Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣
Kamin direban ya isa gida duk wanda ke cikin motar ya dauka Hurriya shudewa zata yi, saboda kukan da take yana yin sama da nufashinta kamar nunfashin zai fice daga jikinta gaba daya. Namra ce take rike da ita tana kuka tana bata hakuri.
“Yi Hakuri Hurriya In Sha Allah zai dawo lafiya Allah zai tsare su”
Hurriya bata iya furta komai, gashin idon nata ya rufe gaba daya saboda kukan hawayen ya hanata ganin dishe-dishe ma da take gani idan babu gilashi a idonta. Direban na fakawa Salma da Khairi suka fita suna kuka suka nufi bangaren Hajiya Kaltume suna kuka, Namra kuma ta tsaya ta riko Hurriya suka fito.
“Bana ganin komai Yaya Namra idon ya rufe gaba daya... Karki bar ni nan dan Allah tsoro nake ji... Kira min Yaya Yasir ko ki kaini gurin Amma ko ki kira min Appa na dan Allah”
Tana maganar muryarta na rawa saboda numfashim da ya sarke ta. Ta san a gurin dayan su ne kadai zata yi kukanta ta more kuma ta fada musu abun da ya faruwa. Kowane ďa ko ƴa idan abun farinciki ko kishiyarsa ya same shi guduwa yake gurin uwarsa, sai dai ita a yau bata da wannan gatan, ba dan mahaifiyarta bata raye ba sai dan bata tare da ubanta, bata taba sanin zafin rashin Amma a gidan ba sai yau, ko wane ďa yana bukatar uwa a kusa da shi balle kuma ita da take da lalaurar ido. Dukawa ta yi a gurin ta dora duka hannayenta biyu a kai ta kwalla ihu da kukam muryarta tana kuka har sai da duk wanda ke harabar gidan hankalinsa ya dawo kanta.
“Wayyo Amma ma, Amma..... Amma... Amma... Ke..... Amma na”
Namra ta yi saurin rika hannunta tana kuka.
“Hurriya ba gani nan ba, ta zo muje ciki Momy tana nan ai”
Ta fisge hannunta, sanin kanta ne daga Momy har Hajiya Kaltume babu wanda ta isa ta jingina a cikinsa ta yi kuka, domin ba su dauke ta kamar sauran ƴaƴansu ba.
“Kira min Yayana kira Yayana”
Namra na cira kafa da zimmar tafiya kiran Yasir sai ta hangoshi ya fito da saurinsa ya nufo inda yake.
“Hurriya”
Hurriya na jin muryarsa ta mike tsaye da sauri ta fara lalaben inda zata ganshi.
“Yayana Yayana Yayana”
Kusan duk wanda ke tsaye yana kallonta sai da ya tausaya mata, domin lalurar rashin gani babbar matsala ce. (Alhamdulillah da kyautar Allah, if you can read this ku gode Allah, ba zabinku ba ne, kyautar Allah ce, and don't forget littafin na kudi ne idan kika karanta baki biya ba, ko kika min sharing na barki da Allah)
Yasir na isowa ya rika hannunta dake ta rawa take da fatar bakinta.
“Yayana dan Allah ka kai ni gurin Amma... Dan Allah..”
Without second thought yaja hannunta ya karbi key hannun dayan direban da ya aje Hajiya Kaltume few minutes before the incident happen. Ya bude motar Namra bata kara jin tausayinta ba sai da ta ga yadda take lalaben motar zata shiga, Yaisr ya taimaka mata ya saka ta a back seat sannan ya zagaya ya shiga mazaunin direba ya murza key ya juya motar cikin tashin hankali, ba dan yana namiji ba da tuni shi ma ya fashe da kukan kamar yadda kanensa da mahaifiyarsa suke kukan. Shiru Hurriya ta yi a cikin motar domin bata ganin komai sai duhu zucuyarta kuma ta cika fa tsoron abun da ya faru. A harabar gate din gidan Yasir ya faka motar sannan ya budr ya fito da Hurriya. Sai da ya daga gate din gidan sai kuma ya ji ba zai iya shiga ciki ba domin ba zai iya zama mutum ya farko da ya labartawa Amma labarin an sace danta ba, ya san idan ya shiga gidan ta ga yarta a wannan halin sai ta tambaye shi shi kuma ba zai iya mata karya ba. Haka kuma ba zai iya barin Hurriya ta shiga cikin gidan ita kadai ba a wannan yanayin.
“Hurriya ko dai ki hakura mu koma? Ba zan iya shiga cikin gidan nan ba, bana son na daga hankalin Amma a yanzu”
Tana jin haka sai ta saka dayan hannunta ta kwance hannunsa dake rike da nata.
“Tafi zan.... Iya... Shiga... Daga... Nan”
Be san bata gani gaba daya ba, a zatonsa tana gani dishe-dishe kamar da, dan haka be musa mata ba ya bude mata gate ta lalaba ta shiga, ya maida kofar ya rufe sannan ya koma cikin motar ya fice daga unguwar. Hannu Hurriya ta mika tana lalaba hanya, tare da amfani da zuciyarta tana ayyana yadda hanyar take a lokacin da take gani.
