ziyararmu, sannu da zuwa dana”

Sai a lokacin ya zauna yana murmushi da murna arba da yar'uwar mahaifinsa kuma mace mai tsakanin kaunarsa fiye da kowa a familynsu.

“Momy ya gida”

“Lafiya kalau, yanzu ka dauki wata bakar dabi'a da ba zaka fada min yaushe zaka zo ba sai dai na gane ka kawai ko? Balle na shirya maka wani abu”

“Ni kaina bana sanin zan biyo ta nan sai dai na biyo kawai, kuma idan ina ra'ayin wani abu ai zan iya kira na fada miki”

“Captain sannu da zuwa”

Namra ta fada sannan ta nufi kitchen.

“Ya aikin? Yanzu ka dawo nan kenan? Yaushe ka dawo kasar wai?”

“Just two days ba, shi ne suka sake kawo ni nan na yi wata biyu zuwa uku sannan na koma gida”

“Kaduna za a maida kai kenan?”

“Yeah na dade ina yawo, so yanzu fitar da na yi waje da kuma sa hannun Daddy, za a bar ni Kaduna na zauna a nan, amman idan aikin ya taso na wasu garuruwa zan tafi mu yi, akwai aikin da ban karasa ba nan Gusau kuma kin san tana ta kokarin a magance matsalar tsaron nan shiyasa aka dage sai na dawo”

“Maa Shaa Allah, Allah ya taimaka gashi nan ka yi Fresh ka kara samun lafiya”

Yayi murmushi tare da kallon Namra data aje masa abun tabawa a mini center table dake gefen kujerar daya zauna.

“Maganar aure dai shi ke nan ka watsar da ita Captain”

“Zan yi aure Momy dolena”

“To na tsorata da lamarinka fa, wacan ma ana daf da daura aure komai ya lalace kuma tun daga lokacin baka sake gabatar mana da kowa ba”

“Bata min rai ta yi da yawa, taya ana daf da daura aurena zaki yi chat da wani saurayi har ya daukeki ku fita, ni fa ina da mugun kishi da zai iya sakawa na kashe mutum, bana iya daukar irin wadannan abubuwan, idan ina son mace ko kallonta bana son ayi”

Ya aje ayar maganar tare da daukar lemun da Namra ta aje masa ta sha. Momy ta yi murmushi.

“Toh Allah ya bada ta gari, yasa kamin ka bar garin nan ka samu wanda kake so, kuma ya rage maka wannan fushi idan ba haka ba zaka yi wahalar zaman aure”

“Amin”

Ya amsa yana dauke fuskarsa da murmushi tare da shan lemun a hankali. Namra ma ta yi murmushi tana taba wayar hannunta kamin ya dago ta kalleshi.

“Yauwa Captain wai a ina ka san Salim?”

Ya juyo ya kalleta.

“Salim Sarauta, abokina ne sosai tun a jami'a muke tare, ke ina kika san shi?”

Ya daga kafada tana dan zare ido kadan kamar wanda ta rasa abun cewa.

“A hanya muka hadu, ya nuna yana so na daga baya kuma ya koma gurin Hurriya, shiyasa na kai shi gidan ma har ka ganshi, amman ban san me ka fada masa ba na ga yanayinsa ya canja kuma har yau be sake kirana ba”

Captain yayi murmushi kasaita murmushin dake kara masa kyauta da haiba

“Ban fada masa komai ba, maybe dai ita ta bata masa rai, na je karbar abu ne na gansu tare, amman karki sake kai shi gurinta, haka yake duk garin da yaje sai yayi budurwa, musamman idan ya ga mai kyau ce just like your sister....”

“Hum himm”

Ya dan kalli Momy kamin ta sake kallonsa dan amsa masa tambayarta.

“Ina yarinyar take ta dawo?”

Momy zata yi magana Namra ta yi karaf ta tari numfashinta ta ce.

“Eh tana dakinta”

Ya maida dubansa gurin Momy fukarsa shimfide da murmushi yayi mata godiya.

“Thank You Momy, ko wace mace ta fi daraja da martaba a gidan iyayenta ko mijinta, kuma a matsayinki na uwa daman haka ya kamata ki yi”

Ya dubansa gurin tsadaden agogon hannunsa sannan ya mike tsaye.

“Ya kamata na tafi kar na bata lokaci”

Momy dake mamaki yadda Namra ta yi masa karya ta ce.

“Nan da nan, baka wani dadewa”

“Yanayin aikin ne a haka, wai Musib har yanzu ba su dawo ba?”

