a hankali.

“Hurriya kina ina? Jiranki fa ake”

Ta bude idon da sauri, ta bude drawer madubin ta saka takardar ta rufe sannan ta mike tsaye ta share hawayenta ta dauki mayafin abayarta ta shafa a saman kanta sannan ta nufi kofar fita da saurinta. Tana bude kofar Momy na bude tata kofar da kan kace kwabo Hurriya ta sauko idonta kasa ta tsaya jikin kofar har sai da Momy ta sauka sannan ta sauko ta fice daga bangaren. Tun kamin ta isa bangaren ta fahimci kowa ya gama tafi domin babu mota ko daya a bangaren Hajiya Kaltume, cikin zullumi ta karasa ta shiga falon sai ta ga ko'ina wayan babu kowa. To daman waye zai tsaya jiranta ita banza a banza.

“Yauwa yar abaya daman a komai ai ke ce baya, kowa ya tafi ke kina can boye yanzu zaki fara karyar baki san sun tafi ba, daman ina bakinciki zai barki ki tafi abun yan'uwa? Hassada ai ta gama cinye ki”

Ta dago tana duba Hajiya Kaltume dake saukowa tana jefar Hurriya da duk kalmar data fado bakinta. Hurriya ta rike hannayenta kana kallon fuskarta zaka san kalaman Hajiya Kaltume ba su mata dadi ba, sai dai ta saba jin wadanda suka fi su ma daga bakinta ko na yayanta babu abun da yake sabo a gareta yanzu, ɗacin kuma ta barwa zuciyarta. Ta juya jiki babu gwari da zimmar ficewa sai aka turo kofar falon, kyakkyawan bakin saurayin nan mai matukar cikar kamala da mazantaka ya shigo falo fuskarsa dauke da murmushi bakinsa kuma kunshe da sallama. A take Hajiya Kaltume ta washe baki.

“Maraba da Fadeel yanzu ake tafe?”

“Eh ina wuni Hajiya?”

“Lafiya kalau ya aikin?”

“Alhamdulillah”

Har ya zauna Hurriya dake tsaye yake kallo, be dauke idonsa ba har sai da ta mika masa gaisuwa da muryarta mai matukar sanyi, so innocent.

“Ina wuni”

Kamar daman gaisuwar yake jira sai ya dauke idonta after ya amsa ya kalli Hajiya Kaltume.

“Hajiya ce tace na zo na dauki Khairi wai ko bata samu mota ba?”

Hajiya Kaltume ta dan yi shiru kamar mai tunani kamin ta karasa saukowa ta amsa masa.

“Eh... Amman ta samu daga baya, sai dai ko idan zaka ka leka ne”

“No daman akwai inda zan je kawai saboda Hajiya ta matsa ne ya saka na zo na kaita, amman tun da ta samu shi ke nan ai”

Ya mike tsaye, Hurriya ta dan kalleshi tana jin kamar tace masa ya aikata ya kaita, kuma bata isa ba domin Hajiya Kaltume na tsaye a falon, ko da ma ace bata gurin abu ne mai wahala Hurriya ta iya rokon abu.

“Ba zaka tsaya ka sha ko ruwa ba? Hurriya kawo masa ruwa mana”

“No tafiya zan yi ai”

“Sai fa ka sha zauna mana sa nan da gurin Hajiya Fatee ai duk gidanku ne, kunya kuma na miye?”

Baya son musa mata dan haka ya zauna yana murmushi kamar yadda ita ma take murmushin. Hurriya ta nufi hanyar kitchen bata jima ba ta fito rike da gorar ruwa da cup tana kokarin ajewa ya mika hannu ya karbi gorar ya bar mata cup din, kamar ya san burin da take da shi a zuciyarta sai ya tambaye ta.

“Ke miyasa baki je ba? Ko baki samu motar ba ne?”

Ta daga masa kai a hankali kamar wadda bata son motsi.

“Muje na sauke ki”

Ta juya zata kalli Hajiya sai ta jiyo Hajiyar na fadar.

“Aa haba ka tafi kawai gurin aikinka, ai bata yi niyar zuwa ba ne, shiyasa ta boya sai da kowa ya watse sannan ta fito”

Kalma daya bata isa ta musa ba a cikin kalaman Hajiya Kaltume, dan haka bata ce komai ba ta sauke kanta kasa.

“Ko maybe bata son shiga mutane ne, na lura she's different, can i drop you?”

Ya karasa da son ya ji amsarta sai ta daga masa kai ba tare da ta kalleshi ko ta kalli Hajiya ba, domin har ga Allah tana son zuwa birthday party din na Khari da ta hade da graduation dinta.