“Ke Hurriya...”
Ta ji muryar Rukayya sai wani sanyi ya ziyarceta. Ta karaso kusa da ita ta rika hannunta.
“Waya kawo ki? Mun ji an bude kofar gate ba mu ga an shigo ba shiyasa na fito na duba”
“Yaya Yasir ne ya kawo ni, ya tafi Mama Rukayya kai ni gurin Amma na”
“Me ya same ki Hurriya?”
“Kai ni gurin Amma please, bana gani yanzu bana iya ganin komai sai hudu, gaba daya idon ya rufe, na daina gani dishe-dishen ma”
“Innalillahi”
Rukayya ta fada tare da jan hannunta suka shiga ciki, Amman dake zaune dakin Gwaggo tana kwadon zogale ta aje kwanon zogalen ta yunkura da cikinta wata tara ta mike tsaye da sauri ganin Hurriya da hawaye a fuska kacha-kacha har ya bata gaban hijabinta, gata sanye da uniform din makaranta da bata cire ba kuma babu gilashi a idonta.
“Hurriya me ya same ki?”
Kunne da jikin da yayi kewar uwa ne kadai zai iya fahimtar yadda ruhu yake ji idan ya ji ko yayi arba da uwa.
“Amma ina kike?”
Ta saki hannun Rukayya ta fara lalaben inda take jin muryar Amma. Amma ta mika hannu ta rikota sai Hurriya ta rumgume ta ta kwanta jikinta tana wani irin kuka da ya saka Amma ta kasa rike kanta ita ta fashe da kuka.
“Me ya faru Hurtiya? Me ya same ki? Waya kawo ki? Me ya samu idon naki ina gilashinki”
Har Hurriya ta bude baki ta yi magana, zancen da Yasir yayi a waje ya fado mata a rai. Shi ma kenan ya ce ba zai iya sanar da Amma ba balle kuma ita da take yarta. Kamar an saka allura da zare an dinki bakin Hurriya haka ta zama, ta kasa furta komai kuma ma sai ya koma mata cikin zuciya hawaye kawai take ita yi.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Amma ta furta gabanta na bugawa da karfi. Ta san ba lafiya zata kawo yarta a irin wannan yanayin ba, kuma gashi ta kasa fadar komai sai rumgume ta take kamar zata shige jikinta.
“Hurriya yi a hankali mana, kin san akwai kanenki a jikinta, ko kuma ki zo ni na rumgume ki idan rumgumar kike so”
Gwaggo ta fada, sai Hurriya ta girgiza kai tana kara kankame Amma.
“Hurriya dukanki aka yi?”
Ta girgiza kai.
“Wani abu aka watsa miki a ido?”
Ta girgiza kai.
“Fada kika yi da wani?”
Ta girgiza kai.
“Dan Allah ki bude baki ki yi magana mana minene? Ko dai fada kika yi da Hamad? Na san zai iya cewa yayi miki mugun duka saboda bana gidan?”
Maganar da Amma ta yi ta Hamad ta saka Hurriya fashewa da sabon kuka.
“Yasir ya kawo ta, ta fa yi magana dazun yanzu ne dai ta kasa cewa komai”
“Wata kila fadan ta yi da Hamad shiyasa ta kasa fada tana tsoron kar na yi masa fada ya kara mata”
Zuciyar Amma ta fi aminta da fada suka yi da Hamad shi yasa har ta furta hakan, ganin Hurriya ta fashe fa kuka a lokacin da ta ambace shi.
“Kai Hamad yana da matsala Wallahi sai ace baka iya zaman lafiya fa yan'uwarka, ko tausayinta baya ji”
Rukayya ta fada. Sai Gwaggo ta ce.
“Kusan duk mabiyi da mabiyi haka ake, ba kowa ke shiri da juna ba”
“Amman dai shi nashi yayi yawa”
Amma dai ta yi shiru tana ta saurare numfashin Hurriyya dake fita da karfi..
FAMILY HOUSE...
A rikice Appa ya fito motar tun kamin direban sa ya gama fakin, ya nufi hanyar Falon Hajiya Kaltume cikin tashin hankali, hausawa suka ce ba a saka masa rana. Gaba daya kuka suke cikin falon har Namra da ta shigo. Hajiya Kaltume na ganin Appa ta kara mulmulawa a kasa tana dafa kai ta tashi zaune ta koma ta kwanta kamar wata bayarba...
“Eyyyy Eyyyy Eyyyy ni Kaltume yau na shiga uku yata, wayyo Umm Ruman, Alhaji ina cikin matsala da bala'i sun sace min yar auta, wai ni mi na yi ma mutane ne ne? Wayyo Allah na”
“Haba Hajiya ki yi hakuri mana, idan ke kina haka su kuma yara waye zai rarrashensu? Dan Allah ki tashi”
“Alhaji wasu sun tare mota sun tafi da Ruma”
“Hamad ma yana can hannunsu ai, ba ita kadai ba, kuma In Shaa Allahu zaku dawo lafiya”
“Mutanen nan ba su da imani shi Hamad ai namiji ne, ita kuma mace ce yarinyar yar shawalwala”
Appa ya zauna a kujera ya cire hular kansa duk sanyin ac falon gumi ne ke keto masa ta ko'ina. Salma da Khairi suka fara fada masa abun da ya faru suna kuka ba tare da ya tambaya ba, Kamin ya dago ya bi kowa da kallo.