“Suna da daf da dawowa, muna waya da su ai”

“Good”

Ya nufi kofar fita falon, Momyda Namra suka mike tsaye domin yi masa rakiya. Yana bude kofar da zimmar fita Hurriya ta dake rike da kofar tana murdawa da zimmar shigowa, dayan hannunta kuma yana rike da luggage ta sake naushin kirjinsa da kanta daidai saitin zuciyarsa, a karo na biyu by mistake. A take daga hannun sama saitin fuskarta. Kamin hannun ya kai fuskarta ta yi saurin lumshe idanuwanta dake cike da yalwatacce gashin ido ga kuma na gira da ya kara masa kyau a sama, ta dauke numfashinta tana jiran jin tafin hannunsa a fuskarta.

“Yarinyar bata da hankali komai a haukace take yinsa”

Kalaman Momy da kuma jin shiru babu mari babu alamarsa a fuskarta ya saka ta bude ido a hankali pink lips dinta suna motsawa kamar zata ce wani abu. Hannu ta gani a tsaye saitin fuskarta ba tare da ya kai hannun a fuskarta ya mareta, kuma be sauke hannun ba, haka zalika be dauke idonsa daga kallonta ba, kamar yadda fuskarsa take daure saboda abun da ta yi masa. Da sauri ta duke kasa ta ratsa gefenta ta shige falon har Luggage dinsa na dukan kafarsa, abun da ya kara bata masa rai. A lokacin ne ta tuna cewar shi ne mutumen da ya taba marinta.

“Yi hakuri”

Ya ta fada tana kara matsawa baya da sauri domin jin take kamar zai iya rikota yayi mata hukunci ne, gashi babu Hamad mai rama mata. Ya sauke hannu ya juyo sai dai ba ita ya kalla ba, Namra ya kalla.

“Why do you lie?”

Ta dan yi baya kadan ta rasa yadda zata wanke kanta, Momy ta kalleta sannan ta kalli Captain ta already ya fice har yana kokarin rufe kofar. Sannan ta juyo ta watsawa Hurriya harara

“Kin dawo ko? To shiga ciki ki zauna, gida kam na ubanki ne amman ikonsa nawa ne domin bangarena ne”

Hurriya ta sauke kanta ta juya tare da taja kayanta ta haye sama. After ta shige Momy ta kalli Namra ta ce.

“Me yasa kika yi haka? Namra ki daina yin abun da zai saka Captain ya tsaneki fa”

Ta dan cize baki cikin yanayin damuwa ta ce.

“Ban dauka zata shigo yanzu”

“Ki kiyaye next, domin ni ban ki kum fahimci junanku ba har ya kai ku ga aure, ko ranar da ya bar gidan nan sai da muka yi magana da Ammy, akan ke da shi, amman saboda lura da hankalinku baya kan juna ya saka ba ma son matsawa, kuma ko da babu irin wannan be kamata kina haka ba be careful...”

“I will...”

Ta amsa tare da kallon kofar kamar mai tunani, tare da saka hannunta tana taba wuyanta. Momy kuma ta nufi upstairs cikin matukar bacin rai.



Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/23, 5:23 AM] AMINA KABIR CAPS: 𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

𝐏𝐚𝐠𝐞 2⃣3⃣

Tana tsaka da cire tufafinta a luggage Momy ta turo kofar dakin ta tsaya daga wajr tana kallonta.

“Mun ga sakon da Hajiya da ta aiko mana akanki, kuma mun gode ke ma kuma zaki ga irin nawa sakon, mahaifinki yayi gaskiya gidansa ni da ke duk muna karkashin ikonsa, amman nan bangarena ne ina da nawa rules and regulations, dole kuma ki kiyaye domin ba bangaren Iyami ba ne”

Hurriya ta sauke kanta ba tare da ta cewa Momy komai ba, ganin haka ya saka Momy ta bar kofar a bude ta nufi nata dakin. Ajiyar zuciya Hurriya ta sauke ta dafa goshinta.

“Allah ka kara min hakura zama a gidan nan, kowa da kallar tsanar da yake min”

Ta sake aje numfashi mai karfi sannan ta cigaba da cire tufafin ta jera a closet ta aje luggage din gefe ta cire hijab dinta ta saka talkaminta ta fito daga dakin. Ko da ta sauko babu kowa a falon kai tsaye ta nufi kofa ta bude ta fita. By this time ta san cewa mahaifinta baya a gidan sai idan wani abu ya dawo da shi ko kuma ya hana shi fita, dan haka Hajiya Kaltume uwargida, nan ma sai da ya ki bacin ranta da take ganin za a cusa mata, ta bawa zuciyarta hakuri ta danne duk wani abu da zata ji tun gabanin su fada mata, sannan ta tura kofar ta shiga. Sukan na su falon a cike yake suna ta murnar dawowar Salma, sai dai ganin Hurriya ya saka sun tsaya cak suna kallonta kamar irin wanda aka jefo daga sama daga gabansu.

