amman ba hali.

“Zan sallami mai napep din sai na sauke ki gida”

“Aa na gode yanzu zan tafi”

Ta saki hannu Hurriya ta fara tafiya sai ya kirata.

“Rukky”

Ta juyo ta kalleshi.

“Na ce zan sallami mai napep zamu sauke ki gida tare da hurriya daga nan ta duba Amma”

Bata son tace masa no, kuma ta san Hurriya zata so ganin Amma domin ta dauki lokaci bata saka ta a ido ba, ko da tace zata je sai Appa ya hana saboda Hajiya Kaltume tace zuwan da take tana tafiya ne dan ta fadi karya da gaskiya.

“Tahm”

“Hurriya shiga ki dauko Hijabinki”
[11/3, 4:06 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 13*



“Muna fatan haka, shi dai mutane da dama sun karba kuma an dace, mu ma muna fatar mu dace wannan ciwon nata ya isheni Allah kadai ya san abun da take ji a ranta, ina fatar na ga ta warke kamin na mutu”

Cikin kuka Gwaggo ta karaso maganar ita kanta a yanzu bata da wata damuwa da ta wuce ta Iyami. Hurriya ta tashi rike da littafin ta fito sai ta tsaya daga bakin kofar dakin tana kallon Amma dake kallon kofar dakin tun da suka shiga ciki, wasu hawayen ne suka subuce mata sai ta fashe da kuka. Amma ta girgiza mata kai tana jin kamar ta yi mata magana a dama, shigowar Rukayya ne ya saka Hurriya boye fuskarta Gwaggo kuma ta taso ta fito daga dakin tana fada.

“Wane irin abu ne zaki je ki zauna har dare haka Rukayya”

Yasir dake bayanta yana sallama yayi saurin tare mata fadan.

“Tun isha'i take nan kofar gida Gwaggo laifina ne ni na tsayar da ita, ayi hakuri dan Allah”

Rukayya ta juya ta kalleshi shi kuma yaki yarda au hada ido sai hakikancewa yake yana ba Gwaggo hakuri kamar shi yayi laifin. Ya zauna saman kujerar da Amma take jingine yana mata ya jiki.

“Amma ya jikin?”

Ta amsa murmushi kadan alamar jikin Alhamdulillah. Gwaggo kuma ta amsa masa.

“Jikin sai Godiya”

“Allah ya kara sauki”

Ya kalli Hurriya dake labe jikin curtains din dakin.

“Muje Hurriya kar Appa ya fara neman mu”

Hijabin ta janyo ya sauko ya rufe mata fuska sannan ta tako ta iso gurin Amma ta kwanta jikinta ba tare da tace komai ba ta mike tsaye, Amma ta bita da kallo har suka fice. Har sun isa gurin mota ta tuna bata shiga ta duba kanenta ba.

“Yaya dan Allah minti daya zan koma na duba Twins”

“Karki dade”

“Toh”

Ta koma cikin gidan da gudunta ta duba su ta fito ta shiga motar, sai da suka kama hanyar gida sannan Yasir ya kalleta ya ce.

“Hurriya da gaske baki san yaron nan ba?”

“Wallahi ban san shi ba Yaya”

“To ya aka yi yanzu ya kira ni wai yana neman Hurriya na tambayi sunansa ya ce sunansa Adam Sarauta ina ya samu number ta?”

Hurriya ta ji gabanta ya fadi.

“Ni kuma? Wallahi ban bashi ba ko sunana ni ban san inda ya ji ba”

“Bana son ki min karya, kuma bana son ki aikata wani abin da zai zubar miki da kima ko gidanmu, saboda haka ki kiyaye karki wani abu ya sake hadaki da shi, na san gayen nan na yaron kwarai ba ne, idan ba haka ba ni ma zan saba miki”

“Toh Yaya amman Wallahi ban san shi ba”

“To ya aka yi ya sami number ta?”

Har zata ce bata sani ba, sai kuma tuna da ta karbi wayarsa ta kira Yasir.

“Da wayarsa na kiraka, lokaci da yace na saka masa number ta sai na kiraka na ce ka zo ka dauke ni, ai har na fada maka Adam yace I'm not safe here”

“Na tuna, zan ja masa kunne”

“Toh Yaya”

Ta amsa tana gyara zaman littafin da Gwaggo ta bata a hannunta.