“Ku daina mana kuka tun da ba mutuwa aka yi ba, ku yi ta addu'a, idan ma wani abun suke so ai dole za su kira. Ina Hurriya?”
Appa na rufe baki Yasir da shigowar falon kenan ya amsa masa.
“Yanzu na kaita gida?”
Appa ya masa wani kallo.
“Gida ina?”
“Gurin Amma tana ta kuka ta ce a kaita can, shiyasa na kaita amman ban shiga gidan ba”
Appa ya dafe kai cike da takaici kamin ya dago ya kalli Yasir yana jin kamar ya mareshi.
“Ban taba sanin baka da hankali ba, sai yau Yasir ka kaita ta fadawa Iyami abun da ya faru kamar baka san halin da Iyami take ciki ba? Ciki ne fa a jikinta kuma tsohon ciki idan ta fadi ta rikice wani abu ya same ta ko ya samu abun da ke cikinta kai zaka mata magani? Wani irin shashanci ne wannan?”
Yasir yayi shiru sai a lokacin shi ma yake ganin abun da yayi na kai Hurriya a irin wannan lokacin be dace ba. Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.
“Haba Alhaji wake da Iyami yanzu an dauke min yar shawalwalar yarinyar, mace ce fa, al kara ma Hamad namiji ne”
Appa ya tashi ya fice, Yasir ya bi bayansa, daga gidan station suka nufa daman kamin su isa Appa ya kira CP ya fada masa abun da ya faru, suna isa ya saka aka shigar da report kamin yan sanda da suke sashen kidnapping su tafi gidan aka kwaso duka yaran, ana tambayarsu yadda abun ya faru suna fada. Babban cikin su dake tambayar ya kalli Namra da ta kare nata bayanin ya ce.
“Wacece Hurriya? Ina ita Huriyyar take?”
“Tana gidansu”
“Okay ita ba yar'uwarku ba ce?”
Appa yayi gyaran murya dan ya san Namra zata iya wata kwabar.
“Yata ce, ni na haifeta amma yanzu tana gurin mahaifiyarta da ta koma gida haihuwa”
“To zamu iya ganin ita Huriyyar? Domin ga dukan alama ita aka zo dauka, ita da Ruma din a yadda na fahimta Hamad din tsautsayi ne ya rutsa da shi, rashin samun Hurriyya sai suka dauke Hamad din, dole akwai tambayoyin da nake son yi mata”
“Ni ma na yi wannan tunanin duba da irin labarin da suka ba ni, zan je na zo da ita”
Appa ya fada sannan ya kalli Yasir.
“Idan an gama ka maida su gida, ni zan je na taho da Huriyya”
“To Appa”
Yasir ya amsa cikin ladabi da biyayya, Appa ya ma Officer sallama ya fice. Tare da direbansa suka isa gidan Gwaggo, a waje suka faka motar direban ya fito ya bude masa mota ya fito. A ransa yana son shiga amman jin hake kamar ana tsikara masa allura a zuciya saboda ya doso gurin da Amma take.
“Bala, ka sallamo Hurriyya”
“Toh ranka ya dade”
Malam Bala ya wuce cikin gidan, Appa kuma ya jingina da mota, Malam Bala be dade ba ya dawo yana sanar masa Gwaggo tace ya shigo tana son magana da shi. Rasa yayi me zai ce, shi dai be isa ya juya yayi tafiyarsa ba, kuma yana jin kunyar hada ido da iyayenta ita kanta Amma a yanzu kunyarta yake ji. Haka dai ya daure ya danne duk wani abun azabar da yake ji ya shiga cikin gidan, sai da ya hada da addu'a sannan ya samu courage din shiga har cikin falon Gwaggo. Be zauna ba sai da ya risina ya gaishe da ita kamar yadda ya saba, ba dan ta girme shi ba, sai dai ma shi ya girme ta, yana bata girmata ne tun a lokacin da ta zama sukurukarsa a yanzu ma be yada girmanawarba, domin har a yanzu sun din suna da kima da daraja a idonsa.
“Hurriya ta shigo tana ta kuka, amman bata yi magana ba har yanzu ta kasa fadar abun da ya faru, a baki Rukayya muka ji cewar Yasir ne ya kawo ta ma, kuma da kayan makaranta ta shigo, babu gilashi a idonta, yanzu kuma sai ga Malam Bala ya shigo wai kana kiran Hurriya shiyasa na ce ya shigo da kai ciki mu ji abun da ya faru domin mu ma hankalinmu duk a tashe yake”
“Gwaggo, ni ma kaina ban san abun da ya faru ba. Shiyasa na kira Hurriyar na ji ta bakinta”
“Can gida ba su fada maka komai ba.?”
Appa ya ki yarda su hada ido.
