ta girgiza kai sannan ta juya ta fita tana fadin.

“Shiyasa lokacin zuwa makaranta kike late ba zaki shirya ba sai a lokacin da ake jiranki”

Murmushi kawai ta yi ta jira tare da Namra suna sauka tare, Hurriya na ganin Momy ta yi saurin risinawa kamar yadda ta saba gaishe da manya.

“Momy barka da yamma”

Momy ta watsa mata harara.

“Sai yanzu kika ga damar gaishe ni, ba kin san ina cikin gidan ba? Me yasa baki gaishe ni ba sai yanzu”

Ta yi shiru ba dan bata da abun fada ba, sai dan ta san tana fadar wani abu Momy zata iya tsinka mata mari, kamar yadda bata isa ta shiga dakinta da sunan ta zo gaishe ta, sai dai ta tsaya jiranta idan ta fito ta gaisheta kamar wata yar aiki, wannan ne abin da Hurriya ta kasa yi, Momy kuma take jin haushinta.

“Momy mu dai mun tafi”

A take murmushi ya cika fuskarta tana kallon yar gudaliyar yarta mace daya tak data haifa.

“Allah ya tsare, ya dawo lafiya yar Auta”

Ta yi murmushi sannan ta yi ma Hurriya alama da ta tashi su tafi, Hurriya ta tashi suka fice tare. A tare suka shiga motar Namra na tuki Hurriya na zaune gaba tana sauraren sautin da Namra ta kure a motar idanuwanta kuma suna kallon wani gurin dabam har suka isa Sarauta Mall. A harabar Namra ta faka ta fito sannan Hurriya, after ta rufe motar suka nufi cikin Mall din tana fadawa Hurriya abubuwan da take son siya.

“Zaki iya daukar wani abu da kika ga kina so amman fa kar ya wuce 20k”

Fuskar Hurriya ta cika da murmushi.

“Na gode Yaya Namra amman ni ki ba ni kudin akwai abun da zan yi da su”

Da mamaki Namra ta kalleta tana kokarin kai hannu ta dauki turare.

“Me zaki yi?”

“Wani abu dai bana son na fada, amman yana da muhimmanci sosai”

“Shi ke nan to idan mun koma ki turo min account dinki sai na miki transfer”

Take a gurin Hurriya ta rumgume ta.

“Na gode Yaya Namra ke ma kina so na kamar Yaya Yasir”

Namra ta yi murnushi suka ci gaba da siyayyar after sun gama suka nufi gurin biya, Namra ta bude jakarta ta dauko cart dinta ta mika.

“Aa an biya muku Hajiya”

“An biya kuma?”

“Eh ba na yau kadai ba har ma da wanda zaku sake zuwa nan gaba ko da kuwa za ku yaye shagon nan ne gaba daya”

“Waya biya? Wanene wanda baya son kudinsa haka?”

“Gashi can bayanku”

Daga Hurriya har Namra juyawa suka yi kallon mai neman barar da kudi saboda be san kimarsu ba. Suna hada ido kowanensu ya gane waye. Shi kuma ya nufo inda suke idonsa na kan Hurriya.

“Kai ka biya kudi?”

Namra ta tambaya tana hade masa rai.

“Eh”

“Saboda me?”

Ya kalli Hurriya dake tsaye tana kallon ikon Allah.

“Saboda Hurriya”

“Miye tsakaninka da ita? Kuna da wata alaka ne?”

“Alakar dai nake kokarin kullawa, waye ke?”

Wannan karon Hurriya ce da kanta ta tari numfashin yayarta ta amsa masa rai a bace.

“Yayata ce, kuma daga yau karka sake nuna ka san ni domin ni ba yarka ba ce, kuma karka sake kiran Yayana a waya kana cewa a hada ka da ni”

Adam yayi murmushi.

“Ya fada miki kenan? Na kira Khairi ta ki hada ni da ke, the last kiran da na yi ma yayanki ma be saurare ni ba ya rufe ni da fada, Na gode Allah ma da na ganki a nan”

“Eh saboda basa son kana kirana kuma karka sake, sunana ya fita daga bakinka, mu tafi Yaya Namra”

Namra ta bita da kallo she never thought Hurriya zata iya bude baki ta yi masifa haka. Shi ma kallonta yake domin bata yi kama da irin yan matan nan masu masifa ba. Adam ya maida dubansa gurin Namra da ta mika hannu ta dauki ledar kayanta.

“Khairiyya ce ta ce muku ni dan'iska ne?”

Namra ta kalleshi sama da kasa at his age ba zai wuce 25-26 ba that's mean ya bata shekara daya kenan ko biyu.

