da Daddy yake sauka dabam idan ya zo gidan. Fitarta da minti biyu Captain ya shigo falon, a kasa ya zauna ya gaishe da iyayensa.
“Ya karfin jikin Captain”
“Alhamdulillah daman stress me kawai Abba na ji sauki”
Ya amsawa Alhaji Munzali, kamin ya daga kansa yana kallon dinkakkiyar Shaddar dake Ikilima take mika masa, ya saka hannu biyu ya karba.
“Shiga ka yi wanka ka saka wannan shaddar ka feshe turaren nan gaba daya a jikinka”
“Daddy why?”
Ya tambaya da confused.
“Ina son ka raka ni airport ne kuma ina son mutane su ga yarona cikin mutunci, kuma karka dade ka fito yanzu nan ina jiranka”
“Toh Daddy”
Captain ya mike tsaye ya fice daga falon na Nene. Dakin da ya zama masaukinsa ya shiga ya cire tufafin jikinsa yayi wanka ya fito ya shafa mai ya saka shaddar ya dauko turaren ya feshe jikinsa gaba daya sai da kwalbar turaren ta kai kasa sannan ya dauki hula ya saka a kasan shi kansa, ya dubi kansa a jikin madubi shi kanshi ya san yayi kyau abun da ake kira da kyau, farar shaddar ta haske shi matuka... Wayarsa ya dauka ya saka aljihu da wallet dinsa sannan ya nufi kofar dakin ta bude ya fita yana wani irin kamshi mai sanar da zuwansa tun kamin ya iso. Ga mamakinsa sai ya samu babban falon na kakarsa a cike da mutane ciko har da mahaifiyarsa da kakarsa da abokiyar zamanta da duka wanda yake gidan a lokacin. Da mamaki ya sauko falon yana kallon kowa kowa kuma yana kallonsa...
“Zo nan Jamal...”
Daddy ya fada yana murmushi, Captain ya nufi gurinsa sai Daddy ya mike tsaye ya saka hannunsa aljihu ya ciro goro da dabino ya ce.
“Bude min hannunka... ”
Captain ya bude tafin hannunsa na dama ya mikawa Daddy, sai Daddy ya zuba masa dabino da goro dake hannunsa.
“Mun je jaje, kuma mun roki iri, kuma an ba mu, na nema maka auren Hurriya a yau, kuma an daura mun bada zinari na miliyan 50, a matsayin sadakinta, saboda dka fada mana mai tsada ce, shiyasa muka siye ta da kima, yau mai tsada ta zama mallakinka, Hurriya ta zama matarka halak malak...”
Kamar an aje hoto haka falon yayi tsit kamar babu wani abu mai rai a ciki, daga Captain har iyayensa babu mai motsi....
MASU KARATU BA BIYA A ZO A BIYANI HAKKINA A SAUKE NAUYI A HUTA
500 to Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[12/18/2023, 2:14 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURRIYA*
4️⃣3️⃣
Hajiya Binta ya jinjina kai tana kara girmama labarin Allah, a duk lokacin da ake son mutun ya kunyata idan Allah yana tare da bawa ba a taba ganin abun da ake bukata, kariyace da sakamako mai kyau tare da kyau da kariya mai yawa daga Allah zuwa ga bayinsa da suka rike shi kuma suka dogara a gareshi.
“Duk wanda ya aikata wannan abun ya aikata ne saboda ya ci mutuncin Hurriya ya ci namu, ashe be sani ba yana kara kusance da mata da alheri ne”
Appa yayi murmushi a yayin da yake zaune a kasa rike da sarka ya kalli Yasir dake gefensa ya mika masa sarka.
“Budewa Hajiya ta gani”
Yasir ya karba ya mike tsaye ya bude mata sarka, Hajiya Binta ta saka hannu ta karba idonta na cika da hawaye.
“Allah na gode maka da ka nuna min wannan ranar, Allah ka sakawa wannan auren Albarka, kuma ka nuna min na sauran yaran”
“Amin Hajiya Amin”
Appa ya amsa da kansa, fadar irin farinciki da yake ciki a yanzu bata lokaci ne, farinciki da yake a yanzu ya fi wanda ya samu kansa a lokacin da aka haifo masa ita.
“Be kamata mu zauna ba Tsoho tafiya zamu yi mu sanar gidan mahaifiyarta da kuma ita yarinyar halin da ake ciki”
“Haka ne... ”
A nan kam sai yanayin Appa ya canja, ya sauke kai kasa damuwa na bayyana a fuskarsa. Yasir ya aje sarkar zinarin dake hannunsa ya mike tsaye ya fice daga dakin yana taba wayarsa. Appa ya bishi da kallo har ya fice sannan ya juyo da kansa ta inda Hajiya Binta take zaune ya ce.
