Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻*HURIYYA*

*BOOK 2 PAGE 3*


𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660


𝐏𝐚𝐠𝐞 3️⃣

Tun a ranar Bappa ya so ya samu Appa su tattauna kan lamarin amman hakan be samu ba sakamakon dare da yayi, daman daf da magariba Maama taje gidan. The following the day Bappa yayi ta kiran Appa a waya amman yaki dagawa, cikin yanayin damuwa Bappa ya kalli Iyami dake rike da carbi ya ce.

“Haka nake da bawan Allah nan, babu ranar da zan kira shi ya amsa min, tun da lamarin nan ya faru idan na kira shi baya daga wayata”

“Wata kila har yanzu yana jin kunyarka ne, ina ganin abun da zai fi ka shirya ka same shi gida da safen nan da wuri sai ka yi magana da shi”

“Ko kuma ita Iyamin ta kira shi a wayarta ba, ta yi magana da shi ko kuma ta ba ni wayar mu yi magana”

Ya karasa yana kallon Amma. Amma ta dauki wayarta ta lalabo number Appa da rabon ta yi waya da shi tun tana gidan, kamin ta danna masa kira ma sai da ta yi da gaske ta danne zuciyarta, sanin cewar saboda matsalar Hamad zata kira shi ya karfafa mata guiwar kiran, sai ita ma ta yi rashin sa'a kamar Bappa, be daga kiran ba, tun kiran na ringing har ta kai an fara rejecting.

“To wai lafiya ko kuma dai yana tsoron kar a fada miki ne, wata kila be san Maama ta zo gidan nan ba, ina tunanin a boye ta zo ta fada miki, domin irin wannan magana mai nauyi shi ya kamata ya taho da kansa ya fada miki, anya ba Hajiya Kaltume ta taro ta ba?”

A take Bappa ya gwatsale Gwaggo daman shi be cika yarda da irin abubuwan nan na zafin kishi ba, ko wani abun da za ace kishiya ta aikata ganin yake duk karya ne, ko wane bangaren daman ba zai so dayan bangaren ba dan haka kazafi da kage babu kalar wanda ba zai yi ma abokin adawarsa ba.

“Ku dai kullum baku da wata magana sai ta Hajiya Kaltume, ina ce saboda Hajiya Kaltume nan Iyami ta hadu da Alhaji, ni fa a gurina bani da kamar Hajiya Kaltume domin sanadinta Iyami ta auri Alhaji Haruna Mai Yadi, idan na fita har nuna ni ake ga surukin Alhaji, da can ba a kwano muke zaune ba? Amman ya zo ya siya mana babban gida ga kuma lalurar komai ya dauke mana, duk sanadin waye ba Hajiya Kaltume me? Dan Allah ku daina kawo min maganarta ma”

Gwaggo ta rausayar da kai.

“Toh Malam ai daman ba zaka yarda ba, baka san makircin mata ba”

“Ban sani ba, kuma bana son sani, yanzu ki tashi ki shirya mu tafi tare can mu same shi mu yi magana da shi”

“Toh bari na dafawa Hurriya Indome ta fi son karyawa da ita”

Amma dai bata ce komai ba, har suka ci suka shude, ita dai tunaninta na halin da danta yake ciki ne. Sai da Gwaggo ta dafawa jikarta Indomie ta zuba mata a karamar cooler sannan ta yi wanka Bappa ma yayi wanka suka shirya sannan suka bar gidan.





MAI YADI'S HOUSE.

Hajiya Kaltume ta dan leki wayar da Appa ya aje a gefe daya ta kalleshi.

“Iyami ce fa Alhaji?”

Appa kamar wanda aka rikita sai ya fara fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.

“To me zan mata? Ba za a bar mutum da damuwarsa ba? Ta san halin da nake ciki ne? Mahaifinta yanzu ya gama kirana ita kuma ta dora da nata”

A kaikace Hajiya Kaltume ta ce.

“Ka sani ko zancen dawowarta za su maka ko kuma na Hamad?”

“Dawowarta? Ta zo ta yi me? Hamad kuma ai ni ma dana ne ba ita kadai ta haife shi ba balle ta nuna min sonsa”

“Gaskiya kam, ni ma da aka dauke min Ruma ai dole na zuba ido sai abun da ka yi, amman duk da haka dai Alhaji da dai ka bada kudin”

Appa yayi shiru kamar mai tsoron musa mata, ya kasa cewa komai.