“Ba su fada min ba, Hurriya tana kusa?”
“Eh tana dakin mahaifiyarta, bari a kirata”
Gwaggo ta tashi ta fita. Bata jima ba Iyami ta shigo falo tana sanye da digon Hijab har kasa Hurriya na rike da hannunta. Appa na kallonsa sai gashi ya mike tsaye yana kallon cikin dake jikinta cikin wani yanayi na rashin jindadi.
“Na fada maka babu uwar da zata so yayan wasu kamar nata, yanzu wannan tashin hankali duk na minene? Ba komawa gidanka nake bukata ba kwanciyar hankalin yayana kawai nake bukata a yanzu...”
“Iyami zauna”
Amma har ta yi kamar ta ce masa ba zata zauna ba, domin niyarta ta kawo Hurriya kuma ta jadda masa amanar yayanta ta koma, sai kuma ta zauna domin bata saba musa masa a komai ba. Sai da ta zauna sannan shi ma ya zauna.
“Ba wani abu aka yi mata ba, ki daina saka kishi da son cusa kiyayyar Kaltume ko Nafisa a zuciyar yayanki, ba dukan Hurriya aka yi ba, ba wata bakar magana aka fada mata ba, babu wanda ya mata komai, ba mutuwa aka yi ba”
“To miyasa ta zo tana min kuka? Kuma Yasir da ya kawo ta be shigo gidan ba ya fita?”
“Ni ma shi na zo tambayarta”
Amma ta kalli Hurriya har lokacin hawaye take sai dai ba kamar dazun ba. Ta kalli Appa
“Ina Hamad...!”
Appa ya ji tambayar kamar saukar aradu. Appa ya kalleta ya kasa cewa komai.
“Ina Hamad Appan Hurriya?”
“Dan Allah kin kwantar da hankalinki”
“Kamar ya na kwantar da hankalina? Miye abun tashin hankali a tambayar Hamad? Ko kuma shi ya aikata wani laifin?”
“be aikata laifin komai ba Wallahi, ki ba mu guri zamu yi magana da Hurriya”
Amma ta kalli Hurriya kamin ta mike tsaye ya fice daga falon. Appa ya tashi daga inda yake zaune ya koma kusa da Hurriya ya zauna ya rika yarsa.
“Hurriya”
“Na'am Appa”
“Ki kwantar da hankalinki kin ji, Hamad zai dawo soon da yardar Allah, babu abun da zai same shi, kuma na ji dadin da baki fadawa Iyami abun da ya faru ba, kin ga tana da ciki zata iya daga hankalinta,”
Ta daga kai ta kama hannun Appa ta jimke da karfi.
“Appa bana ganin komai yanzu, bana ganin komai sai abun da ya faru, me yasa suka dauke Hamad? Me yayi musu?”
“Wallahi dukanmu ba su sani ba, amman dai an san ba zai wuce su ce a ba su kudi ba, kamar yadda suka yi ma Kaltume kuma shi ma za su sako shi”
“Hadda Ruma aka kama”
“Na sani duka zamu biya kudi mu karbo su Da yardar Allah, amman yanzu zamu tafi dake gurin police za su miki tambayoyi akan abun da ya faru, saboda kun sanar da ya sanda, kamin nan kuma ina son ki min alkawarin ba zaki fadawa Iyami ba, kuma ki daina kukan nan har sai mun karbo shi”
Kamin Hurriyya ta dauki alkawarin suka jiyo Amma daga jikin curtains din kofar dakin tana furta.
Daga Appa har Hurriya ba su san Amma ta yi labe ba sai a lokacin. Appa ya taso ya fito da sauri yayinda Gwaggo ma ta fito da sauri daga dakin Amma ta nufota.
“Gwaggo sun dauke min Hamad, su biyu Allah ya ba ni sun dauke daya, kashe shi za su yi Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma ambaton Allah ta shiga yi tare da rike Amma dake shirin faduwa.
“Allah yasa kaddara ba musanya zata min ba, Allah yasa ba Hamad za a dauke a ba ni wani ba, La'ilaha Illallahu, Allah kasa kari zan samu ba musanya ko ragi ba, su wa suka dauke shi? Na san ďana be jin magana amman su yi hakuri dan Allah idan wani laifin yayi, kowa ya min haka be kyauta min ba, me suke so Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma sai da ta fashe da kuka saboda kukan da Amma take yi. Appa kuma yayi tsaye a gurin hopeless yana kallon tsohuwar matarsa dake dauke da cikinsa ya rasa me zai yi.
Littafin nan kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
________________
https://chat.whatsapp.com/F1ch00M9VNvFxrVVgCEeXo
Ina Yan uwan Yan gayu makotan Masu Kudi?
Daku nake Magana.
Matan da suka san ciyon kansu masu hada goma ta zamo ishirin kuzo ku sari Kaya acikin sauki da rahusa a Ummu Ahmad store muna kawo kayan mu ne daga Lagos masu quality da karancen farashi akwai kayan kitchen akwai shoes and bags, Akwai kayan abinci na awo laces,kayan
*BOOK 2 PAGE 1*
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣
Kamin direban ya isa gida duk wanda ke cikin motar ya dauka Hurriya shudewa zata yi, saboda kukan da take yana yin sama da nufashinta kamar nunfashin zai fice daga jikinta gaba daya. Namra ce take rike da ita tana kuka tana bata hakuri.