“Ina jin kunyar hada ido da mahaifiyar yarinyar Hajiya, abun da na yi mata ban kyau ba, be kamata na aikata hakan ba, ban san me yasa na sake ta ba, kuma na kasa samun dalilin har yanzu da muke maganar nan dake, Iyami bata min komai ba face biyayya da kyautatawa, amman na saka mata da mafi munin sakamako na juya mata baya na wulakanta yaran da ta haifa min”
Ya shigar da lips dinsa duka biyu a bakinsa ya rufe dantse bakin zuciyarsa na ƙuna da abun da bakinsa yake furtawa.
“Alhamdulillah, ganin ka gane kuskure ni a gurina abun farinciki ne, babu daren da bana addu'ar Allah ya baka ikon gane gaskiya, domin abun da ka aikata kamar baka aikata shi cikin hayyacinka ba”
“Ban san me ya rufe min ido na aikata haka ba, ina jin nauyin iyayenta da ita kanta Iyamin a yanzu”
“Ka kawar da komai a ranka, daman shi aure ya gaji haka, a tsaba kuma a shirya ko a yanzu dare be maka ba, lokaci be kure ba zaka iya gyara inda ka yi kuskure ka share inda ka bata, kar wannan jin nauyin ya hanaka sanar da yarka Hurriya cewar ka bada aurenta a yau, kai da kanka nake son ka fada mata wannan”
Ya amsa mata da kai sannan ya mike tsaye yana hade rigarsa.
“Zamu jiraki a waje Hajiya sai ki shirya mu tafi”
“Toh...”
A waje suka jira Hajiya ta fito tana rike da sadakin jikarta, ta shiga baya Appa da Yasir kuma suka shiga gaba. A motar Hajiya sai godiya take yi ma Allah na yadda ya kawo auren Hurriya a kusa kuma da mutumen da ba ayi tsammani ba, Appa kuma fargaba da kunya na lullube shi a yayin da Yasir yake kara kusanta gidansu Gwaggo.
“Ni na manta ban tambaya ba, yaron dai yana da kirki ko? Murna da farinciki sun mantar da ni wannan”
“Ba shi matsala Hajiya na san shi, yana da kirki kuma babu wanda zai fadi sherinsa, Hurriya ta yi dacen miji fatan mu dai Allah ya bata lafiya kuma ya basu zaman lafiya”
Hajiya Binta farinciki sai ya kara ninkuwa, ta kara yi ma Allah godiya.
HURRIYA POV.
“Wannan jaraba da kuke ta fadawa Allah ya yaye muku, idan wannan ya wuce sai kuma wani ya zo, ke kin tashi baki ya bude ita kuma ido ya rufe”
Gwaggo ta kalli Hindu wanda ke kallon Hurriya tana lalaben gini har ta iso gurin da Amma take zaune tare da Gwaggo da kawar Amma wato Hindu ta zauna.
“Abun da Allah yayi annabi sai ceto, likitocin sun ce wai damuwarce ta taba mata ido, amman ni ban yarda ba na fi zaton wani aikin ne aka yi mata idon ya rufe gaba daya, gashi an yada hotunanta kin ga shikenan an gama da rayuwarta, ba ido balle ta yi karatu ta gina kanta kuma babu wanda zai aureta a haka”
Hindu ta rafka uban tagumi.
“Oh Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, wannan mugun kishi da me yayi kama? To ko ita ma za mu nema mata taimakon a gurin da aka nemawa Amma? Tun da gashi dai mun fara ganin haske”
Amma ta kama Hurriya ta kwantar da ita a cinyarta hawaye na sauko mata.
“Mun dai ga haske Hindu, Wallahi ban dauka zan iya kara yin magana ba, na dauka kalmaina sun kare a duniyar nan, ina kallon abu na zan iya cewa a bani ba, ina da maganganu da yawa a bakina amman ba zan iya furta ko daya ba, bana iya motsa jiki bana iya komai, amman ki duba yanzu magana fa nake yi, bana jin karfi a jikina sosai amman Alhamdulillah na gode Allah”
“Shi ma duk zai bari da yardar Allah, lafiya daman da rarafe take shiga a jiki har a tashi tsaye, ciwo ne yake jefar da mutum farat daya”
Cewar Hindu. Kamin su daga kansu gaba daya su kalli kofar gidan, Hajiya Binta ce ta shigo Appa yana bayanta sai Yasir a bayan Appa.
“Sallamu Alaikum”
Gwaggo da Hindu suka amsa mata, Amma kuma ta sauke kai kasa tana nadamar kallon Appa da ta yi kamar wanda ta yi arba da bakin maciji.