“Kuma ba ka san shakkuwarta ba, da ka karba wayar ka ji abun da za su fada”

“Bana son na ji wani abun da da ya shafi Iyami ko gidansu a yanzu, damuwa ta min yawa kaina ma kamar ya fashe nake ji, na san kuma damu za su yi da maganar Hamad”

“Ikon Allah yau Alhaji Iyamin ce baka son jin wani abun da ya shafe ta? Toh Allah ya kyauta bari na kwashe kayan”

Ta fara kwashe kayan da ya ci abinci zuciyarta na wani irin zillo kamar zata fado tsabar farinciki. Jikinta har rawa yake kamin ta bar part din, tana shiga bangarenta ta aje tray a falo ta shige dakinta ta dauki wayarta sai kira ta aikawa Hajiya Fatee.

“Toh Allah dai ya sa lafiya wannan kira haka tun da safe?”

“Lafiya kalau sai alheri, Hajiya Fatee yau bana da inda zan saka ki, bani da wanda ya fi min ke a duniyar nan, Hajiya Fatee kin biyani Allah dai ya bar zumuncinmu”

Cikin mamaki da farinciki kawar tata ta amsa.

“Toh Ameen, amman ba ni an sha me ya samu?”

“Komai ma ya samu Hajiya Fatee yanzu zan fara samun kan mijina, abun da na kwashe shekaru ina nema ban samu ba, Hajiya Fatee yau Alhaji da kansa yake ta fada saboda Iyami da mahaifinta sun kira shi a waya, har yake fadar shi yanzu baya son wani abun da ya shafi iyami ya hada shi da ita”

Hajiya Fatee ta saka dariya irin mai ruguzawar nan.

“Hajiya Kaltume ni kaina na gasgata aikin Malamin nan, kuma na yarda ba da wasa yake aikinsa ba, domin ni na fi kowa shaidar hakan tun da ga ciki ya kwanta lafiya kamar babu shi, wata kila ma cireshi yayi gaba daya, amman har asibiti na tafi an auna babu ciki babu labarinsa”

“Ni Wallahi da farko nan na dauka ko aikin be yi ma, kwana nawa aka dauka amman shiru sai yau na fara ganin ikon Allah”

“Ai daman wani abun haka yake, kin manta yadda muka yi na auren Iyami? Shi ma ai sai da kika fara korafin be yi be yi ba, har ya ce kin yi gajin hakuri, yanzu ba gashi ta tafi ta bar miki idan ba”

“Na yarda, tabbas ni kuwa zan saka masa da sakamako mai kyau, sai yayi alfahari da ni”

“Ni ma ai na fada masa idan yayi abun da zai raba auren Fadeel da Afrah sai na masa kyauta mai tsoka da sai ya kasa mantawa da ni, kuma ya ce zai yi, sai dai ta inda lamarin ya sanyaya min guiwa cewar da yayi idan yayi mata aika dawo masa ake da ita”

Hajiya Kaltume ta rike baki. “Ai kin san bata tsawaya kanta ba, ita ma shigen shigen take”

“Ai na sani, shiyasa ta mallake min da komai sai Afrah gaba daya baya jin maganar kowa sai nata, kuma bana da ikon zaginta a gabansa sai ya fara masifa, ni daman tun farko bana son aurenta da yaron nan Wallahi, Allah dai ya riga da kaddara ne kawai”

“Ki sa ido ki yi kallo kamar yadda Iyami ta bar gidana, Afrah ma sai ta bar gidan danki da yardar Allah”

“Haka nake fata Hajiya Allah ya amsa”

“Ameen”

Hajiya Kaltume ta aje wayar tana murmushi kamar wadda aka yi ma bushara.

“Hmmmm Iyami.... Lallai kin zama labari a gidan nan, yaranki ma da yardar Allah sai sun zama su da babu duk daya a gidan nan”

Ta nufi bakin gadonta ta zauna tana kokarin sake yin wani kiran Khairi ta shigo dakin ta zauna kusa da ita ta kwanta jikinta.

“Hajiya yaushe Ruma zata dawo ne?”

Hajiya ta yi saurin saka wayar key tare da gefenta.

“Babu jimawa Khairi, mahaifinki ne yace a bashi lokaci zai nemi ragi, kuma kin ga ai ana neman ragi a komai”

“Toh Hajiya da zai yarda da sai ya bada kudin ya karbo Ruma, albashi Hamad din a barsa sai an shirya daman ya fitini kowa a gidan nan”

“Ai kin san ba zai yarda ba, kuma mutane ma sai su saka mana ido, ace saboda uwarsa bata gidan ne, kara dai a karbo su tare gaba daya”

“Allah sarki Ruma, Allah dai ya tsare ta”

“Ya ma tsare In Shaa Allah ba za su mata komai ba, ai yarinya ce kuma kin ga ba ita kadai suka dauka ba ko dan ganin idon Hamad za su raga mata tun da dan'uwanta ne”

“Allah yasa”

“Ameen tashi kuje ku karya, ni wanka zan yi yanzu”

“Na karya ai”

“Yayi kyau Maama da Salma duk sun karya? Yayanki fa?”