“Hajiya na gode zan ajeta sai na wuce”

“Toh Allah ya kai ka lafiya”

Ya wuce gaba, Hurriya ta bi bayansa har lokacin kanta na kasa, Hajiya Kaltume na watsa mata harara kamar ta fisgota ta yi ta duka haka take ji. Suna ficewa ta tashi ta nufi stairs duk yadda ta so yin sauri bata iyawa saboda jikinta baya barinta ta wala yadda take so. Tana isa bakin kofar dakinta ta kai hannu ta tura kofar dakin zata shiga sai ta ji kamar an turata haka ta tafi suuuuu ta fadi kasa ridd rub da ciki.

“Subhanallahi”

Ta fada sannan ta yunkura ta tashi zaune tana jan kafa ta isa bakin gadonta ta zauna ta daga zane ta duba kafar dake mata mugun ciwo.

“Ya haka abu dai kamar an turo ni”

Ta latsa cinyarta dake cike da tsokar nama tana runtse ido saboda zafin da yake mata. Karar wayarta ne ya dago hankalinta ta kai dubanta gurin da wayar take Hajiya Fatee ce a line hannu ta kai ta dauka ta danna picking ta saka a hands-free ta aje wayar saman gado.




HURRIYA POV.

Tun da suka fita daga gidan idonta na gurin titi da motocin dake ta zirga zirga, Fadeel ma be ce mata komai ba kwarjininta ya cika masa ido ta yadda har ya kasa tambayarta gurin da zai kaita. Kallonta ma sai yayi da gaske yake yi, shi ma kasa kasa, yayi kanwa ta hudu da ita amman ya samu kansa da jin nauyinta, maybe because tana so Innocent ne kuma saboda tana kyau ne irin mai cika idon nan da haifar da natsuwa, or maybe kuma saboda tana karama ne she's too young yaja ta da hira. Ganin suna ta dawowa the same road da suke tafiya ya saka ta dago ta kalleta sai yayi mata dan murmushi kadan.

“Ban san even center din da za'ayi party ba”

“K_Candy Event Center”

Muryar ta fito between her two soft lips.

“Okay....”

Ya cigaba da tukin, after like ten minutes ya sake yin magana ba tare da ya kalleta ba.

“Yaushe za'ayi naki birthday”

Ta yi shiru kamar bata ji shi ba.

“Ko an yi?”

“Ba ayi ba, amman ya wuce”

“How old are you?”

Uffan bata ce masa ba har suka isa gurin ya faka motarsa ta bude zata fita sannan ta ce.

“19...”

Ya bita da kallo har ta fice.

“Thank You”

Ta rufe masa motar a hankali sannan ta nufi hanyar shiga tana tafiya kamar mai tausayin kasa.






Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/3, 5:26 AM] AMINA KABIR CAPS: *HURIYYA*


𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660


𝐏𝐚𝐠𝐞 8⃣


Tana isa gurin masu aikin tsaron kofar suka tareta.

“Ina zuwa?”

“Ciki”

“Ina katinki?”

Sai a lokacin ta tuna ta ji Khairi da kawayenta suna maganar gate pass amman bata maida hankali ta karba ba ganin ita din ta gida ce.

“Yayata ce take yin biki ciki, ba na bukatar gate pass”

“Gaskiya ba zaki ita wucewa ciki ba sai da gate pass”

“Toh ko zaka taimaka ka kira min ita dan Allah”

“Ki kirata da wayarki mana”

“Ba ni da waya, amman zaka iya ara min taka”

Har yayi kamar zai hanata sai kuma ya ciro karamar wayar ya mika mata. Number Ya Yasir ta saka ta kira shi few rings ya daga.

“Hello Yayana”

Yana jin kalmar Yayana ya san cewa Hurriya ce.

“Hurriya waya waye wannan”

“Na wani ne, na zo gurin birthday din Yaya Khairi ne, kuma ba ni da gate pass shi ne suka hana ni shiga”

“Kin fada musu ke kanwarsu ce? Ya aka yi ma baku shiga tare da su ba”

“Eh na fada musu, sun riga ni zuwa ne na ji muryar Namra tana min magana ko da na fito ita ma ta wuce, sai wannan dan Hajiya Fatee ne ya kawo ni”

“Zan kirata ta fito ta shiga da ke”

“Toh Yayana na gode”

Ta katse kiran ta mika masa wayarsa.

“Na gode Allah ya saka da alheri”

“Amin”

Ya amsa sannan ya maida wayar aljihu. Rumgume hannayenta ta dan ja baya kadan tana kallon kofar. Wani matashin saurayi ne ya fito yana tambayar masu gadin ina wadda ke tsaye.