“Malam Hurriya ba irin matan nan ba ne, dan Allah ka kama gabanka”

Ta dauki ledarta ta nufi kofar fita, suka bar shi a gurin kunya kunya ma'aikatan gurin na kallonsa. Ko da Namra ta isa gurin motar Hurriya na tsaye ta hade rai ya rungume hannayenta tana jiran fitowarta.

“Ashe kin iya fada”

“Ya bata min rai fa, jiya saboda shi Appa kamar zai dake ni, Kuma Yaya yayi ta fada sosai”

Ta fada ba tare da ta kalleta ba.

“Shiga muje”

Hurriya ta bude motar ta shiga, Namra ta fara tukawa. A motar Namra sai zaginsa take yana tsine masa tare da fadar daman irin samarin nan haka suke.

“Ni da na sani ma ba zan birthday din ba”

“Abun yar'uwa ace ba za aje ba? Ai dole ka je Khairy dai ta zama wata kalar mace daman tun kamin ta kare karatun na wata friend dinta ke fada mana tana shan shisha, kamar kar ta fara sami'ar nan sai ta hadu da friends din banza suka canja mata rayuwa gaba daya ta canja”

Tana maganar tana kokarin kwaucewa motar take gabansu. Overtaking take son yi amman mai motar ya hanata hanya, kasancewar titi express ne idan ta yi dama sai ya koma can idan ta yi hagu sai yayi hagu. Horn ta danna da karfi shi ma ya mayar mata, at first ranta ya baci har ta yi kamar ta bugu motar dake gabansu sai kuma ta danne zuciyarta.

“Mai motar nan lafiya yake kuwa?”

“Ko yayi shaye shaye”

“Maybe”

Namra ta rage gudun motar shi ma sai ya rage, the second thing she did was laugh irin abun yanzu kuma ya zama out of sence. Ta dan gwada kara gudun shi ma sai ya kara, ta sake raguwa sai ya rage. Tana samun sa'a ta yi overtaking ta wuce da gudu, shi ma sai ya danna a guje ya wuce, wannan karon har da Hurriya sai da ta yi dariya, Namra ta sake yin gaba ta wuce shi sai ta sauya hanya, ga mamakinta sai ya biyota a baya ya wuce, daga lokacin ne suka fara tseren gudu ita da shi ba dan sun san waye a motar ba. Ita dai daman gilashin motarta a bude yake daga ita har Hurriya ana kallon yadda suke shakar dariya su ne basa iya ganin wanda ke cikin motar. Da gangan Namra ta sake sauya hanya tana dariya tana kallon nearby mirror bata ga ya biyo ba, sai da suka kusa isa karshen Titi sai gashi ya bullo ta gabansu.

“Mun shiga uku Hurriya waye mutumen nan?”

Hurriya dariya kawai take ta kasa cewa komai, domin a gurinta abun is so funny ita bata tsorata kamar yadda Namra ta fara tsorata yanzu ba. Namra ta rage gudun motarta ta sauka gefen titi shi ma sai ya rage gudun ya sauka gefen titi ya faka gabansu.

“Ki daina dariya what if he want to kidnap us? Ko kuma wannan saurayin ne na dazu?”

Hurriya ta ji gabanta ya fadi a take ta daina dariyar, A daidai lokacin da aka bude motar wani matashin saurayi ya fito sanye da black T-shirt da wandon soja haka ma kafarsa na sanye da black shoes. Murmushin da suka gani a fuskarsa ne ya dan sanyaya musu zuciya domin alama da yanayin jikinsa be yi kama da masu aikata mummunan aiki ba. Ya iso gurinta ya duko yana kallon fuskokinsu ko wannensu da tsoro a idonsa.

“Nice race”

Namra ta dan yi murmushin karfin yana kallonsa, daga fuskarsa har hasken fatarsa be yi kama da dan nigeria ba rigar soja dake jikinsa da kuma wandon. Sai dai kafarta na kan burki jiran kawai take ta ga wani abu ba daidai ba ta taka burkin da karfi.

“Na zo na bi ku har gida sai kuma na yi gudun kar na tsorata ku”

“Yanzu ma a tsorace muke”

Yayi murmushi sosai ya shafa kansa.

“Na gani ai a idon wannan”

Ya nuna Hurriya.

“But i like it, tun da kuka fito Mall nake binku shiyasa na so na bi ku har gida in case of na yi mussing race sai na biyo na kwankwasa muku”

Namra ta yi murmushi, Hurriya kam har lokacin a tsorace take. Hannu ya saka Aljihu ya ciro karamin kati ya aje mata.

