ba shi shawara ya fita safgar yarinyar nan, wani rashin mutunci ne take ji yanzu, ko da yake ni ban ki ta samu miji an mata aure ta bar bangaren nan ba”
Kamin Captain yace wani daman kuma ba shi da niyar fadar wani abu akan maganar. Hurriya ta turo kofa ta shigo falonta ta kofar da ake shigowa, bayan ta bata lokaci a Garden ta wanke hannunta a fanfo da fuskarta. Gaba dayansu dubansu ya koma kanta, tana isowa tsakiyar falon ta kalli Momy sai kuma ta yi saurin kauke kai kasa ta nufi hanyar stairs.
“Ke zo ki dauki abincin nan idan zaki ci”
Captain ya fada in a game way, yana binta da kallo, ita ma juyowa ta yi ta kalleshi kamin ta kalli Momy dake kallonta.
“Zo ki dauka mana”
Ya saka fada ganin tana jiran umarnin Momy, Namra ta yi karaf ta ce.
“Domin ku fa aka yi?”
“To ai shi ya tafi be ci ba, kuma ni ma a koshe nake maybe next time”
Hurriya na jin haka ta dawo ta duka a gurin ta dauki plate ta zuba rice din sai karamin bowl ta zuba miyar sai da tsame rabin naman kazar dake ciki miyar sannan ta dauki cup ta zuba fresh apple juice da Namra ta hada ta dauki wani plate din ta zuba plantain duk abun da ta zuba wanda ta san zai isheta ne har anjima, sannan ta dauka ta mike tsaye.
“Na gode”
Ta furta with sweet voice dinta tana musa laɓɓanta masu kyau. Sannan ta nufi stairs sai da ta kusa haye sannan ta juyo ta kalleshi ta juya ta cigaba da tafiyarta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/25, 5:23 AM] AMINA KABIR CAPS: *KHADIJA CANDY*
*PAGE2️⃣5️⃣*
“Baka dai ci abincin ba”
Ya kalli Momy yana saka hananyensa aljihu.
“Abokina ya tafi ransa a bace, taya zan zauna ni na ci abinci? Maybe next”
Ya kalli Namra dake tsaye ya kira sunanta. ”Namra”
“Hmmm”
“Be a good girl please”
Ta yi murmushi mai kyau.
“I will as always”
Ya mayar mata da murmushi sannan ya juya ya nufi kofa, da kansa ya bude ya fita Momy ta take masa baya ita da yarta. Momy na nade hannayenta ta aika masa tambaya.
“Sai yaushe kuma Captain”
“Anytime kina iya ganina ma anjima, ai yanzu ina garin nan har na tsawon wata uku kuma ina tunanin wannan ne best place da zan iya zuwa na yi yadda nake so, ba kamar a bariki ba”
“Me yasa ba zaka dawo nan gaba daya ba?”
“Ban sani ba ko za a su bar ni zan gwada haka”
Ya bude motarsa bayan ya amsawa Namra sannan ya shiga yayi mata key, Momy na daga masa hannu Namra kuma ta bishi da kallo da murmushi har ya fice. Momy ta juyo ta kalleta.
“Wata kila ya jidadin yadda kika karbi bakonsa a yau”
“Ni ma na ga alama”
“Yayi kyau”
Momy ta fada tana murmushi sannan ta sauke kai kasa ta juyo cikin tafiyar kasaita ta shiga falonta. Namra ta dade a gurin tana ta karatun wasikar jaki kamin ita ma ta juya ta koma ciki. Hurriya ta ci abincinta yadda take so, sauran ta saka dayan plate din ta rufe domin idan ta tashi ci anjima ba ta nema ba, kusan ita da marainiya duk daya agidan, wata kila ma marainiya ta fita gata da samun kulawa. Hakan ya taimaka mata bata fito neman abincin dare, shimkafar ta sake ci da dare ta kwanta abunta. Da safe ma bata fito gudun kar ta yi wani laifin ko kuma Momy ta rufe ta fada saboda ta zuba abinci da yawa ta kwashe nama, tana zaune a dakin har karfe goma na safe, tana unkurin tashi ta yi wanka aka turo kofar falon aka shiga, da sauri ta kalli kofar tana zaton ganin Momy ko Namra ga mamaki sai ta yi arba da Khairy.
“Yaya Khairy”
“Na'am Hurriya yanzu kika tashi?”
“Tun dazun amman ban sauko ba sai yanzu”
“Kin yi breakfast?”
“Aa”
“Ni ma ban karya ba, zo muje mu karya bangarenmu, idan mun gama ina son ki rakani wani gurin kin ji”
Ta dan yi shiru kamar mai tunanin yadda zata amsa mata kamin ta daga mata kai.