“Yi Hakuri Hurriya In Sha Allah zai dawo lafiya Allah zai tsare su”
Hurriya bata iya furta komai, gashin idon nata ya rufe gaba daya saboda kukan hawayen ya hanata ganin dishe-dishe ma da take gani idan babu gilashi a idonta. Direban na fakawa Salma da Khairi suka fita suna kuka suka nufi bangaren Hajiya Kaltume suna kuka, Namra kuma ta tsaya ta riko Hurriya suka fito.
“Bana ganin komai Yaya Namra idon ya rufe gaba daya... Karki bar ni nan dan Allah tsoro nake ji... Kira min Yaya Yasir ko ki kaini gurin Amma ko ki kira min Appa na dan Allah”
Tana maganar muryarta na rawa saboda numfashim da ya sarke ta. Ta san a gurin dayan su ne kadai zata yi kukanta ta more kuma ta fada musu abun da ya faruwa. Kowane ďa ko ƴa idan abun farinciki ko kishiyarsa ya same shi guduwa yake gurin uwarsa, sai dai ita a yau bata da wannan gatan, ba dan mahaifiyarta bata raye ba sai dan bata tare da ubanta, bata taba sanin zafin rashin Amma a gidan ba sai yau, ko wane ďa yana bukatar uwa a kusa da shi balle kuma ita da take da lalaurar ido. Dukawa ta yi a gurin ta dora duka hannayenta biyu a kai ta kwalla ihu da kukam muryarta tana kuka har sai da duk wanda ke harabar gidan hankalinsa ya dawo kanta.
“Wayyo Amma ma, Amma..... Amma... Amma... Ke..... Amma na”
Namra ta yi saurin rika hannunta tana kuka.
“Hurriya ba gani nan ba, ta zo muje ciki Momy tana nan ai”
Ta fisge hannunta, sanin kanta ne daga Momy har Hajiya Kaltume babu wanda ta isa ta jingina a cikinsa ta yi kuka, domin ba su dauke ta kamar sauran ƴaƴansu ba.
“Kira min Yayana kira Yayana”
Namra na cira kafa da zimmar tafiya kiran Yasir sai ta hangoshi ya fito da saurinsa ya nufo inda yake.
“Hurriya”
Hurriya na jin muryarsa ta mike tsaye da sauri ta fara lalaben inda zata ganshi.
“Yayana Yayana Yayana”
Kusan duk wanda ke tsaye yana kallonta sai da ya tausaya mata, domin lalurar rashin gani babbar matsala ce. (Alhamdulillah da kyautar Allah, if you can read this ku gode Allah, ba zabinku ba ne, kyautar Allah ce, and don't forget littafin na kudi ne idan kika karanta baki biya ba, ko kika min sharing na barki da Allah)
Yasir na isowa ya rika hannunta dake ta rawa take da fatar bakinta.
“Yayana dan Allah ka kai ni gurin Amma... Dan Allah..”
Without second thought yaja hannunta ya karbi key hannun dayan direban da ya aje Hajiya Kaltume few minutes before the incident happen. Ya bude motar Namra bata kara jin tausayinta ba sai da ta ga yadda take lalaben motar zata shiga, Yaisr ya taimaka mata ya saka ta a back seat sannan ya zagaya ya shiga mazaunin direba ya murza key ya juya motar cikin tashin hankali, ba dan yana namiji ba da tuni shi ma ya fashe da kukan kamar yadda kanensa da mahaifiyarsa suke kukan. Shiru Hurriya ta yi a cikin motar domin bata ganin komai sai duhu zucuyarta kuma ta cika fa tsoron abun da ya faru. A harabar gate din gidan Yasir ya faka motar sannan ya budr ya fito da Hurriya. Sai da ya daga gate din gidan sai kuma ya ji ba zai iya shiga ciki ba domin ba zai iya zama mutum ya farko da ya labartawa Amma labarin an sace danta ba, ya san idan ya shiga gidan ta ga yarta a wannan halin sai ta tambaye shi shi kuma ba zai iya mata karya ba. Haka kuma ba zai iya barin Hurriya ta shiga cikin gidan ita kadai ba a wannan yanayin.
“Hurriya ko dai ki hakura mu koma? Ba zan iya shiga cikin gidan nan ba, bana son na daga hankalin Amma a yanzu”
Tana jin haka sai ta saka dayan hannunta ta kwance hannunsa dake rike da nata.
“Tafi zan.... Iya... Shiga... Daga... Nan”
Be san bata gani gaba daya ba, a zatonsa tana gani dishe-dishe kamar da, dan haka be musa mata ba ya bude mata gate ta lalaba ta shiga, ya maida kofar ya rufe sannan ya koma cikin motar ya fice daga unguwar. Hannu Hurriya ta mika tana lalaba hanya, tare da amfani da zuciyarta tana ayyana yadda hanyar take a lokacin da take gani.