_________________
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo...
[11/3, 4:06 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 12*


Ya fada sannan ya nufi gurin motarsa ya ja motar ya iso har gurin da Rukkaya take tsaye, bata shiga motar ba sai da Hurriya ta fito sanye da dogon hijab dinta har kasa, sannan ta bude ta shiga front seat Hurriya ta shiga baya, ya fara driving suka fito gate a nan ya sallami mai Napep din sannan ya ja motar suka kama hanya.

“Rukky please bana son wani abu marar dadi yana shiga tsakaninki da Hajiyata, idan ma ta fada miki wani abu marar dadi ko ta yi miki abun da bw dace ba, ki danne ina son ki dauke ta kamar mahaifiyarki, saboda ni kuma ina tunanin ina da alfarmar da zaki yi haka a gareni”

Ta hade yawu can cikin ranta take cewa Allah ya tsare ta Hajiya Kaltume ta zama uwarta.

“In Shaa Allah”

Ya kalleta yana murmushi.

“Thank you”

Ita ma ta mayar masa da murmushin daga haka be sake cewa komai ba ita ma kuma bata sake cewawa har suka isa gidan. Hurriya ce ta fara budewa ta fita motar Rukayya na kokarin fita Yasir ya shigo ya dakatarda ita.

“Ina zaki je?”

Ta masa kallon rashin fahimta.

“Gida mana...”

“Ni kuma sai ki bar ni a nan?”

Ta yi dariya.

“To ka fito mu shiga gidan bakonka ne?”

“Ki dai tsaya mu yi hira ko raina zai saki ni raina ma duk a bace yake”

“Waya bata maka rai Hurriya?”

“Idan kina son jin labari zauna”

Ta yi murmushi sannan ta dawo ta zauna ba tare da ta kalleshi ba.


Hurriya na shiga cikin gidan ta fada dakin Gwaggo da sallama da muryar dake nuna alamar kuka ta yi. Amma na jingine jikin kujera ita kadai a falon tana fuskantar tv dake falon, ta dan karkato kadan ta kalli Hurriya. Hurriya ta isa gurin sai ta kwanta saman jikinta ta fara hawaye, bata son ta fada mata abun da ya faru saboda kar ranta ya bace gashi ba magana take ba balle ta bata shawara.

“Amma na Allah ya baki lafiya, Allah ya tashi kafadunki”

Ta cikin Amma ta iya amsawa da ameen ta kwanto da kanta saman kan Hurriya ta rufe ido. Gwaggo ta fito daga dakinta tana mata maraba.

“Yau Hurriya ce a gidan nan kuma da dare, amman dai Alhaji be san kin zo nan ba ko?”

Hurriya ta dago hawaye shakaf a fuskarta ta kalli Gwaggo.

“Be sani ba, Ya Yasir na biyo zamu kawo Rukayya ne”

“Daman tace sai ta biyo ta ganki, na dauka ma can zata kawana gidan Hauwa, saboda na ga dare yayi sosai”

“Tana waje ita da Yaya Yasir, Gwaggo zo”

Hurriya ta kama hannunta suka koma cikin dakin, ta zauna bakin gado Gwaggo ma ta zauna daman tana ganin ruwa hawaye a fuskarta ta san akwai abun da ya faru.

“Wani abu aka yi Hurriya?”

“Sheri aka yi min Gwaggo.... ”

Ta labarta mata abun da ya faru, sannan ta dora da abun da mahaifinta yayi mata recently before birthday Khairi.

“Appa ya siyawa kowa sabon kaya na birthday din Yaya Khairi amman ni Hajiya tace kar ya siya min ina da kaya da yawa, na masa magana sai yayi min fada, Gwaggo yanzu Appa baya so na ko kadan idan na matsa kusa da shi sai yayi ta min fada, zaman gidan ba ya min dadi kowa tsarguwata yake”

“Ki yi hakuri Hurriya zalinci be taba doreba, kuma komai yana da iyaka wata rana sai labari, ke dai ki yi ta addu'a ki yi ta fadawa Allah matsalarki zai magance miki ita, mu ma muna nan muna yi kuma akwai wani littafi da na siya miki na addu'o'i mantawa na yi ban bawa Rukayya ta kai miki ba”

Gwaggo ta tashi ta nufi gurin da ta aje littafin husnul muslim ta dauko ta mika mata.