“Gata can”

“Ku barta ta shigo”

Hurriya na jin haka ta nufi gurin, guy ya kalleta sama da kasa.

“Shigo”

Ta cira kafa ta fara takawa ta shiga ciki, dim Light ne ko'ina sai sauti ke tashi, tun daga yanayin samari da yan matan da aka tara a gurin zaka fahimci ba biki ne na masu mutunci da sanin ciwon kai ba. Kusan ita kadai ce take sanye da abaya dukan nin kawayen Khairi suna sanye da English wears, wasu ma kansu babu dankwali tsabar wayewa da rashin tarbiya.

“Ga Khairi can”

Gayen dake take mata baya ya nuna mata yayarta. Hurriya ta daga kai ta kalleta tana sanye da wata riga kamar yar bayahuda, kanta babu dankwali kanta ya sha gyara an zuba mata attachments din har gadon bayanta, makeup din da aka yi mata ta kara mata kyau gaba daya ta canja kamar ba ita ba. Mamaki ya saka Hurriya bude baki tana kallonta bata sanin wayewar Khairi ta kai haka ba, aranta take ayyana yadda Yasir zai ci ubanta idan ace yana gurin.

“Muje ki ganta”

Ta juyo ta kalli gayen. Ta san idan ta je ba mutunta Khairi zata yi ba, wata kila ma zata gwatsale ta ne a gaban mutane.

“Aa ba sai na je ba”

“Okay to muje ki zauna”

Ta kalleshi kamin ta kalli gurin da ya nuna mata. Sannan ta fara takawa da kansa yaja mata kujera ta zauna ta dan jin kunya abun ka da wanda be saba ba, not like bata saba zuwa birthday ba she used to amman ba irin wannan ba, kuma wani namiji be taba ja mata kujera ta zauna ba.

“Thank you”

“You're welcome kyakkyawa, kina son shan wani abu?”

“Aa na gode”

Ta dauke kai tana kallon yadda kawayen Khairi suke ta takawa MC sai zuba mata kirari yake kamar wata amarya.

“Me yasa kika saka Abaya baki san birthday za'ayi ba?”

Ta juyo ta kalli abayarta.

“Na sani”

“To why do you wear abaya?”

Ta yi masa shiru kamar bata gurin, idonsa na kan wuyanta zuwa kirjinta domin wuyan abayar mai yankan V ne dake bayyana kasan wuyan mutum, wani abokinsa ne ya kai masa duka yana dariya.

“Shegen kaya ashe nan ka boye who's this?”

Gayen ya kalleshi yana murmushi.

“My new friend i think kawar Khary ce”

“Her Blood Sister”

Hurriya ta amsa masa da kanta sannan ta tashi ta bar taburin ta nufi wanda babu kowa a kai ta zauna tana bawa idonta abinci. Bata ankara ba ta ji ana mata magana dama da ita.

“Sai kuma kika gudu? Tsoron mutane kike ne? Na ga kin kasa sakewa ma what's wrong”

Ta kalleshi ta dauke kai ba tare da tace komai ba, hannunsa ta ji a fuskarta yana kokarin juyowa da ita, da sauri ta buge hannu ta mike tsaye.

“Miye haka? Akan me zaka taba min fuska?”

Ya daga kafadunsa.

“Fuska ce fa kawai”

Kwafa ta yi ta juya zata bar gurin sai yayi dariya ya mike tsaye da gangan ya riko hannunta, shi dai kam ta masa kyau and as she know friend dinsa Khairy ba zai yarda duk wanda ya zo party ta a yau yace ba a saba rika hannunsa ba, domin kusan rabin yan bikin duka suna rike da hannayen juna ne, saboda wasu are in relationships wasu a dating wasu kuma a new friends to them hugging ko rike hannu is nothing in their team.

“Ya kike yanga yan mata saboda kina da kyau ne?”

Jin ta yi kamar ta tsinka masa mari sai kuma ta ji bata da wannan kuzarin.

“Karka sake taba ni, ni ba irin sauran matan da suke nan ba ne”

“Miya banbanta ki da su? Saboda kina da kyau?”

Ta masa banza, a abu mai muhimmanci ma Hurriya bata cika son amsawa ba balle na banza. Ya dan cize baki yayi murmushi.

“Shikenan zauna ba zan sake ba”

Bata zauna ba ta bar masa gurin tana rabon ido ko zata hango wanda ta sani ta zauna a kusa da shi.

“Wani kike nema?”