“Ban sani ba gaskiya”

“Je ki fada masa ya fito ya karya”

Khairi ta tashi ta fice daga dakin, sai da Hajiya Kaltume ta tabbatar ta rufe kofar dakin sannan ta fiddo wayarta ta fara danne danne. Misalin sha daya na safe Bappa da Gwaggo suka dira a gidan, Bappa ya faka a harabar da ya saba fakawa duk lokacin da wani abu mai muhimmanci ya kawo shi gidan, duk kuwa da kasancewar Iyami bata gidan. Shi ya fara fita sannan Gwaggo ta fito tana sanye fa farin hijabinta.

“Ki fara shiga ki yi magana da Hajiya Kaltume a sallamo mana Alhaji mu yi magana da shi”

“Ko kuma dai ayi mana iso ba”

Gwaggo ta gyara masa domin a ganinta ba bara ko roko suka zo gurinsa ba da za ace a sallamo musu shi. Bappa dai be sake cewa komai ba domin be shirya musu da Gwaggo a yanzu ba, ya san duk gyaran da zai mata ba zata fahimta ba. Gwaggo ta daga kai ta kalli apartment din Amma da kyau sai ta ji ranta ya bace, domin a yanzu yarta bata cikin gidan ba kamar da ba. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta fito ta nufi bangaren Hajiya Kaltume, ba dan zuwan ya zame musu na dole ba ba za su zo a gidan ba, musamman ma ita da Hajiya Kaltume har Hajiya Nafisa basa girmamawa, Hajiya Nafisa na yi musu kallon matalauta masu kwadayi Hajiya Kaltume kuma na yi musu kallon maciya amana wadanda suka hanata zaman lafiya da kwanciyar hankali, Appa ne mai girmamata idan yaje mata ko kuma ita ta zo gidan ya rasa ina zai dauke ta ya dora tsabar farinciki da girmamawa. Ta murda kofar falon ta shiga da sallama fuskarta dauke da damuwar data kasa boyuwa.

Salma da Maama suka amsa mata ba dan sun ga fuskarta ba, domin su ma ba girma suke bata ba. Yasir ya aje cup din hannunsa da sauri ya baro dinning din ya nufota yana mata sannu da zuwa har da dan risinawa.

“Sannu Yasir ya hakurin lamarin nan?”

“Alhamdulillah Gwaggo Bismillahi zauna”

Ya nufi kujerar da sauri ya dauke pillows din da suke kai ya mata mazauni.

“Ya gida ina Rukayya?”

“Gida Lafiya kalau, Rukayya ta tafi makaranta tun safe”

“Ya Hurriya da Amma?”

“Toh Alhamdulillah Hajiya Kaltume na ciki? Tare muke da Malam ai”

“Oh... Ya tsaya a waje?”

“Eh ai ba jimawa za mu yi ba, magana kawai za mu yi da Mahaifinku”

“Okay Salma shiga ki kira Hajiya bari na tafi gurin Bappa”

Salma ta motsa hanci ta mike tsaye ba tare da ta gaishe da Gwaggo ba ta nufi upstairs, Maama tun da ta kalli Gwaggo sau daya bata sake juyowa ba balle har ta gaishe ta. Ba abun mamaki ba ne a gurin Gwaggo domin sun saba yi mata haka kishi suke taya uwarsu. Daga kiran Hajiya Salma bata sauko ba balle Gwaggo ta san halin da ake ciki haka ta zauna a gurin har kusan minti ashiri sannan Hajiya Kaltume ta sauko tana sanye da wata gizna mai fari da baki irin ta mutanen nijar ta irin aikinsu a gaban rigar da ta sauko mata har guiwa.

“Gwaggo ce yau a gidan na mu”

“Ni ce, halan Salma bata fada miki na zo ba Hajiya Kaltume”

“Ta fada min ba shi na sauko ba? Ina dan abu ne shiyasa Allah yasa dai lafiya”

Gwaggo ta tabe baki ta girgiza kai.

“Ba lafiya ba kan, tun da kowa ya san abun da ya faru, tare muke da Malam muna son magana da Alhaji ne”

Hajiya Kaltume ta zauna tana yamutsa fuska irin an takura musu din nan, kamin ta fara magana da izza.

“Oh Allah sarki, dazun ma ai na ga Bappa ya kira Iyamin ma ta kira, Alhaji sai fada yake Gwaggo ba a haka, ku baku san shirinsa ba, kuna son daga masa hankalin ne kawai shi ma fa ya damu da yaran nan kuna neman ku daga masa hankali”

Gwaggo ta nuna Hajiya Kaltume da yatsa.