“Addu'o'i ne da suka zo daga bakin Annabi Muhammad, karki yi wasa da su, domin ba mu san me za a sake jifanke ko mahaifiyarki da shi ba, kuma duk abun da zaki ci ki yi bismillah, sannan kar tsoro ya saka a baki wani abun da aka san an cutarwa ne ki ci ko ki aikata, yanzu girma kike yi ya kamata ace kina kara wayo”

Ta share hawayenta

“Na gode Gwaggo”

“Ba komai Allah dai ya tsareki, kuma ina kara gargadinki ban da sakaci da addu'a, kin ga rashin daukar addu'a da muhimmanci ne ya jefa Iyami a halin da take yau, sannan kuma zan karbo miki maganin tsari akwai wani mai bada taimako na yi magana da shi ya ce sai an ba shi 150k sannan zai fara yi na Iyami aiki, ya fada mana jefa ce aka yi mata mai hatsarin gaske, kuma idan ba mu yi fa gaske ba zamu rasata”

“To yanzu ina za'a samu 150k Gwaggo?”

“Ina nan ina ta kokari Hurriya, idan kuma haka bw samu ba dole gidan nan zamu siyar mu nemi karamin wannan mu siya sauran kudin sai mu yi maganin da su domin lafiyarta ta fi mana komai”

“Amman idan aka yi zata warke Gwaggo? Kin san ana ta yi amman babu wani sauyi”
[11/9, 5:22 AM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*

*PAGE 11*


Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣1️⃣

Hajiya Kaltume na tsaye rumgume da Hanayenta Yasir ya faka motarsa ya fito, sannan Hurriya ma ta fito sau daya ta kalli gurin da Hajiya take ta dauke kai ta fice daga apartment din ta nufi na Momy, wata kalar harara Hajiya take watsawa Yasir har ya iso.

“Ina ka fito?”

Ya juya ya kalli Hurriya da tuni ta fice daga bangaren sannan ya kalli mahaifiyarsa.

“Mun sauke Rukayya ne”

“Kun sauke Rukayya kamar ya?”

“Hajiya dare yayi shiyasa na kaita gida a mota, daga can Hurriya ta duba Amma”

“Ita bata san dare yayi ba ta kama hanya ta zo? Kasan ma a ina ta fito? Wace yarinya mai tarbiya ce zata fita yawon dare?”

“Hajiya Stop...”

Ya fada yana kokarin danne bacin ransa.

“Ba sai ka min turanci ba, daman yaran zamani ne ku ai, sai ka zage ni ban sani ba, amman dai bari ka ji na fada maka ka fitar sapgar Rukayyar nan ba yarinyar kirki ba ce”

“Hajiya please karki munanawa Rukayya zato, yarinyar nan tana da hankali da tarbiya, na san wacece ita, saboda ta yi dare baki san dalilin da ya saka ra yi haka ba, ki daina fadar bata da tarbiya bata min rai kike, yanzu da wani yayi abun da Khairi ta yi da yanzu kin zage shi, amman kin tsallaketa kina ganin laifin yar wasu, dan Allah wannan ya zama na karshe da zaki fadi wata magana marar dadi akan Rukayya”

Yana gama fadar haka be tsaya jin abun da zata fada ba ya wuce ciki ya barta a gurin tsaye da mamaki.

“Ikon Allah baka son a fadi wata magana marar dadi akan Rukayya saboda Rukayya kanwar uwarka ce? Anya dai Iyami bata Zuba maka ka sha ba, kai duk wani abu da ya shafeta sonshi kake, daga kan Hurriya har Iyami yanzu kuma abun ya koma kan kanwarta, eh lallai tun da ka ga farar fata, to Wallahi baka isa ba ba Rukayya ba ko keya ce sai na ga bayanta, wato ma wani abu ne a cikin zuciyarka da har idan an fadi sunanta da mugun abu ranka yake ba ci, har da wani tashi ka kaita gida kai ga Sharukhan baban Soyayya, to da ni kake zancen”

Ta juya ta bi bayansa tana masifa, a falo ta zame shi zaune yana lasa wayarsa yana ganinta yayi saurin tashi ya nufi stairs dan ya san fada zata masa, da kallo da bishi har ya haye sama.