“Ke Hurriya...”
Ta ji muryar Rukayya sai wani sanyi ya ziyarceta. Ta karaso kusa da ita ta rika hannunta.
“Waya kawo ki? Mun ji an bude kofar gate ba mu ga an shigo ba shiyasa na fito na duba”
“Yaya Yasir ne ya kawo ni, ya tafi Mama Rukayya kai ni gurin Amma na”
“Me ya same ki Hurriya?”
“Kai ni gurin Amma please, bana gani yanzu bana iya ganin komai sai hudu, gaba daya idon ya rufe, na daina gani dishe-dishen ma”
“Innalillahi”
Rukayya ta fada tare da jan hannunta suka shiga ciki, Amman dake zaune dakin Gwaggo tana kwadon zogale ta aje kwanon zogalen ta yunkura da cikinta wata tara ta mike tsaye da sauri ganin Hurriya da hawaye a fuska kacha-kacha har ya bata gaban hijabinta, gata sanye da uniform din makaranta da bata cire ba kuma babu gilashi a idonta.
“Hurriya me ya same ki?”
Kunne da jikin da yayi kewar uwa ne kadai zai iya fahimtar yadda ruhu yake ji idan ya ji ko yayi arba da uwa.
“Amma ina kike?”
Ta saki hannun Rukayya ta fara lalaben inda take jin muryar Amma. Amma ta mika hannu ta rikota sai Hurriya ta rumgume ta ta kwanta jikinta tana wani irin kuka da ya saka Amma ta kasa rike kanta ita ta fashe da kuka.
“Me ya faru Hurtiya? Me ya same ki? Waya kawo ki? Me ya samu idon naki ina gilashinki”
Har Hurriya ta bude baki ta yi magana, zancen da Yasir yayi a waje ya fado mata a rai. Shi ma kenan ya ce ba zai iya sanar da Amma ba balle kuma ita da take yarta. Kamar an saka allura da zare an dinki bakin Hurriya haka ta zama, ta kasa furta komai kuma ma sai ya koma mata cikin zuciya hawaye kawai take ita yi.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Amma ta furta gabanta na bugawa da karfi. Ta san ba lafiya zata kawo yarta a irin wannan yanayin ba, kuma gashi ta kasa fadar komai sai rumgume ta take kamar zata shige jikinta.
“Hurriya yi a hankali mana, kin san akwai kanenki a jikinta, ko kuma ki zo ni na rumgume ki idan rumgumar kike so”
Gwaggo ta fada, sai Hurriya ta girgiza kai tana kara kankame Amma.
“Hurriya dukanki aka yi?”
Ta girgiza kai.
“Wani abu aka watsa miki a ido?”
Ta girgiza kai.
“Fada kika yi da wani?”
Ta girgiza kai.
“Dan Allah ki bude baki ki yi magana mana minene? Ko dai fada kika yi da Hamad? Na san zai iya cewa yayi miki mugun duka saboda bana gidan?”
Maganar da Amma ta yi ta Hamad ta saka Hurriya fashewa da sabon kuka.
“Yasir ya kawo ta, ta fa yi magana dazun yanzu ne dai ta kasa cewa komai”
“Wata kila fadan ta yi da Hamad shiyasa ta kasa fada tana tsoron kar na yi masa fada ya kara mata”
Zuciyar Amma ta fi aminta da fada suka yi da Hamad shi yasa har ta furta hakan, ganin Hurriya ta fashe fa kuka a lokacin da ta ambace shi.
“Kai Hamad yana da matsala Wallahi sai ace baka iya zaman lafiya fa yan'uwarka, ko tausayinta baya ji”
Rukayya ta fada. Sai Gwaggo ta ce.
“Kusan duk mabiyi da mabiyi haka ake, ba kowa ke shiri da juna ba”
“Amman dai shi nashi yayi yawa”
Amma dai ta yi shiru tana ta saurare numfashin Hurriyya dake fita da karfi..
FAMILY HOUSE...
A rikice Appa ya fito motar tun kamin direban sa ya gama fakin, ya nufi hanyar Falon Hajiya Kaltume cikin tashin hankali, hausawa suka ce ba a saka masa rana. Gaba daya kuka suke cikin falon har Namra da ta shigo. Hajiya Kaltume na ganin Appa ta kara mulmulawa a kasa tana dafa kai ta tashi zaune ta koma ta kwanta kamar wata bayarba...
“Eyyyy Eyyyy Eyyyy ni Kaltume yau na shiga uku yata, wayyo Umm Ruman, Alhaji ina cikin matsala da bala'i sun sace min yar auta, wai ni mi na yi ma mutane ne ne? Wayyo Allah na”
“Haba Hajiya ki yi hakuri mana, idan ke kina haka su kuma yara waye zai rarrashensu? Dan Allah ki tashi”
“Alhaji wasu sun tare mota sun tafi da Ruma”
“Hamad ma yana can hannunsu ai, ba ita kadai ba, kuma In Shaa Allahu zaku dawo lafiya”
“Mutanen nan ba su da imani shi Hamad ai namiji ne, ita kuma mace ce yarinyar yar shawalwala”
Appa ya zauna a kujera ya cire hular kansa duk sanyin ac falon gumi ne ke keto masa ta ko'ina. Salma da Khairi suka fara fada masa abun da ya faru suna kuka ba tare da ya tambaya ba, Kamin ya dago ya bi kowa da kallo.
