isgili yayi na cewar kada Allah ya tashe shi lafiya idan har ƙarya yayi. Babu irin kuka da Mardiya ba tayi ba sai nanata zancen take wai daman tasan haka zai faru tun da yace be sake ta bayan kuma ya san ya sake ta.
Ganin har rana ta faɗi babu wani sauyi, yasa suka ɗauke shi zuwa asibiti, ana kiran magariba aka bashi gado, likitoci suka shiga bashi taimakon gaggawa, sannan suka tura shi ɗakin hoto. Allura suka masa a nan ya samu bachi.
***
Ƙarfe tara dai-dai aka jera motoci ƙofar gidan da su Namra suke wato masaukinsu. Hajiya Shafa da wasu family na mai Martaba suka shiga ciki suka yi bikon amarya da kuɗi da kuma siyayya.
Ana guda aka fito da Namra tana cikin lifaya fuskarta a lulluɓe, sai ƙamshin turare take.
Barorinta suka buɗe mata mota ta shiga sai aka maida ƙofar motar aka rufe, sai sauran suka shiga sauran motocin, aka akama hanyar gidan Mai Martaba da ita, lokacin da aka shiga da ita faɗar Mai Martaba na shaƙe da mutane da kuma talakawa, sai ta yi gaisuwar ban girma Mai Martaba yayi musu addu'a sannan aka shiga ɗakin ɗayar matarsa tayi musu addu'ah sannan aka yi canji mutane da wato mutanen da suka je bikonta ba su zasu raka ta ɗakinta ba.
Ko da aka isa da ita ɗakinta shaɗaya har ta gota, babu wanda beyi mamakin ganin irin gidan da aka kaita ba duk kuwa da kasancewar dare ne, baka iya banbance shi da rana saboda hasken da gidan ke da shi, yanayin gidan zuwa fenti da kwaliyar gidan duka irin na masarautarsu ne yayi, wani abun burgewa kuma yadda aka ƙawata gidan da komai fari kamar fentin gidan, wato furnitures da aka zubawa Namra komai fari ne har labulayenta, da center carpet, kai har agogon bangonta fari ne, duk inda suka yi masu camera na biye suna ɗauka, tun farkon fitowarta har zuwa gaisuwa da kuma kawo ta gidan.
A ɗakin da yafi ko wannne haɗuwa aka kaita, kasancewar ɗakuna biyar ne a gidan kuma ko wanne sai da aka saka masa kaya, sai ta hau tsakiyar gadon ta zauna, kanta lulluɓe da mayafi.
Wasu daga dangin ango suka mata Allah sa albarka suka fice, sannan wasu daga ƴan'uwanta suka kama hanya, sai aka bar Maryam kawai sai Raihanatu da kuma wata ƴar'uwarsu Husaina.
Bayan kamar minti talatin sai suka soma jin busa da algaita da kirari irinta ta ƴaƴan sarakuna, shi ma mai nasa video yana biye da shi yana ɗauka. Har aka shigo da shi cikin ɗakin, sai ya zauna bakin gado yana ƙamshin turare, fuskarsa ta sha rawani kamar Mahaifinsa. Abokaninsa sai zolayarasa suke shi ko bakinsa har kunne.
Nasiha suka musu akan zamantakewar aure da kuma haƙuri, masu auren cikinsu sai zolayar samarin suke, wasu kuma na zolayar Abdool wai ango sai sha mai. Sai da suka ga shabiyu ta gota sannan suka musu addu'ah da fatan alheri, sannan suka saka Maryam da waɗanda suke tare gaba, har wasu na cewa suna son Maryam a zatonsu budurwa ce.
[8/5, 7:03 PM] Khadeeja Candy♥: *96*
Bayan abokansa sun wuce Abdool ya tashi ya rufe ƙofor falo ya dawo ɗakin fuskarsa da murmushi, rawanin kansa ya fara cirewa ya aje sannan cire babbar rigarsa.
“Amaryata wacce ta wacce amarya tsada”
Ya kai hannu zai yaye gyalenta, sai ta matsa baya ta ƙara jan gyalen ya sauko. Matsawa yayi kusa da ita ya sake miƙa hannun sai ta kauce hannunta mai zanen lalle ta ziro masa. Murmushi yayi yasa hannunsa aljihu ya ɗauko wani ɗan ƙaramin box ya ɗora mata saman hannu, sai ya miƙa hannun ya yaye mata mayafin. Idonta a rufe fuskarta ɗauke da murmushi
“Har da idon sai na siya...?”
“Ai kace wannan amaryar ta fi ko wace Amarya tsada”
Murmushi ya sake yi sai ya cire tsadadden agogon hannunsa ya ɗora mata saman hannu, sai a lokacin ta buɗe ido ta saka su cikin nashi haƙoranta a washe.
“Kin manta ban siye murmushin ba”
“Maganar ma ai baka siya ba an yi maka nasiha ne kawai”
Hannu ya kai ya riƙa gefen fuskarta yana shafa shi da babban yatsansa.
“Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar, lallai na fi ko wane Namiji sa'a a duniyar nan”
“Kana koɗa Namra da yawa, har kana sa tana jin kamar ta fi ko wace mace zama sarauniya”
“Na haɗu da mata da yawa ciki da wajen ƙasar nan amman babu wacce ta sace min zuciya sai Namra, she ko ma ƙaramar sarauniyace ba”
Lumshe ido tayi tana murmushi. Box ɗin ya amsa ya buɗe ya fiddo zobe mai kyau ya kama hannunta ya saka mata.