“Maa Shaa Allahu, Iyami ce a waje? Haka nake so lafiya ta samu”
“Alhamdulillah, Rukkaya dauko tabarma ki kawo ma baki”
Gwaggo ta amsa tana bawa Rukkaya umarni. Appa ya kasa daga ido ya kalli kowa kamar wanda ya aikata abun kunya. Rukkaya ta fito rike da tabarmar ta shimfida kusa da wanda Amma take zaune. Hajiya ta fara zaunawa sannan Appa Yasir, daman haka tarbiyar take, sai iyayen sun fara zama ake zama, idan kuma suna zaune ba ka tsaya a kansu ba sai dai rankwafa ko na zauna a kasa.
“Jama'a ina kwananku ko wuni zan ce domin dai yanzu ai 12pm ta yi”
“Lafiya Kalau Hajiya ya gidan”
Gwaggo ta amsa ba yabo ba fallasa. Appa ma ya mikawa Gwaggo gaisuwa, ba dan yana a gaban Hajiya Binta ba da kuma tunanin dalilin zuwansa wata kila da ba zata amsa gaisuwar Appa ba.
“Lafiya Kalau”
Amma ta daga kai ta kalli Rukayya dake zaune ta ce.
“Dauko min hijabina Rukayya”
A rude Appa ya dago kai ya kalli Amma, Hajiya Binta ma ta kalleta Yasir ma kallonta, dukansu sun yi turus suna mamakin jin furuci ya fito daga bakinta.
“Iyami kina iya magana yanzu?”
“Allah ya nufa Hajiya”
Amma ta guntun murmushi tana amsawa Hajiya Binta dake rike da baki.
“Allah da iko kake, kai Alhamdulillah yau farinciki ya mana yawa”
“Amma....”
Yasir ya kirata sai ta kalleshi ta yi murmushi ta amsa.
“Na'am Yasir”
“Alhamdulillahi”
Wannan karon Appa ne ya jaddada godiyarsa ga Allah yana kallon Amma, irin kallon da ya dauki shekaru be yi mata ba, nadama da damuwa bayyane a fuskarsa karara. Rukkayya ta kawo Hijab ta mikawa Amma, sai Amman ta karba ta saka domin tana ganin Appa da Yasir ba muharramanta ba ne a yanzu.
“Hurriya ta so mahaifinki na son magana da ke”
Hurriya ta amsa kiran da Hajiya Binta ta yi mata ta tashi zaune, sai ta lalaba ta matsa gurin da Hajiya take ta zauna, Appa ya kai hannayensa ya kama nata hannayen ya juyo da ita ta fuskance sai ta nade kafafuwanta irin zaman da musulunci ya koya mana yayin da zamu ci abinci, wato ta nade kafafuwanta tana fuskantar mahaifinta.
A lokacin da Appa ya kalli yarsa sai tausayinta da kaunarta da kuma kunyarta a lokaci daya mamayeshi. Ya sauke ajiyar zuciya sau uku sai a hudu ya samu damar hada kalmomin da zai gamsar da yarsa da su ya hada guri daya ya fara magana.
“Hurriya na san kin san cewar ni mahaifinki ne, a cikin abubuwan da Allah ya dora min nauyinsu akwai ciyar da ke da shayar da ke da tufatar da ke da halak, idan kuma kin kai munzali Annabi yace na zaba miki mijin na kwarai wanda na yarda da addinsa da dabi'arsa kuma mai abun yi. Ban sani ba ko na kokarta a tarbiyarki, wata kila na yi jarumta a ciyar da ke da tufatarwa, ba zan gane hakan ba sai ranar alkiyama, a cikin kokarin sauke nauyin da Allah ya dora min, na aiwatar da wani a yau. Yake ƴata yau kina zaune a gabana ne a matsayin matar wani, wanda cin ki da sha da tufatarwarki za su koma a kansa, a yau kin shiga sahun manyan mata, a yau kin tashi daga budurwar kin zama matar aure, daga yau ladarki zata riɓanyya har zuwa lokacin da za ki bar duniya, neman aljannarki a yau ya sauka daga kan kafata ya koma karkashin kafar mijinki.... A yau na aurar da ke Hurriya...”
Ta daga kanta ta kalli gurin da take kyautata zaton fuskar Appa take, bata iya ganin komai saboda rashin masoya biyu, wato idanuwa, amman a haka zuciyarta take ayyana mata yadda fuskar mahaifinta take. Bata ganin komai sai duhu, sai dai makanta bata hana idanuwanta suke zubar da hawayen da tun da Appa ya fara magana suke mata zuba. Appa ya dauki sarkar dake gaban Hajiya Binta ya dora a cinyoyin Hurriya.
“Wannan sadakinki ne... An umarci iyaye su bawa yarinya sadakinta domin nata ne... Wannan naki ne Hurriya...”
Hurriya ta kasa cewa komai bata jin komai sai _A yau na aurar da ke Hurriya_ haka kalmar ta yi ta maimaita kanta a kunnenta kwakwalwarta na juya kalamin.
“Aure....”
Amma ta tambaya domin Mamaki ya hana Gwaggo cewa komai.