“Ba shakka, wato ubanka ya dandana nan bakin cikin Iyami shi ne kai ma zaka gwada naka ko? Dadin abu kai haihuwar ka na yi ba aure ba, baka da ikon kanka sai ikon da ake da shi akanka”

Ta zauna a inda ya tashi tana jin zuciyarta na wani irin zafi, domin bata da makiya a yanzu kamar Iyami da iyalinta...


HURRIYA POV.

Da sallama ta shiga falon Momy ta dago ta kalleta ta dauke kai, Namra kuma dake kwance cinyar Momy labarin da take da Momy ya hanata amsa mata.

“Ni Wallahi tausayi yake ba ni gaba daya ya koma kamar ba shi ba, dan murmushin da yake da yanzu duk ya daina”

Momy ta shafa goshinta.

“Fadan kuma ya karu ba, sai bakar zuciya da ganin laifin kowa”

“Ai dole”

Hurriya ta risina tana yi ma Momy sannu da dare.

“Ina kika fito?”

“Tare da Yaya muka fita ya aje Mama Rukayya a gida ne, ni kuma na duba Amma”

Hurriya ta amsa tana jin kamar ace ita ce take kwance a cinyar Amma, Amma na shafa kanta yadda ta shigo falon ta tararda Momy da Namra abun ya burgeta sai ya kara mata kewar mahaifiyarta sosai. Namra ta tashi zaune

“Wayyo ban sani ba da naje dubata ya jikanta Hurriya”

“Da sauki”

“Allah ya kara sauki”

Hurriya ta amsa da amin sannan ta mike tsaye ta, Momy ta bita da wani kallo kamar na tuhuma tana tsire baki. Hurriya ta shiga dakinta ta cire hijabin jikinta ta nufi gaban madubi ta zauna tana kallon kanta, sai hawaye suka fara zubo mata. A take ta sauke kanta kasa tana kallon hannayenta.
Rayuwar baya take tunawa lokacin da take cikin farinciki, Amma na kusa da ita Appa yana kaunarta ga dan'uwanta abokin fadanta kuma mai tare mata fada. Ta tashi kamar marar lafiya ta nufi gadonta ta zauna sannan ta cire gilashin idonta ta kwanta. Bata farka ba sai asuba, bata fito dakinta ba sai 12pm shi ma kuma saboda yunwa ta matsa mata lamba ne daman bata son fita ko'ina sai idan tana bukatar abinci, yanzu ba irin da ba ne da take zuwa makaranta balle fita ta zame mata dole, tun bayan da ta kammala Secondary school ta samu yancin zama a gida domin Appa be yi making wani effort da zai nuna yana son ta cigaba da karatu ba. Ita kuma tana tsoron yi masa magana sai dai ta yi ma yayanta shi kuma idan ya tunkari Appa da maganar sai yace masa akwai abun da yake jira. Daga Momy har Hajiya Kaltume kuma babu wanda ya damu da karatunta da ta yi da kar ta yi duk daya suke a gurinsu, Momy da yaranta take da kanta daman rayuwar wani bata dame ta ba, Hajiya Kaltume kuma bata son Hurriya da alheri ta ina zata damu da karatunta.
A hankali ta sauko kasa tana sanye da doguwar riga kanta babu dankwali, gashin kanta a dan yamutse saboda rashin gyara shi da bata yi ba after ta yi wanka.

“Yauwa Hurriya dan Allah ki shirya anjima kadan zaki raka ni Mall na siye wani abu”

Ta juya ta kalli saitin gurin da Namra take zaune tana shafa abu a fuskarta.

“Toh Yaya Namra”

Sannan ta juya ta shiga Kitchen din ta hada tea ta fito ta nufi dining ta zuba abun da zata iya ci ta dauka ta sake dawowa dakinta ta zauna a kasa ta nade kafafuwanta ta fara ci, bata wani ci sosai ba ta fi ta koshi sai ta ja komai gefe ta aje. Tana zauna a gurin har aka yi azahar, bata sake fitowa dakin ba sai da Namra ta tura kofar ta leka ta.

“Kin shirya kuwa?”

Sai ta sauko saman gadon ta nufi gurin madubi ta dauka ta gyara kanta ta saka ribbon ta dauki mayafin abayar ta rufa.

“Eh mu tafi yanzu”

Namra ta yi dariya
Showing 30001 words to 33000 words out of 215510 words