tafi yar gidan Gwaggo, ke ko kishinki bata yi sai fada take min ban raka kishiyarta ba”
“To idan ma ba yar wuta ba, wace kishiyar ce zata yi kishi da Hurriya baiwar Allah, kifi musulmin nama”
Hurriya ta yi dariya, ita kanta Gwaggo dake maganar dariyar ta yi, kamin ta raka da addu'a, Amma kuma ta bita da kallo tana dan murmushi kadan. Tare suka isa da Rukayya har titi suna tafe suna hira, Rukayya sai tambayarta take wai halin Hajiya Kaltume na nan ko ta daina.
“Me zata daina kuwa Mama Rukayya ni dai arzikina, daya bana gidan yanzu duk wani abun da zata fada ko ta yi ba zai shafe ni ba”
“Wallahi kin huta, ai kara da Hajiya Binta ta dauke ki, kika rabu da wannan bakar kalwal mai bakar zuciya”
Hurriya ta kalleta tana murmushi.
“Amman dai Mama Rukayya wasa kike so? Hajiya fa mahaifiyar Yaya Yasir ce”
“And so what? Ke baki ga yadda ta maida Amma ba? Ta mallake Appanku baya jin maganar kowa sai nata? Ni fa da zan samu sa'arta sai na dauko fansar duk abun da ta yi mana, saboda tana tsaye nan a makoshi?”
“Toh kuma ki yi Yaya da Yaya Yasir?”
“Wai ke ina ruwanki da Yasir din ne? Ke fa wata rana kamar munafuka haka kike”
Hurriya bata san lokacin da dariya ta subuce mata ba.
“Mama Rukayya ke dai yi a hankali, dan kin san Yayana fa, shi yake zane mu idan muka yi laifi”
“To ni sai ya dake ni? Ke yarinya kama kanki, ai ko kirana yayi ban daga ba sai kin ga yadda hankalinsa yake tashi, idan kuma ya zo ya karbi wayata ko ya gan ni da wani ya fara kishi kenan, ni Rukayya i no dey carry last, haba ni ba halin Amma ne da ni ba, kowa ya ce min kule chasss zan ce masa”
A karo na barkatai Hurriya ta yi murmushi, ta tsayar da mai napep ta shiga bayan ta fada masa unguwar da zai kaita.
“Toh Allah ya tsare, damo sarkin hakuri”
“Amin Mama Rukayya na gode”
Mai napep yaja suka dauki hanya. A bakin gate ya sauke ta ta ba shi kudinsa sannan ta shiga cikin gidan, tana yin arba da daya daga cikin motocin da mahaifinta ya fi yawan hawa gabanta ya yanke ya fadi, tun a nan ta fara rage tafiyarta, hakalimlnta be tashin ba sai da ta kunna kai cikin falon ta yi arba da Hajiya Kaltume da Appanta, Hajiya Binta kuma tana zaune saman kujera.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻[11/22, 5:45 AM] AMINA KABIR CAPS: 𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
𝐏𝐚𝐠𝐞 2⃣2⃣
“Hurriya an dawo”
Far'ar da Hurriya ta gani a fuskar Hajiya Kaltume lokacin da take fadar haka ya fi daga mata hankali fiye da ganinsu da ta yi a gidan. Cikin rashin kuzari da faduwar gaba ta karasa kusa da Hajiya Binta ta zauna a kasa, sannan ta mikawa Appa gaisuwa.
“Lafiya Kalau”
Ya amsa ba tare da ya kalleta ba, Hajiya Kaltume na murmushi tana kallon Hurriya irin murmushi na murnar ganinta, bayan kuma a kasan zuciyarta ba haka ba ne.
“Hajiya Ina wuni?”
“Lafiya Kalau mutan aljanna, an dawo? Tun dazun muke nan ai, Hajiya ta ce kin tafi duba Iyami ya jikin nata”
“Tana jin sauki?”
“Sosai?”
“Eh”
“Maa Shaa Allah...”
Ta kasa cewa Allah ya bata lafiya, saboda hausawa suna cewa addu'ar fatan alheri ta makiyi karbabbiya ce, wai idan yayi maka sai an karba. Hurriya ta juya a hankali ta kalli Hajiya Binta dake zaune fuska ba yabo ba fallasa.
“Hurriya an dawo?”
“Eh Hajiya sannu da gida”
“Sannu dai yar Albarka, kin yi Sallah?”
“Aa ina tahowa ne aka yi kira”
“To tashi ki shiga ciki ki yi Sallah ki”
Hajiya Kaltume ta ce
“Ai da ta bari sai mun tafi sai ta yi sallah a can”
“Babu inda Hurriya zata tafi, ai na fada miki tun da ya koreta ta dawo nan kenan idan kika ga ta bar gidan nan to bana raye ne”
A take Hajiya Kaltume ta saka kukan munafurci.