“Okay”
Ita kam gaba da ta kai ta ko ba komai zata karya, ba kamar jiya ba, already ta san Momy ko masu aikinta za su ce mata abincin safe ya kare kamar jiya, gashi kuma bata isa ta ce zata shiga kitchen ta girka ba ko ta saka a girka mata. Dan haka ta sauko saman gadon suka fice a dakin tare da Khairy, kamin su isa bangaren Hajiya Kaltume Khairy ta kama hannunta ta rike tana bata labarin guraren da za su da kawayenta da ta kwana biyu bata hadu da su ba. A dinning suka zauna ita Khairy da kanta ta hadawa Hurriya tea ta zuba mata komai na karyawa. Hurriya na tauna wainar kwai zuciyarta na raya mata akwai abun da Khairy take shirya mata, domin a iya saninta Khairy bata tana sonta ba ko na rana daya, idan ma kowa zai raga mata a gidan ban da Khairy amman me yasa take nuna mata kulawa tana janta a jiki yanzu? Anya ba wani abu take shirya mata ba? Ta mike tsaye sai Khairy ta kalleta da sauri.
“Ya aka yi baki sha tea ba fa?”
“Ruwa zan dauko a kitchen”
“Zauna bari na dauko miki”
Ta mike tsaye, Hurriya kuma ta koma ta zauna tana kallonta, Khairy na shiga kitchen ta dauko ruwan da cup ta fito, sai mamaki ya kara rafe Hurriya. Haka dai ta karya ba dan zuciyarta natsu da yadda Khairy take mata ba.
“Yaya Khairy saboda Adam ne?”
Khairy ta kalleta
“Ban gane ba?”
“Kike min haka kuma kike son na rakaki mu fita”
“Haba Hurriya Adam din da Appa yace kar ya sake ganinki da shi, kuma yaya ma yayi gargadi akan haka, shi ne zan hadaku? Na rantse miki da Allah indai ni ce ba zaki taba ganin na kawo miki Adam da idonki biyu ba, haba Hurriya kawai ina kokarin ganin na kyautata miki ne, ni yar'uwarki ce be kamata ace muna samun tsabani ba, kin ga yanzu ni aure zan yi, duk kuwa da ba a saka rana ba, amman ban san ya rayuwata zata zama a gidan auren ba, kuma hausawa suna cewa idan kana son gani da kyau to ka aikata mai kyau, and trust me daga yanzu an fara kenan har gaban abada da yardar Allah sai kin ji cewar baki da wata yar'uwa kamar ni a duniyar nan”
Hurriya ta dan yi murmushi ba dan ta yarda ba.
“Amman ina tsoron wani abun da zai saka Appa yayi fushi ko yayi fada, musamman ma ni na batawa Appa rai da yawa idan an sake ban san abun da zai biyo baya ba”
“Hakan ba na fatan ya faru, komai zai zama labari Hurriya, tashi ki shirya da wuri dan bana son mu yi latti”
“Tou”
Ta tashi cikin sanyi jiki ta fice daga falon, ko da ta dawo bangaren Momy mai aikin gyara dakuna ta gyara mata dakinta ta fitar da plate din da ta ci abinci. Tufafinta kawai ta cire ta fada bandaki ta dauki lokaci a bandakin dakin tana Khairy, bata son zafafawa akan negative mind, dan haka take kyautatawa yar'uwarta zato. Ko da fito wanka wani bachi mai dadi ke ziyartarta haka dai ta murje ido ta hana kanta bachin ta shirya cikin ready-made bata damu da daukar jaka ba ganin bata da kudi ko wayar da zata saka a ciki, ta fito tana tafiya a hankali har ta sauko falon. Gaban Momy dake zaune a falon ta fara risinawa ta gaisheta.
“Momy ina kwana?”
“Lafiya kalau”
Ta amsa mata a takaice.
“Zamu fita da Khairy tace na rakata wani gurin”
Nan kam Momy bata ce mata je ko karki je ba, balle ta tambayi inda za su je, a lokacin da Hurriya ta gaji sai ta mike tsaye ta fice daga falon ga bachi ga hawayen da suka cika idonta suna son zubo mata, ba dan komai ba sai dan abin da Momy ta yi mata, ta tabbatar da uwarta ce ba zata bari ta fita ba ba tare da ta tambaye ta me za su je yi ina za su je yaushe za su dawo, ko ma ta hana ta zuwa gaba daya. Amman bata yi ba saboda ita din ba uwarta ba ce
“Na yi marmarinki Amma”
Ta fada tana tsayawa ta kalli bangaren da mahaifinyarta dake zama a da.
