kin rame saboda tashin hankali, lokacin da kike gida ma kin fi kiba, an yi aure dan huta amman hutun ya gagara”

Yasir ya mike tsaye.

“Hajiya tana da gaskiya, akwai abubuwa da yawa ba be zama dole iyaye su ji ba, kuma tun da har ta fadi cewar laifinta ne sai a barta ta gyara”

Hajiya Kaltume ta dube shi.

“Yasir ba yau aka saba irin tashin hankalin nan ba, kuma yanzu tun da ya fara gwada mata da duka ba raga mata zai yi ba, musamman ma idan ya ga an kyaleshi”

“Toh ya zamu yi Hajiya, kina jin abun da take fada da bakinta fa, kuma daman ko wane gidan aure da kalar tashi jarrabawar maybe tata ke nan, kuma tun da har bata son mu ji sai mu daga mata kafa”

Maama ta lumshe ido hawaye na sauko mata ita kadai ta san yadda take ji a zuciyarta haka zalika ita kadai ta san kalar zaman auren da take da mijinta, abubuwa da yawa ta kan rufewa iyayenta da kawayenta saboda kar ran mijinta ya bace, ta wani bangaren kuma tana gudun haka ya zama silar lalacewar aurenta da mutumen da take jin idan baya tare da ita zata iya mutuwa.

“Shi ke nan, Allah ya kyauta idan ya san wata ai be san wata ba, zan tashi tsaye da rokon Allah ya kawo miki kwanciyar hankali a gidan mijinki, kuma za'ayi nasara”

Hajiya ta fada ita kanta Maama ta san Hajiya na fada ne kawai saboda Yasir yana zaune a gurin, amman ba rokon Allah take nufi ba. Yasir ya nufi dakinsa be dade ba ya sauko ya fice daga gidan gaba daya, Hajiya Kaltume ta mikawa Maama hannu alamar ta dawo kusa da ita, haka kuwa aka ayi Maama ta bar kujerar da take ta dawo ta zauna ta kusa da Hajiya Kaltume.

“Sha kuruminki, ko yanzu zamu sake Zub kudi da yardar Allah sai mun mallake shi, sai na saka an yi masa aikin da sai ya dawo karkashin kafarki yana tsoronki, yadda nake iya juya mijina a yanzu yadda nake so ke ma haka zaki juya naki mijin, ki kwantar da hankalinki komai zai wuce”

Ta share hawayenta, ba dan ta gamsu ba, domin sun sha gwada yi amman shiru ko abun yayi kamar zai kama shi sai ya kuma ya watse. Ta daga kai ta kalli Khairi wanda ta shigo rai a bace hannunta rike da waya. Ta nufi yar'uwarta da sauri hankali a tashe.

“Innalillahi Maama ji fuskarki”

Wani hawaye ya sakd taruwa a idon Maama.

“Wai ke ba zaki iya rabuwa da wannan azzalumin mutunen ba? Ba haihu kika yi da shi ba balle ko ace saboda Yaya”

Maama ta rike hannunta sosai ta jimke.

“Khairy ba zaki gane ba, duk wani abun da kike ganin zaki iya yi ko kin iya a waje ne, da zarar an yi aure labari ya sauya, kuma ki roki Allah kar ya dora miki jarabawar son namiji fiye da yadda yake sonki”

Daga Hajiya har Khairi tausaya mata suka yi, domin su duk yan kallo ne babu wanda ya san abun da take going though sai idan ta fada ko kuma shi ya fada. Khairi bata tada balli ba sai da dare yayi ta ga Maama ta shirya Yasir zai maida ita gida, a lokacin ta fara fada tana ganin be dace abar Maama ta koma ba bayan duk abun da yayi mata, ba a kira shi an masa gargadi ba.

“Ni ma dai haka na gani, abun ya fara kaiwa ga duka ya kamata ai iyaye su shigo ciki, ko da baki fadi abun da ya hada ku ba sai ayi masa gargadi”

Ta girgiza ma Hajiya Kaltume kai tana fashewa da kuka.

“Aa Hajiya dan Allah, bana son kowa ya ji, kuma abun be kai ace za a saka iyayensa ba, duk abun da ya faru laifina na na fada muku”

“Toh Allah ya kyauta gaba, tashi ku tafi”

Khairi ta bita da kallo baki sake tana ayyana idan ita ce ba zata iya daukar wannan iskancin ba. A mota babu kalar nasiha da jan kunnen da Yasir be mata ba, bayan ya yaba mata na boye sirrinta da ta yi.