“Hajiya ban fahimta ba, wane irin aure kuma? ”
“Ki kwantar da hankalinki zaki fahimta”
“Ban gane na kwantar da hankalina ba, taya zai shigo cikin gidanmu kai tsaye ya fada mana ya aurar da Hurriya? Saboda ya mayar da mu talakawa? Ni ba ni da hakki akan Hurriya kenan? Wane irin magana ne wannan?”
“Kin fini hakki akanta Iyami, Annabi ya ambaci uwa sau uku sannan ya ambaci Uba... Ban aurar da ita yau saboda na wulakanta ki ba, ban aikata hakan da wata manufa ba sai dan ina ganin hakan ne abun da ya cancanci ko wane uba na gari aikata, na aurar da ita ne a inda nake kyautata zaton za mutunta a rike ta amana, Iyami ki yi hakuri tabbas na yi kuskure ban nemi shawararki ba na aurar da Hurriya”
“Wa ka aurawa ita? Saboda abun kunyar da ya faru ne ka yanke shawarar aikata haka?”
Gwaggo ta tambaya a fusace. Appa ya tausasa murya ya ce.
“Aa Wallahi su suka zo neman aurenta da kansu, sunan yaron Jamal da ne ga Nafisa, dan wajen Alhaji Aliyu Turaki...”
Hawaye ya subucewa Amma.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, me ya sa zaka aurar min da ya a inda ba a san darajar mutane ba? Macen da bata son hada hanya da talaka? Zaka dauki Hurriya ka jefa a cikin danginta? Yarinya karama ta kafa fuskantar irin bala'in da na fuskanta a gidanka, da na san haka rayuwa zata zama gaba daya Wallahi da ban aureka ba, amman kaddara ta yi min zanen da ban isa na goge ba”
“Subhanallahi Subhanallahi Subhanallahi”
Appa ya maimaita har sau uku sannan ya ce.
“Na san ban kyauta miki ba Iyami, amman ki tausasa ko dan yaran nan”
Amma ta masa wani kallo na takaici da bakinciki.
“Yara? Wadannan twins din da aka haifa ka kasa zuwa ka tara hannu ka karba? Ko kuma ďan da aka kama ka ce ba zaka bada kudin fansar sa ba! Sai da na hada komai da na mallaka na bada, sannan Hajiya Kaltume ta baka umarnin biya? Ko kuma Hurriyar da ka juyawa baya?”
Appa ya kasa amsawa ya sauke kansa kasa yana mai jin kunya da nauyin abun da ya aikata.
“Bari na fada maka da bakina ka ji, yata bata auru ba, ba zan bada ita a inda za a wulakanta ta ba, abun kunyar da aka yi mata kazafin aikatawa ni zan iya rumgumarsa”
Ba tare da Appa ya dago kai ba ya ce.
“Iyami karki furta kalami cikin fushi”
“Irin kalamin da ka furta a lokacin da na ke cikin gidanka da cikin yayanka? Irin zuwan da iyayena suka yi ka wulakanta su? Yata ba zata je ko'ina ba Haruna.... Ban amince da wannan auren ba...”
Hajiya Binta ta ce.
“Adai hakuri Iyami a daina tuna baya, a bar baya ta wuce”
“Haka ne Hajiya, da dan yaran nan ba da be isa ya shigo cikin gidan nan ya zauna a nan yana magana da ni ba”
Appa ya share hawayen da suke masa zuba.
“Na cancanci tozarci da wulakanci da rashin mutunci a gurinki Iyami, ban kyauta ba na sani, kuma na karbi hakan”
Ya kalli Hurriya dake amayar da ruwan hawaye ya ce.
“Ba zaki ce komai ba Hurriya? Wata kila ban kyauta miki ba, domin ban tsaya na ji ra'ayinki ba”
Hurriya ta mika hannayenta ta kama hannayen mahaifinta ta rike.
“Hakika kai uba ne na gari Appa, ba zaka aurar da ni a inda kake tunanin zan wahala ba, ba zaka aurar da ni a inda za a musguna min ba, ko da ban gani a aikace ba na san a cikin zuciyarka haka ne, Appa ko kare ka aura min a matsayin miji, Wallahi zan karbe shi na zauna da shi, balle kuma mutumen da kake kyautatawa zato, na gode da zabin da ka yi min. Ya Allah mahaifina na ciyar da ni da halak, Allah ka ciyar da shi da abinci da ya fi ko wane abinci dadi a aljanna, mahaifina ya shayar da ni da halak, Ya Allah ka shayar da shi da ruwan alkausara, ruwan da bayan su babu sauran ƙishi bayan shansu, Mahaifina ya tufatar da ni da ni da Halak, Ya Allah ya tufatar da shi da mafi kololuwar darajar tufafi a aljanna, Mahaifina ya sama min muhalli, Ya Allah ka yi masa muhalli kusa da Annabi Muhammad S A W, Ya
Showing 150001 words to 153000 words out of 215510 words
“Ya karfin jikin Captain”
“Alhamdulillah daman stress me kawai Abba na ji sauki”
Ya amsawa Alhaji Munzali, kamin ya daga kansa yana kallon dinkakkiyar Shaddar dake Ikilima take mika masa, ya saka hannu biyu ya karba.