“Haba Hajiya yanzu duk hakurin da muka yi ta baki baki hakura ba, ita dai Hurriya na san bata da matsalar komai kuma ko yanzu zata so komawa gidan ubanta domin babu kamar gidan uba a duniyar nan”
“Nan da take ai daji ne, da bata da alaka da kowa, ke ni kar nake ganinki, halinki babu wanda ban sani ba Kaltume, tun kina da kurciyarki har yanzu da kika yi yaya, saboda na aika muku da shi ne kika taso mijinki gaba kuka ta so wai azo a kalailaye ni da dadin baki a tafi da Hurriya ku karasa kasheta a can ko?”
“Wallahi ba manufata kenan ba, ni taya zan ce na kashe rai balle kuma Hurriya haba Hajiyaba zan iya aikata haka ba, kawai maganar da kika fada mana ne, na lura da haka ya kamata na yi kasancewa uwa, a wacan lokacin idona ya rufe ne ni da Alhaji shiyasa har ya koreta, ni kuma na kasa dakatar da abin amman na bashi hakuri Hajiya, ita kanta da zata fadi gaskiya ta sani”
Cikin kuka Hajiya Kaltume take maganar da hawaye shabe shabe a fuskarta. Kukanta ya bata ran Appa har yayi sanadin da ya watsawa Hurriya wani kallo daya saka ta sauke idonta kasa da sauri.
“Hajiya, ki yi hakuri haka ba zai sake faruwa ba”
“Ba fa zata koma ba, daman can ni bana son zamanta a gidan nan, ba za a kula da ita ba yadda ya dace, gashi ba iya magana take ba fa ma Hamad ne shi ne mai iya magana da fadar abun da aka yi har ma ya rama, amman ita ba zata fadi komai ba, ko a lokacin da aka ce taje ta yi gulmarka a wani guri ai be kamata ka yarda ba, domin idan akwai wanda ya san halin Hurriya ciki da waje a duniyar nan kai ne, yadda ta shaku da kai bata shaku da mahaifiyarta haka ba”
Appa ya sauke kansa kasa har lokacin hakuri yake badawa yana neman yafiyar Hajiya.
“Ni na yafe maka amman tabbas da baka zo ba kam, ina nan rike da wannan abun a raina kuma ba zai maka dadi ba saboda ni uwa ce, ko ban fada ba idan raina ya bace zaka iya gani a al'amurranka ko a jikinka ma”
“Toh a yafe min Hajiya hakan ba zai sake faruwa ba, kuma dan Allah ki bar mu mu tafi da Hurriya”
“Ba za a tafi da Hurriya ba, idan ka ga ta bar gidan nan to a dayan biyu ko dai ta yi aure ko kuma na mutu”
Hajiya ta sake fashewa da kuka, ita kanta Hurriya ta tsorata da yadda Hajiya take son komawarta a gidan har da hawayenta. Cikin kukan Hajiya Kaltume ta kalli Hurriya data kasa tashi a gurin da take zaune ta ce.
“Subhanallahi, ki yi hakuri dan Allah, kuma ki sak baki Hajiya ta hakura ita ma, wannan maida magana baya da ake ba shi da dadi, takas mahaifinki ya zo saboda ya tafi da ke, dan Allah ki yi hakuri Hurriya”
Hajiya Binta ta yamutse baki.
“Hurriya bata da ikon kanta, ikonta yana gurin mahaifinta da mahaifiyarta sai kuma ni, dan haka ki daina saka Hurriya a cikin maganar nan”
Hajiya na fadar haka Appa yayi karaf ya kalli Hurriya ya ce.
“To idan haka ne, Hurriya ina baki umarni a matsayina na mahaifinki ki koma gida cikin yan'uwanki, idan ba haka ba zaki yi mamakin abun da zai biyo baya...”
Appa na gama fadar hakan ya kalli Hajiya Kaltume ya ce.
“Tashi mu tafi”
Sannan ya mike tsaye, Hurriya ma ta mike tsaye da sauri, cikin karfin hali na tsufa Hajiya Binta ma ta mike tsaye ta rike hannun Hurriya.
“Hurriya ba zata koma ba, gaba daya ka canja tsoho ta ya zan yi umarni kuma ka yi kokarin karya wannan umarni? Anya kana cikin hayyacin Tsoho?''
Ya kada kansa kasa.