“Sai dai ba komai yake bukatar boya ba, wani abun idan yayi yawa yana da kyau iyaye su ji saboda a dauki mataki”

“Na gode Yaya kuma In sha Allah zan dauki shawarka”

“Allah ya sauwake kuma ya kawo kwanciyar hankali a tsakaninku”

“Ameen”

Ta bude motar ta fita kamar ba ita ba, aure mai saka ladabo in ji hausawa. Tsayawa ta yi a gurin har sai da yayi reverse mai gadi ya bude masa gate ya fice sannan ta juyo ta shigo ciki.




HURRIYA POV.

Hurriya ta shiga dakinta ta aje mata siyayyar da suka yi sannan fito ta shige dakinta. Namra kam ta dade a motar tana sannan ta fito ta rufe ta shiga cikin gidan. Ko'ina na falon kamshi yake alamar an sauke abincin dare tun kamin magariba, tun kamin ta haura sama ta cire mayafinta ta shiga dakinta, saman gadonta ta aje mayafin kuma a saman dai ta zauna tana duba kayan shower gel ne da perfume. Bandaki ta nufa ta fara jera gel din sannan ta fito ta jera turaren ta dauki daya ta nufi dakin Hurriya, ko da ta shiga Hurriya na tsaye jikin windows rumgume da hannayenta tana kallon waje.

“Hurriya”

Ta juyo ta kalleta

“Ga turare daya ki yi amfani da shi, kuma ki tura min account din sai na saka miki kudin, amman dan Allah me zaki yi da su?”

“Wani abu ne na sirrina Yaya Namra karki takura please”

“Shikenan i trust you na san ba zaki yi wani abu marar kyau da har za ace waya baki kudin ba? You're not a bad girl”

Namra na magana tana kai hannu ta ja naman fuskarta cikin salon wasa. Hurriya ta yi murmushi ta sauke kanta kasa. Namra ta aje mata turaren saman gado ta fice zuwa dakin Momy. Ta tura kofar dakin tana sosa kanta.

“Momy wai ni kam Sarauta nan suna da Family da yawa ne?”

Momy dake kokarin cire sarkar zinarin dake wuyanta ta kalleta.

“Sarauta sunan kakansu sai ya zama yaya da jikoki suna amfani da shi, me ya faru”

“Ba komai kawai ina mamaki ne, wani muka ji ana fadarsa wai Sarauta”

“Sunan da suke bearing ne, kuma ba laifi suna da kudi kamar dai mu, yanzu kuka dawo?”

“Eh na ji gidan sai kamshi yake an sauke girki”

Momy ta yi murmushi ta mike tsaye, ta nufi bathroom Namra kuma ta kwanta a gurin ta dauki wayar Momy tana tabawa.

After fitar Namra Hurriya ta nufi gurin da turaren yake ta kai hannu ta dauka ta bude kamin ta shinshina kamshinsa Khairi ta turo kofar dakin ta shigo a kufule, waya a hannunta ba tare da ta ce komai ba ta mikawa Hurriya wayar. Sai da Hurriya ta fara kallon wayar sannan ta kalleta. Khairi ta daka mata tsawa.

“Ki karba mana”

Ta karba da sauri ta kai kunnenta ba tare da sanin waye ba.

“Hurriya i wanted to talk to you so badly duk wani abun da kika ji akaina karya ne, kawai Khairi tana fadar son ranta ne”

Hurriya kallon Khairi kawai take wayar a kunnenta ta kasa cewa komai.

“Hello... Are you there”

Ta sauke wayar ta mikawa Khairi ba tare da tace komai ba, Khairi ta karbi wayar ta kai kunnenta.

“Bata son magana da kai ya kamata ka gane mana”

“Yeah that's because you told I'm a bad person, dazun nan babu kalar maganar da bata fada min ba a gaban mutane kuma duk laifinki ne”

“Ta ina abun kuma ya zama laifina Adam? Ni ban fadi wata magana marar kyau akanka ba, idan ma zan bata ka ko na zage ka ai kamar na yi ma kaina ne”

Cikin fushi ya tsinke kiran ba tare da ya sake cewa komai ba, ita kuma ta kalli Hurriya daman kowa da wanda ya raina.

“Cikin mutane kika ci masa mutumci? Kuma kika ce masa na ce yana shaye shaye?”

“Ni ban ce kin ce ba”

“Amman dai kin masa cin mutunci a gaban mutane ko?”

Ta yi shiru, a take Khairi ta kai mata duka a baki daman tana da haushinta, tana ganin saboda ita Yayanta yaya mata duka ya ci mutuncinta a gaban friends dinta, yanzu kuma saboda ita Adam ya kira yana fada mata magana son ransa.