Wani ne kuma dabam yayi mata magana har kara wacan gayen da wannan domin wannan kansa ma wani kalar aski ne na yan iska. Shi ma dai bata ce masa na ta nufi gaba gaba ta inda Khairi zata hangota ko zata samu su daga mata kafa. Wani gurin ta nufa ta zauna tana kallon yadda yar'uwarta take rangaji kamar ta sha kwaya, gayen da ya fara yi mata iso ta hango ya isa gurin Khairi yana mata magana a kunne, kamin ya nuna gurin da take zaune har Khairiya ta kalleta ita ma ta mayar masa da maganar a kunne. Sannan ya sauko daga gurin ya nufi gurin MC, before she know sunanta ya cika gaba daya hall din.

“Ina Gimbiyar take, Hurriya ki fito kin yi farar tafiya daya daga cikin kananan matasan mu masu ji da kudi dan gidan Alhaji Buba Sarauta yana nemanki ya ce a kira masa kanwar Hajiyar ta mu wato Khairy domin ta taya yayarta murnar wannan birthday da take da kuma na graduation dinta”

Kowa sai ya fara rabon ido ana ta ga wayw Hurriya wacece Hurriya, Khairi kuma ta kasa boye mamakin dake fuskarsa, tambayarta sunan kanwarta da yayi ta fada masa bayan ya nuna mata ita bata dauka abun da zai yi kenan nan ba. Gaban Hurriya kamar zai fado tsabar bugawar da yake domin bata saba ba, irin haka ma be taba faruwa da ita ba. Kasa tashi ta yi ta rasa me zata yi ba zata iya zuwa gurin da aka bukace ba, bata san ma'anarsa na yin haka ba, so she decided to hide herself, tana kokarin janye kujerar ta boya karkashin teburin, gayen ya nufo inda take MC na biye da shi, hakan ya hanata boya sai kallonsa take ta cikin gilashinta tana jin ta ga abun da zai mata, gaba daya sai hankali ya dawo gurinta ita kanta Khairy sai ta sakar musu ido tana son ganin me ke shirin faruwa. Tun kamin ta karaso gurin da Hurriya take zaune ya cire rapper dollars ya fara bararwar har ya isa gurin da take ya tsaya akanta yana ta zuba mata dollars, idan suka kare sai ya dauko wata a aljihunsa ya cigaba da zuba mata, a take gurin ya dauki ihu aka fara daukarsu da manyan wayoyi wasu yan matan da suke crushing akansa kuma suka kasa boye kishinsu. Gaba daya mantawa aka yi da wani birthday party sai ihu ake ana daukar Hurriya, da gayen dake zuba mata kudin kamar be san zafinsu ba. Hurriya ta mike tsaye da sauri tana kallon Namra da sai a lokacin suka ga juna, bata tsaya komai ba ya nufi kofar fita ta fice daga gurin da gudunta, abun da ta yi ya bawa kowa a gurin mamaki domin at first wasu sun dauka ko budurwarsa ce, sai dai guduwar da tayi ya saka shakku a zukatan mutane. Khairy kan ta cika har tana kusan fashewa domin ta san saboda ita ya zo birthday even though ba saurayinta ba ne he's just her friend amman ta san kudin da ya zo da su ita ya kamata yayi ma kari da su gashi be yi ba ya karar da su gurin kanwarta.

Hurriya ta fito da sauri ta biyo hanya tsoro duk ya gama cika ta gaba daya ma a firgice take, hankalinta be kara tashi ba sai da ta iso titi, ko'ina tsit yake kamar babu mutane, arzikinta daya rana ce ba dare ba, wannan ya saka ta dan ji sauki. Juyawa ta yi kamar zata koma sai kuma ta ga ba mafita ba ce, tafiya ta fara yi tana rumgume da hannayenta sai ta ji an mata horn, juyowa ta yi ta kalli motar da bakin gilashi ya hana a ga wanda ke ciki. Ta juya ta cigaba da tafiya kamin ta tsake tsayawa kamakon fakawar da mai motar yayi gefenta ya sauke gilashin motar.

“Saboda na miki karin kudi zaki gudu? Idan ni ne ki koma ba zan sake ba”

Ta kalleta ta dauke kai ta cigaba da tafiya, shi ma tafiyar yake slowly cikin motar yana kallonta..

“Idan kuma gida kike son zuwa shigo na kai ki, you're not safe hare”

Kalmarsa ta karshe ta saka tsoron dake cikinta ya karu, ta dan karkato kadan ta kalleshi sai ya kai hannu ya bude mata front seat. Tsayawa ta yi kamar mai tunani shi ma sai ya tsaya daidai ita.

“Gida zan kai ki, shigo”

Ta kalli abun da ke aje a kasan inda mutum zai dora kafafuwansa idan ya shiga, sai yayi saurin kai hannu ya dauke ya jefata baya.

“Shisha ce please
Showing 21001 words to 24000 words out of 215510 words