“Hajiya ba umarninki nake kokarin karyawa ba, bana son zaman Hurriya a ko'ina sai a gida, sanin kanki ne tun kamin yau kin ce na baki ita ban baki ba, saboda bana son kowa ya rika min da”
Hajiya Binta ta masa wani kallo na tsanaki, shi kuma ya ki yarda ya daga kansa ya kalleta sai yawo yake da idon a kasa. Tun tashinsa har girmansa bata ba shi umarni ya tsaba sai a yanzu, ba kuma yanzu ta yau ba, yanzu da girma ya cin masa ita kuma take gangarawa. Ko a lokacin da ya saki Iyami babu yadda bata so ya dawo da ita ba yaki, yanzu kuma saboda Hajiya Kaltume ta sako shi a gaba ya zo a maida Hurriya yake wannan bubutan.
“Kai ma haihuwarka aka yi, kamar yadda ka haifi Hurriya idan baka yi hankali ba, kai ma sai na baka umarnin da idan ka saba ba zaka ga da kyau ba”
Hajiya Kaltume ta kama gafen mayafinta tana share hawaye tare da mikewa tsaye domin ta lura ran Appa ya bace kamar yadda na Hajiya Binta ma ya bace har ta fusata.
“Ba za'ayi haka ba, ba ta kai ga haka ba, Alhaji mu tafi, tun da Hajiya na zon zaman Hurriya a nan ka barta ta zauna Allah ya bada hakurin zama”
Appa ya kalli Hurriya sai da hantar cikinta ta kada ta fara kokarin zare hannun Hajiya Binta a hannunta, ba kuma dan komai ba sai dan saboda Hajiya Kaltume, sannan ya dan risina ya ce.
“A tashi lafiya Hajiya”
Hajiya bata amsa masa ba bata ce masa komai ba har ya fice, kana ita ma Kaltume ta yi ma Hajiya sai da safe ka roki gafararta sannan ta fice. Sai a lokacin Hajiya Binta ta zauna ranta a jagule.
“Hajiya dan Allah ki yi hakuri ki bar na tafi, kar na kawo rudani tsakaninki da Appa, ko kuma Appa yayi fushi da ni kamar yadda ya fada”
Hajiya bata kula hawayen Hurriya dake saukowa ba ta daka mata tsawa.
“Ke rufe min baki nemi guri ki zauna babu inda zaki je, gaba daya sun canja masa kwakwalwarsa, idan yace ya yafe ke ni ma sai na yafe ki, idan takamar yana da kudi yana kula da ni, ai ai ba haka ya tashi yana ciyar da ni ba, Allah ke min komai”
Hurriya ta duka tana kallon Hajiya bi ta data koma ta zauna.
“Idan kika samu tsabani da Appa saboda ni, zai kara wutar kiyayyata a zuciyarsa ne, kuma zai tsine min domin baya a cikin hayyacinsa a yanzu, da ba ke ma ba zai tsaba umarninki ba, idan kika yi fushi da shi ba zai ga da kyau ba, idan kuma hakan ta faru da shi, ke da mu abun zai shafa, domin ke uwarsa ce babu yadda zaki da danki sai hakuri, mu kuma yayansa har kasa ta hade bamu da wanda ya fi shi, amman matansa za su iya gina kansu har su manta da shi, wuya bata kisa Hajiya, kuma duk yadda suke nufina da sheri Allah zai kareni, ina jin tsoron fushin iyayena akaina, yardar Allah tana tare da yardar iyaye, mahaifiyata bata da lafiya kuma bana kusa da ita, ki fahimta Hajiya su suke su raba ni da Appa, dan Allah karki bari haka ta faru, ki yafe mishi ki sauko daga fushin ki yi hakuri na koma...”
Hawaye ya zubo a idon Hajiya Binta, kalaman Hurriya na hankali sun ratsa kwakwalwarta, sai ta saka hannunta biyu da tsufa ya canja musu halittar fata ta rike fuskar Hurriya.
“Ke yata ce ta gari Hurriya, kuma kamar kore kamar kumbonsa, barewabata gudu danta yayi rarrafe, kin fi duka Yaya da Tsoho ya haifa hankali da hangen nesa, karamar yarinya mai kwakwalwar manya, Allah ya miki albarka, na barki na barki ki koma gidan ki zauna, zalinci baya dorewa kuma da yardar Allah sai kin fi su albarka, sai sun koma karkashinki sai rayuwarki ta dawo tana burgesu, ki shirya gobe zan saka direba ya kai ki, kuma zan biki da addu'a, zan rika zuwa ina dubaki”
Hurriya ta lumshe ido tana kwantar da kanta a hannun Hajiya binta hawayenta na sauka a tafin hannun kakarta. Ita kanta bata son komawarma amman ta lura kamar wani abu suke shirya mata kuma suke son hada mata ita da mahaifinta shiyasa suka har Hajiya Kaltume ta nace sai an koma da ita.