“Na yi marmarin rayuwarmu ta baya, a lokacin da kike nan kuma kike cikin koshin lafiya da farinciki, Hamad ma yake nan”
Ta sauke ajiyar zuciya tare da saka hannunsa ta share hawayen da suka zubo mata, sannan ta dauke kai ta shiga bangaren Hajiya Kaltume kamin ta karasa kofar falon Khairy ta bude kofar ta fito da nata shirin tana rike da keys din mota.
“Oh yanzu fa nake cewa zan biya na kiraki na ga kin dade ga garin da hadari”
Hurriya ta daga kai ta kalli sama dake cike da hadari da alama za a iya sako ruwa at any time kuma za a iya yaye hadarin duk cikin ikon Allah ne da abun da ya zo. Ta sauke kai tana hamma.
“Bachi ma nake ji?”
“Bachi yanzu? Ko zaki koma ki kwanta next time sai mu tafi”
“No mu tafi kawai zai sake ni ai”
“Okay”
Suka nufi motar Khairy sai da ta fara shiga ta yi mata key ta juya motar sannan Hurriya ta shiga suka kama hanya. At first Hurriya ta saka ido ne kawai tana sauraren inda Khairy zata kaita duk wani labari da take bata, bata yarda ya dauke mata hankali ba har suka isa gidan dake cike da yan mata suna ganin Khairy suka hau ihu ana rumgume juna irin an dade ba a hadu ba din nan, babu bata lokaci Khairy ta gabatar musu da Hurriya a matsayin kanwarta, Hurriya ta gaishe su sannan ta zauna. Aka kawo abubuwan tabawa ana ci ana hira, ita dai bata yarda ta ci komai ba domin zuciyarta bata natsu da gidan ba, kamar yadda bata gama yarda Khairy ba da sheri take bibiyarta. Tun suna abu tana binsu da kallo har ta kai ta kan yi dariya ko murmushi idan suka fadi wani abun ko suka yi wani abun, daya daga cikin kawayen Khairy ne ta dauko chewing gum ta mikawa kowa ciko har da Hurriya kowa ya karba ya ci, har dayar tana fadar a karo mata daya ba zai isheta ba.
“Zo ki karba idan kina da karfi, daman ke komai aka baki sai kin raina”
“Ni zaki cewa haka kam bala'i”
Suka fara kokawa da juna, Hurriya dai ta yi murmushi sauran kuma suna ta dariya, tana ta kallonsu gwanin burgewa rayuwarsu da alama babu mai wata damuwa a cikinsu sai nishadi suke ba kamar ita ba, tana tunani tana binsu da kallom sai hamma take har bacin ya fara fisgarta tun tana iya daga ido ta kallesu tana jin hayaniyarsu can cikin kamta har bachi ya sace ta gaba daya ta manta da wace duniyar take ma. Bachin da bata farka ba sai La'arsar shi ma kuma Khairy ce ta tashe ta saboda hadarin da ake da iska ruwan zai iya dadewa gashi basa gida.
“Kina ta bachi tashi mu tafi gida an fara ruwa”
Ta mitsintsika idonta kamin ta cire gilashin ta murza idon ta maida.
“Karfe nawa?”
Khairy ta duba agogo hannunta, Hurriya ma ta duba nata sai suka furta a tare.
“4:30pm”
Hurriya ta yunkura da karfi zata tashi sai ta ji jikinta da dan nauyi saboda ta dade kwance gashin kanta ma duk ya sha birjice saboda ta sha murja akan gadon saboda nauyin bachin da ta yi, har zuwa yanzu kuma be gama sakinta ba. Khairy ta mike tsaye tana laka jakarta
“Ya aka yi? Ko zaki ci abinci?”
Hurriya dake mika yana jin kamar ta kara yin bachi ta ce.
“Jikina yayi tsami”
“Taimaka mata ta tashi mana wanda ya dade kwance ai dole zai ji dabam”
Wata kawar Khairy dake daga zaune kan sofa tana kallon Hurriya da Khairy dake gurin bed ta fada. Khairy ta rika Hurriya ta mike tsaye.
“Baki tashe ni na yi sallah ba”
Ta fada har lokacin tana hamma.
“Bachi naki ne ya ga yayi nauyi shiyasa hala baki yi bachi jiya ba?”
“Na yi”
Ta fara takawa tana jin jikinta kamar ba nata saboda nauyin da yayi mata na bachin da ta sha.