“Here is my cart duk lokacin da kika yi marmarin race just give me a call I'm Salim Sarauta aka Ethiopian nice to meet you All”

Still idonsa ya kan Hurriya da tsoro ya gama bayyana a fuskarta, ya juya ta nufi gurin motarsa ya shiga ya yi reverse ya hau titi, sai da ya kawo saiti mn gurin da Hurriya take sannan ya danna horn sau biyu. Namra ta danna ta masa sau daya murmushi yayi ya dauke kai yaja motarsa, Namra ta bi motar da kallo ta mirror ta kai hannu ta dauki katin tana dubawa kamin ta kai babban yatsanta ta shafa. It take her some minutes tana kallon katin sannan ta ja motar suka cigaba da tafiya, bata yarda baya binsu ba sai da suka isa ta faka motarta.

“Yaya Namra na fada miki account din a yanzu”

“Bari sai mun shiga ciki na huta”

“Toh”

Ta bude motar ta fita tare da ledar da suka yi siyayya, har ta isa bakin kofar falon ta tura ta shiga Namra na zaune a motar bata zare key ba sai kallon katin take, har yanzu zuciyarta bata gama yarda mutumen kwarai ne ko na banza ba, and ta kasa zaba mata tsakanin jefar da katin da kuma barinsa...



•••••
•••••
•••••

khairi ta tashi zaune da sauri tana kallon Hajiya Kaltume dake yakar hakora tana murmushi.

“Haba Hajiya ni dai gaskiya”

Sai kuma ta yi shiru.

“Ke dai gaskiya me? Kin san dai tarenmu da Hajiya Fatee ko wani dabam ta dauko ta ce ki aura ba zaki ce aa ba balle kuma danta, yaro kuma yana da nasa rufin asiri daidai gwargwado”

“Amman yana da mata fa Hajiya”

“Ina ruwanki da matarsa? Matar da uwarsa ma ba sonta take ba, kuma saboda ita ne ake son hada aurenku”

“Ni gaskiya ba zan auri mai mata ba da kurciyata haka nan, kuma yana da yara fa, Hajiya kin fa san sha'anin kishiya yadda yake”

“Ko rabuwa suka yi ba hannunki yaran zasu zauna ba, kuma muna fatar kamin ki shiga ma ita ta fita kin ga shi kenan an huta”

Ta bata fuska sosai kamar zata yi kuka.

“Gaskiya Hajiya ina da sauran time yanzu fa na gama makaranta kuma nake rayuwa”

“Matsalata dake wani lokacin baki da wayo Wallahi gaba Khairi”

Ran Hajiya ya fara baci ganin tana kokarin taro yarta tana kaucewa.

“Tashi dauko min wayata tana ringing”

Ta tashi yana turo baki gaba domin ta ko'ina bata ganin ta dace da aure a yanzu da take cikin cin lokacinta.

“Maama ce”

Ta fada tana juyowa tare da picking din call din.

“Innalillahi”

Ta yi saurin mikawa Hajiya Kaltume jin yayarta tana kuka. Hajiya Kaltume ta karba ta kai a kunne gabanta na faduwa.

“Subhanallahi Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, abun har ya kai haka? Wai anya Rilwan yana da hankali kuwa? Be san waye ubanki ba a garin nan da zai saka hannu ya dake ki”

“Duka...!”

Khairi ta amsa da karfi tana kai hannu a gaba da mugun mamaki.

“Shi kenan gani nan zuwa, ki fada masa sai ya san ya saka miki hannu, ni da nake uwarki ban doke ki ba sai shi da ya ganki da hakoranki talatin da 2”

Ta sauke wayar tana masifa

“Ni da na san haka yaron nan yake Wallahi ba za'ayi auren nan ba, tun da aka yi auren nan kullum cikin tashin hankali nake, shiyasa idan na ga kiranta gabana har faduwa yake, yanzu abun ya kai har da duka da zagin iyaye”

Khairi ta tabe baki.

“Wannan mijin nata fa dan shaye shaye ne Wallahi komai zai iya aikatawa”

“Wane irin shaye shaye halinsa ne, tun tana amarya yake mata wannan iskanci yanzu kuma abun ya fara wuce gona da iri, yau shekara uku da aure nan amman kullum cikin fitina ake ita ba kishiya ba balle ace asiri ake mata”

“Amman dai ai yana neman mata kuma yana shaye shaye”

“Ta ina kika sani kin jiki da zancen banza, ke ba zako iya shaidar mutane da abun kirki ba sai na banza”

“Ni Wallahi na san abun da yake nan Hajiya ke ce baki wayanci duniya ba”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye daker tana latsa kafarta dake ciwon tun faduwar da tayi.