“Kin fadi gaskiya, Tsoho be taba musa ba sai a yanzu ta aka cire masa kowa a zuciyarsa, yau a gaban matarsa nake cewa ba za'ayi ba yace za'ayi Allah mai girma”
Hajiya Binta ta sake fada tana hawaye. Hurriya ta bude ido ta kalleta
“Daman na yi tunanin haka Hajiya, saboda kin fadawa Yaya Namra sakon da zata fada musu, suna ganin kamar kin zafafa sona ne akan na kowa, ita kanta Yaya Namra ta fada min bakar magana, gaba daya a munafuka suke kallona ganin suke kamar zan iya hada ki da Appa ne, Allah kadai ya san fushi da Appa zai yi da ni akan wannan, ni kaina ina tunanin zafafan da Appa yayi ne a kaina ya saka suka raba ni da shi, hawayen nan kuma Hajiya dan Allah ki share su kar wani abu ya sami Appana”
“kin yi tunani kuma na yaba da hankalinki, daman ina masa addu'a kuma zan kara, zan dage, ke ma kuma zan cigaba da yi min kuma ba zan zauna haka nan sai na nemi maganin tsari kala kala na baki, daga kuma karki sake wasa da addu'a Allah ya miki albarka”
Hajiya Binta ta share hawayenta, tare da bawa zuciyarta.
*** *** ***
A mota babu kalar wutar da Hajiya Kaltume bata hurawa Appa a zuciyata akan Hurriya, har tana fadar Hurriya ta hada shi da Hajiya gashi nan har ta yi fushi gashi kuma ta hana Hurriyar komawa.
“Ni daman abun da nake ta ji ma tsoro kenan, nan gaba kuma ba san me zata kulla ba, yarinya karama ta zama munafuka. Ko yanzu karka yarda ka barta a can idan ba haka ba, Hajiya sai ta tsine maka nan gaba, amman karka sake waiwayar gidan sai idan ta huce”
Kwafa kawai Appa yayi be ce komai ba har suka isa gida.
WASHE GARI.
I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah...!
Misalin karfe goma sha biyu na rana 12:00pm Captain ya shigo gidan, ya bude tsadadiyar motarsa ya fito ipod a kunnesa yana magana cike da gadata, shi alaka dole ga soja, kuma jinin sarauta ga kuma naira, shigar kananan kaya ce a jikinsa kamar yadda ya saba, domin abu ne mai wahala ka ga Captain Da Shadda sai idan wani abun ya taso. With little strong ya hau entrance din ya murda kofar falon Momy ya shiga, hakan nan dai ya ji yau baya ra'ayin yin sallama even though ba fushi yake ko bacin rai ba, haka kuma ba cikin farinciki yake ba, not happy not sad. Kulu na ganinsa ta mike tsaye ta sauri tana kallonsa bakinta da jikinta suna rawa saboda kwarjinsa, abu mai wahala ka yi arba da shi baka ji tsoro da fargaba ba, musamnan idan haduwar farko ce, ba kuma tsoro na wanda zai maka wani abu, kwarjini da yake da shi da murufa ta tsananin mazantaka da zakantaka ya wuce ka lalleshi baka ji kwarjinsa ba, balle kuma ace ka san yadda yake da saurin fushi da tsananin fada kamar gawurtaccen zaki.
“Sannu da zuwa Sannu da zuwa...”
“Yauwa sannu ya gida ya aiki?”
“Lafiya Kalau Yallabai”
Ya dan juyarta da kai yana kokarin yin murmushi
“No ki kira ni da Captain ko Jameel that's my name, amman wani Yallabai Yaya ko ranka da ya dade old fashion ne, bana so. Ina Momy?”
“Toh toh na tuba, carpet bari a kirata tana sama”
Ya runtse ido saboda yadda ta sauya masa suna saboda rashin iya pronouncing din. Ta haura sama da sauri, sanin kanta ne ba a shiga dakin Momy kai tsaye idan ba ita ta kira mutum ba, musamman masu aiki, dan haka ta fara ya da zango a dakin Namra ta sanar mata domin ita kuma ta sanar da Momy. Sannan ta sauko da saurinta kamar zata fadi.
“Na fadawa Namra zata fada mata yanzu”
“Na gode”
Ta fice da sauri tana amsawa da babu komai, ai aikinta ne. Namra ce ta fara sauko da far'a jin cewar dan'uwanta ya dawo kamin Momy ta biyo bayansa tana masa lale marhabun.