“Kowa fa ya wuce mu kadai muka rage, ita wannan yar iskar gidansu ne bata da matsala”
Budurwa da Khairy ta fadawa haka ta mike tsaye tana dariya.
“Dan Allah yaushe zaku dawo?”
“Wa zai dawo nan yanzu kam ai sai dai a hadu a gidansu wata kuma, Hurriya cira kafa kar ruwan yayi karfi sosai da alama fa zai kai magariba ana yi”
“Eh gaskiya, tun dazun fa hadarin nan yake na dauka ma ma da rana za ayi ruwan”
“Eh Wallahi”
Kawar ta rakosu har Balcony, Khairy ta juya ta kalleta.
“Toh mu kam idan Momy ta zo ki ce muna gaisheta”
“Zata ji, Allah ya kiyaye sai mun yi waya”
Ta koma ciki su kuma suka nufi motarsu, Khairy na hadawa da gudu dan kar ruwan ya jikata Hurriya kam ta tsaya tana tafiyarta a hankali, wata zuciyar na raya abun da be zo mata a rai ba sai yanzu, why take ta jin bachi bayan kuma ita ta san jiya ta yi bachi ko da ma ace bata yi ba chi ba ai be kamata ta rika irin wannan mashalon da nauyin bachin just because of bata ta yi bachi ba na rana daya, balle ma ta yi. Kamin ta shiga motar ta raya ma zuciyarta cewar ba zata sake yarda ta sake raka Khairy wani gurin ba, domin idan wani abun be faru a yau ba, zai iya faruwa wata rana, kuma ta fi kyautata zaton wata kila kwaya ta saka mata ta yi bachi, waya sani ma ko so take ta koya mata shan wani abu, daman ana kishen kishen tana sha kuma ta lura da hakan domin ta ga tarin mutanen da ta tara a birthday ta babu na kwarai, gashi kuma Adam din da ya nuna yana sonta shi ma yana shan shisha.
A ranta take ta sake sake bayan ta daukarwa kanta alkawarin ba zata sake rakata ko'ina ba ko da kuwa ta yi mata magijiya haka kuma ba zata sake cin wani abu da zata janyota ta ci su ci ba, ko da kuwa yunwa zata kasheta, domin mutum ba zai ƙi ka da da maraice da dare ya ce yana kaunarka ba, idan bata da masu mata fada su nuna mata mata daidai da kuskure, ya takama ta fadawa kanta.
“Kina bachi wata kawarmu ta zo na so kin ganta”
Khairy na tuki tana bata labarin abubuwan da suka faru kuma tana tambayarta wai bata ji lokacin da aka yi kaza da kaza ba.
“Ban ji ba, na yi bachi ne sosai”
“Ai na ga alama kam, shiyasa na ce ki koma ki kwanta baki yarda ba, Allah yasa jibi idan zamu fita kar ki yi irin haka, dan Allah ki rika yin bachin dare Hurriya ki daina sakawa kanki damuwa ta hana ki bachi, na san ba zai wuce tunanin Amma ba ko Appa, Amma zata samu sauki da yardar Allah”
“Amin”
Hurriya ta amsa a takaice, hakan ya saka Khairy ta kalleta jin ta katse mata magana ba tare da ta kare ba, kuma ta amsa da Amin. Sai kuma ta dauke kai ta cigana ta tukin ba, bata sake cewa wani abu ba har suka isa gida by that time ruwan yayi karfi sosai. A gaban gate din Momy Khairy ta faka Hurriya ta bude ta fita ta rufe mata motar sannan ta yi baya kadan ta nufo gate dinsu. Da tafiyar da ta fi kama da kasaita ko kuma ace tausayin kasa Hurriya ta rika takawa ruwan saman dake sauka da karfi suka ce me suke jira da ita ba su jikata ba. Tun da ta hango mota fake a harabar dake kusa kusa da Entrance din Momy ta san suna bako ko bakuwa a gidan domin ba motar da ta sani ba ce. Tana isa daf da motar aka bude farar motar mai farin gilashi Captain ya fito rike da System dake cikin jakarta da wasu takardu, da kuma wata yar jakar karama a hannunsa, shi kan da gudu ya rufe motar ya haye Entrance din. Gudun kar ta isa gurin Momy ko Namra su zo bude masa kofa su disgata gabanshi ya saka ta sauya hanya ta nufi hanyar da zata kai ta bayan dakunan bangaren na Momy. Sai da ta kusa shigewa sannan Captain ya juya ya bita da kallo yana kai hannunsa yayi knocking din kofar falon, ya hada da taba bell. Mai aikin Momy ce ta bude kofar tana zaton ma ko Hurriya ce ta dawo domin sun san bata gidan.