“Ku daina mana kuka tun da ba mutuwa aka yi ba, ku yi ta addu'a, idan ma wani abun suke so ai dole za su kira. Ina Hurriya?”
Appa na rufe baki Yasir da shigowar falon kenan ya amsa masa.
“Yanzu na kaita gida?”
Appa ya masa wani kallo.
“Gida ina?”
“Gurin Amma tana ta kuka ta ce a kaita can, shiyasa na kaita amman ban shiga gidan ba”
Appa ya dafe kai cike da takaici kamin ya dago ya kalli Yasir yana jin kamar ya mareshi.
“Ban taba sanin baka da hankali ba, sai yau Yasir ka kaita ta fadawa Iyami abun da ya faru kamar baka san halin da Iyami take ciki ba? Ciki ne fa a jikinta kuma tsohon ciki idan ta fadi ta rikice wani abu ya same ta ko ya samu abun da ke cikinta kai zaka mata magani? Wani irin shashanci ne wannan?”
Yasir yayi shiru sai a lokacin shi ma yake ganin abun da yayi na kai Hurriya a irin wannan lokacin be dace ba. Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.
“Haba Alhaji wake da Iyami yanzu an dauke min yar shawalwalar yarinyar, mace ce fa, al kara ma Hamad namiji ne”
Appa ya tashi ya fice, Yasir ya bi bayansa, daga gidan station suka nufa daman kamin su isa Appa ya kira CP ya fada masa abun da ya faru, suna isa ya saka aka shigar da report kamin yan sanda da suke sashen kidnapping su tafi gidan aka kwaso duka yaran, ana tambayarsu yadda abun ya faru suna fada. Babban cikin su dake tambayar ya kalli Namra da ta kare nata bayanin ya ce.
“Wacece Hurriya? Ina ita Huriyyar take?”
“Tana gidansu”
“Okay ita ba yar'uwarku ba ce?”
Appa yayi gyaran murya dan ya san Namra zata iya wata kwabar.
“Yata ce, ni na haifeta amma yanzu tana gurin mahaifiyarta da ta koma gida haihuwa”
“To zamu iya ganin ita Huriyyar? Domin ga dukan alama ita aka zo dauka, ita da Ruma din a yadda na fahimta Hamad din tsautsayi ne ya rutsa da shi, rashin samun Hurriyya sai suka dauke Hamad din, dole akwai tambayoyin da nake son yi mata”
“Ni ma na yi wannan tunanin duba da irin labarin da suka ba ni, zan je na zo da ita”
Appa ya fada sannan ya kalli Yasir.
“Idan an gama ka maida su gida, ni zan je na taho da Huriyya”
“To Appa”
Yasir ya amsa cikin ladabi da biyayya, Appa ya ma Officer sallama ya fice. Tare da direbansa suka isa gidan Gwaggo, a waje suka faka motar direban ya fito ya bude masa mota ya fito. A ransa yana son shiga amman jin hake kamar ana tsikara masa allura a zuciya saboda ya doso gurin da Amma take.
“Bala, ka sallamo Hurriyya”
“Toh ranka ya dade”
Malam Bala ya wuce cikin gidan, Appa kuma ya jingina da mota, Malam Bala be dade ba ya dawo yana sanar masa Gwaggo tace ya shigo tana son magana da shi. Rasa yayi me zai ce, shi dai be isa ya juya yayi tafiyarsa ba, kuma yana jin kunyar hada ido da iyayenta ita kanta Amma a yanzu kunyarta yake ji. Haka dai ya daure ya danne duk wani abun azabar da yake ji ya shiga cikin gidan, sai da ya hada da addu'a sannan ya samu courage din shiga har cikin falon Gwaggo. Be zauna ba sai da ya risina ya gaishe da ita kamar yadda ya saba, ba dan ta girme shi ba, sai dai ma shi ya girme ta, yana bata girmata ne tun a lokacin da ta zama sukurukarsa a yanzu ma be yada girmanawarba, domin har a yanzu sun din suna da kima da daraja a idonsa.
“Hurriya ta shigo tana ta kuka, amman bata yi magana ba har yanzu ta kasa fadar abun da ya faru, a baki Rukayya muka ji cewar Yasir ne ya kawo ta ma, kuma da kayan makaranta ta shigo, babu gilashi a idonta, yanzu kuma sai ga Malam Bala ya shigo wai kana kiran Hurriya shiyasa na ce ya shigo da kai ciki mu ji abun da ya faru domin mu ma hankalinmu duk a tashe yake”
“Gwaggo, ni ma kaina ban san abun da ya faru ba. Shiyasa na kira Hurriyar na ji ta bakinta”
“Can gida ba su fada maka komai ba.?”
Appa ya ki yarda su hada ido.