“Ina jin ciwon kafar nan haka dole zan tafi, wannan wane irin tashin hankali ne, ga mu cikin makiya yaro yana son kwance mana zane a kasuwa”

Ta nufi gurin da tufafinta suke ta shirya ta dauki jakarta tana tafiya kamar zata yi gurmanta saboda zugin da kafar take mata duk kuwa da zuwan da ta yi asibiti jiya ta kai kafar. Rai a bace ta shiga mota direba ya ja motar suka fice. Shekara uku kenan da auren babbar yarta da ke bin Yasir wato Maama amman ta kasa samun kwanciyar hankali irin na uwayen da suka aurar da yaransa, kusan duk wani kira da Maama zata mata daya gaisuwa daya kuma na karar mijinta ne ko kuma shi ya zo har gidansu ya kawo kararta.



__________

A gafarce ni please Wallahi uzuri ya rike ni. Amman In Shaa Allah ba zan sake post late ba, idan na sake ku ce min Hajiya Kaltume 🌚🥺
[11/9, 5:22 AM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 12*


Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻


𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660


𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣2️⃣



Tun daga falo Hajiya Kaltume take jin kukan Maama, hankalinta be kara tashi ba sai da ta shiga cikin dakin ta ga halin da yarta take ciki.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Maama? Haka Rilwan yayi miki da jiki?”

Maama ta kara narkewa da kuka tana daga idonta da yayi ja ta kalli Hajiya.

“Hajiya Rilwan kashe ni zai yi, Hajiya makure ni yayi Wallahi, yau babu kalar zagin da be yi min ba”

“Saboda me? Me kika masa? Wai me ya dauki kansa ne? Ko an fada masa baiwa aka kawo a gidan?”

Maama ta rike kafar Hajiya da sauri tana kuka.

“Hajiya ki kai ni asibiti kar idona ya siyaye”

“Haba idon yayi? Wai me kika masa ne?”

Kasa magana ta yi sai kuka take sosai tana taba jikinta, kana ganinta zaka san an doketa amman ba irin dukan dake bayyana jini ko fatar mutum a waje ba, ma'ana be fasa mata fata ba amman yayi nasarar kumbura mata jiki, idon kuma yayi ja sosai saboda kuka da kuma dukan idon da yayi. Cikin takaici da bacin rai Hajiya ta daga wayarta ta kira Yasir ta fada masa halin da ake ciki, sannan ta rika Maama suka fita daga gidan suka nufi asibiti.
Duk wata kulawa da ya kamata a bata likitocin sun bata, bayan an yi mata allura suka rubuta mata magani, a asibitin Yasir ya same su shi ya karbi takardar maganin ya siyo sannan suka dawo gida. Zama kawai ta yi Yasir be jira ta huta ba ya fara tambayar ta abun da ya hadata da mijinta.

“Maama me ya hada ku?”

Kasa kallonshi ta yi balle har ta amsa mata, ko kadan bata son bude dalilin fadansu, domin ta san yadda ransu zai bace idan ta fada, gashi mijin nata ba shi fa hakuri bata san iya inda yamutsin zai kai ba.

“Ba magana yake miki ba?”

Hajiya ta saka bakinta.

“Hajiya tsabani ne kawai irin na mata da miji”

“Tsabani dai amman sai yayi miki wannan dukan? Kullum da kalar matsalar da ake fama yanzu kuma abun ya kai ga duka”

“Ai har da zagin iyaye dazun da ta kira wayata ce min ta yi ya doke ta ya zageta, amman yanzu ta kasa fadar komai, idan mu baki fada mana ba ai dole shi mahaifinki ki fada masa”

Ta sauko kan kujerar da take zaune da sauri.

“Hajiya dan Allah karki fadawa Appa, dan Allah wannan abun ya tsaya iya nan?”

Yasir yayi mata kallon mamaki, Hajiya Kaltume ta rike baki.

“Yau na ga abu, Maama wane iri son kike yi ma bawan Allah nan ne? Mutum ya cutar da kai ka kasa fada saboda a daukar masa mataki kuma yanzu zaki ce kar a fadawa mahaifinki? To idan ya ganki me zaki ce?”

“Zan koma anjima Hajiya bana son Appa ya sani please bana son kowa ma ya sani, laifina na duk abun da ya faru amman na miki alkawari daga wannan ba za a sake ba”

Cikin kuka sosai take maganar tana hade hannayenta.

“Kin sha fadar haka, amman babu wani canji gashi nan duk ki bi
Showing 33001 words to 36000 words out of 215510 words