“Sannu
Showing 81001 words to 84000 words out of 215510 words
Kamin Captain yace wani daman kuma ba shi da niyar fadar wani abu akan maganar. Hurriya ta turo kofa ta shigo falonta ta kofar da ake shigowa, bayan ta bata lokaci a Garden ta wanke hannunta a fanfo da fuskarta. Gaba dayansu dubansu ya koma kanta, tana isowa tsakiyar falon ta kalli Momy sai kuma ta yi saurin kauke kai kasa ta nufi hanyar stairs.
“Ke zo ki dauki abincin nan idan zaki ci”
Captain ya fada in a game way, yana binta da kallo, ita ma juyowa ta yi ta kalleshi kamin ta kalli Momy dake kallonta.
“Zo ki dauka mana”
Ya saka fada ganin tana jiran umarnin Momy, Namra ta yi karaf ta ce.
“Domin ku fa aka yi?”
“To ai shi ya tafi be ci ba, kuma ni ma a koshe nake maybe next time”
Hurriya na jin haka ta dawo ta duka a gurin ta dauki plate ta zuba rice din sai karamin bowl ta zuba miyar sai da tsame rabin naman kazar dake ciki miyar sannan ta dauki cup ta zuba fresh apple juice da Namra ta hada ta dauki wani plate din ta zuba plantain duk abun da ta zuba wanda ta san zai isheta ne har anjima, sannan ta dauka ta mike tsaye.
“Na gode”
Ta furta with sweet voice dinta tana musa laɓɓanta masu kyau. Sannan ta nufi stairs sai da ta kusa haye sannan ta juyo ta kalleshi ta juya ta cigaba da tafiyarta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/25, 5:23 AM] AMINA KABIR CAPS: *KHADIJA CANDY*
*PAGE2️⃣5️⃣*
“Baka dai ci abincin ba”
Ya kalli Momy yana saka hananyensa aljihu.
“Abokina ya tafi ransa a bace, taya zan zauna ni na ci abinci? Maybe next”
Ya kalli Namra dake tsaye ya kira sunanta. ”Namra”
“Hmmm”
“Be a good girl please”
Ta yi murmushi mai kyau.
“I will as always”
Ya mayar mata da murmushi sannan ya juya ya nufi kofa, da kansa ya bude ya fita Momy ta take masa baya ita da yarta. Momy na nade hannayenta ta aika masa tambaya.
“Sai yaushe kuma Captain”
“Anytime kina iya ganina ma anjima, ai yanzu ina garin nan har na tsawon wata uku kuma ina tunanin wannan ne best place da zan iya zuwa na yi yadda nake so, ba kamar a bariki ba”
“Me yasa ba zaka dawo nan gaba daya ba?”
“Ban sani ba ko za a su bar ni zan gwada haka”
Ya bude motarsa bayan ya amsawa Namra sannan ya shiga yayi mata key, Momy na daga masa hannu Namra kuma ta bishi da kallo da murmushi har ya fice. Momy ta juyo ta kalleta.
“Wata kila ya jidadin yadda kika karbi bakonsa a yau”
“Ni ma na ga alama”
“Yayi kyau”
Momy ta fada tana murmushi sannan ta sauke kai kasa ta juyo cikin tafiyar kasaita ta shiga falonta. Namra ta dade a gurin tana ta karatun wasikar jaki kamin ita ma ta juya ta koma ciki. Hurriya ta ci abincinta yadda take so, sauran ta saka dayan plate din ta rufe domin idan ta tashi ci anjima ba ta nema ba, kusan ita da marainiya duk daya agidan, wata kila ma marainiya ta fita gata da samun kulawa. Hakan ya taimaka mata bata fito neman abincin dare, shimkafar ta sake ci da dare ta kwanta abunta. Da safe ma bata fito gudun kar ta yi wani laifin ko kuma Momy ta rufe ta fada saboda ta zuba abinci da yawa ta kwashe nama, tana zaune a dakin har karfe goma na safe, tana unkurin tashi ta yi wanka aka turo kofar falon aka shiga, da sauri ta kalli kofar tana zaton ganin Momy ko Namra ga mamaki sai ta yi arba da Khairy.
“Yaya Khairy”
“Na'am Hurriya yanzu kika tashi?”
“Tun dazun amman ban sauko ba sai yanzu”
“Kin yi breakfast?”
“Aa”
“Ni ma ban karya ba, zo muje mu karya bangarenmu, idan mun gama ina son ki rakani wani gurin kin ji”
Ta dan yi shiru kamar mai tunanin yadda zata amsa mata kamin ta daga mata kai.
