikinta kira.
“Bilki”
Tsohuwar ta fito da gudu daga kitchen, daman haka take da yan aiki idan tana falo sai dai su boya a wani guri bata zama daki daya da su, idan har ka gansu a falo to tana dakinta ne ko kuma ta fita.
“Hajiya ga ni”
“A dauke plate din nan kuma ga yar Iyami nan idan zata ci abinci a zuba mata”
“Toh Hajiya”
Tsohuwar ta dauke plate din sannan ta kalli Hurriya dake zaune.
“Hurriya a zuba miki abinci?”
Hurriya ta girgiza kai alamar aa, Momy tabe baki ta dauki wayarta.
“Dan kan masa in ji sure, cikinki ko na wani, kin san dai ba rarrashinki zan yi dan ki daina kuka ko ki ci abinci ba, ina da tausayi da zuciyar imani amman laisa son dan wani kamar nawa kam karya haram babu boye boye ba munafurci, shiyasa ni na fi sha'awar uwarku ta dawo ta rike yayanta”
Tana fadan tana hawa sama har ta haye ta shige dakinta, Mai aikinta kam tuni ta san inda dare yayi mata. Hurriya ta bi ta kallo har ta haye stairs din, ji ta yi kamar ace wani na nan ta fada jikinsa ya rumgume ta yi kuka ammab babu wannan damar, saukowa ta yi daga saman kujera ta zauna kasa sai ta dora kanta sama kujera ta takure guri daya. Ta rufe ido hawaye na sauko mata. After like 30min ta ji an zungureta sai ta farka da sauri gilashin idonta ya fadi da sauri ta dauka ta saka ta gyara mayafin abayarta ta kalli Musib dake tsaye kanta.
“Miye na yi ma mutane bachi a kujera kin wani takure salon wani ya shigo ace ke ce marar gata a gidan ke ga munafuka, wato kin dawo babu zaman lafiya, mun rabu da Hamad ke kuma zaki kirkiri mugun abu ko?”
Kamar wani mace haka yake fada da ita yana gautsina fuska, gently ta mike tsaye domin ita ma bata san bacci ya dauke ta sai da ya tasheta. Tafiya ta fara yi ta haye sama ta dade a tsaye tana kallon kofar dakin Hamad tana jin kamar idan ta tura zata ganshi kwance ya ba kofar baya kamar yadda ya saba kwanciya. Wani hawayen ya sake cika idonta wani abu mai kama da dutse ya tsaya mata a tsakiyar zuciya ya mata nauyi. Cikin karfin hali ta kai hannu ta tura kofar dakinta ta shiga sai da maida kofar ta rufe ta jingina jikin kofar ta rumgume hannayenta not knowing what to do ita dai ba kuka take ji ba a yanzu, hawaye ne kawai ke mata zuba, tunanin dake mabanbantan duniyoyi ya hade mata guri daya, idan ta tuna Hamad ta tuna Amma, ta tuna Appa. Jin ta yi an yi knocking kofar dakin wani abu mai kama da tsoro ya fisgeta ta tashi tsaye da sauri jikinta na rawa ta yi baya tana kallon kofar, Namra ce ta turo kofar ta shigo da far'arta.
“Hurriya kin dawo”
Kamin ta rufe baki Yasir ya shigo cikin yanayi na damuwa yana kallonta.
“Hurriya”
Ta kasa amsawa Namra balle Yasir da ya shigo bayanta, ta hade yawu da karfi tana kallonsu. Yasir ya nufi gadonta ya zauna ya rasa me zai ce mata shi kansa be jin dawowarta gidan a yanzu mafita ne a gareta, babu yadda be yi ba wajen ganin ya fahintar da Hajiya Kaltume akan ta hana Appa dauko ta amman ta kasa fahimtarshi.
“Hurriya zauna”
Ta zauna a gurin kamar wata wadda tunani ya birkicewa kwakwalwa. Namra dai ta tsaya jikin kofar ita ma tara ran duk babu dadin ganin yar'uwarta cikin damuwa.
“Hurriya ki yi hakuri dan Allah, idan kina kukan nan sai ki saka kanki a damuwa”
Yasir ya daga ma Namra hannu alamar ta daina maganar sai ta yi shuru ta juya ta fice daga dakin, dan zumudin da ta zo da shi na murnar dawowar Hurriya sai ya gushe.