“I Love you so Much Abnam”
“Na gode sosai”
Matsawa yayi kusa da ita.
“Godiya kawai? Ai hausawa na cewa yaba kyauta tukuici”
Ta rufe fuskarta domin ta gano ma'anar zancensa. Shi ma dariyar ya yi, ya jata ƙirjinsa ya rumgume, a hankali ya sauke numfashi ya ɗora kansa kaman nata.
“Gani komai nake kamar a mafarki, ina tuna lokacin da na fara ganinki irin halin rayuwar da na shiga saboda ke kuma gashu yanzu komai ya zama tarihi, inshallah ni ne mijinki ke kuma matana har Aljanna”
Lafewa ta yi a ƙirjinsa kamar babu wanzuwarta a doron ƙasa, gudun zuciyarsa take sauraren tana auna yada nata zuciyar yake hawa da sauka tare da ta shi.
Sun daɗe a haka sannan ya ɗagota ya mata kiss saman ido.
“Karki min bachi saman jiki kisa na ƙarye”
Tayi dariya tana bugar masa chest.
“Ouuuuch”
Ya faɗa yana kanne mata ido ɗaya. Shi ya fara sauka saman gadon sannan ya miƙa mata hannun, ta riƙa hannunsa ta sauƙo suka shiga bathroom ɗin tare, shi ya fara alwalar sannan ya taimaka mata ita ma tayi suka fito. Sallaya biyu ya shinfiɗa ɗaya a gaba ɗayar kuma tana baya da shi kaɗan.
Mayafinta ya ɗauka ta rufe jikinta kasancewar fafaɗa ne kuma mai kauri. Yana gaba tana biye har suka yi raka'ah biyu, sannan suka sallame. Hannunsa ya ɗaga masa ya riƙa kwaroro musu addu'ah tana amsawa da amin sanna suka shafa, sai ya juyo ya kalleta.
“Hajiya Akwai wata sunnar bayan wannan?”
Ta zare masa ido. Sai ta gurgiza masa kai alamar a'a. Dariya yayi ya tashi ya ɗauko ledojin da gefen gadon ya kawo gabanta ya aje, sannan ya fita daga ɗaga ɗakin gaba ɗaya. Be ɗauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo da plate da cup ta aje a gabanta sannan ya zauna yaja ledar ya buɗe ya fido ƙatuwar kaza ta ɗora saman plate ɗin sai ya mayardar ragowar gajin a gefe ɗaya, ya buɗe madara ya zuba musu a cup ɗaya sannan yasa hannu ɓare kazar ya soma kai mata a baki. Kawar da fuska ta yi tana murmushi.
“Ki taimaki bawan Allah nan ki bar shi ya ciyarda dake a wannan daren da yafi ko wane dare muhimmanci da daraja a gareshi”
“Na hutar da kai, zan iya wannan aikin”
“Ai bana son hutun ne, idan dare ya lula ke da kanki zaki min kukan gajiya ki neman na hutar da ni, amman ba yanzu ba yanzu ai ai ba aiki na ke ba”
Ta ɗan fiddo ido tana kallonsa, sai ya kanne mata ido ɗaya, ba shiri ta buɗe baki tana mamakin yadda yake ƙoƙarin faɗar maganganu kai tsaye. Hakan ya bashi damar saka mata naman a bakin.
Cikin so da ƙauna yayi feeding ɗinta, sai da ya tabbatar ta ƙoshi sannan ya cilasta mata ita ma ta yi feeding ɗinsa a dole ba dan ranta ya so ba, bayan sun ƙare ya kwashe plate ɗin ya buɗe wardrobe ya fiddo kayan bachi kala ɗaya amman na maza da mata, na matan ya miƙa mata shi kuma ya shiga ƙoƙarin zame kayan jikinsa ya canja zuwa na bachin sai ta zaro ido.
“Wai nan zaka canja su?”
“To miye? Naga an zama ɗaya”
“A'a da saura, bari na baka guri ka canja”
Wani shu'umin murmushi yayi har da cije baki.
“No ba sai kin fita ba, bari na baki guri ki canja nima kuma sai na canja a wani ɗakin ko, ƙina da gaskiya ai ba mu zama ɗaya ba amman mun kusa raba gari”
Ya fice yana dariya kamar ba shi ba. Yana fita ya ɗauki kayan bachi da zimmar canjawa sai ta ga ɗan ƙaramin wando sai wata fikicar riga iya cibiya sai kuma babbar mai kamar rariya wacce zata rufe jikin gaba ɗaya. Mayardar kayan ta yi ta aje taja gyalenta ta ƙara rufe jiki.
Shima irin kayan bachinta ne jikinsa bancanci shi baya da wannan ficikar rigar ƙirjinsa a sake yake. Tana kallonsa gabanta yayi mugun faɗuwa, ta razana sosai kamar bata taɓa ganin ƙirjin namiji a waje ba, yana doso inda take ƙanshin turaren da ya saka ya riƙa dukan hancinta, ko da ya ƙaraso kusa da ita ta rufe idonta gan numfashinta har rawa yake.
“Baki canja kayan ba?”
“Da wannan zan kwanta”
Ta faɗa ba tare da ta buɗe idon ba.
“To tashi ki hau gadon ki kwanta”
“Na fi jindaɗi a ƙasan”
“Ƙasa zamu kwanta kenan”
“A'a kai ka kwanta saman gadon, ni na kwanta a ƙasa”
Duk maganar da sukw bata yarda ta buɗe idonta ba. Shi kuma ya lura da hakan.