“Okay”
Ita kam gaba da ta kai ta ko ba komai zata karya, ba kamar jiya ba, already ta san Momy ko masu aikinta za su ce mata abincin safe ya kare kamar jiya, gashi kuma bata isa ta ce zata shiga kitchen ta girka ba ko ta saka a girka mata. Dan haka ta sauko saman gadon suka fice a dakin tare da Khairy, kamin su isa bangaren Hajiya Kaltume Khairy ta kama hannunta ta rike tana bata labarin guraren da za su da kawayenta da ta kwana biyu bata hadu da su ba. A dinning suka zauna ita Khairy da kanta ta hadawa Hurriya tea ta zuba mata komai na karyawa. Hurriya na tauna wainar kwai zuciyarta na raya mata akwai abun da Khairy take shirya mata, domin a iya saninta Khairy bata tana sonta ba ko na rana daya, idan ma kowa zai raga mata a gidan ban da Khairy amman me yasa take nuna mata kulawa tana janta a jiki yanzu? Anya ba wani abu take shirya mata ba? Ta mike tsaye sai Khairy ta kalleta da sauri.
“Ya aka yi baki sha tea ba fa?”
“Ruwa zan dauko a kitchen”
“Zauna bari na dauko miki”
Ta mike tsaye, Hurriya kuma ta koma ta zauna tana kallonta, Khairy na shiga kitchen ta dauko ruwan da cup ta fito, sai mamaki ya kara rafe Hurriya. Haka dai ta karya ba dan zuciyarta natsu da yadda Khairy take mata ba.
“Yaya Khairy saboda Adam ne?”
Khairy ta kalleta
“Ban gane ba?”
“Kike min haka kuma kike son na rakaki mu fita”
“Haba Hurriya Adam din da Appa yace kar ya sake ganinki da shi, kuma yaya ma yayi gargadi akan haka, shi ne zan hadaku? Na rantse miki da Allah indai ni ce ba zaki taba ganin na kawo miki Adam da idonki biyu ba, haba Hurriya kawai ina kokarin ganin na kyautata miki ne, ni yar'uwarki ce be kamata ace muna samun tsabani ba, kin ga yanzu ni aure zan yi, duk kuwa da ba a saka rana ba, amman ban san ya rayuwata zata zama a gidan auren ba, kuma hausawa suna cewa idan kana son gani da kyau to ka aikata mai kyau, and trust me daga yanzu an fara kenan har gaban abada da yardar Allah sai kin ji cewar baki da wata yar'uwa kamar ni a duniyar nan”
Hurriya ta dan yi murmushi ba dan ta yarda ba.
“Amman ina tsoron wani abun da zai saka Appa yayi fushi ko yayi fada, musamman ma ni na batawa Appa rai da yawa idan an sake ban san abun da zai biyo baya ba”
“Hakan ba na fatan ya faru, komai zai zama labari Hurriya, tashi ki shirya da wuri dan bana son mu yi latti”
“Tou”
Ta tashi cikin sanyi jiki ta fice daga falon, ko da ta dawo bangaren Momy mai aikin gyara dakuna ta gyara mata dakinta ta fitar da plate din da ta ci abinci. Tufafinta kawai ta cire ta fada bandaki ta dauki lokaci a bandakin dakin tana Khairy, bata son zafafawa akan negative mind, dan haka take kyautatawa yar'uwarta zato. Ko da fito wanka wani bachi mai dadi ke ziyartarta haka dai ta murje ido ta hana kanta bachin ta shirya cikin ready-made bata damu da daukar jaka ba ganin bata da kudi ko wayar da zata saka a ciki, ta fito tana tafiya a hankali har ta sauko falon. Gaban Momy dake zaune a falon ta fara risinawa ta gaisheta.
“Momy ina kwana?”
“Lafiya kalau”
Ta amsa mata a takaice.
“Zamu fita da Khairy tace na rakata wani gurin”
Nan kam Momy bata ce mata je ko karki je ba, balle ta tambayi inda za su je, a lokacin da Hurriya ta gaji sai ta mike tsaye ta fice daga falon ga bachi ga hawayen da suka cika idonta suna son zubo mata, ba dan komai ba sai dan abin da Momy ta yi mata, ta tabbatar da uwarta ce ba zata bari ta fita ba ba tare da ta tambaye ta me za su je yi ina za su je yaushe za su dawo, ko ma ta hana ta zuwa gaba daya. Amman bata yi ba saboda ita din ba uwarta ba ce
“Na yi marmarinki Amma”
Ta fada tana tsayawa ta kalli bangaren da mahaifinyarta dake zama a da.