“Hurriya”

Hajiya Kaltume ta fada da mamakinta karara a fuskarta.

“Na'am Hajiya ina wuni, Yaya Khairy Yayana, ina wuni yaya Salma sannu da zuwa”

Salma ta amsa tana kokarin boye munafurcinta a cikinta.

“Lfy kalau”

Yasir kuma ya ce.

“Lafiya Kalau kanwata, na jidadin da kika dawo, Hajiya kin yi abun da ya dace”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi, wani abun da ya bawa kowa dake falon mamaki ciki har da Hajiya Kaltume da ita kanta Hurriya shi ne tashin da Khairy ta yi ta koma kusa da ita ta rumgumeta tana far'a.

“Alhamdulillah, Allah ya kawar da bacin rana na jidadin da kika dawo, I'm so happy”

Hurriya ta kalleta har tana rasa abun furtawa, mamaki ya lake mata a zuciya.

“Ina taje ne ake ta murnar dawowarta?”

“Abubuwa da yawa suka faru Salma sai kin zauna zaki sha labari”

Khairy ta amsa bayan ta saki Hurriya.

“Ni ma fa ina da labarin da zan baku, kuma dukansu sai mamaki ya kama ku”

“Mamaki zai wuce ki ce kin samu wanda kike so zaku yi aure soon bla bla bla ni ma aurar da ni Hajiya take kokarin yi fa, ga Fadeel kin san shi ai dan Hajiya Fatee”

A yanzu ma Khairy ce ke amsawa Salma tana dorawa da zancen auren dake ci mata rai. Da mamaki Salma ta kalli Hajiya ta ce.

“Da gaske Hajiya? Fadeel ba yana da mata ba?”

Hajiya ta daga mata kai.

“Yana da mata amman kirkinsa ne ya saka nake son ba shi auren saboda ya nuna yana son Khairy”

Yasir ya mike tsaye daman shi ba gwani ne na sauraren irin wadannan maganganun na mata ba, dan haka ya kalli Hurriya.

“Muje waje Hurriya ina son magana dake”

Hurriya ta juya ta nufi kofa, tana gaba daya bayanta, sai da suka fice sannan Salma ta kalli Hajiya Kaltume ta ce.

“Har yanzu yaya ganin mutuncin yarinyar yake yi?”

Khairy ta tabe baki.

“Hmmm me za'a fasa kwanan baya saboda yarinyar nan ya lalata min birthday”

“Amman hugging dinta kika yi yanzu fa, kina murna dawowarta”

“Toh ai Salma idan baka iya kama barawo ba sai barawo ya kama ka, kara ina haka idan ba haka ba wani abun na samunta nan gaba za a iya cewa ni ce”

“Nikam i can't fake love, shiyasa wannan kawar tawa ma na ja mata kunne”

“Wace kawa wai?”

Salma ta gyara zama tana kara fitar da sauti saboda labarta musu abun da ta kumso.

“Hmmm Appa be fada muku zai kara aure ba?”

Sai a nan Hajiya Kaltume ta yi murmushi mai sauti ta ce.

“Ya ma isa Salma? Duk bayan wahalar da muka sha, ga tarin tashin hankali da munafurci da ba mu gama fuskantarsa ba saboda Nafisa da Iyami? A yanzu kuma da ya kamata ace ina da ikon gida ya tunkare da zancen aure? Haba wa..... Ba dai shi ba sai idan wani kuma ko kuma idan na mutu”

“Hajiya wannan fa ba wasa ba ne, abu ne da na gani da idona, and she's my friend muna daf da kare karatun nan take suka hadu, tana da va ni labarinsa but ban dauka Appa ba ne sai yau da muka sauka airport”

Hajiya Kaltume ta karkata da kyau tana kallon Salma dake magana with full confidence.

“Motar da ta dauke ta ma daga Airport ta kaita gida, Appa ya kawo, ban kara yarsa shi din ba ne har sai yau da ta fada min cewar shi ne mamallakin Yadi's Motors”

“Ho... How... How... Comes....”

Cewar Khairy tana kallon yar'uwarta.

“Boye min ta yi, amman ta fada min cewar yana da mata biyu ya saki 3rd wife dinsa yana da yaya maza hudu dayan ya rasu, yana da yan mata bakwai, amman na zama wata sakarai da ban gane ba har sai a yau da ta fada min wai sunan wanda take son ta aura Alhaji Haruna Mai Yadi, and she was telling me shi ya aiko da motar nan a dauke ta”

“Amman baki mareta ba? Ta fa san mahaifinki ne?”