“Look Abnam karki tauye kan ki, ni ba baƙon tsanani ba ne, ma zan zo na takurawa masu gida ba, idan kina son kwantawa saman gadon kawai ki kwanta”
Ta yi saurin kwantawa a gurin.
“Ni ko gida ƙasa na ke bachi”
Ya ɗaga gira ɗaya like serious. Ya sauko da bedsheet ɗin ƙasa.
“Tashi a shimfiɗa”
“Dan Allah Abdallah ka bar ni nan”
Ta faɗa kamar mai shirin yin kuka. Sai kawai yayi murmushi ya mayardar bedsheet ɗin ɗale saman gadon ya jefo mata matashin kai.
“Gashi nan kar na matso kuma ki ce wani abun zan miki, amman kin san shure-shire baya hana mutuwa ko?”
Sai a lokacin ta buɗe ido ta ɗauki filon ta tare kanta ta yi rufa da gyalenta. Hannu ya kai gurin kan bed ɗin ya kashe wutar ɗakin. Wani tsoro ne ya ƙara baibayeta, kwatakwata ta manta da irin rayuwar da ta yi a gidan Asim, ta fi jin sakewa da shi fiye da Abdool wata ƙila saboda yanayin hallitarsu ba ɗaya ba.
“Ka kunna wutar man...”
Bata ƙarasa rufe baki ba taji mutun a bayanta yasa duka hannayensa yajata jikinsa ya rumgume ta. Sai ya kawo bakinsa dai-dai kunnenta.
“Shiiiiiiii ba wani abun zan miki ba, kawai dai ba zai yayu nakwana da mace ɗaki ɗaya ba kuma ace mu kwana a rabe ba, kawai ina son jinki ne a jikina that's all”
A dole ya gunɗe bakinta ta rumtse ido, tana jin yana ɗan taɓa ta amman ta haƙura har bachi yayi gaba da ita. Washe gari ta rigashi tashi saboda bachin rabi da rabi tayi ko da aka kira assalati idonta huɗu ba ma biyu ba. Tana unƙurin tashi sai shi ma ya tashi saboda tana a ƙirjinsa ne duk wani numfashinta yana ji balle kuma motsinta.
Sai da ya fara shiga bathroom ɗin yayi wanka da alwala sannan ita ma ta shiga ta yi alwalah, tare suka yi sallah sannan ta koma bachi, shi kuma ya buɗe ƙur'ane dake cikin wayarsa ya soma karatu, ba shi ya tashi daga gurin da yake ba sai da aka buga masa waya aka sanar masa an aiko musu da abinci. Wannan karon Ummi bata aiko masa ba saboda ta san za'a aiko masa daga gidan Mai Martaba.
Sai da ya zuba abinci sannan ya shiga ɗakinta. Zaune ya sameta a gurin da ta yi bachin tana kallon ƙofa.
“Acici daga jin motsin ƙuloli har kin tashi”
Dariya ta yi
“Ai ba kai aka kawo ma abincin ba ni aka aiko ma”
“Ai ba kai aka kawo ma abincin ba ni aka aiko ma, yanzu ai kin kina da baki ko?”
Ya kai kayeta yana wani girgiza kai da kashe murya. Ya miƙa mata hannunsa
“Zo nan muje ki wanke bakin ki”
Kamar wata ƙaramar yarinya haka ta miƙa masa hannun ya tasota, da kanshi ya wanke mata bakin bayaɓ sun gama ya ɗauke ta ya kaita dinning.
“Kai a she nauyi ne da ke, na ji kamar jijiyoyina zasu katse”
Ya faɗa yana dariya. Shi yayi feeding ɗinta sannan yayi feeding kansa. Ko da aha biyu ta yi daga ita har shi duk sun shirya cikin fari yadi mai kamar shadda sky blue. Tana gaban madubi tana kwaliya ya ƙaraso kusa da ita ya ɗauki sarƙa ya saka mata sannan ya juyo da ita ya kalleta.
“Kin yu kyau Abnam”
“Faɗa min ma'anar sunan nan”
Bakinsa ya kai dai-dai nata ya haɗe ya tsotse jan bakin da ta sha sannan ya ɗauke bakinsa ya mayar gurin hancinta idonsa kamar mai jin bachi. Ita kan nata a lumshe.
“A-B Abdallah N-A-M Namra = ABNAM”
Murmushi ta yi ta buɗe ido tana jin yadda danshin yawunta ke zaga ko ina na bakinta, shi ma murmushin ya mayar mata yasa yatsunsa ya riƙa lips ɗinta yana murzawa a hankali, cikin hikima ya zura mata manuninsa cikin bakinta ya riƙa wasa da halshenta.
“Zan je na gaishe da su Mai Martaba da Ummi”
Ya faɗa yana kallonta, sannan ya zare hannun daga bakinta ya miƙe tsaye yana saka yatsan cikin bakinsa ya tsotse yawun.
“Allah ya tsare”
Ta faɗa tana tsotsa halshen nata. Sai kawai yasa mata dariya ya zuba hannayensa aljihu ya fice zuciyarsa cike da farincikin.
Bayan fitar da ƴan mintuna su Maryam suka dawo saboda yi mata sallama,ragowar kajin da suka tarar suka cinye suna zolayar Namra da ke ta aikin kuka wai zasu je su barta.
Sai da ya fara biyawa gurin Ummi ya gaisheta sannan ya wuce gurin Mai Martaba, Wannan karon har da Mai Martaba gurin jansa.