“Yau kuma an sake
Showing 69001 words to 72000 words out of 215510 words
“To idan ma ba yar wuta ba, wace kishiyar ce zata yi kishi da Hurriya baiwar Allah, kifi musulmin nama”
Hurriya ta yi dariya, ita kanta Gwaggo dake maganar dariyar ta yi, kamin ta raka da addu'a, Amma kuma ta bita da kallo tana dan murmushi kadan. Tare suka isa da Rukayya har titi suna tafe suna hira, Rukayya sai tambayarta take wai halin Hajiya Kaltume na nan ko ta daina.
“Me zata daina kuwa Mama Rukayya ni dai arzikina, daya bana gidan yanzu duk wani abun da zata fada ko ta yi ba zai shafe ni ba”
“Wallahi kin huta, ai kara da Hajiya Binta ta dauke ki, kika rabu da wannan bakar kalwal mai bakar zuciya”
Hurriya ta kalleta tana murmushi.
“Amman dai Mama Rukayya wasa kike so? Hajiya fa mahaifiyar Yaya Yasir ce”
“And so what? Ke baki ga yadda ta maida Amma ba? Ta mallake Appanku baya jin maganar kowa sai nata? Ni fa da zan samu sa'arta sai na dauko fansar duk abun da ta yi mana, saboda tana tsaye nan a makoshi?”
“Toh kuma ki yi Yaya da Yaya Yasir?”
“Wai ke ina ruwanki da Yasir din ne? Ke fa wata rana kamar munafuka haka kike”
Hurriya bata san lokacin da dariya ta subuce mata ba.
“Mama Rukayya ke dai yi a hankali, dan kin san Yayana fa, shi yake zane mu idan muka yi laifi”
“To ni sai ya dake ni? Ke yarinya kama kanki, ai ko kirana yayi ban daga ba sai kin ga yadda hankalinsa yake tashi, idan kuma ya zo ya karbi wayata ko ya gan ni da wani ya fara kishi kenan, ni Rukayya i no dey carry last, haba ni ba halin Amma ne da ni ba, kowa ya ce min kule chasss zan ce masa”
A karo na barkatai Hurriya ta yi murmushi, ta tsayar da mai napep ta shiga bayan ta fada masa unguwar da zai kaita.
“Toh Allah ya tsare, damo sarkin hakuri”
“Amin Mama Rukayya na gode”
Mai napep yaja suka dauki hanya. A bakin gate ya sauke ta ta ba shi kudinsa sannan ta shiga cikin gidan, tana yin arba da daya daga cikin motocin da mahaifinta ya fi yawan hawa gabanta ya yanke ya fadi, tun a nan ta fara rage tafiyarta, hakalimlnta be tashin ba sai da ta kunna kai cikin falon ta yi arba da Hajiya Kaltume da Appanta, Hajiya Binta kuma tana zaune saman kujera.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻[11/22, 5:45 AM] AMINA KABIR CAPS: 𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
𝐏𝐚𝐠𝐞 2⃣2⃣
“Hurriya an dawo”
Far'ar da Hurriya ta gani a fuskar Hajiya Kaltume lokacin da take fadar haka ya fi daga mata hankali fiye da ganinsu da ta yi a gidan. Cikin rashin kuzari da faduwar gaba ta karasa kusa da Hajiya Binta ta zauna a kasa, sannan ta mikawa Appa gaisuwa.
“Lafiya Kalau”
Ya amsa ba tare da ya kalleta ba, Hajiya Kaltume na murmushi tana kallon Hurriya irin murmushi na murnar ganinta, bayan kuma a kasan zuciyarta ba haka ba ne.
“Hajiya Ina wuni?”
“Lafiya Kalau mutan aljanna, an dawo? Tun dazun muke nan ai, Hajiya ta ce kin tafi duba Iyami ya jikin nata”
“Tana jin sauki?”
“Sosai?”
“Eh”
“Maa Shaa Allah...”
Ta kasa cewa Allah ya bata lafiya, saboda hausawa suna cewa addu'ar fatan alheri ta makiyi karbabbiya ce, wai idan yayi maka sai an karba. Hurriya ta juya a hankali ta kalli Hajiya Binta dake zaune fuska ba yabo ba fallasa.
“Hurriya an dawo?”
“Eh Hajiya sannu da gida”
“Sannu dai yar Albarka, kin yi Sallah?”
“Aa ina tahowa ne aka yi kira”
“To tashi ki shiga ciki ki yi Sallah ki”
Hajiya Kaltume ta ce
“Ai da ta bari sai mun tafi sai ta yi sallah a can”
“Babu inda Hurriya zata tafi, ai na fada miki tun da ya koreta ta dawo nan kenan idan kika ga ta bar gidan nan to bana raye ne”
A take Hajiya Kaltume ta saka kukan munafurci.