“Hurriya kina son zama nan ko kin fi son zama gurin Amma? Idan gurin Amma kike so zan mu tafi tare da ni dake mu yi ma Appa magana, idan be amince ba sai mu fadawa Hajiya Binta”
Ta girgiza kai alamar bata aa.
“Kina son zama nan din?”
Ta daga masa kai.
“Shi ke nan zo ki kwanta, kin yi sallah ko?”
Ta amsa masa da kai sannan ta nufi gadon ta kwanta shi kuma ta tashi ya fice, kai tsaye bangaren mahaifinsa ya nufa sai dai yayi rashin sa'a be tararda shi ba, domin tuni ya fita after ya kai Hurriya bangaren Momy daman ita kawai yake jiran a dawo da ita gidan ya fita, saboda Hajiya Kaltume ta fada masa idan be yi da gaske ba Amma ba zata ba shi Hurriya ba.
Hurriya bata tabbatar da mahaifinta ya daina yayinta ba sai da ya canja mata makaranta ya saka ta makarantar government, yayinda sauran yan'uwanta da suke ajin karshen a private school suke can suna karatu. Ita kuma aka bata direba daya da zai rika kaita makaranta yana daukota ita kadai, ba karama ta kaddama aka yi ba kamin Appa ya saka ta government school, domin malaman dake karantar da ita a private school suna sonta sosai saboda kokarin da take da shi, ga kuma gasar da suke ta shirye shiryen turata. Har komiti suka hada na manyan makarantar suka zo har gida suka tarardar Appa suka tattauna da shi tare da nuna masa illar cire Hurriya a makarantar amman ya ki saurarensu saboda Hajiya Kaltume ta ba shi shawarar kaita makarantar Government, daga karshe ma sai suka rabu cikin rashin dadin rai domin Appa rufe su yayi da fada ya nuna musu Hurriya yarsa ce shi ke da iko da ita babu wanda ya isa ya fada masa me zai yi akan yarsa hukuncin da ya yanke ke nan kuma babu fashi.
Ta bangaren Hurriya ma hakan ya taba ta sosai domin yin sabin abokai da kuma canja wasu abubuwa na karantu domin malaman ba daya ba be ya zama abu ne marar sauki a gareta, hakan sai ya saka ta zama weak ta yadda bata iya maida hankali ta yi karatun yadda ya dace, gaba daya ta koma kamar ba ita ba, karatun da take ganewa a can bata ganewa yanzu, sai ayi darasi a gama bata fahimci komai ba, tunani da damuwa suka taru suka yi mata yawa, gashi kullum ita ce cikin kebe kanta bata son shiga cikin yan makarantar da bata saba da su ba.
**** **** ****
Hindu ta mika mata jaririn dake kuka.
“Iyami ina ta fada miki banza bata fitar da ke gidan Alhaji, amman kika sa kafa kika yi biris da maganata, yanzu gashin bayan fitar da ke ta dauke hankalinsa daga kan Yayansa, bayan an a kashe miki daya, kuma han karbe dan abun da yake hannunki, ina dadi ka haihu gari daya da miji amma yaki ya tako ya duba yara, ke da da ns yadda Alhaji yake sonki ai
Showing 15001 words to 18000 words out of 215510 words
Hajiya Kaltume ta yi saurin rufewa Ruma baki tana juyata ta kalli kofar dakin, sannan ta juyo ta kalli Ruma tana kuka.
“Wallahi ban ce a kashe shi ba, Yaushe zan ce a kashe shi? Wallahi ban ce a kashe shi ba, kuma Wallahi idan wani ya ji maganar nan Ummu Rumana sai kin yi bakincikin zuwa duniya”
Hajiya Kaltume ta sake ta fice daga dakin da sauri tana share hawayenta, da hakki ta isa nata dakin ta zauna bakin gado kamar wadda ta yi gasar tsere hakki ne na mai jin tsoro da fargaba faruwa wani ba, ba na wanda yayi wani aiki ba. Da sauri ta lalabi wayarta ta kira macen da ke share mata kukanta...
“Hajiya Fatee ke kadai kike?”
“Ni kadai nake Hajiya Kaltume Lafiya?”
Hajiya Kaltume ta fashe da kuka tana fada mata abun da Ruma ta yi mata.