“Ango ango”
Wata kunya ce ta kamashi sai ya zauna ya kasa haɗa ido da Mai Martaba. Cikin girmamawa suka gaisa, sannan Mai Martaba ya ce
“Ɓan sani ba ko matarka bata da buƙatar barori shiyasa ban aika mata da su ba, idan ka yi shawara da ita tace maka tana buƙata sai ya faɗa min”
“Godiya muke Mai Martaba Allah ya ƙara lafiya, amman ina tunanin ba sai an kawo mana su ba, saboda ba nan zamu zauna ba, hutun da suka ba ni ma na sati biyu, dole Abuja zan koma da ita, kuma ga karatun da take a sokoto sauran wata bakwai ta ƙare diploma”
“Hakan na da kyau, amman kasa ido kan rayuwa, Babana kana da maƙiya da yawa matarka ma sai ta yi taka tsantsan, ni kaina a yanzu hankalina zai fi kwanciya idan kana abujar fiye da ace kana kusa da ƴan uwanka, saboda za a iya amfanin da su a cutar da kai ko kuma a cutar da matarka, duk da bana jin akwai wanda zai sake wani unƙurin sake aikata abunda Hajiya ta yi Unƙurin aikata maka”
“Wace Hajiya Mai Martaba?”
“Hajiya Karima, (Matar ƙanensa) itace tasa waɗanda ƴan bindigar unƙurin hallaka ka, saboda ita da mijinta suna tunanin idan bana raye babu wanda ya dace ya hau sarautar Katsina sai mijinta, ni kuma ina tutuyar kai ne zaka yi milkin garin Katsina ko da bana raye”
“Mai Martaba ina ka samu wannan labarin?”
“Abdallah kenan, ai ko babu komai na kan aa ido akan ƴaƴa balle kuma kai da mahaifiyarka bata cikin gidan nan, tun daga lokacin da aka maka wannan aika aikar tunani ya bani ba daga waje ba ne, sai dai ko daga nan cikin gida ne, saboda bana tunanin ina da wasu maƙiya bayan na cikin familynmu kuma akan sarautar mu, hakan yasa na zurfafa bincike ta ƙarƙarshin ƙasa sai gashi wanda aka aika gurin yin abun ya same nan a cikin faɗar nan ya faɗa min komai, wannan yasa ya tara su ita da mijin nata da duka family mu na gargasu a lokacin hankalinka yana gurin Amaryarka shiyasa ban taɓa labarta maka wannan ba”
Abdallah yayi murmushi yana auna irin son da Mai Martaba yake masa.
“Babana idan na kalleka na kan jidaɗi nasan ko bana raye kai mutum ne zaka iya riƙe gidan nan kuma ka riƙe ƴan'uwanka, iyakar soyayyar da zan nuna maka na tarbiyantar da kai na baka ilimi kuma na baka duka, yanzu addu'a ce kawai zan binka da ita, Allah ya maka albarka”
“Amin Mar Martaba na gode, Allah ƙara maka imani da lafiya”
“Amin”
Daga haka suka ɗauko wata fira, na familynsu da kuma sarautar Katsina, be bar gidan ba sai la'asar.
***
Bayan sun yi sallah azahar suka yi shirin tafiya aiko Namra ta ƙara tsaresu da kuka tun suna juriyar sai da ta saka Maryam ma ta yi kukan, isowar familynsu Abdool waɗanda suka zo ganin Amarya ne tasa ta tsagaita kukan har suka samu suka tafi. Mota mota suka riƙa zuwa ganinta kasancewar wasu yau zasu tafi wasu kuma gobe har na ɓangaren Ummi wasu ma nan suka yi sallah magariba ana kiran isha'i sannan suka fice.
Ko da Abdool ya dawo ya tarar bata cikin daɗin rai, shi ma kamar jira take yana taɓa fuskarta ta faɗa jikinsa ta fashe masa da kuka, daman yasan za a rina, saboda ya samu labari a faɗar mai Martaba cikin mutanen da suka kawo kara suna cewa tare zasu koma gaba ɗaya.
“Ooo an tafi an bar ƴar Mamarta”
Ya faɗa yana zama saman kujera riƙe da ita.
“Bari na kira miki mamanki”
Ya fiddo wayarsa ya kira Ummi ya miƙa mata ba ko kunya har da faɗa nata wai kuka take masa su Maryam sun tafi su barta. Ummi ta yi dariya
“Aure ai haka ya gada yi haƙuri kinji ƴata, duk abunda yayi miki ki faɗa min”
“Toh Ummi, na gode”
Abdool ya karɓe wayar.
“Mai Martaba ma haka ya faɗa mata wai idan na mata abu ta zo ta faɗa masa, ni idan ta min wa zan faɗawa”
“Ai mata basa laifi kuma su ƴan gata ne shiyasa, kai duk abunda ta yi maka sai ka yi haƙuri ka haɗiye”
Namra ta masa gwalo, shi kuma ya kama kunenta ɗaya ya mirɗe.
“Ummi sai da safe tun da ƴarki kika shigarwa”
“Ato da kai zan shigarwa? Dan baka da kunya ƙato da kai, Allah ya shirya ka”
Ta katse kiran. Shi kuma yasa ɗayan hannunsa ya riƙe kunnen nata ya ƙara mirɗewa.
“Wallahi da zafi”
Ta faɗa cikin shagwaɓa, sai ya saki kunnen yana dariya.