“Haba Yaya Khairi”

“Au haba ne? Ni banza kika saka aka yi min duka? Munafuka yar kasan wuta, haka kawai kika ja min cin mutunci da duka a gaban jama'a”

Ta kai mata duka a fuska, Hurriya ta matsa baya ganin tana son yi mata illa.

“Wallahi tallahi sai na miki fiye da abun da kika min Hurriya, sai na dandana miki bakinciki”

Hurriya dai bata ce mata komai ba sai kallonta take, Khairi ta yi kwafa ta juya ta fita daga dakin, sai kuma ta dawo da sauri ta nuna da yatsa.

“Sauran kuma ki fadawa Yaya Adam ya kira na kawo miki waya, ki ga yadda zan taka wuyanki wannan kassan na jikinki duk sai na karya su”

Ta yi kwafa a karo na biyu sannan ta fice, Hurriya ta zauna bakin gadonta tana taba bakinta dake mata zugi...

“Allah ya saka min in one way or the other”

Ta fada idonta na cika da hawaye, sai da ta gama taba bakin sannan ta tashi ta dauko pen ta dubuta account dinta ta fice daga dakin, kofar dakin Namra ta fara turawa ganin bata ciki ya saka ta aje mata takardar a kan gadonta juyo ta fito. Dakinta ta sake komawa ta dauki littafin da Gwaggo ta bata na addu'o'in ta sauko, Garden ta nufa sai da ta zauna sannan ta bude ta fara karanta addu'o'in yamma.



HAJIYA KALTUME.

A waya ta labartawa Malaminta abun da ya faru, tana hada masa da magiya tare da alkawarin yi masa duk abun da yake so matukar ya taimaka mata Maama ta samu kan mijinta.

“Haba Malam kai da ka ra kwafar min da Alhaji, kuma ga Iyami ma sai labari za ace wannan ya gagareka”

“Ba gagarata yayi ba Hajiya, wato yaron nan iyayensa suna tsaye akansa, duk lokacin da zamu yi aiki ba ma samunsa ko da ma ya kama zaki ga abin ya bi ruwa, amman duk da haka zamu kokarta zam sake yi masa aiki mai karfi”

“Dan Allah a taimaka Wallahi yanzu ba ni da tashin hankali sai na yarinyar nan, kasan yadda uwa take jin idan ta aurar yarta a gidan tashin hankali, burina ace tana zaune da mijinta lafiya kamar yadda nake da nawa”

“Karki damu zamu yi haka, yau da daren nan akwai wuridin da zan yi mata, komai zai wuce”

“Toh shikenan zan sako mata na goro yanzu a account in Shaa Allah”

“Hajiya kenan toh sai na ga sakonki”

Daga haka suka yi sallama, bata aje wayar ba ta kira aminiyarta, sai da ta fara shimfida mata halin da suka sami Maama sannan na Malam ya biyo baya.

“Oh wannan yaro dai ya zama butulu, an yi aure lafiya lafiya ashe mugu ne”

“Ai ni da na san haka yake Wallahi ba zan yarda ta aure shi, daman can ni be wani kwanta min ba”

“To yaran zamani ne ko kin hana ta ai ba zata hanu ba saboda tana son shi, kuma wani ba za a gane halinsa ba sai an yi auren ba”

“Amman dai Malam yace min zai yi aiki yanzu”

“Ai haka yafi, ni wasu mamaki suke ba ni fa ki duba ko yarinyar nan Afrah yadda aiki be kamata, da yana kamata da yanzu ta bar gidan nan amman sai kashe kudi nake a banza ko gezau”

“Shi ma yace iyayensa suna tsaye a kansa, amman duk da haka na san ba zai gagara ba, karki so ganin yadda Maama ta lalace kamar marar lafiya saboda babu kwanciyar hankali a gidan miji”

“Ai kam dole a tashi mata tsaye, ni ma na kiransa domin ina jin alamar motsi a cikina”

Hajiya Kaltume ta zare ido kamar kawarta na gabanta

“Motsi kuma?”