“Haba Hajiya yanzu duk hakurin da muka yi ta baki baki hakura ba, ita dai Hurriya na san bata da matsalar komai kuma ko yanzu zata so komawa gidan ubanta domin babu kamar gidan uba a duniyar nan”
“Nan da take ai daji ne, da bata da alaka da kowa, ke ni kar nake ganinki, halinki babu wanda ban sani ba Kaltume, tun kina da kurciyarki har yanzu da kika yi yaya, saboda na aika muku da shi ne kika taso mijinki gaba kuka ta so wai azo a kalailaye ni da dadin baki a tafi da Hurriya ku karasa kasheta a can ko?”
“Wallahi ba manufata kenan ba, ni taya zan ce na kashe rai balle kuma Hurriya haba Hajiyaba zan iya aikata haka ba, kawai maganar da kika fada mana ne, na lura da haka ya kamata na yi kasancewa uwa, a wacan lokacin idona ya rufe ne ni da Alhaji shiyasa har ya koreta, ni kuma na kasa dakatar da abin amman na bashi hakuri Hajiya, ita kanta da zata fadi gaskiya ta sani”
Cikin kuka Hajiya Kaltume take maganar da hawaye shabe shabe a fuskarta. Kukanta ya bata ran Appa har yayi sanadin da ya watsawa Hurriya wani kallo daya saka ta sauke idonta kasa da sauri.
“Hajiya, ki yi hakuri haka ba zai sake faruwa ba”
“Ba fa zata koma ba, daman can ni bana son zamanta a gidan nan, ba za a kula da ita ba yadda ya dace, gashi ba iya magana take ba fa ma Hamad ne shi ne mai iya magana da fadar abun da aka yi har ma ya rama, amman ita ba zata fadi komai ba, ko a lokacin da aka ce taje ta yi gulmarka a wani guri ai be kamata ka yarda ba, domin idan akwai wanda ya san halin Hurriya ciki da waje a duniyar nan kai ne, yadda ta shaku da kai bata shaku da mahaifiyarta haka ba”
Appa ya sauke kansa kasa har lokacin hakuri yake badawa yana neman yafiyar Hajiya.
“Ni na yafe maka amman tabbas da baka zo ba kam, ina nan rike da wannan abun a raina kuma ba zai maka dadi ba saboda ni uwa ce, ko ban fada ba idan raina ya bace zaka iya gani a al'amurranka ko a jikinka ma”
“Toh a yafe min Hajiya hakan ba zai sake faruwa ba, kuma dan Allah ki bar mu mu tafi da Hurriya”
“Ba za a tafi da Hurriya ba, idan ka ga ta bar gidan nan to a dayan biyu ko dai ta yi aure ko kuma na mutu”
Hajiya ta sake fashewa da kuka, ita kanta Hurriya ta tsorata da yadda Hajiya take son komawarta a gidan har da hawayenta. Cikin kukan Hajiya Kaltume ta kalli Hurriya data kasa tashi a gurin da take zaune ta ce.
“Subhanallahi, ki yi hakuri dan Allah, kuma ki sak baki Hajiya ta hakura ita ma, wannan maida magana baya da ake ba shi da dadi, takas mahaifinki ya zo saboda ya tafi da ke, dan Allah ki yi hakuri Hurriya”
Hajiya Binta ta yamutse baki.
“Hurriya bata da ikon kanta, ikonta yana gurin mahaifinta da mahaifiyarta sai kuma ni, dan haka ki daina saka Hurriya a cikin maganar nan”
Hajiya na fadar haka Appa yayi karaf ya kalli Hurriya ya ce.
“To idan haka ne, Hurriya ina baki umarni a matsayina na mahaifinki ki koma gida cikin yan'uwanki, idan ba haka ba zaki yi mamakin abun da zai biyo baya...”
Appa na gama fadar hakan ya kalli Hajiya Kaltume ya ce.
“Tashi mu tafi”
Sannan ya mike tsaye, Hurriya ma ta mike tsaye da sauri, cikin karfin hali na tsufa Hajiya Binta ma ta mike tsaye ta rike hannun Hurriya.
“Hurriya ba zata koma ba, gaba daya ka canja tsoho ta ya zan yi umarni kuma ka yi kokarin karya wannan umarni? Anya kana cikin hayyacin Tsoho?''
Ya kada kansa kasa.