“Gobe ma bakinki ya sake min gwalo”
Dariya tayi ta unƙura zata tashi sai ya jata ta faɗa jikinsa. Hannunsa yasa
Showing 270001 words to 273000 words out of 280121 words
Ganin har rana ta faɗi babu wani sauyi, yasa suka ɗauke shi zuwa asibiti, ana kiran magariba aka bashi gado, likitoci suka shiga bashi taimakon gaggawa, sannan suka tura shi ɗakin hoto. Allura suka masa a nan ya samu bachi.
***
Ƙarfe tara dai-dai aka jera motoci ƙofar gidan da su Namra suke wato masaukinsu. Hajiya Shafa da wasu family na mai Martaba suka shiga ciki suka yi bikon amarya da kuɗi da kuma siyayya.
Ana guda aka fito da Namra tana cikin lifaya fuskarta a lulluɓe, sai ƙamshin turare take.
Barorinta suka buɗe mata mota ta shiga sai aka maida ƙofar motar aka rufe, sai sauran suka shiga sauran motocin, aka akama hanyar gidan Mai Martaba da ita, lokacin da aka shiga da ita faɗar Mai Martaba na shaƙe da mutane da kuma talakawa, sai ta yi gaisuwar ban girma Mai Martaba yayi musu addu'a sannan aka shiga ɗakin ɗayar matarsa tayi musu addu'ah sannan aka yi canji mutane da wato mutanen da suka je bikonta ba su zasu raka ta ɗakinta ba.
Ko da aka isa da ita ɗakinta shaɗaya har ta gota, babu wanda beyi mamakin ganin irin gidan da aka kaita ba duk kuwa da kasancewar dare ne, baka iya banbance shi da rana saboda hasken da gidan ke da shi, yanayin gidan zuwa fenti da kwaliyar gidan duka irin na masarautarsu ne yayi, wani abun burgewa kuma yadda aka ƙawata gidan da komai fari kamar fentin gidan, wato furnitures da aka zubawa Namra komai fari ne har labulayenta, da center carpet, kai har agogon bangonta fari ne, duk inda suka yi masu camera na biye suna ɗauka, tun farkon fitowarta har zuwa gaisuwa da kuma kawo ta gidan.
A ɗakin da yafi ko wannne haɗuwa aka kaita, kasancewar ɗakuna biyar ne a gidan kuma ko wanne sai da aka saka masa kaya, sai ta hau tsakiyar gadon ta zauna, kanta lulluɓe da mayafi.
Wasu daga dangin ango suka mata Allah sa albarka suka fice, sannan wasu daga ƴan'uwanta suka kama hanya, sai aka bar Maryam kawai sai Raihanatu da kuma wata ƴar'uwarsu Husaina.
Bayan kamar minti talatin sai suka soma jin busa da algaita da kirari irinta ta ƴaƴan sarakuna, shi ma mai nasa video yana biye da shi yana ɗauka. Har aka shigo da shi cikin ɗakin, sai ya zauna bakin gado yana ƙamshin turare, fuskarsa ta sha rawani kamar Mahaifinsa. Abokaninsa sai zolayarasa suke shi ko bakinsa har kunne.
Nasiha suka musu akan zamantakewar aure da kuma haƙuri, masu auren cikinsu sai zolayar samarin suke, wasu kuma na zolayar Abdool wai ango sai sha mai. Sai da suka ga shabiyu ta gota sannan suka musu addu'ah da fatan alheri, sannan suka saka Maryam da waɗanda suke tare gaba, har wasu na cewa suna son Maryam a zatonsu budurwa ce.
[8/5, 7:03 PM] Khadeeja Candy♥: *96*
Bayan abokansa sun wuce Abdool ya tashi ya rufe ƙofor falo ya dawo ɗakin fuskarsa da murmushi, rawanin kansa ya fara cirewa ya aje sannan cire babbar rigarsa.
“Amaryata wacce ta wacce amarya tsada”
Ya kai hannu zai yaye gyalenta, sai ta matsa baya ta ƙara jan gyalen ya sauko. Matsawa yayi kusa da ita ya sake miƙa hannun sai ta kauce hannunta mai zanen lalle ta ziro masa. Murmushi yayi yasa hannunsa aljihu ya ɗauko wani ɗan ƙaramin box ya ɗora mata saman hannu, sai ya miƙa hannun ya yaye mata mayafin. Idonta a rufe fuskarta ɗauke da murmushi
“Har da idon sai na siya...?”
“Ai kace wannan amaryar ta fi ko wace Amarya tsada”
Murmushi ya sake yi sai ya cire tsadadden agogon hannunsa ya ɗora mata saman hannu, sai a lokacin ta buɗe ido ta saka su cikin nashi haƙoranta a washe.
“Kin manta ban siye murmushin ba”
“Maganar ma ai baka siya ba an yi maka nasiha ne kawai”
Hannu ya kai ya riƙa gefen fuskarta yana shafa shi da babban yatsansa.
“Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar, lallai na fi ko wane Namiji sa'a a duniyar nan”
“Kana koɗa Namra da yawa, har kana sa tana jin kamar ta fi ko wace mace zama sarauniya”
“Na haɗu da mata da yawa ciki da wajen ƙasar nan amman babu wacce ta sace min zuciya sai Namra, she ko ma ƙaramar sarauniyace ba”
Lumshe ido tayi tana murmushi. Box ɗin ya amsa ya buɗe ya fiddo zobe mai kyau ya kama hannunta ya saka mata.
“I Love you so Much Abnam”
“Na gode sosai”
Matsawa yayi kusa da ita.