“Shiga ka yi wanka ka saka wannan shaddar ka feshe turaren nan gaba daya a jikinka”
“Daddy why?”
Ya tambaya da confused.
“Ina son ka raka ni airport ne kuma ina son mutane su ga yarona cikin mutunci, kuma karka dade ka fito yanzu nan ina jiranka”
“Toh Daddy”
Captain ya mike tsaye ya fice daga falon na Nene. Dakin da ya zama masaukinsa ya shiga ya cire tufafin jikinsa yayi wanka ya fito ya shafa mai ya saka shaddar ya dauko turaren ya feshe jikinsa gaba daya sai da kwalbar turaren ta kai kasa sannan ya dauki hula ya saka a kasan shi kansa, ya dubi kansa a jikin madubi shi kanshi ya san yayi kyau abun da ake kira da kyau, farar shaddar ta haske shi matuka... Wayarsa ya dauka ya saka aljihu da wallet dinsa sannan ya nufi kofar dakin ta bude ya fita yana wani irin kamshi mai sanar da zuwansa tun kamin ya iso. Ga mamakinsa sai ya samu babban falon na kakarsa a cike da mutane ciko har da mahaifiyarsa da kakarsa da abokiyar zamanta da duka wanda yake gidan a lokacin. Da mamaki ya sauko falon yana kallon kowa kowa kuma yana kallonsa...
“Zo nan Jamal...”
Daddy ya fada yana murmushi, Captain ya nufi gurinsa sai Daddy ya mike tsaye ya saka hannunsa aljihu ya ciro goro da dabino ya ce.
“Bude min hannunka... ”
Captain ya bude tafin hannunsa na dama ya mikawa Daddy, sai Daddy ya zuba masa dabino da goro dake hannunsa.
“Mun je jaje, kuma mun roki iri, kuma an ba mu, na nema maka auren Hurriya a yau, kuma an daura mun bada zinari na miliyan 50, a matsayin sadakinta, saboda dka fada mana mai tsada ce, shiyasa muka siye ta da kima, yau mai tsada ta zama mallakinka, Hurriya ta zama matarka halak malak...”
Kamar an aje hoto haka falon yayi tsit kamar babu wani abu mai rai a ciki, daga Captain har iyayensa babu mai motsi....
MASU KARATU BA BIYA A ZO A BIYANI HAKKINA A SAUKE NAUYI A HUTA
500 to Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[12/18/2023, 2:14 PM] AMINA KABIR CAPS: *HURRIYA*
4️⃣3️⃣
Hajiya Binta ya jinjina kai tana kara girmama labarin Allah, a duk lokacin da ake son mutun ya kunyata idan Allah yana tare da bawa ba a taba ganin abun da ake bukata, kariyace da sakamako mai kyau tare da kyau da kariya mai yawa daga Allah zuwa ga bayinsa da suka rike shi kuma suka dogara a gareshi.
“Duk wanda ya aikata wannan abun ya aikata ne saboda ya ci mutuncin Hurriya ya ci namu, ashe be sani ba yana kara kusance da mata da alheri ne”
Appa yayi murmushi a yayin da yake zaune a kasa rike da sarka ya kalli Yasir dake gefensa ya mika masa sarka.
“Budewa Hajiya ta gani”
Yasir ya karba ya mike tsaye ya bude mata sarka, Hajiya Binta ta saka hannu ta karba idonta na cika da hawaye.
“Allah na gode maka da ka nuna min wannan ranar, Allah ka sakawa wannan auren Albarka, kuma ka nuna min na sauran yaran”
“Amin Hajiya Amin”
Appa ya amsa da kansa, fadar irin farinciki da yake ciki a yanzu bata lokaci ne, farinciki da yake a yanzu ya fi wanda ya samu kansa a lokacin da aka haifo masa ita.
“Be kamata mu zauna ba Tsoho tafiya zamu yi mu sanar gidan mahaifiyarta da kuma ita yarinyar halin da ake ciki”
“Haka ne... ”
A nan kam sai yanayin Appa ya canja, ya sauke kai kasa damuwa na bayyana a fuskarsa. Yasir ya aje sarkar zinarin dake hannunsa ya mike tsaye ya fice daga dakin yana taba wayarsa. Appa ya bishi da kallo har ya fice sannan ya juyo da kansa ta inda Hajiya Binta take zaune ya ce.