“Ah toh ita kuma duk saboda wa kike abun?”
“Ita wannan bata gani ai, da ma Khairi ce ita ce mai irin zuciyata, kuma ni Wallahi ban dauki yaron nan dan a kashe shi ba, kaddara ce kawai ni ba ma shi na so a dauka ba, yar makauniyar na so a dauka, amman abu ya zo a haka”
“To yanzu me ye abun yi?”
“Abun yi kawai a rufe mata baki, domin na lura tona min asiri zata yi, tun da ta dawo gaba daya ta bi ta canja, sai zancen barin gidan take nan gaba kadan zata iya cewa zata fadawa wani idan abu ya cika”
“Lallai da maganarki, haka ya kamata, daman ita bata san kan duniya ba shekara goma sha bakwai miye ta sani, ai da gaskiyarki da baki saka ta a lamurranki duk da shige miki da take da sabon da kuka yi, wannan ai sai ta fadawa duniya mun je gurin kaza da kaza”
“Ina zan yarda? Ai duk yarana bana zuwa da ko daya, sai dai na fada musu”
“Haka ya kamata gaskiya ki kirashi ki fada masa komai idan akwai yadda za ayi a danne bakinta nan dan kar ta fada”
“Zan kira shi, daman ban gama fita bakincikin Iyami ba yanzu kuma ita zata tsirar min wani sabon shafi”
“Wallahi kuwa shegiyar dagar ta sake jefo masa yan biyu haihu kamar karya kuma duk maza, ta dai rantsa sai ta ci gadon Alhaji daman shi ne take ta yi ma wannan haife haifen, ai Wallahi an rage mugun iri ma, yaron nan ba fadar kike yana damunku”
“Wallahi ya addabi kowa, kuma ni ba shi na ce a dauka ba, iya yar macijiyar na ce a dauka, su kuma sai suka bata aikin suka kira wayata a gabansu yaro ya ji muryata, shi ne duk sila ni kaina kullum tunanin yaron nan nake nake Wallahi abun ya hana ni sukuni sam”
“Allah dai ya rufe asiri kar wannan yar autar taki ta janyo mana jagwal”
“Ameen, ai maganinta zan yi”
Daga haka suka yi sallama, babu bata lokaci Hajiya Kaltume ta lalabo number Malaminta a wayar ta kira shi domin kai masa kukanta, daman kiran Hajiya Fatee da ta yi na neman jin shawarar abun da zata ce ne domin bata yanke hukunci sai ta shawarci aminiyarta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻*HURIYYA*
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 6️⃣
The following week Appa ya aika mota dauko Hurriya, a lokacin ne hankalin Amma ya tashi sosai daman babu irin magiyar da bata yi ma Hajiya Binta ba a lokacin da ta zo mata da sakon cewar Appa zai aiko da mota a dauki Hurriya next week, Hajiya Binta ma ta yi iya kokarinta amman be saurareta ba, saboda ba zai iya tsabawa abun da Hajiya Kaltume take so a yanzu ba, ita kadai zata ba shi shawara ya dauka bayan ita baya sauraren kowa ciki har da mahaifiyarsa da kuma Momy da bata ma gane kansa yanzu, sai dai bata cika damuwa da al'amurransa ba domin ta bussinees dinta take da harka da manyan mutane. Son ta mallaki gida ko ta mallake Alhaji Haruna baya gabanta domin jin take kamar ma ta kusa gogawa da shi a arziki. Hurriya kamar zata shide haka aka fito da ita daga gidan ita kuka Amma kuka Gwaggo kuka Rukayya kuka tana rikon Amma amma na rike ta kamar wadanda za a raba rabuwa ta har abada. Ita dai bata son komawa gidan saboda babu dan'uwanta mai tare mata fada a cikin haka kuma babu mahaifiyarta, kuma a yadda ta fahimta ba zata sha da dadi kamar da ba a hannun Appa yanzu. Amma kuma tana jin kamar za a kara mata kewa ne domin babu Hamad a kusa da ita a yanzu Hurriyar take gani tana jin sanyi yanzu kuma za a dauke ta. Har aka iso gida da ita kuka take sosai kamar na mutuwa, gaba daya ta bi ta rike ce da direban yayi parking ta rasa ina zata shiga bangaren Hajiya Kaltume ko Momy gurin da dakinta yake a yanzu, ko kuma bangaren mahaifiyarta da babu kowa a cikin, kamar wata bakuwa haka ta rika kallon gidan.