“Wallahi, na fada masa sai yace na bashi lokaci zai bincika yake ga me kenan a jiya na fara jin abun”

“Haba Hajiya Fatee kuma kike magana kamar kina kalau? Ai zama be gan mu ba, kira shi yanzu nan idan ma zuwa ya kamata yayi sai ya zo ayi abun da ya dace, an samu danne abu shekara uku yanzu kuma ace Labari ya canja, ai yanzu ne zamu fi shiga tashin hankali ma fiye da baya”

“Ni ma ai hankalin nawa ba a kwance yake ba, ina jiran na ji daga gareshi ne”

“Muna aje waya yanzu nan ki kira shi, har sai kin jira ya kira ai mai nema bi yake, kira shi yanzu nan”

“Toh Hajiya”

Hajiya Fatee ta katse kiran, ta shiga contact dinta ta nemo number sa da ta yi saving da Yaya Malam saboda badda kama. Fuskarta shimfide da damuwa ta kara wayar a kunne, sai dai har kiran ya katse ba daga ba, ta sake kiransa ya sake katsewa ba daga ba sai a na biyar a lokacin da hankalinta yayi kololuwar tashi. Yana daga kiran sai da ta sauke ajiyar zuciya tana jin wata rahma na sauko mata.

“Salamu alaikum Malam ina ta kira baka daga wayata ba lafiya”

“Toh Hajiya gani dai Alhamdulillah”

Tana kokarin karantar damuwar dake son aika mata ta sautin muryarsa ta ce.

“Ba lafiya ba Malam, me ya faru? Akwai wata matsala ne?”

“Babba ba karama ba, shi ya hana ni daukar wayarki, ni kaina ina cikin tashin hankali”

Ta mike tsaye sai kuma ta koma ta zauna.

“Malam fada min me ya faru”

Malam yayi shiru kamar baya gurin can kuma ya numfasa ya ce.

“Wato Hajiya cikin nan ne ya sake tashi”

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, garin ya Malam? Ya aka yi haka ta faru”

“Ni kaina abun ya ba ni mamaki, shiyasa na ce ki ba ni dama na yi bincike kuma da na yi bincike na gane yadda matsalar take, sai dai maganinta ne da wuya”

“Kamar ya Malam na shiga uku”

Ta mike tsaye again ta fara safa da marwa tana kuka da babu hawaye mai cike da tashin hankali.

“Ba ki shiga uku ba, indai zaki iya domin wannan mafitar da na samu na sha wahala kam amman kuma karshe ce”

“Malam fada min kai tsaye dan Allah ka saka ni cikin rudani”

“Wato Aljannun da muka saka suka yi aikin nan, su suka warware shi, kuma suka waiwayo suna bukatar wani abu a gurinki mai girma....”

Hajiya Fatee bata san lokacin da gumi ya karyo mata ba, ta ji kamar ta dora hannu akai.
[11/9, 10:58 AM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 13*



Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻


𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660


𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣3⃣


“Fada min Malam na ji idan abun da zan iya ne, kana ta kara jefani cikin tashin hankali”

“Wato Hajiya maganar ce da nauyi, sai dai ya zama dole a fada, Hajiya Aljannuna nan suna bukatar kwanciya dake”

Hajiya Fatee ta dora hannu saman kai ta matsa baya.

“Ni kuma? Ina Aljanni ina mutum Malam”

Yayi dariya dake kara tabbatar da gaskiyar abun da yake fada.

“Hajiya kenan ai suma suna son mata sosai fiye da yadda maza bil'adam suke son mata, shiyasa suke auren matan hausawa”

A take hankalin Hajiya Fatee ya kara tashi.

“Malam ni ai ka kara firgita ni, ni ba yarinya ba balle ace sun ga wani abu a jikina ya burgesu”

“Ko tsohuwa ce ke babu ruwansu matukar kin yi musu, balle ke Hajiya jikinki ma ba za'ace kin yi shekarunki ba ga ki fara kin san aljannu suna son farar mace, dan haka ki natsu ki yi shawara da zuciyarki, kuma karki kuskura ki fadawa kowa domin suna nan tare da ke kuma sun ce basa son magana, saboda haka ki yi shawara da zuciyarki duk abun da ta yanke miki sai ki yi amfani da shi, amman lallai kin ji abun da suke bukata”

“Amman Malam ba za'a iya ba su wani abun ba su hakura?”

“Babu wani abu da suke so sai abun da na gabatar miki, wato abun da baki sani ba shi ne, kamin na same ki da maganar nan sai da na yi ta lallaba su amman ina suka ki yarda, dama na san zaki tsorata ai amman ina son ki kwantar da hankalinki ba wai zai zo miki a mutum ba ne, a cikin jikina zai shiga, kuma babu wani abu nawa da zaki ga ya canja, ni zaki gani a zahiri amman a badini ba ni ba ne Aljanine”

“Shi ke nan Malam zan yi shawara”

Ta sauke wayar cikin tashin hankali, ta rasa ta ina ma zata fara tunani, anya aljannu ke bukatar haka ko kuma Malam? Ta ina
Showing 36001 words to 39000 words out of 215510 words