“Godiya kawai? Ai hausawa na cewa yaba kyauta tukuici”
Ta rufe fuskarta domin ta gano ma'anar zancensa. Shi ma dariyar ya yi, ya jata ƙirjinsa ya rumgume, a hankali ya sauke numfashi ya ɗora kansa kaman nata.
“Gani komai nake kamar a mafarki, ina tuna lokacin da na fara ganinki irin halin rayuwar da na shiga saboda ke kuma gashu yanzu komai ya zama tarihi, inshallah ni ne mijinki ke kuma matana har Aljanna”
Lafewa ta yi a ƙirjinsa kamar babu wanzuwarta a doron ƙasa, gudun zuciyarsa take sauraren tana auna yada nata zuciyar yake hawa da sauka tare da ta shi.
Sun daɗe a haka sannan ya ɗagota ya mata kiss saman ido.
“Karki min bachi saman jiki kisa na ƙarye”
Tayi dariya tana bugar masa chest.
“Ouuuuch”
Ya faɗa yana kanne mata ido ɗaya. Shi ya fara sauka saman gadon sannan ya miƙa mata hannun, ta riƙa hannunsa ta sauƙo suka shiga bathroom ɗin tare, shi ya fara alwalar sannan ya taimaka mata ita ma tayi suka fito. Sallaya biyu ya shinfiɗa ɗaya a gaba ɗayar kuma tana baya da shi kaɗan.
Mayafinta ya ɗauka ta rufe jikinta kasancewar fafaɗa ne kuma mai kauri. Yana gaba tana biye har suka yi raka'ah biyu, sannan suka sallame. Hannunsa ya ɗaga masa ya riƙa kwaroro musu addu'ah tana amsawa da amin sanna suka shafa, sai ya juyo ya kalleta.
“Hajiya Akwai wata sunnar bayan wannan?”
Ta zare masa ido. Sai ta gurgiza masa kai alamar a'a. Dariya yayi ya tashi ya ɗauko ledojin da gefen gadon ya kawo gabanta ya aje, sannan ya fita daga ɗaga ɗakin gaba ɗaya. Be ɗauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo da plate da cup ta aje a gabanta sannan ya zauna yaja ledar ya buɗe ya fido ƙatuwar kaza ta ɗora saman plate ɗin sai ya mayardar ragowar gajin a gefe ɗaya, ya buɗe madara ya zuba musu a cup ɗaya sannan yasa hannu ɓare kazar ya soma kai mata a baki. Kawar da fuska ta yi tana murmushi.
“Ki taimaki bawan Allah nan ki bar shi ya ciyarda dake a wannan daren da yafi ko wane dare muhimmanci da daraja a gareshi”
“Na hutar da kai, zan iya wannan aikin”
“Ai bana son hutun ne, idan dare ya lula ke da kanki zaki min kukan gajiya ki neman na hutar da ni, amman ba yanzu ba yanzu ai ai ba aiki na ke ba”
Ta ɗan fiddo ido tana kallonsa, sai ya kanne mata ido ɗaya, ba shiri ta buɗe baki tana mamakin yadda yake ƙoƙarin faɗar maganganu kai tsaye. Hakan ya bashi damar saka mata naman a bakin.
Cikin so da ƙauna yayi feeding ɗinta, sai da ya tabbatar ta ƙoshi sannan ya cilasta mata ita ma ta yi feeding ɗinsa a dole ba dan ranta ya so ba, bayan sun ƙare ya kwashe plate ɗin ya buɗe wardrobe ya fiddo kayan bachi kala ɗaya amman na maza da mata, na matan ya miƙa mata shi kuma ya shiga ƙoƙarin zame kayan jikinsa ya canja zuwa na bachin sai ta zaro ido.
“Wai nan zaka canja su?”
“To miye? Naga an zama ɗaya”
“A'a da saura, bari na baka guri ka canja”
Wani shu'umin murmushi yayi har da cije baki.
“No ba sai kin fita ba, bari na baki guri ki canja nima kuma sai na canja a wani ɗakin ko, ƙina da gaskiya ai ba mu zama ɗaya ba amman mun kusa raba gari”
Ya fice yana dariya kamar ba shi ba. Yana fita ya ɗauki kayan bachi da zimmar canjawa sai ta ga ɗan ƙaramin wando sai wata fikicar riga iya cibiya sai kuma babbar mai kamar rariya wacce zata rufe jikin gaba ɗaya. Mayardar kayan ta yi ta aje taja gyalenta ta ƙara rufe jiki.
Shima irin kayan bachinta ne jikinsa bancanci shi baya da wannan ficikar rigar ƙirjinsa a sake yake. Tana kallonsa gabanta yayi mugun faɗuwa, ta razana sosai kamar bata taɓa ganin ƙirjin namiji a waje ba, yana doso inda take ƙanshin turaren da ya saka ya riƙa dukan hancinta, ko da ya ƙaraso kusa da ita ta rufe idonta gan numfashinta har rawa yake.
“Baki canja kayan ba?”
“Da wannan zan kwanta”
Ta faɗa ba tare da ta buɗe idon ba.
“To tashi ki hau gadon ki kwanta”
“Na fi jindaɗi a ƙasan”
“Ƙasa zamu kwanta kenan”
“A'a kai ka kwanta saman gadon, ni na kwanta a ƙasa”
Duk maganar da sukw bata yarda ta buɗe idonta ba. Shi kuma ya lura da hakan.