“Ke Kaltume ke kin sani ko ban haife ki ba, na yi kanwa da ke, dan haka na cancanci girmamawa a gareki ko dan Iyami”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi da ya fi kama da yar siririyar dariya.

“Wannan kuma ai da ne Gwaggo, yanzu babu wannan alakar, kuma da kuke neman daga mana hankali ni ma fa tawa yar tana can tare da Hamad aka sace su, ko kuma ita ba mutum ba ce?”

Gwaggo ta mike tsaye.

“Kwarai kuwa mutum ce, shiyasa ai na ganki kin sha wanka kina ta far'a da jindadi an sace miki auta, gashi nan ai ya nuna a fuskarki”

“Gwaggo karki gayan magana, to faduwa zan yi na yi birgima? Ko kuma an fada miki ni din kamar yarki ce Iyami da bata yarda da kaddara ba? Ai ma dai da kunya Wallahi ku tako gidan nan da sunan ganin Alhaji shi be nemu ba ku za su neme sa, abu dai kamar ba Fulani ba”

“Ba rokonsa muka zo akan ya ba mu wani abu ba, kuma ba zuwa muka yi akan ya maida Iyami ba, shi ne abun kunya, mun zo ne saboda Hamad, ai kin san ko an rabu idan akwai yaya kamar ba a rabu ba ne, sai hakuri Hajiya Kaltume Iyami dai ta zama murucin kan dutse, ta zama kadangaren bakin tulu, kuma ta zama ƙashin wuya bata haɗuwa bata amayuwa”

Maama ta juyo tare da tasowa daga dinning din zata fadawa Gwaggo magana Hajiya Kaltume ta yi saurin daga mata hannu.

“Babu ruwanki Maama je ki cigaba da cin abincinki, Allah dai baya baci zalinci da kuka min sai ya saka min macuta kawai masu abun kunya”

Hankali kwance Gwaggo ta ce.

“Ba mu da abun kunya, da muna da abun kunya mijinki ba zan lallaba ya nemi hada iri da mu ba, kuma Alhamdulillah ko yanzu kasuwa ta watse ɗan koli mai rabo ya ci riba, tun da ga ƴaƴa nan Allah ha raya su ya saka musu albarka”

Gwaggo na kaiwa nan ta kabe Hijabinta ta fice daga falon ta bar Hajiya Kaltume da ciwon rai. Ko da Gwaggo ta iso gurin Bappa na nasa masifar Yasir na bashi hakuri.

“Bappa ka yi hakuri Wata kila ransa ne a bace”

“Idan ransa ne a bace be san waye ni ba da zai fada min maganar banza?”

Gwaggo ta dubi Yasir ta dubi Bappa.

“Malam lafiya?”

“Yasir ya shiga ya kira min Alhaji Haruna, daker mutumen ya fito, kuma abun da yake fada min shi be da miliyan dari biyu da zai bada yanzu, kuma ina damunsa da kira ban san damuwarsa ba, ai ba Hamad kadai aka dauka ba har da yarsa amman mun daga masa hankali kamar Hamad ne kadai ďa, idan muna da kudin mu ba su mu karbo Hamad din har da rubuto min number mutanen ya turo min, wai shi ba zai bada kudi ba police sun ce za su karbo su”

“Hmmm Allah ya kyauta, tun da ya baka Number mu tafi Malam”

Yasir ya nufi Gwaggo cikin rashin jindadin abun da ya faru yana bata hakuri

“Gwaggo dan Allah ku yi hakuri, maybe damuwa ce ta yi ma Appa yawa, dan Allah ku yi hakuri ba halinsa ba ne Wallahi”

“Karka damu Yasir babu komai”

Gwaggo ta fada sannan ta bude motar ta shiga, Bappa yaja motar sai masifa yake ta yi domin yau Alhaji Haruna yayi masa abun da be taba masa ba.

“Har yana cewa muje mu biya kudin ganin yake kamar ba zamu iya ba ko? Har yaushe za a bata lokaci gurin jiran abun da baka san faruwarsa ba? Ko bayan haka ni bana je akan ya bada kudi ba, naje ne mu yi magana ta fahimta da shi na ji halin da ake ciki, amman mutumen ko kallona baya son yi, sai fada yake kamar shi ne uban ni ne dan, na fada masa ni ba zan dauki wannan rainin wayon ba, kuma ni da gidansa har abada, wato saboda ya saki Iyami shiyasa yanzu baya ganin kimarmu ko?”

“Allah kadai ya san abun da yake nan Malam, Allah dai ya isarwa Iyami da yaranta Allah ya saka mata da gaggawa”

Gwaggo tana addu'a tana kuka daman idan ranta ya bace bata da wuyar kuka.



_________________

Ina masu fama da ciwon dajin?
Showing 6001 words to 9000 words out of 215510 words