“Hajiya ba umarninki nake kokarin karyawa ba, bana son zaman Hurriya a ko'ina sai a gida, sanin kanki ne tun kamin yau kin ce na baki ita ban baki ba, saboda bana son kowa ya rika min da”
Hajiya Binta ta masa wani kallo na tsanaki, shi kuma ya ki yarda ya daga kansa ya kalleta sai yawo yake da idon a kasa. Tun tashinsa har girmansa bata ba shi umarni ya tsaba sai a yanzu, ba kuma yanzu ta yau ba, yanzu da girma ya cin masa ita kuma take gangarawa. Ko a lokacin da ya saki Iyami babu yadda bata so ya dawo da ita ba yaki, yanzu kuma saboda Hajiya Kaltume ta sako shi a gaba ya zo a maida Hurriya yake wannan bubutan.
“Kai ma haihuwarka aka yi, kamar yadda ka haifi Hurriya idan baka yi hankali ba, kai ma sai na baka umarnin da idan ka saba ba zaka ga da kyau ba”
Hajiya Kaltume ta kama gafen mayafinta tana share hawaye tare da mikewa tsaye domin ta lura ran Appa ya bace kamar yadda na Hajiya Binta ma ya bace har ta fusata.
“Ba za'ayi haka ba, ba ta kai ga haka ba, Alhaji mu tafi, tun da Hajiya na zon zaman Hurriya a nan ka barta ta zauna Allah ya bada hakurin zama”
Appa ya kalli Hurriya sai da hantar cikinta ta kada ta fara kokarin zare hannun Hajiya Binta a hannunta, ba kuma dan komai ba sai dan saboda Hajiya Kaltume, sannan ya dan risina ya ce.
“A tashi lafiya Hajiya”
Hajiya bata amsa masa ba bata ce masa komai ba har ya fice, kana ita ma Kaltume ta yi ma Hajiya sai da safe ka roki gafararta sannan ta fice. Sai a lokacin Hajiya Binta ta zauna ranta a jagule.
“Hajiya dan Allah ki yi hakuri ki bar na tafi, kar na kawo rudani tsakaninki da Appa, ko kuma Appa yayi fushi da ni kamar yadda ya fada”
Hajiya bata kula hawayen Hurriya dake saukowa ba ta daka mata tsawa.
“Ke rufe min baki nemi guri ki zauna babu inda zaki je, gaba daya sun canja masa kwakwalwarsa, idan yace ya yafe ke ni ma sai na yafe ki, idan takamar yana da kudi yana kula da ni, ai ai ba haka ya tashi yana ciyar da ni ba, Allah ke min komai”
Hurriya ta duka tana kallon Hajiya bi ta data koma ta zauna.
“Idan kika samu tsabani da Appa saboda ni, zai kara wutar kiyayyata a zuciyarsa ne, kuma zai tsine min domin baya a cikin hayyacinsa a yanzu, da ba ke ma ba zai tsaba umarninki ba, idan kika yi fushi da shi ba zai ga da kyau ba, idan kuma hakan ta faru da shi, ke da mu abun zai shafa, domin ke uwarsa ce babu yadda zaki da danki sai hakuri, mu kuma yayansa har kasa ta hade bamu da wanda ya fi shi, amman matansa za su iya gina kansu har su manta da shi, wuya bata kisa Hajiya, kuma duk yadda suke nufina da sheri Allah zai kareni, ina jin tsoron fushin iyayena akaina, yardar Allah tana tare da yardar iyaye, mahaifiyata bata da lafiya kuma bana kusa da ita, ki fahimta Hajiya su suke su raba ni da Appa, dan Allah karki bari haka ta faru, ki yafe mishi ki sauko daga fushin ki yi hakuri na koma...”
Hawaye ya zubo a idon Hajiya Binta, kalaman Hurriya na hankali sun ratsa kwakwalwarta, sai ta saka hannunta biyu da tsufa ya canja musu halittar fata ta rike fuskar Hurriya.
“Ke yata ce ta gari Hurriya, kuma kamar kore kamar kumbonsa, barewabata gudu danta yayi rarrafe, kin fi duka Yaya da Tsoho ya haifa hankali da hangen nesa, karamar yarinya mai kwakwalwar manya, Allah ya miki albarka, na barki na barki ki koma gidan ki zauna, zalinci baya dorewa kuma da yardar Allah sai kin fi su albarka, sai sun koma karkashinki sai rayuwarki ta dawo tana burgesu, ki shirya gobe zan saka direba ya kai ki, kuma zan biki da addu'a, zan rika zuwa ina dubaki”
Hurriya ta lumshe ido tana kwantar da kanta a hannun Hajiya binta hawayenta na sauka a tafin hannun kakarta. Ita kanta bata son komawarma amman ta lura kamar wani abu suke shirya mata kuma suke son hada mata ita da mahaifinta shiyasa suka har Hajiya Kaltume ta nace sai an koma da ita.