“Na yi marmarin rayuwarmu ta baya, a lokacin da kike nan kuma kike cikin koshin lafiya da farinciki, Hamad ma yake nan”
Ta sauke ajiyar zuciya tare da saka hannunsa ta share hawayen da suka zubo mata, sannan ta dauke kai ta shiga bangaren Hajiya Kaltume kamin ta karasa kofar falon Khairy ta bude kofar ta fito da nata shirin tana rike da keys din mota.
“Oh yanzu fa nake cewa zan biya na kiraki na ga kin dade ga garin da hadari”
Hurriya ta daga kai ta kalli sama dake cike da hadari da alama za a iya sako ruwa at any time kuma za a iya yaye hadarin duk cikin ikon Allah ne da abun da ya zo. Ta sauke kai tana hamma.
“Bachi ma nake ji?”
“Bachi yanzu? Ko zaki koma ki kwanta next time sai mu tafi”
“No mu tafi kawai zai sake ni ai”
“Okay”
Suka nufi motar Khairy sai da ta fara shiga ta yi mata key ta juya motar sannan Hurriya ta shiga suka kama hanya. At first Hurriya ta saka ido ne kawai tana sauraren inda Khairy zata kaita duk wani labari da take bata, bata yarda ya dauke mata hankali ba har suka isa gidan dake cike da yan mata suna ganin Khairy suka hau ihu ana rumgume juna irin an dade ba a hadu ba din nan, babu bata lokaci Khairy ta gabatar musu da Hurriya a matsayin kanwarta, Hurriya ta gaishe su sannan ta zauna. Aka kawo abubuwan tabawa ana ci ana hira, ita dai bata yarda ta ci komai ba domin zuciyarta bata natsu da gidan ba, kamar yadda bata gama yarda Khairy ba da sheri take bibiyarta. Tun suna abu tana binsu da kallo har ta kai ta kan yi dariya ko murmushi idan suka fadi wani abun ko suka yi wani abun, daya daga cikin kawayen Khairy ne ta dauko chewing gum ta mikawa kowa ciko har da Hurriya kowa ya karba ya ci, har dayar tana fadar a karo mata daya ba zai isheta ba.
“Zo ki karba idan kina da karfi, daman ke komai aka baki sai kin raina”
“Ni zaki cewa haka kam bala'i”
Suka fara kokawa da juna, Hurriya dai ta yi murmushi sauran kuma suna ta dariya, tana ta kallonsu gwanin burgewa rayuwarsu da alama babu mai wata damuwa a cikinsu sai nishadi suke ba kamar ita ba, tana tunani tana binsu da kallom sai hamma take har bacin ya fara fisgarta tun tana iya daga ido ta kallesu tana jin hayaniyarsu can cikin kamta har bachi ya sace ta gaba daya ta manta da wace duniyar take ma. Bachin da bata farka ba sai La'arsar shi ma kuma Khairy ce ta tashe ta saboda hadarin da ake da iska ruwan zai iya dadewa gashi basa gida.
“Kina ta bachi tashi mu tafi gida an fara ruwa”
Ta mitsintsika idonta kamin ta cire gilashin ta murza idon ta maida.
“Karfe nawa?”
Khairy ta duba agogo hannunta, Hurriya ma ta duba nata sai suka furta a tare.
“4:30pm”
Hurriya ta yunkura da karfi zata tashi sai ta ji jikinta da dan nauyi saboda ta dade kwance gashin kanta ma duk ya sha birjice saboda ta sha murja akan gadon saboda nauyin bachin da ta yi, har zuwa yanzu kuma be gama sakinta ba. Khairy ta mike tsaye tana laka jakarta
“Ya aka yi? Ko zaki ci abinci?”
Hurriya dake mika yana jin kamar ta kara yin bachi ta ce.
“Jikina yayi tsami”
“Taimaka mata ta tashi mana wanda ya dade kwance ai dole zai ji dabam”
Wata kawar Khairy dake daga zaune kan sofa tana kallon Hurriya da Khairy dake gurin bed ta fada. Khairy ta rika Hurriya ta mike tsaye.
“Baki tashe ni na yi sallah ba”
Ta fada har lokacin tana hamma.
“Bachi naki ne ya ga yayi nauyi shiyasa hala baki yi bachi jiya ba?”
“Na yi”
Ta fara takawa tana jin jikinta kamar ba nata saboda nauyin da yayi mata na bachin da ta sha.
“Kowa fa ya wuce mu kadai muka rage, ita wannan yar iskar gidansu ne bata da matsala”
Budurwa da Khairy ta fadawa haka ta mike tsaye tana dariya.