“Look Abnam karki tauye kan ki, ni ba baƙon tsanani ba ne, ma zan zo na takurawa masu gida ba, idan kina son kwantawa saman gadon kawai ki kwanta”
Ta yi saurin kwantawa a gurin.
“Ni ko gida ƙasa na ke bachi”
Ya ɗaga gira ɗaya like serious. Ya sauko da bedsheet ɗin ƙasa.
“Tashi a shimfiɗa”
“Dan Allah Abdallah ka bar ni nan”
Ta faɗa kamar mai shirin yin kuka. Sai kawai yayi murmushi ya mayardar bedsheet ɗin ɗale saman gadon ya jefo mata matashin kai.
“Gashi nan kar na matso kuma ki ce wani abun zan miki, amman kin san shure-shire baya hana mutuwa ko?”
Sai a lokacin ta buɗe ido ta ɗauki filon ta tare kanta ta yi rufa da gyalenta. Hannu ya kai gurin kan bed ɗin ya kashe wutar ɗakin. Wani tsoro ne ya ƙara baibayeta, kwatakwata ta manta da irin rayuwar da ta yi a gidan Asim, ta fi jin sakewa da shi fiye da Abdool wata ƙila saboda yanayin hallitarsu ba ɗaya ba.
“Ka kunna wutar man...”
Bata ƙarasa rufe baki ba taji mutun a bayanta yasa duka hannayensa yajata jikinsa ya rumgume ta. Sai ya kawo bakinsa dai-dai kunnenta.
“Shiiiiiiii ba wani abun zan miki ba, kawai dai ba zai yayu nakwana da mace ɗaki ɗaya ba kuma ace mu kwana a rabe ba, kawai ina son jinki ne a jikina that's all”
A dole ya gunɗe bakinta ta rumtse ido, tana jin yana ɗan taɓa ta amman ta haƙura har bachi yayi gaba da ita. Washe gari ta rigashi tashi saboda bachin rabi da rabi tayi ko da aka kira assalati idonta huɗu ba ma biyu ba. Tana unƙurin tashi sai shi ma ya tashi saboda tana a ƙirjinsa ne duk wani numfashinta yana ji balle kuma motsinta.
Sai da ya fara shiga bathroom ɗin yayi wanka da alwala sannan ita ma ta shiga ta yi alwalah, tare suka yi sallah sannan ta koma bachi, shi kuma ya buɗe ƙur'ane dake cikin wayarsa ya soma karatu, ba shi ya tashi daga gurin da yake ba sai da aka buga masa waya aka sanar masa an aiko musu da abinci. Wannan karon Ummi bata aiko masa ba saboda ta san za'a aiko masa daga gidan Mai Martaba.
Sai da ya zuba abinci sannan ya shiga ɗakinta. Zaune ya sameta a gurin da ta yi bachin tana kallon ƙofa.
“Acici daga jin motsin ƙuloli har kin tashi”
Dariya ta yi
“Ai ba kai aka kawo ma abincin ba ni aka aiko ma”
“Ai ba kai aka kawo ma abincin ba ni aka aiko ma, yanzu ai kin kina da baki ko?”
Ya kai kayeta yana wani girgiza kai da kashe murya. Ya miƙa mata hannunsa
“Zo nan muje ki wanke bakin ki”
Kamar wata ƙaramar yarinya haka ta miƙa masa hannun ya tasota, da kanshi ya wanke mata bakin bayaɓ sun gama ya ɗauke ta ya kaita dinning.
“Kai a she nauyi ne da ke, na ji kamar jijiyoyina zasu katse”
Ya faɗa yana dariya. Shi yayi feeding ɗinta sannan yayi feeding kansa. Ko da aha biyu ta yi daga ita har shi duk sun shirya cikin fari yadi mai kamar shadda sky blue. Tana gaban madubi tana kwaliya ya ƙaraso kusa da ita ya ɗauki sarƙa ya saka mata sannan ya juyo da ita ya kalleta.
“Kin yu kyau Abnam”
“Faɗa min ma'anar sunan nan”
Bakinsa ya kai dai-dai nata ya haɗe ya tsotse jan bakin da ta sha sannan ya ɗauke bakinsa ya mayar gurin hancinta idonsa kamar mai jin bachi. Ita kan nata a lumshe.
“A-B Abdallah N-A-M Namra = ABNAM”
Murmushi ta yi ta buɗe ido tana jin yadda danshin yawunta ke zaga ko ina na bakinta, shi ma murmushin ya mayar mata yasa yatsunsa ya riƙa lips ɗinta yana murzawa a hankali, cikin hikima ya zura mata manuninsa cikin bakinta ya riƙa wasa da halshenta.
“Zan je na gaishe da su Mai Martaba da Ummi”
Ya faɗa yana kallonta, sannan ya zare hannun daga bakinta ya miƙe tsaye yana saka yatsan cikin bakinsa ya tsotse yawun.
“Allah ya tsare”
Ta faɗa tana tsotsa halshen nata. Sai kawai yasa mata dariya ya zuba hannayensa aljihu ya fice zuciyarsa cike da farincikin.
Bayan fitar da ƴan mintuna su Maryam suka dawo saboda yi mata sallama,ragowar kajin da suka tarar suka cinye suna zolayar Namra da ke ta aikin kuka wai zasu je su barta.
Sai da ya fara biyawa gurin Ummi ya gaisheta sannan ya wuce gurin Mai Martaba, Wannan karon har da Mai Martaba gurin jansa.