“Ina jin kunyar hada ido da mahaifiyar yarinyar Hajiya, abun da na yi mata ban kyau ba, be kamata na aikata hakan ba, ban san me yasa na sake ta ba, kuma na kasa samun dalilin har yanzu da muke maganar nan dake, Iyami bata min komai ba face biyayya da kyautatawa, amman na saka mata da mafi munin sakamako na juya mata baya na wulakanta yaran da ta haifa min”
Ya shigar da lips dinsa duka biyu a bakinsa ya rufe dantse bakin zuciyarsa na ƙuna da abun da bakinsa yake furtawa.
“Alhamdulillah, ganin ka gane kuskure ni a gurina abun farinciki ne, babu daren da bana addu'ar Allah ya baka ikon gane gaskiya, domin abun da ka aikata kamar baka aikata shi cikin hayyacinka ba”
“Ban san me ya rufe min ido na aikata haka ba, ina jin nauyin iyayenta da ita kanta Iyamin a yanzu”
“Ka kawar da komai a ranka, daman shi aure ya gaji haka, a tsaba kuma a shirya ko a yanzu dare be maka ba, lokaci be kure ba zaka iya gyara inda ka yi kuskure ka share inda ka bata, kar wannan jin nauyin ya hanaka sanar da yarka Hurriya cewar ka bada aurenta a yau, kai da kanka nake son ka fada mata wannan”
Ya amsa mata da kai sannan ya mike tsaye yana hade rigarsa.
“Zamu jiraki a waje Hajiya sai ki shirya mu tafi”
“Toh...”
A waje suka jira Hajiya ta fito tana rike da sadakin jikarta, ta shiga baya Appa da Yasir kuma suka shiga gaba. A motar Hajiya sai godiya take yi ma Allah na yadda ya kawo auren Hurriya a kusa kuma da mutumen da ba ayi tsammani ba, Appa kuma fargaba da kunya na lullube shi a yayin da Yasir yake kara kusanta gidansu Gwaggo.
“Ni na manta ban tambaya ba, yaron dai yana da kirki ko? Murna da farinciki sun mantar da ni wannan”
“Ba shi matsala Hajiya na san shi, yana da kirki kuma babu wanda zai fadi sherinsa, Hurriya ta yi dacen miji fatan mu dai Allah ya bata lafiya kuma ya basu zaman lafiya”
Hajiya Binta farinciki sai ya kara ninkuwa, ta kara yi ma Allah godiya.
HURRIYA POV.
“Wannan jaraba da kuke ta fadawa Allah ya yaye muku, idan wannan ya wuce sai kuma wani ya zo, ke kin tashi baki ya bude ita kuma ido ya rufe”
Gwaggo ta kalli Hindu wanda ke kallon Hurriya tana lalaben gini har ta iso gurin da Amma take zaune tare da Gwaggo da kawar Amma wato Hindu ta zauna.
“Abun da Allah yayi annabi sai ceto, likitocin sun ce wai damuwarce ta taba mata ido, amman ni ban yarda ba na fi zaton wani aikin ne aka yi mata idon ya rufe gaba daya, gashi an yada hotunanta kin ga shikenan an gama da rayuwarta, ba ido balle ta yi karatu ta gina kanta kuma babu wanda zai aureta a haka”
Hindu ta rafka uban tagumi.
“Oh Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, wannan mugun kishi da me yayi kama? To ko ita ma za mu nema mata taimakon a gurin da aka nemawa Amma? Tun da gashi dai mun fara ganin haske”
Amma ta kama Hurriya ta kwantar da ita a cinyarta hawaye na sauko mata.
“Mun dai ga haske Hindu, Wallahi ban dauka zan iya kara yin magana ba, na dauka kalmaina sun kare a duniyar nan, ina kallon abu na zan iya cewa a bani ba, ina da maganganu da yawa a bakina amman ba zan iya furta ko daya ba, bana iya motsa jiki bana iya komai, amman ki duba yanzu magana fa nake yi, bana jin karfi a jikina sosai amman Alhamdulillah na gode Allah”
“Shi ma duk zai bari da yardar Allah, lafiya daman da rarafe take shiga a jiki har a tashi tsaye, ciwo ne yake jefar da mutum farat daya”
Cewar Hindu. Kamin su daga kansu gaba daya su kalli kofar gidan, Hajiya Binta ce ta shigo Appa yana bayanta sai Yasir a bayan Appa.
“Sallamu Alaikum”
Gwaggo da Hindu suka amsa mata, Amma kuma ta sauke kai kasa tana nadamar kallon Appa da ta yi kamar wanda ta yi arba da bakin maciji.
“Maa Shaa Allahu, Iyami ce a waje? Haka nake so lafiya ta samu”
“Alhamdulillah, Rukkaya dauko tabarma ki kawo ma baki”
Gwaggo ta amsa tana bawa Rukkaya umarni. Appa ya kasa daga ido ya kalli kowa kamar wanda ya aikata abun kunya. Rukkaya ta fito rike da tabarmar ta shimfida kusa da wanda Amma take zaune. Hajiya ta fara zaunawa sannan Appa Yasir, daman haka tarbiyar take, sai iyayen sun fara zama ake zama, idan kuma suna zaune ba ka tsaya a kansu ba sai dai rankwafa ko na zauna a kasa.