“Dan Allah yaushe zaku dawo?”
“Wa zai dawo nan yanzu kam ai sai dai a hadu a gidansu wata kuma, Hurriya cira kafa kar ruwan yayi karfi sosai da alama fa zai kai magariba ana yi”
“Eh gaskiya, tun dazun fa hadarin nan yake na dauka ma ma da rana za ayi ruwan”
“Eh Wallahi”
Kawar ta rakosu har Balcony, Khairy ta juya ta kalleta.
“Toh mu kam idan Momy ta zo ki ce muna gaisheta”
“Zata ji, Allah ya kiyaye sai mun yi waya”
Ta koma ciki su kuma suka nufi motarsu, Khairy na hadawa da gudu dan kar ruwan ya jikata Hurriya kam ta tsaya tana tafiyarta a hankali, wata zuciyar na raya abun da be zo mata a rai ba sai yanzu, why take ta jin bachi bayan kuma ita ta san jiya ta yi bachi ko da ma ace bata yi ba chi ba ai be kamata ta rika irin wannan mashalon da nauyin bachin just because of bata ta yi bachi ba na rana daya, balle ma ta yi. Kamin ta shiga motar ta raya ma zuciyarta cewar ba zata sake yarda ta sake raka Khairy wani gurin ba, domin idan wani abun be faru a yau ba, zai iya faruwa wata rana, kuma ta fi kyautata zaton wata kila kwaya ta saka mata ta yi bachi, waya sani ma ko so take ta koya mata shan wani abu, daman ana kishen kishen tana sha kuma ta lura da hakan domin ta ga tarin mutanen da ta tara a birthday ta babu na kwarai, gashi kuma Adam din da ya nuna yana sonta shi ma yana shan shisha.
A ranta take ta sake sake bayan ta daukarwa kanta alkawarin ba zata sake rakata ko'ina ba ko da kuwa ta yi mata magijiya haka kuma ba zata sake cin wani abu da zata janyota ta ci su ci ba, ko da kuwa yunwa zata kasheta, domin mutum ba zai ƙi ka da da maraice da dare ya ce yana kaunarka ba, idan bata da masu mata fada su nuna mata mata daidai da kuskure, ya takama ta fadawa kanta.
“Kina bachi wata kawarmu ta zo na so kin ganta”
Khairy na tuki tana bata labarin abubuwan da suka faru kuma tana tambayarta wai bata ji lokacin da aka yi kaza da kaza ba.
“Ban ji ba, na yi bachi ne sosai”
“Ai na ga alama kam, shiyasa na ce ki koma ki kwanta baki yarda ba, Allah yasa jibi idan zamu fita kar ki yi irin haka, dan Allah ki rika yin bachin dare Hurriya ki daina sakawa kanki damuwa ta hana ki bachi, na san ba zai wuce tunanin Amma ba ko Appa, Amma zata samu sauki da yardar Allah”
“Amin”
Hurriya ta amsa a takaice, hakan ya saka Khairy ta kalleta jin ta katse mata magana ba tare da ta kare ba, kuma ta amsa da Amin. Sai kuma ta dauke kai ta cigana ta tukin ba, bata sake cewa wani abu ba har suka isa gida by that time ruwan yayi karfi sosai. A gaban gate din Momy Khairy ta faka Hurriya ta bude ta fita ta rufe mata motar sannan ta yi baya kadan ta nufo gate dinsu. Da tafiyar da ta fi kama da kasaita ko kuma ace tausayin kasa Hurriya ta rika takawa ruwan saman dake sauka da karfi suka ce me suke jira da ita ba su jikata ba. Tun da ta hango mota fake a harabar dake kusa kusa da Entrance din Momy ta san suna bako ko bakuwa a gidan domin ba motar da ta sani ba ce. Tana isa daf da motar aka bude farar motar mai farin gilashi Captain ya fito rike da System dake cikin jakarta da wasu takardu, da kuma wata yar jakar karama a hannunsa, shi kan da gudu ya rufe motar ya haye Entrance din. Gudun kar ta isa gurin Momy ko Namra su zo bude masa kofa su disgata gabanshi ya saka ta sauya hanya ta nufi hanyar da zata kai ta bayan dakunan bangaren na Momy. Sai da ta kusa shigewa sannan Captain ya juya ya bita da kallo yana kai hannunsa yayi knocking din kofar falon, ya hada da taba bell. Mai aikin Momy ce ta bude kofar tana zaton ma ko Hurriya ce ta dawo domin sun san bata gidan.
“Sannu
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28 Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72