“Hurriya”
Ta dago da sauri ta kalli Dattijon direban da ya kawo ta, jikinta na rawa.
“Ki yi hakuri ki yi da addu'a babu abun da yake daurewa”
Tana kokarin amsa masa da kai sai ta kasa, daman shi kam baki ba zata iya furta komai ba.
“Ina zaki je? Gurin Momy ko gurin Hajiya Kaltume?”
Sai kawai ta fashe masa da kuka.
“Ko kuma gurin Alhaji zaki je? Yana nan ciki daman yace ba zai fita ba sai kin dawo”
Ta daga kai da sauri, sai ya kama hannunta suka isa bangaren mahaifinta sai da suka isa daf da kofar falonsa sannan ya saki hannunta.
“Ki shiga ciki”
Ta daga masa kai, sai da ya wuce sannan ta kwankwasa kofar part din kamar wata bakuwa bayan ba haka ta saba ba, idan zata shiga bangaren Appanta sai dai ta tura ta shiga da murnarta tana rangada sallama. Sai da ta yi knocked sau uku sannan ta tura kofar falon ta shiga, sanyin ac ya fara yi mata maraba da zuwa, kaminnta juyo muryar mahaifinta a dayan falon da alama waya yake, babu komai a hannunta sai carbin Amma da ta dauko, tufafinta ma sai daga baya za a dauko mata ko kuma ta yi using wadanda suke gidan na bangaren Momy. Hawaye na sauko mata kamar ba gobe haka ta shiga karamin falon tana ta son ta bude baki ta yi sallama amman ta kasa. Appa na ganinta a take annurin dake fuskarsa ya gushe kamar wanda yayi arba da bakin maciji, a take ya yanke wayar da yake ya mike tsaye ya nufota yana fada.
“Ya aka yi? Kin dawo kina ta yi ma mutane kuka mutuwa aka yi? Ni ba dan Kaltume ta matsa ba ai sai ki zauna can a gurin uwar taki”
“Appa”
Ta furta tana kallonsa gilashin dake mata garkuwa na daf da faduwa. A madadin ya amsa sai yace waye bana son jin muryarsa ba ke ba, a take korata ya saka ta gaba.
“Muje can bangaren Nafisa tafi tafi”
Ta tsaya a gurin tana kallonsa kamar hoto har ya iso, ganin ba tafiya zata yi ba ya saka shi fisgar hannunta ya wuce gaba ya hanyota sai kallonsa take har suka isa cikin falon Momy ya sannan ya saki hannunta. Kamin ya ce komai Momy ta aje plate din doyar dake hannunta ta rafka salati.
“Haba Alhaji, ina laifi ka barwa Iyami yarinyar tana ganinta tana jin sanyi? Ni dai tsakani da Allah hankali ya fi kwanciya yarinyar ta zauna a gurin uwarta”
Ita ma kamar Appa na jiranta sai ya rufeta da fada.
“A nan nake son ta zauna, a nan zata zauna ke kanki gurin da na ga dama zaki zaun balle kuma ita da take yata, karki sake fada min abun da ya kamata na yi, ba shawararki nake nema ma”
Tabe baki ta yi bata sake cewa komai ba har ya fice, sannan ta ce
“Ni ma dan an rasa ya za'ayi da ni ne, na cika na make gurin kuma sai hakuri Wallahi, ni da zai maida Iyami ki koma can gurinta ya fi min kwanciyar hankali, ina zan iya da rikon yayan wasu yayan da idan suka girma suka samu arikin uwarsu za su nema”
Hurriya dai tana tsaye a gurin da Appa ya barta ta kasa matsawa ko'ina sai hawaye take. Mahaifinta ya canja mata, ta rasa dan'uwanta kuma ta rasa mahaifiyarta a kusa da ita.
“Lafiya kika tsaya nan kika zuba min ido? Mahaifinki ma baki da amfani a gurinsa yanzu balle kuma ni, wuce ki tafi dakinki tun da an kawo min kaya ya zan yi, Iyami ta haifa mana ta tafi ta bari”
Huriyya ta dauke kai da sauri ta fara tafiya, sai kuma Momy ta kirata.