“Jama'a ina kwananku ko wuni zan ce domin dai yanzu ai 12pm ta yi”
“Lafiya Kalau Hajiya ya gidan”
Gwaggo ta amsa ba yabo ba fallasa. Appa ma ya mikawa Gwaggo gaisuwa, ba dan yana a gaban Hajiya Binta ba da kuma tunanin dalilin zuwansa wata kila da ba zata amsa gaisuwar Appa ba.
“Lafiya Kalau”
Amma ta daga kai ta kalli Rukayya dake zaune ta ce.
“Dauko min hijabina Rukayya”
A rude Appa ya dago kai ya kalli Amma, Hajiya Binta ma ta kalleta Yasir ma kallonta, dukansu sun yi turus suna mamakin jin furuci ya fito daga bakinta.
“Iyami kina iya magana yanzu?”
“Allah ya nufa Hajiya”
Amma ta guntun murmushi tana amsawa Hajiya Binta dake rike da baki.
“Allah da iko kake, kai Alhamdulillah yau farinciki ya mana yawa”
“Amma....”
Yasir ya kirata sai ta kalleshi ta yi murmushi ta amsa.
“Na'am Yasir”
“Alhamdulillahi”
Wannan karon Appa ne ya jaddada godiyarsa ga Allah yana kallon Amma, irin kallon da ya dauki shekaru be yi mata ba, nadama da damuwa bayyane a fuskarsa karara. Rukkayya ta kawo Hijab ta mikawa Amma, sai Amman ta karba ta saka domin tana ganin Appa da Yasir ba muharramanta ba ne a yanzu.
“Hurriya ta so mahaifinki na son magana da ke”
Hurriya ta amsa kiran da Hajiya Binta ta yi mata ta tashi zaune, sai ta lalaba ta matsa gurin da Hajiya take ta zauna, Appa ya kai hannayensa ya kama nata hannayen ya juyo da ita ta fuskance sai ta nade kafafuwanta irin zaman da musulunci ya koya mana yayin da zamu ci abinci, wato ta nade kafafuwanta tana fuskantar mahaifinta.
A lokacin da Appa ya kalli yarsa sai tausayinta da kaunarta da kuma kunyarta a lokaci daya mamayeshi. Ya sauke ajiyar zuciya sau uku sai a hudu ya samu damar hada kalmomin da zai gamsar da yarsa da su ya hada guri daya ya fara magana.
“Hurriya na san kin san cewar ni mahaifinki ne, a cikin abubuwan da Allah ya dora min nauyinsu akwai ciyar da ke da shayar da ke da tufatar da ke da halak, idan kuma kin kai munzali Annabi yace na zaba miki mijin na kwarai wanda na yarda da addinsa da dabi'arsa kuma mai abun yi. Ban sani ba ko na kokarta a tarbiyarki, wata kila na yi jarumta a ciyar da ke da tufatarwa, ba zan gane hakan ba sai ranar alkiyama, a cikin kokarin sauke nauyin da Allah ya dora min, na aiwatar da wani a yau. Yake ƴata yau kina zaune a gabana ne a matsayin matar wani, wanda cin ki da sha da tufatarwarki za su koma a kansa, a yau kin shiga sahun manyan mata, a yau kin tashi daga budurwar kin zama matar aure, daga yau ladarki zata riɓanyya har zuwa lokacin da za ki bar duniya, neman aljannarki a yau ya sauka daga kan kafata ya koma karkashin kafar mijinki.... A yau na aurar da ke Hurriya...”
Ta daga kanta ta kalli gurin da take kyautata zaton fuskar Appa take, bata iya ganin komai saboda rashin masoya biyu, wato idanuwa, amman a haka zuciyarta take ayyana mata yadda fuskar mahaifinta take. Bata ganin komai sai duhu, sai dai makanta bata hana idanuwanta suke zubar da hawayen da tun da Appa ya fara magana suke mata zuba. Appa ya dauki sarkar dake gaban Hajiya Binta ya dora a cinyoyin Hurriya.
“Wannan sadakinki ne... An umarci iyaye su bawa yarinya sadakinta domin nata ne... Wannan naki ne Hurriya...”
Hurriya ta kasa cewa komai bata jin komai sai _A yau na aurar da ke Hurriya_ haka kalmar ta yi ta maimaita kanta a kunnenta kwakwalwarta na juya kalamin.
“Aure....”
Amma ta tambaya domin Mamaki ya hana Gwaggo cewa komai.