“Ango ango”
Wata kunya ce ta kamashi sai ya zauna ya kasa haɗa ido da Mai Martaba. Cikin girmamawa suka gaisa, sannan Mai Martaba ya ce
“Ɓan sani ba ko matarka bata da buƙatar barori shiyasa ban aika mata da su ba, idan ka yi shawara da ita tace maka tana buƙata sai ya faɗa min”
“Godiya muke Mai Martaba Allah ya ƙara lafiya, amman ina tunanin ba sai an kawo mana su ba, saboda ba nan zamu zauna ba, hutun da suka ba ni ma na sati biyu, dole Abuja zan koma da ita, kuma ga karatun da take a sokoto sauran wata bakwai ta ƙare diploma”
“Hakan na da kyau, amman kasa ido kan rayuwa, Babana kana da maƙiya da yawa matarka ma sai ta yi taka tsantsan, ni kaina a yanzu hankalina zai fi kwanciya idan kana abujar fiye da ace kana kusa da ƴan uwanka, saboda za a iya amfanin da su a cutar da kai ko kuma a cutar da matarka, duk da bana jin akwai wanda zai sake wani unƙurin sake aikata abunda Hajiya ta yi Unƙurin aikata maka”
“Wace Hajiya Mai Martaba?”
“Hajiya Karima, (Matar ƙanensa) itace tasa waɗanda ƴan bindigar unƙurin hallaka ka, saboda ita da mijinta suna tunanin idan bana raye babu wanda ya dace ya hau sarautar Katsina sai mijinta, ni kuma ina tutuyar kai ne zaka yi milkin garin Katsina ko da bana raye”
“Mai Martaba ina ka samu wannan labarin?”
“Abdallah kenan, ai ko babu komai na kan aa ido akan ƴaƴa balle kuma kai da mahaifiyarka bata cikin gidan nan, tun daga lokacin da aka maka wannan aika aikar tunani ya bani ba daga waje ba ne, sai dai ko daga nan cikin gida ne, saboda bana tunanin ina da wasu maƙiya bayan na cikin familynmu kuma akan sarautar mu, hakan yasa na zurfafa bincike ta ƙarƙarshin ƙasa sai gashi wanda aka aika gurin yin abun ya same nan a cikin faɗar nan ya faɗa min komai, wannan yasa ya tara su ita da mijin nata da duka family mu na gargasu a lokacin hankalinka yana gurin Amaryarka shiyasa ban taɓa labarta maka wannan ba”
Abdallah yayi murmushi yana auna irin son da Mai Martaba yake masa.
“Babana idan na kalleka na kan jidaɗi nasan ko bana raye kai mutum ne zaka iya riƙe gidan nan kuma ka riƙe ƴan'uwanka, iyakar soyayyar da zan nuna maka na tarbiyantar da kai na baka ilimi kuma na baka duka, yanzu addu'a ce kawai zan binka da ita, Allah ya maka albarka”
“Amin Mar Martaba na gode, Allah ƙara maka imani da lafiya”
“Amin”
Daga haka suka ɗauko wata fira, na familynsu da kuma sarautar Katsina, be bar gidan ba sai la'asar.
***
Bayan sun yi sallah azahar suka yi shirin tafiya aiko Namra ta ƙara tsaresu da kuka tun suna juriyar sai da ta saka Maryam ma ta yi kukan, isowar familynsu Abdool waɗanda suka zo ganin Amarya ne tasa ta tsagaita kukan har suka samu suka tafi. Mota mota suka riƙa zuwa ganinta kasancewar wasu yau zasu tafi wasu kuma gobe har na ɓangaren Ummi wasu ma nan suka yi sallah magariba ana kiran isha'i sannan suka fice.
Ko da Abdool ya dawo ya tarar bata cikin daɗin rai, shi ma kamar jira take yana taɓa fuskarta ta faɗa jikinsa ta fashe masa da kuka, daman yasan za a rina, saboda ya samu labari a faɗar mai Martaba cikin mutanen da suka kawo kara suna cewa tare zasu koma gaba ɗaya.
“Ooo an tafi an bar ƴar Mamarta”
Ya faɗa yana zama saman kujera riƙe da ita.
“Bari na kira miki mamanki”
Ya fiddo wayarsa ya kira Ummi ya miƙa mata ba ko kunya har da faɗa nata wai kuka take masa su Maryam sun tafi su barta. Ummi ta yi dariya
“Aure ai haka ya gada yi haƙuri kinji ƴata, duk abunda yayi miki ki faɗa min”
“Toh Ummi, na gode”
Abdool ya karɓe wayar.
“Mai Martaba ma haka ya faɗa mata wai idan na mata abu ta zo ta faɗa masa, ni idan ta min wa zan faɗawa”
“Ai mata basa laifi kuma su ƴan gata ne shiyasa, kai duk abunda ta yi maka sai ka yi haƙuri ka haɗiye”
Namra ta masa gwalo, shi kuma ya kama kunenta ɗaya ya mirɗe.
“Ummi sai da safe tun da ƴarki kika shigarwa”
“Ato da kai zan shigarwa? Dan baka da kunya ƙato da kai, Allah ya shirya ka”
Ta katse kiran. Shi kuma yasa ɗayan hannunsa ya riƙe kunnen nata ya ƙara mirɗewa.
“Wallahi da zafi”
Ta faɗa cikin shagwaɓa, sai ya saki kunnen yana dariya.
“Gobe ma bakinki ya sake min gwalo”
Dariya tayi ta unƙura zata tashi sai ya jata ta faɗa jikinsa. Hannunsa yasa
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91 Chapter 92Chapter 93Chapter 94