“Ban mareta ba, amman na fada mata zata jefa kanta a matsala ne kawai dan haka ta rabu da mahaifina tun wuri, ni babu abun da ya fi bata min rai ma kamar yadda na zama sha sha ban fahimci mahaifina ba ne har sai da ta fada min, bayan kuma ita din ta sam cewa mahaifina ne domin sunana Salma Haruna Mai Yadi, and the most annoying part is yarinya ce kamar ni sai barikin tsiya”

Hajiya Kaltume ta girgiza kai.

“Aa ni dai ban yarda da wannan ba, ko dai akasi aka samu ko kuma wani abun ya hada su take zaton sonta yake, amman ni na san dalilin da ya saka mahaifinku ba zai kara aure ba, kuma idan har zai kara din zan riga kowa sani”

Salma ta yi dariya.

“Okay idan baki yarda ba, zan baki duka nunbers dinta ki saka a wayar Appa, ko kuma ki kawo ni na saka ko Khairy ko kuma ki yi wata dabara mu duba Instagram chat dinsa dan na fi kyautata zaton nan suka hadu”

Khairy taja tsaki.

“Ni Wallahi wannan auren auren na Appa yana damuna, daman tun da na ga gidan nan da part hudu na san yana da burin karo wata, kuma yanzu Fisabilillahi ace sa'ar yarsa kawarta ma? Haba...!”

“Wannan burin ada ne ba, ba yanzu ba duk wacan rayuwar ta kau, ku kwantar da hankalinku babu wani aure da zai kara, ni ban ma yarda zancen aure ne tsakaninsu ba ko soyayya”

Cewar Hajiya Kaltume tana murmushi, sannan ta mike tsaye yana fadar.

“Yanzu dai an huta yar'uwar shawara ta dawo, sai ku shirya duk abun da kuke ganin ya dace, zan sanarwa Appanku kamin Iyayen Fadeel din su zo”

“Hajiya Fadeel dai? Yana da mata fa? Kuma kin san yadda sherin kishiyoyi suke tun da muna cikinki”

Taku kadan Hajiya Kaltume ta yi ta dafa kafardar Salma fuskarta da murmushi.

“Kyakkyawar makoma ake buri, bana fatar kowa ya sake yin irin auren da Maama ta yi, tana can yana gana mata azaba, matarsa ba matsala ba ce domin Hajiya Fatee bata sonta, kuma saboda matarsa take son ya auri Khairiya saboda Khairiyyah ta share mata hawayenta, fata muke kamin ma ta shiga cikin gidan matarsa ta fice”

“Idan ta fita kina ganin Khairy zata iya rainon yayanta? Kuma yadda Hajiya Fatee ta tsani matarsa zata iya juyowa ta tsani Khairy fa...”

Khairy ta kada kai kamar kadangaruwa domin an taba mota gurin da yake mata kaikaiyi.

“Shi nake kokarin nunawa Hajiya ta gagara ganewa, ni har yanzu Fadeel din nan be kwanta min a rai ba”

“Ku yara ne ba zaku gane ba, gaba nake hango muku Hajiya Fatee kuma bata isa ta tsani Khairy ba har abada, kar ta san kar ne ni da ita, kuma ba ido zan zuba mata ba, tun kamin a tafi ake shiri ba sai an dawo ba, dan haka ki kwantar da hankalinki Khairy ki saki jiki ki saka kaunar Fadeel a ranki”

Salma da Khairy suka kalli juna kamin su kalli Hajiya su saka dariya, ita kuma ta yi murmushi ta fice ta bar musu falon, su suna dariyar ta kasa fahimtarsu kuma duk yadda take ganin abun zai zo da sauki ba zai zo, ita kuma tana murmushin abun da take hango ma Khairy wanda ta kasa ganewa.

“Hajiya ba zata gane ba”

Salma da har lokacin dariya take ta ce.

“Ina fa, kin ga ko maganar Appa musawa take yi, kuma Wallahi gaskiya ne, haka ta yi a auren Maama tana cewa tana hango mata jindadi ne saboda yana da kudi gashi nan yanzu kullum da kalar azabar da yake nuna mata, last week na muna chat take fada min yanzu har mata yake kawo mata a gida idan ta fita”

“Kullum fa iskancinsa gaba yake, ni ba zan ma iya daukar wannan iskancin da yake mata ba, ita kuma kamar an mata magani ta kasa rabuwa da shi”

“Ni kaina ba zan iya ba, kuma wai Hajiya ta kyaleta sai iskanci yake ma mutane yadda ya ga dama”

“To ya za'ayi idan ace za a masa magana ita take shiga ta tare, kar a taba mijinta wata kila sai da ya mallaketa sannan ya aureta”

Salma ta tabe baki ta sauka daga kan kujerar ta zauna a kasa.
Showing 72001 words to 75000 words out of 215510 words