“Hajiya ban fahimta ba, wane irin aure kuma? ”
“Ki kwantar da hankalinki zaki fahimta”
“Ban gane na kwantar da hankalina ba, taya zai shigo cikin gidanmu kai tsaye ya fada mana ya aurar da Hurriya? Saboda ya mayar da mu talakawa? Ni ba ni da hakki akan Hurriya kenan? Wane irin magana ne wannan?”
“Kin fini hakki akanta Iyami, Annabi ya ambaci uwa sau uku sannan ya ambaci Uba... Ban aurar da ita yau saboda na wulakanta ki ba, ban aikata hakan da wata manufa ba sai dan ina ganin hakan ne abun da ya cancanci ko wane uba na gari aikata, na aurar da ita ne a inda nake kyautata zaton za mutunta a rike ta amana, Iyami ki yi hakuri tabbas na yi kuskure ban nemi shawararki ba na aurar da Hurriya”
“Wa ka aurawa ita? Saboda abun kunyar da ya faru ne ka yanke shawarar aikata haka?”
Gwaggo ta tambaya a fusace. Appa ya tausasa murya ya ce.
“Aa Wallahi su suka zo neman aurenta da kansu, sunan yaron Jamal da ne ga Nafisa, dan wajen Alhaji Aliyu Turaki...”
Hawaye ya subucewa Amma.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, me ya sa zaka aurar min da ya a inda ba a san darajar mutane ba? Macen da bata son hada hanya da talaka? Zaka dauki Hurriya ka jefa a cikin danginta? Yarinya karama ta kafa fuskantar irin bala'in da na fuskanta a gidanka, da na san haka rayuwa zata zama gaba daya Wallahi da ban aureka ba, amman kaddara ta yi min zanen da ban isa na goge ba”
“Subhanallahi Subhanallahi Subhanallahi”
Appa ya maimaita har sau uku sannan ya ce.
“Na san ban kyauta miki ba Iyami, amman ki tausasa ko dan yaran nan”
Amma ta masa wani kallo na takaici da bakinciki.
“Yara? Wadannan twins din da aka haifa ka kasa zuwa ka tara hannu ka karba? Ko kuma ďan da aka kama ka ce ba zaka bada kudin fansar sa ba! Sai da na hada komai da na mallaka na bada, sannan Hajiya Kaltume ta baka umarnin biya? Ko kuma Hurriyar da ka juyawa baya?”
Appa ya kasa amsawa ya sauke kansa kasa yana mai jin kunya da nauyin abun da ya aikata.
“Bari na fada maka da bakina ka ji, yata bata auru ba, ba zan bada ita a inda za a wulakanta ta ba, abun kunyar da aka yi mata kazafin aikatawa ni zan iya rumgumarsa”
Ba tare da Appa ya dago kai ba ya ce.
“Iyami karki furta kalami cikin fushi”
“Irin kalamin da ka furta a lokacin da na ke cikin gidanka da cikin yayanka? Irin zuwan da iyayena suka yi ka wulakanta su? Yata ba zata je ko'ina ba Haruna.... Ban amince da wannan auren ba...”
Hajiya Binta ta ce.
“Adai hakuri Iyami a daina tuna baya, a bar baya ta wuce”
“Haka ne Hajiya, da dan yaran nan ba da be isa ya shigo cikin gidan nan ya zauna a nan yana magana da ni ba”
Appa ya share hawayen da suke masa zuba.
“Na cancanci tozarci da wulakanci da rashin mutunci a gurinki Iyami, ban kyauta ba na sani, kuma na karbi hakan”
Ya kalli Hurriya dake amayar da ruwan hawaye ya ce.
“Ba zaki ce komai ba Hurriya? Wata kila ban kyauta miki ba, domin ban tsaya na ji ra'ayinki ba”
Hurriya ta mika hannayenta ta kama hannayen mahaifinta ta rike.
“Hakika kai uba ne na gari Appa, ba zaka aurar da ni a inda kake tunanin zan wahala ba, ba zaka aurar da ni a inda za a musguna min ba, ko da ban gani a aikace ba na san a cikin zuciyarka haka ne, Appa ko kare ka aura min a matsayin miji, Wallahi zan karbe shi na zauna da shi, balle kuma mutumen da kake kyautatawa zato, na gode da zabin da ka yi min. Ya Allah mahaifina na ciyar da ni da halak, Allah ka ciyar da shi da abinci da ya fi ko wane abinci dadi a aljanna, mahaifina ya shayar da ni da halak, Ya Allah ka shayar da shi da ruwan alkausara, ruwan da bayan su babu sauran ƙishi bayan shansu, Mahaifina ya tufatar da ni da ni da Halak, Ya Allah ya tufatar da shi da mafi kololuwar darajar tufafi a aljanna, Mahaifina ya sama min muhalli, Ya Allah ka yi masa muhalli kusa da Annabi Muhammad S A W, Ya
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51 Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72