“Hurriya”
Ta juyo a hankali ta kalleta ta kasa amsawa har lokacin hawaye take.
“Zo ki zauna yi hakuri kinji”
Hurriya ta dawo ta zauna saman kujerar dake dama da Momy.
“Gaskiya dai Alhaji ya ci amanarki Wallahi, ni ai ko da bala'i sai na karbi yayana, ko da yake Iyami ba zata iya ja da Alhaji ba, ta ina talauci zai ja da arziki, amman dai gaskiya be dace ya rabaki da Iyami yanzu ba, ai sai tunanin ya hade miki ga na dan'uwa ki kamu da hawan jini da kurciyarki, kai Kaltume bata da imani, haka fa ta raba Sapna da ubanta, Sapna bata isa ta tako garin nan ta ce zata zo gurin ubanta ba, tana can kauye cikin talauci shi kuma ya kyaleta... Hmmmm”
Ta mike tsaye tana kwalawa mai aikinta kira.
“Bilki”
Tsohuwar ta fito da gudu daga kitchen, daman haka take da yan aiki idan tana falo sai dai su boya a wani guri bata zama daki daya da su, idan har ka gansu a falo to tana dakinta ne ko kuma ta fita.
“Hajiya ga ni”
“A dauke plate din nan kuma ga yar Iyami nan idan zata ci abinci a zuba mata”
“Toh Hajiya”
Tsohuwar ta dauke plate din sannan ta kalli Hurriya dake zaune.
“Hurriya a zuba miki abinci?”
Hurriya ta girgiza kai alamar aa, Momy tabe baki ta dauki wayarta.
“Dan kan masa in ji sure, cikinki ko na wani, kin san dai ba rarrashinki zan yi dan ki daina kuka ko ki ci abinci ba, ina da tausayi da zuciyar imani amman laisa son dan wani kamar nawa kam karya haram babu boye boye ba munafurci, shiyasa ni na fi sha'awar uwarku ta dawo ta rike yayanta”
Tana fadan tana hawa sama har ta haye ta shige dakinta, Mai aikinta kam tuni ta san inda dare yayi mata. Hurriya ta bi ta kallo har ta haye stairs din, ji ta yi kamar ace wani na nan ta fada jikinsa ya rumgume ta yi kuka ammab babu wannan damar, saukowa ta yi daga saman kujera ta zauna kasa sai ta dora kanta sama kujera ta takure guri daya. Ta rufe ido hawaye na sauko mata. After like 30min ta ji an zungureta sai ta farka da sauri gilashin idonta ya fadi da sauri ta dauka ta saka ta gyara mayafin abayarta ta kalli Musib dake tsaye kanta.
“Miye na yi ma mutane bachi a kujera kin wani takure salon wani ya shigo ace ke ce marar gata a gidan ke ga munafuka, wato kin dawo babu zaman lafiya, mun rabu da Hamad ke kuma zaki kirkiri mugun abu ko?”
Kamar wani mace haka yake fada da ita yana gautsina fuska, gently ta mike tsaye domin ita ma bata san bacci ya dauke ta sai da ya tasheta. Tafiya ta fara yi ta haye sama ta dade a tsaye tana kallon kofar dakin Hamad tana jin kamar idan ta tura zata ganshi kwance ya ba kofar baya kamar yadda ya saba kwanciya. Wani hawayen ya sake cika idonta wani abu mai kama da dutse ya tsaya mata a tsakiyar zuciya ya mata nauyi. Cikin karfin hali ta kai hannu ta tura kofar dakinta ta shiga sai da maida kofar ta rufe ta jingina jikin kofar ta rumgume hannayenta not knowing what to do ita dai ba kuka take ji ba a yanzu, hawaye ne kawai ke mata zuba, tunanin dake mabanbantan duniyoyi ya hade mata guri daya, idan ta tuna Hamad ta tuna Amma, ta tuna Appa. Jin ta yi an yi knocking kofar dakin wani abu mai kama da tsoro ya fisgeta ta tashi tsaye da sauri jikinta na rawa ta yi baya tana kallon kofar, Namra ce ta turo kofar ta shigo da far'arta.