“Kin fadi gaskiya, Tsoho be taba musa ba sai a yanzu ta aka cire masa kowa a zuciyarsa, yau a gaban matarsa nake cewa ba za'ayi ba yace za'ayi Allah mai girma”
Hajiya Binta ta sake fada tana hawaye. Hurriya ta bude ido ta kalleta
“Daman na yi tunanin haka Hajiya, saboda kin fadawa Yaya Namra sakon da zata fada musu, suna ganin kamar kin zafafa sona ne akan na kowa, ita kanta Yaya Namra ta fada min bakar magana, gaba daya a munafuka suke kallona ganin suke kamar zan iya hada ki da Appa ne, Allah kadai ya san fushi da Appa zai yi da ni akan wannan, ni kaina ina tunanin zafafan da Appa yayi ne a kaina ya saka suka raba ni da shi, hawayen nan kuma Hajiya dan Allah ki share su kar wani abu ya sami Appana”
“kin yi tunani kuma na yaba da hankalinki, daman ina masa addu'a kuma zan kara, zan dage, ke ma kuma zan cigaba da yi min kuma ba zan zauna haka nan sai na nemi maganin tsari kala kala na baki, daga kuma karki sake wasa da addu'a Allah ya miki albarka”
Hajiya Binta ta share hawayenta, tare da bawa zuciyarta.
*** *** ***
A mota babu kalar wutar da Hajiya Kaltume bata hurawa Appa a zuciyata akan Hurriya, har tana fadar Hurriya ta hada shi da Hajiya gashi nan har ta yi fushi gashi kuma ta hana Hurriyar komawa.
“Ni daman abun da nake ta ji ma tsoro kenan, nan gaba kuma ba san me zata kulla ba, yarinya karama ta zama munafuka. Ko yanzu karka yarda ka barta a can idan ba haka ba, Hajiya sai ta tsine maka nan gaba, amman karka sake waiwayar gidan sai idan ta huce”
Kwafa kawai Appa yayi be ce komai ba har suka isa gida.
WASHE GARI.
I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah...!
Misalin karfe goma sha biyu na rana 12:00pm Captain ya shigo gidan, ya bude tsadadiyar motarsa ya fito ipod a kunnesa yana magana cike da gadata, shi alaka dole ga soja, kuma jinin sarauta ga kuma naira, shigar kananan kaya ce a jikinsa kamar yadda ya saba, domin abu ne mai wahala ka ga Captain Da Shadda sai idan wani abun ya taso. With little strong ya hau entrance din ya murda kofar falon Momy ya shiga, hakan nan dai ya ji yau baya ra'ayin yin sallama even though ba fushi yake ko bacin rai ba, haka kuma ba cikin farinciki yake ba, not happy not sad. Kulu na ganinsa ta mike tsaye ta sauri tana kallonsa bakinta da jikinta suna rawa saboda kwarjinsa, abu mai wahala ka yi arba da shi baka ji tsoro da fargaba ba, musamnan idan haduwar farko ce, ba kuma tsoro na wanda zai maka wani abu, kwarjini da yake da shi da murufa ta tsananin mazantaka da zakantaka ya wuce ka lalleshi baka ji kwarjinsa ba, balle kuma ace ka san yadda yake da saurin fushi da tsananin fada kamar gawurtaccen zaki.
“Sannu da zuwa Sannu da zuwa...”
“Yauwa sannu ya gida ya aiki?”
“Lafiya Kalau Yallabai”
Ya dan juyarta da kai yana kokarin yin murmushi
“No ki kira ni da Captain ko Jameel that's my name, amman wani Yallabai Yaya ko ranka da ya dade old fashion ne, bana so. Ina Momy?”
“Toh toh na tuba, carpet bari a kirata tana sama”
Ya runtse ido saboda yadda ta sauya masa suna saboda rashin iya pronouncing din. Ta haura sama da sauri, sanin kanta ne ba a shiga dakin Momy kai tsaye idan ba ita ta kira mutum ba, musamman masu aiki, dan haka ta fara ya da zango a dakin Namra ta sanar mata domin ita kuma ta sanar da Momy. Sannan ta sauko da saurinta kamar zata fadi.
“Na fadawa Namra zata fada mata yanzu”
“Na gode”
Ta fice da sauri tana amsawa da babu komai, ai aikinta ne. Namra ce ta fara sauko da far'a jin cewar dan'uwanta ya dawo kamin Momy ta biyo bayansa tana masa lale marhabun.
“Yau kuma an sake
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24 Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72