“Ba su fada min ba, Hurriya tana kusa?”
“Eh tana dakin mahaifiyarta, bari a kirata”
Gwaggo ta tashi ta fita. Bata jima ba Iyami ta shigo falo tana sanye da digon Hijab har kasa Hurriya na rike da hannunta. Appa na kallonsa sai gashi ya mike tsaye yana kallon cikin dake jikinta cikin wani yanayi na rashin jindadi.
“Na fada maka babu uwar da zata so yayan wasu kamar nata, yanzu wannan tashin hankali duk na minene? Ba komawa gidanka nake bukata ba kwanciyar hankalin yayana kawai nake bukata a yanzu...”
“Iyami zauna”
Amma har ta yi kamar ta ce masa ba zata zauna ba, domin niyarta ta kawo Hurriya kuma ta jadda masa amanar yayanta ta koma, sai kuma ta zauna domin bata saba musa masa a komai ba. Sai da ta zauna sannan shi ma ya zauna.
“Ba wani abu aka yi mata ba, ki daina saka kishi da son cusa kiyayyar Kaltume ko Nafisa a zuciyar yayanki, ba dukan Hurriya aka yi ba, ba wata bakar magana aka fada mata ba, babu wanda ya mata komai, ba mutuwa aka yi ba”
“To miyasa ta zo tana min kuka? Kuma Yasir da ya kawo ta be shigo gidan ba ya fita?”
“Ni ma shi na zo tambayarta”
Amma ta kalli Hurriya har lokacin hawaye take sai dai ba kamar dazun ba. Ta kalli Appa
“Ina Hamad...!”
Appa ya ji tambayar kamar saukar aradu. Appa ya kalleta ya kasa cewa komai.
“Ina Hamad Appan Hurriya?”
“Dan Allah kin kwantar da hankalinki”
“Kamar ya na kwantar da hankalina? Miye abun tashin hankali a tambayar Hamad? Ko kuma shi ya aikata wani laifin?”
“be aikata laifin komai ba Wallahi, ki ba mu guri zamu yi magana da Hurriya”
Amma ta kalli Hurriya kamin ta mike tsaye ya fice daga falon. Appa ya tashi daga inda yake zaune ya koma kusa da Hurriya ya zauna ya rika yarsa.
“Hurriya”
“Na'am Appa”
“Ki kwantar da hankalinki kin ji, Hamad zai dawo soon da yardar Allah, babu abun da zai same shi, kuma na ji dadin da baki fadawa Iyami abun da ya faru ba, kin ga tana da ciki zata iya daga hankalinta,”
Ta daga kai ta kama hannun Appa ta jimke da karfi.
“Appa bana ganin komai yanzu, bana ganin komai sai abun da ya faru, me yasa suka dauke Hamad? Me yayi musu?”
“Wallahi dukanmu ba su sani ba, amman dai an san ba zai wuce su ce a ba su kudi ba, kamar yadda suka yi ma Kaltume kuma shi ma za su sako shi”
“Hadda Ruma aka kama”
“Na sani duka zamu biya kudi mu karbo su Da yardar Allah, amman yanzu zamu tafi dake gurin police za su miki tambayoyi akan abun da ya faru, saboda kun sanar da ya sanda, kamin nan kuma ina son ki min alkawarin ba zaki fadawa Iyami ba, kuma ki daina kukan nan har sai mun karbo shi”
Kamin Hurriyya ta dauki alkawarin suka jiyo Amma daga jikin curtains din kofar dakin tana furta.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un.
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Daga Appa har Hurriya ba su san Amma ta yi labe ba sai a lokacin. Appa ya taso ya fito da sauri yayinda Gwaggo ma ta fito da sauri daga dakin Amma ta nufota.
“Gwaggo sun dauke min Hamad, su biyu Allah ya ba ni sun dauke daya, kashe shi za su yi Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma ambaton Allah ta shiga yi tare da rike Amma dake shirin faduwa.
“Allah yasa kaddara ba musanya zata min ba, Allah yasa ba Hamad za a dauke a ba ni wani ba, La'ilaha Illallahu, Allah kasa kari zan samu ba musanya ko ragi ba, su wa suka dauke shi? Na san ďana be jin magana amman su yi hakuri dan Allah idan wani laifin yayi, kowa ya min haka be kyauta min ba, me suke so Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma sai da ta fashe da kuka saboda kukan da Amma take yi. Appa kuma yayi tsaye a gurin hopeless yana kallon tsohuwar matarsa dake dauke da cikinsa ya rasa me zai yi.
Littafin nan kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
________________
https://chat.whatsapp.com/F1ch00M9VNvFxrVVgCEeXo
Ina Yan uwan Yan gayu makotan Masu Kudi?
Daku nake Magana.
Matan da suka san ciyon kansu masu hada goma ta zamo ishirin kuzo ku sari Kaya acikin sauki da rahusa a Ummu Ahmad store muna kawo kayan mu ne daga Lagos masu quality da karancen farashi akwai kayan kitchen akwai shoes and bags, Akwai kayan abinci na awo laces,kayan
Book Chapters
Chapter 1 Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72