“Hurriya kin dawo”
Kamin ta rufe baki Yasir ya shigo cikin yanayi na damuwa yana kallonta.
“Hurriya”
Ta kasa amsawa Namra balle Yasir da ya shigo bayanta, ta hade yawu da karfi tana kallonsu. Yasir ya nufi gadonta ya zauna ya rasa me zai ce mata shi kansa be jin dawowarta gidan a yanzu mafita ne a gareta, babu yadda be yi ba wajen ganin ya fahintar da Hajiya Kaltume akan ta hana Appa dauko ta amman ta kasa fahimtarshi.
“Hurriya zauna”
Ta zauna a gurin kamar wata wadda tunani ya birkicewa kwakwalwa. Namra dai ta tsaya jikin kofar ita ma tara ran duk babu dadin ganin yar'uwarta cikin damuwa.
“Hurriya ki yi hakuri dan Allah, idan kina kukan nan sai ki saka kanki a damuwa”
Yasir ya daga ma Namra hannu alamar ta daina maganar sai ta yi shuru ta juya ta fice daga dakin, dan zumudin da ta zo da shi na murnar dawowar Hurriya sai ya gushe.
“Hurriya kina son zama nan ko kin fi son zama gurin Amma? Idan gurin Amma kike so zan mu tafi tare da ni dake mu yi ma Appa magana, idan be amince ba sai mu fadawa Hajiya Binta”
Ta girgiza kai alamar bata aa.
“Kina son zama nan din?”
Ta daga masa kai.
“Shi ke nan zo ki kwanta, kin yi sallah ko?”
Ta amsa masa da kai sannan ta nufi gadon ta kwanta shi kuma ta tashi ya fice, kai tsaye bangaren mahaifinsa ya nufa sai dai yayi rashin sa'a be tararda shi ba, domin tuni ya fita after ya kai Hurriya bangaren Momy daman ita kawai yake jiran a dawo da ita gidan ya fita, saboda Hajiya Kaltume ta fada masa idan be yi da gaske ba Amma ba zata ba shi Hurriya ba.
Hurriya bata tabbatar da mahaifinta ya daina yayinta ba sai da ya canja mata makaranta ya saka ta makarantar government, yayinda sauran yan'uwanta da suke ajin karshen a private school suke can suna karatu. Ita kuma aka bata direba daya da zai rika kaita makaranta yana daukota ita kadai, ba karama ta kaddama aka yi ba kamin Appa ya saka ta government school, domin malaman dake karantar da ita a private school suna sonta sosai saboda kokarin da take da shi, ga kuma gasar da suke ta shirye shiryen turata. Har komiti suka hada na manyan makarantar suka zo har gida suka tarardar Appa suka tattauna da shi tare da nuna masa illar cire Hurriya a makarantar amman ya ki saurarensu saboda Hajiya Kaltume ta ba shi shawarar kaita makarantar Government, daga karshe ma sai suka rabu cikin rashin dadin rai domin Appa rufe su yayi da fada ya nuna musu Hurriya yarsa ce shi ke da iko da ita babu wanda ya isa ya fada masa me zai yi akan yarsa hukuncin da ya yanke ke nan kuma babu fashi.
Ta bangaren Hurriya ma hakan ya taba ta sosai domin yin sabin abokai da kuma canja wasu abubuwa na karantu domin malaman ba daya ba be ya zama abu ne marar sauki a gareta, hakan sai ya saka ta zama weak ta yadda bata iya maida hankali ta yi karatun yadda ya dace, gaba daya ta koma kamar ba ita ba, karatun da take ganewa a can bata ganewa yanzu, sai ayi darasi a gama bata fahimci komai ba, tunani da damuwa suka taru suka yi mata yawa, gashi kullum ita ce cikin kebe kanta bata son shiga cikin yan makarantar da bata saba da su ba.
**** **** ****
Hindu ta mika mata jaririn dake kuka.
“Iyami ina ta fada miki banza bata fitar da ke gidan Alhaji, amman kika sa kafa kika yi biris da maganata, yanzu gashin bayan fitar da ke ta dauke hankalinsa daga kan Yayansa, bayan an a kashe miki daya, kuma han karbe dan abun da yake hannunki, ina dadi ka haihu gari daya da miji amma yaki ya tako ya duba yara, ke da da ns yadda Alhaji yake sonki ai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6 Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72